Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Haruna." Yace."Babu damuwa, nuna min igiyar hannunaka irin wannan." Hamza da sauri ya mika masa igiyar hannunsa! Ya dinga bin hannun da kallo yana mamakin ashe zarginsa suke yi gashi kuma bashi ne ba tunda gashi yana daure da igiyarsa a hannu! Shatima yace." Wannan igiyar ta nuna mana cewa babu sa hannun d'ayanku a cikin wannan al'amari saboda haka zaku iya tafiya." Dukkaninsu sukayi godiya kafin su fita daya bayan d'aya.


Muddibo murmushi samun nasara yayi ya mike da fadin"Ni zan dan fita amma ba zan dade ba zan dawo." fatan alkairi sukayi masa, hanya ya kama ya fita cikin nishadi! Shatima yace."Kasan Allah ban yarda da Muddibo ba." Kallonsa yayi yace."Shatima me yasa kake da zargi ne?" Shatima murmushi yayi yace."Ba zargi bane halinsa na sani Muddibo baya kaunarka ko kadan duk wannan abin da yake yanayi ne kawai amma zuciyarsa babu alkairi." Ajiyar zuciya ya sauke yace."To idan yana nufi na da sharri Allah ya mayar dashi kansa, babban burina shine nasan wannan igiyar ta waye a cikin bayin dake cikin masarautar nan idan aka gane me wannan igiyar ina ganin 'karshen komai yazo dole ya fadi gaskiya.

Shatima yace."Binkice za'a tsaurara insha Allahu za'a gane mai ita." Yana kokarin magana, sallamarta ta katseshi, gabadaya idanu suka zubo min, a sanyaye na karasa tare da dan risinawa, gaishe su nayi, Shatima ne kawai ya amsa amma shi bina kawai yake da kallo, nace"Ranka ya dade me zan hada maka na break."
"Duk abinda kikayi ra'ayi." Ba tare da nace komai ba nabi hanyar kicin, akan idonsa ta shige ya sauke ajiyar zuciya yana girgiza kansa, Shatima yace."Sosai yarinyar nan take bani tausayi wallahi tana kokari akanka mutuka."

Yace."Nima nasan da haka Shatima yarinyar nan jajirtacciya ce mara tsoro naji dadi mutuka da Allah ya had'ani da ita wallahi daba dan tsayuwarta akaina ba da tuni na zama tarihi! duk wannan abubuwan dake faruwa suna faruwa ne a bisa kaddara shiyasa gabadaya naki bayar da goyan baya a station a d'aureta saboda nasan itama ba tasan yanda al'amarin ya faru ba, tunda tsaf ta kammala komai a lokacin na umarceta data gyara min daki, wannan damar aka samu aka shigo akayi abinda za'ayi aka fita tabbas Sumayya da tasan akwai abin cutarwa a cikin abinda ta dafa ba zata yarda 'kwaro yaci ba ballantana mutum mai rai." Shatima yace."Gaskiya nima na yarda ita duk rintsi ba zata taba yarda a hada baki da ita a cutar da wani ba, naji dadi sosai daka kareta a station din.'' ajiyar Zuciya ya sauke yace.''Yana da kyau muje mu samu jana'izar wad'annan bayin Allah." Shatima yace."Hakan nada kyau." Mikewa sukayi a tare suka fita, kai tsaye inda za'a sallaci gawarwakin suka nufa.

Koda na gama had'a masa abin karyawar kasa barin sashen nayi sabida ina jin tsoro na fita wani ya shigo, guri na nema na zauna ina sa'ke-sa'ke! shikkenan Haruna tashi ta'kare a duniya ya bar wannan duniyar mai cike da rud'ani, hawaye ne suka zubo min nasa hannu na goge ina girgiza kaina, hakika naso nayi rayuwar aure da Haruna saboda shine yake min sahihin so wanda babu algus a cikinsa, tabbas zanfi samun cikakkiyar nutsuwar da nake bukata mutukar na aureshi, ashe duk hasashe nakeyi rayuwar Haruna takaitacciya ce a duniya ya tafi ya barni da kaunarsa a cikin raina...........Hannuwana na daga sama na soma yi masa addua samun rahamar ubangiji ina kuka nace"Ya Allah ka tona asirin wanda yayi sanadiyar mutuwar bayin ka, ya Allah dukkanin wanda yake da hannu a cikin wannan al'amarin Allah ka nuna masa iyakarsa, Allah ka jikan Haruna da dukkanin musulmin da suka gabata bayansa........Adduar na shafa a fuskata, nayi saurin kallon bakin kofa, shine a tsaye yana kallona, ashe ya shigo lokacin hankalina ya dauke gurin addua, Mi'kewa tsaye nayi, ina kallonsa Acp ne ya shigo bakinsa dauke da sallama, sunkuyar da kaina kasa nayi na d'an matsa gefe guda, A nutse suka karaso cikin falon suka samu kujera suka zauna, "Barka da zuwa." nafada ina kallon Acp. kallon mamaki yake min, kafin ya amsa da "barka ka dai." dauke kaina nayi daga gurinsa nace. "Ranka ya dade na kammala komai." A nutse yace." Ki zauna Acp yana so yayi magana dake." a nutse na zauna kasan gurin......Acp ya jima yana kallona kafin yace."Ya sunanki! Nace"Sumayya Lawi." Rubuwata yayi a jikin wata 'yar takarda, Yace."Sumayya jiya da zaki shigo sashen nan suwa kika samu ina nufin mutane nawa kika gani."?

Shuru nayi ina nazari. Nace."Haruna ne da Hamza sai masu gadi da direbobi." Yace."Kin tabbata dukkaninsu kin gansu da idonki."? Nace"Eh na gansu." rubuce rubuce yayi jikin takardar, Ya cigaba da cewa! "bayan kin shiga falon baki samu kowa a gurin ba."? Nace" Eh gaskiya banga kowa ba dan har na gama aikina na fito wani be shigo ba."

Acp ya kalleshi cikin nutsuwa yace."Ranka ya dade jiya bayan fitar ka shin ka rufe kofar falo ko kuma a bude ka barta."? Jim! yayi kafin yace."Acp wallahi ba zan iya tunawa ba saboda a gaggauce na fita so na manta na rufe ko kuma ban rufe ba."

Acp yace."Okey daka fito wa ka samu a harabar gurin."? Yace."Ba zan iya tunawa ba tunda na fada maka a gaggauce na fito kuma ban tsaya amsawa gaisuwarsu ba kai tsaye mota na shiga direba ya jani ya fita dani."

Acp ya kalleni a nutse yace."Sumayya bayan kin hau sama domin gyare-gyare shin ko yaya bakiji motsin da zai nuna miki an shigo ba."

Murmushin takaici nayi nace."Banji motsin komai ba Yallabai ka duba nisan benan da kuma falon koda an shigo ba zanji motsin komai ba saboda akwai tazara mai tsayi."

Yace."Hakane shin da kika sauko ba kiga wata alama ba."? "Eh gaskiya banga wata alama ba dan yanda na bar komai haka na same shi, sai dai jiya da daddare mun tsinci igiyar hannu a kicin d'in." Yace."Eh Yallabai ya nuna min kuma kafin na shigo sai da nayi binkice a kanta." Da sauri nace"Ina fata an samu me ita."? girgiza kansa tayi yace."Ba'a samu me ita ba tunda duk wa'inda muke zargi suna da ita."


Jikina ne yayi sanyi na dinga kallon igiyar hannunsa ina tunani a kanta, Acp ya sauke ajiyar zuciya yana kallonsa yace."Ranka ya dade duk wani binkice da ya kamata ace munyi min gabatar dashi kuma mun rubuta komai insha Allahu zamu cigaba da binkice muna bibiyar lamarin a nutse da izinin Allah sai mun gano masu shirya wannan mugun abu, amma muna bukatar hadin kanka dake Sumayya keda kike kula da abincinsa da abinsha a duk lokacin da kika ga wani abu ko yaya ne to ki kira waya ki sanar damu halin da ake ciki insha Allahu mun shigo cikin al'amarin sai munga karshensa........Ranka ya dade shawara anan shine yana da kyau gabad'aya ka sauya hadiman ka tun daga kan masu gadi har i zuwa kan direbobi ga sanja sabbi tanan zamu gano bakin zare, sannan a cikin ma'aikatanmu zamu kawo mutum biyu domin su sa ido sosai akanka da dukkanin abinda ya shafeka ina ganin idan akayi haka za'a samu sassauci ta wani b'angaran."

Ajiyar zuciya ya sauke yana kallon Acp din yace."Acp dukkanin abinda ka fad'a haka za'ayi insha Allahu zan duba shawararka yau da daddare zan zauna da mahaifiyata domin mu tattauna batun nagode sosai da kokarin ku akan wannan al'amarin ina rokon Allah ya saka muku da Alkairi."

Acp ya bashi hannu yana kokarin mikewa yace."Haba abokina ai babu komai ka daina godiya dan Allah kafi karfin ayi maka komai kuma kada ka manta binkice da kare rayukan al'umma a kanmu yake kaga kuwa dole ne mu tsaya maka a cikin al'amuranka har sai munga komai ya daidaita." Murmushi yayi ya mika masa hannu sukayi musabaha, hannunsu a hade suka fita daga falon.

Bayan fitar su na jima a zaune a falon ina nazari mikewa nayi da sauri na kama hanyar fita, sai nayi karo dashi, fuskarsa kawai na kalla naji jikina ya mutu, kana ganinsa da yanayinsa zaka gane yana cikin tsananin damuwa kawai dan dai yana da kokari ne, tausayinsa ne ya rufe na koma falon ina kallo ya zauna kasan kafet, a sanyaye nace"Na kawo maka kayan karin."?Girgiza kansa yayi yace."Sumayya bana tsammanin zan iya cin wani abu yanzu cikina ya cunkushe da damuwa."

A sanyaye nace"Ka barwa Allah komai da sannu zai kawo maka sauki kada kayi wa kanka horon yunwa." Girgiza kansa yayi bece min komai ba ya cigaba da kallon guri guda.

Nace"Na kawo maka ko."? kansa ya daga alamun "Eh." da sauri na dauko tire din dana shirya kalacin......a gabansa na ajiye, yace."Hada min tea." da sauri na had'a masa, hannu yasa ya dauka yana kur'ba yana kallona, soyayyan dankali da kwai na zuba mishi a plate nace"Ka dinga hadawa da dankalin." Shuru yayi min ya cigaba da kurbar tea din ba tare da ya dauki dankalin ba......a sanyaye na mike da fadin."Ni zan tafi." Ban jira ya amsa ba na kama hanyar fita...."Sumayya." sunana ya kira na juyo ina kallonsa.
"Kizo ki karya kema." girgiza kaina nayi nace"Nace"Na karya a gurinmu." Bata rai yayi yace."Wannan uban dankalin da kika zuba waye zai ci miki." ? kai tsaye nace"Kaine zaka cinye abinka." Girgiza kansa yayi yace."Idan kina so naci to zo ki zauna ki taya ni ci bana so ki tafi ki barni cikin kad'aici.'' Kallan mamaki nayi masa, ya dage min gira yana lumshe idonsa gabadaya ji nayi gwiwata tayi sanyi a duk lokacin da zaiyi min irin wannan kallon nakan shiga cikin wani irin yanayi.

"My love." a firgice! na kalleshi, yayi murmushi da fadin"Meye na furgita dan na kira ki da wannan suna. Nace"Dan Allah ka daina kirana da suna nan."
"Saboda me."? nace" Kawai dai bai dace ba." Yar dariya yayi yace."Sumayya kenan to zan daina amma ba yanzu ba." Nace"To nagode." Juyawa nayi zan bar gurin, Yace."Kada ki fita." Dafe goshina nayi cikin yanayi na damuwa na juyo ina kallonsa.
Yace.'"Na dame ki ko."? shuru nayi, "Ki dawo ki cinye dankalin ki." Saboda ya barni na tafi yasa na koma na zauna, kusa dashi.

Plate din dankalin ya turo min yace."Oya had'a tea mai kauri ki hada da dankalin ba zan barki ki fita ba sai na tabbatar da cewa cikin ki ya cika......ba tare da nayi masa musu ba na tsiyaya tea din daidai misali, ido ya tsira min da cup din tea a hannunsa ya bar kur'ba kawai yana kallona.

Nace"Wannan kallon da kake min yayi yawa za kasa na k'ware dan Allah ka dauke idonka." Ba tare da yace uffan ba ya dauke kansa cigaba yayi da kur'bar tea dinsa, a nutse nake kur'bar tea din ina had'awa da dankalin, ina kallonsa yana kallona ta gefan ido cikin zuciyata nace"Wannan idan maye ne ya kama mutum sai ya kasheshi na rasa abinda yake kallo a jikina.
cikin damuwa na ajiye cup din tea d'in! kawai naga ya ajiye nasa ya dauki nawa, daidai saitin bakina yasa a bakinsa ya sumbuta kafin ya fara kur'ba! ya wani tsatstsare ni da ido, jikina ne yayi sanyi na dinga jin shigar bakon yanayi sunkuyar da kaina kasa nayi kwata-kwata bana san kallonsa saboda yanayin yanda yake sarrafa idonsa a kaina yasa naji bani da kuzari....Cup din tea din ya ajiye a gabana yana nuna min inda bakinsa yake wai na dauka nasha!! kawai na tsinci kaina da bin umarninsa, ina kokarin daidaita bakina a inda yasa nasa Lawisa ta shigo falon, cikin shigar alfarma 'kamshin turaranta duk ya game gurin, 'Kwarewa nayi nayi saurin ajiye cup din ina kallonta a yayin da take kokarin karasowa gurin da muke, sunkuyar da kaina nayi naganin yanda taci kunu! mikewa nayi da sauri, yace."Sumayya koma ki k'arasa.''! girgiza kaina nayi nace."Ranka ya dade na'koshi.'' ido ya tsira min yana so ya tabbatar da maganarsa, Gurin na bari ina fargabar kallon da Lawisa takeyi min..

Kallonta yayi sama da kasa babu laifi tayi kuma za'a huta da ita Lawisa nada kyawun jiki gata fara tas jikinta dam sai dai bata da tsayi sosai, kusa dashi ya nuna mata wai ta zauna, zama tayi tana wani cin magani tace......




*Na kudi ne!*
Kada ki karanta min littafi sai kin biya, keda kika futa da littafin keda Allah idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip gruop#600...normal#300 account... 0543282124....Binta umar gtnank....idan kati zaki turo#400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:27 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
84
"Wai dan Allah me yake tsakanin ka da wannan yarinyar ne? a gaskiya kusancin da nake gani a tsakaninku yana d'aga min hankali wallahi! nasan dai kafi karfin kace kana sonta tunda a karkshinka take to me zai sanya ta dinga zama kusa da kai tana cin abinci da kai."? Cikin yanayi na bacin rai ta karashe maganar,

Shuru yayi yana kallon guri guda bai ce mata uffan ba, Lawisa ta sake sha'ka! murya na rawa tace" Da kaifa nake magana kana jina kayi shuru shin kasan irin son da nake maka kuwa."?

A nutse ya dago kansa yana kallonta, yace." Babu abinda yake tsakanina da ita sai mutunci kada ki manta wannan yarinya itace amintaciyyar baiwa ta yanda na amince da ita ko ke ban amince dake ba saboda haka ki daina damuwa idan kin ganta a kusa dani idan da yiwuwar na aureta zan aureta babu ruwana da 'kas'kancinta."


Lawisa wasu zafafan hawaye suka shigo zubo mata a kumatu tace"Yanzu kai dan Allah sai ka auri yarinyar nan shin me ka gani a tare da ita wanda ya burgeka dan Allah kada kayi min haka kada ka had'ani kishi da wannan ma'kaskanciyar idan aure kake so ka auri 'yar mulki irina amma ni nafi karfin nayi kishi da wannan yarinyar."


Gyara zamansa yayi yana kallonta fuskarsa a 'bace! yace." Ni baki isa ki tsara min ga yanda zanyi ba, Sumayya baiwa tace kuma ta cancanci na aureta na 'yantata daga baiwa ta dawo mai 'yanci! Sumayya ta nayi min abinda ke bakiyi min ba, sannan naji kina fadin cewa mai na gani a tartare da ita nagarta da kyawawan halaye nagani har yasa nayi sha'awar auranta nasan kin san hakan ba haramun bane ko? zan aureku ku biyu a rana daya daga yau kisa a ranki mijinki mijin mace hudu ne bayan na aureku zan iya kara biyu sannan inyi kwarkwara idan ina da ra'ayi saboda haka kada ki kara zama a kusa dani kice zaki tsara min yanda zan tafi da rayuwata."


Lawisa hawaye kawai take sharewa tana kallonsa tsabar bakin ciki da takaici ya hanata cewa komai, da shashshekar kukanta ya dameshi mikewa yayi ya haye sama ya barta zaune a gurin tana kuka na rashin madafa.



"Lallai wannan yaro bashi da kirki wato ta inda ya 'bullo kenan? ya rasa yarinyar da zai aura sai baiwa makaskanciya wacce take karkashinki da ita zai hada ki kishi lallai kuwa zanje na samu mahaifiyarsa akan maganar." Hajiya Karima mahaifiyar Lawisa ce ke wannan bambamin.


Lawisa na kuka tace."Wallahi Hajiya ni kaina nayi mamakin al'amarin kuma abin ya tsoratar dani mutuka dan banyi tsammanin zai iya auranta ba saboda nasan kin san yanda yarinyar take da muni gata 'baka wai har cewa yake zai aureta saboda kyawawan halayenta sannan harda cewa tafi ni a gurinsa sau dubu."

Hajiya karima na girgiza kafa tace"Ki daina kuka kina damunki insha Allah idan 'kura ta lafa zan samu mahaifiyarsa da maganar dole ya za'ba ke ko baiwa dan kinfi karfin kiyi kishi da baiwar gidanku."




Kai tsaye dana fita daga bangaran Yarima gurinsu Haruna na nufa, nan na samu gurun da jama'a sun kewaye mahafiyarsa suna tausarta, ganin yanda idanun jamaa yayi caaa a kaina yasa nayi niyyar juyawa, wata mata dake bakin kofa tace"Aa sumayya ya zaki koma kuma ki shiga mana."

Simi-simi na shige gabana na faduwa na zauna a gabanta ina gaisheta, da kyar ta amsa min tana harara jamaar dake kusa da ita suna taya ta, shuru nayi na minti uku kafin nace"Ubangiji Allah ya jikan Haruna da dukkanin musulmin daya rigamu gidan gaskiya." Tsiraru ne suka amsa adduata, na cigaba da cewa"Lami akwai wata igiya da take daure a hannun Haruna dan Allah ita nake so ki bani domin za'ayi binkice akai."

Hannu ta daga min tace."Sumayya wane binkice kuma bayan bukatarki ta biya kin kasheshi domin ki samu nasarar auran Yarima to bari kiji duk halin da kike ciki keda iyayenki mun sani Yarima ya bukaci ya aureki a lokacin da baikon Haruna akanki koda Maimartaba ya samu labari yace ba za'ayi haka ba dole ki auri Haruna Shi Yarima ya hakura, da kuka ga haka sai kuka shirya kashe Haruna saboda biyan bukatarku ko ba haka bane."?

Ina kuka nace"Hakane maganarki amma inaso ki sani wallahi bamu muka kashe Haruna ba kwanansa ne ya 'kare kuma ni ko kusa ko alama bana kaunar na auri Yarima saboda wani dalili nawa, wallahi nafi bukatar na auri Haruna domin shi nake so muna san junanmu aka shiga tsakaninmu dan Allah kada ki sake wannan maganar Bamu kashe Haruna ba."

Tsaki taja tace"Ni dan Allah ki tashi ki bani guri bani da wata magana dake a yanzu." Hannunta na rike ina kuka nace"dan Allah kiyi hakuri ki dauko min igiyar nan wallahi binkice za'ayi a kanta." Wacce take kusa da ita tace"Ke munafuka tashi ki futa ko kuma yanzu muyi miki duka wallahi wane irin binkice za'ayi bayan mun san gaskiyar lamari zaki zo ki nayi mana kukan munafurci."


Ta kusa da ita tace"Lami ki daina kuka haka dan Allah ku dauko mata igiyar akwai alamun gaskiya a maganar yarinyar nan watakila zarginta kawai muke saboda haka ki dauko mata igiyar."


Shuru lami tayi tana nazari kafin tace."Uwani wallahi ba zance miki ga inda igiyar nan take ba lokacin dai da'aka shigo da gawarsa na ganta a daure a hannunsa, sai dai ku duba gurin da'a kayi masa wanka ko zaku ganta."

Uwani tace"to bari na duba." Mikewa nayi da sauri nabi bayanta, sako da loko na gurin muka duba tsaf ba muga igiyar ba jikina yayi sanyi muka fito daga gurin, Uwani tace"Muje Shara mu duba mugani ko anshare.......Muka zazzage sharar a gurin duka muka tona babu igiya, Uwani tace"Kinga ni babu alamun igiyar nan a gurin, amma bari a kira wa'inda sukayi masa wankan."

Uwani da sauri ta fita ni kuma na jingina a jikin bango(garu) ina tunanin al'amarin, tare suka shigo su uku ita ta hud'u, had'a ido mukayi da Hamza na hango firgici a tare dashi, Uwani tace"Hamza kune kuka wanke gawar Haruna to binkice ne yazo ana bukatar igiyar hannunsa mahaifiyarsa ta tabbatar da cewa lokacin da'aka shigo da gawar akwai igiyar a hannunsa."


Labaran yace."Tabbas kuwa ni ne na kwance igiyar daga hannunsa, na ajiye a gurin." Salisu yace."Kwarai kuwa nima na ganta da idona wallahi." Hamza cikin dauriya yace."Nima naso naga lokacin da kake kwance ta sai dai yanayin tashin hankalin da nake ciki yasa shaf na manta ban dauketa ba." Nace"To gashi dik mun duba guraran da kuka zauna ba muganta ba." Cikin firgici Hamza yace." Ku muje mu sake dubawa." Dukkaninmu muka bi bayansa, ya dinga lalube a gurin baiga komai ba, yana sharce gumi ya dago muka hada ido sai yayi saurin dauke kansa yace."Amma al'amarin nan akwai ban mamaki gashi duk an duba ba'a ganta ba." shuru babu wanda yayi magana yace."Ku muje mu duba shara." Uwani tace"Wace shara kuma bayan duka mun duba." A sanyaye ya tsaya yana kallonmu, ajiyar zuciya na sauke ina wani tunani, anya kuwa babu sa hannun Hamza a gurin kashe abokinsa? nace"Uwani tunda ba'a ganta ba ni zan tafi Allah ubangiji ya tona asirin munafukai." Uwani ta amsa da ameeen ya Allah." gurin na bari na barsu suna sake tattauna maganar.

A ranar yini nayi cikin zullumi da tunanin yanayin furgicin da naga Hamza ya shiga na dinga tunanin anya kuwa be san wani abu daya shafi 'batan igiyar Hannun Haruna ba? tsabar damuwa da tunani ya janyo min ciwon kai mai tsanani idanuna sukayi jawur tamkar wacce taci kuka ta koshi nan kuwa tsabar fargaba da damuwa ce, Tambaya ganina haka yasa ta shiga damuwa ta dinga rarrashina da bani kulawa, ganin yanda duk ta tashi hankalinta yasa na sassautawa kaina tunani kawai na mika al'amarin ga Allah na cigaba da addua akan Allah yayi gaggawar tona asirin wa'ina suke shirya wannan mugun abun.



*Bayan sati hudu*
Al'amura sunyi sauk'i masarautar ta samu nutsuwa kowa ya kwantar da hankalinsa ya koma harkokinsa harshi Magajin sarkin ya koma aiki dama tunda gwamnati tayi dogon binkice ta gane daga inda badak'alar ke fitowa yasa ta bada umarnin bude asibitin tare da kira ga Jamaa cewa su cigaba da shige da fice a asibitin babu abinda zai sake faruwa da yardar Allah." Wannan kira da gwamnati tayi ga al'umma yasa kowa ya kwantar da hankalinsa, Asibitin *Zinariya* ya ci gaba da gudanar da aiki kan tsari da sanin ya kamata.........Al'amarin yayi masifar 'bata rayukan wa'inda suke adawa da samuwar asibitin dukkaninsu sai suka yanke shawarar karshe akan asibitin amma ba zasu aikata aikinsu ba sai ankwana biyu tukkuna sai kowa ya sakin jikinsa sai su kuma su gudanar da abinda suka shirya,

'Bangaran Yarima ya samu sabbin hadimai kamar yanda Acp ya bukata, kuma kamar yanda yayi alkawarin kawo jami'an tsaro guda biyu ya cika al'kawarinsa ya kawo jami'ai gudu uku tare da amincewar gwamnati, sosai gurin yayi lafiya kowa yana gudanar da aikinsa yanda ya kamata, jami'an tsaron sunsa ido sosai da sosai dan ba kowa suke bari ya shiga sashen kai tsaye ba sai sunyi binkice a kansa tukkuna suke bari ya shiga, mutukar kuwa Yarima baya nan to basa barin kowa ya shiga har sai ya dawo nima ina gama ayyukana nake fitowa.


'Karfe hudu da rabi na ranar talata na fito daga gurin karatu kai tsaye sashen Yarima na nufa domin gudanar da aikina, tun daga nesa na hangoshi a tsaye a bakin kofar shida jami'an tsaron, fuskarsa kadai na kalla na hango tsantsar bacin rai a tare dashi,

Koda na k'arasa gurin nan na fahimci akan abinda yake faruwa, wato yana so ya shiga sashen Su kuma sun hana shi sunce yayi hakuri mai gurin ya dawo daga aiki! Muddibo ya dinga huci yana sakar maganar da duk tazo bakinsa, Daya daga cikinsu yace."Ranka ya dade ba wannan muke nufi ba ai mun san kai ba zaka ta'ba cutar dashi ba muna so ka fahimci yanda tsarin namu yake Shugabanmu dashi kansa mai gurin yace kada mu bar kowa yana shiga sai da izininsa saboda haka kayi hakuri idan ya dawo ya bamu umarni sai

Please Login or Register in order to submit comment