Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bakin cikinta yanda taga manya mutane na girmamshi tare da kambaba! darajarsa, bata damu da kyaututtukan da ya samu ba kamar yanda ta damu da taga ya k'askanta!

Washe gari da 'kyar ta fito daga dakin domin breakfast, Asp din ya gidan be fita ba, ta gaisheshi kamar bata so, ya amsa yana nazarinta shi kansa d'abi'un yarinyar gabadaya basu bashi sha'awa, shiyasa yake so su shirya ranar da zasu kaita gaban mahaifinta kamar yanda yayi alkawari.

Ya kalleta sai kumbure-kumbure take alhalin babu abunda akai mata, da kulawa a maganarsa yace."ZINATU Ina fatan dai kina jin dadin zama damu ko."

Da 'kyar tace." Um ina jin dadin karamcinku a gareni nagode amma yaushe ne za'a sallame ni haka, tunda dai duk bukatunku sun biya."

Ya kalleta da mamakin maganarta yace." Kamar akwai abunda yake cikin ranki duba da yanayin maganarki."

Murmushi takaici tayi da fadin." Ranka shi dad'e wannan mutumin fa da kuka d'auki son duniya kuka d'ora masa bai da kirki ko kad'an! mugu! ne azzalimi! ni har yanzu ban yarda da gaskiyarsa ba."

Asp ransa ya baci da jin maganarta sai kawai ya rufeta da fad'a ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba, yace." Ban san wace irin kiyayya kike wa Umaru ba, shin me kike so muyi masa bayan wanda yafi haka? mutumin nan ya taimakeki a lokacin da kike bukatar taimako amma duk sanda za kiyi magana a kansa ba mai kyau bace! shin wai me yayi miki da zafi da kika tsaneshi haka."!

Cikin 'Kunci da takaici tace." Ranka ya dade mu bar maganar kawai domin duk abinda zan fada maka a kansa ba zaka yarda ba duba da ganin yanda zuciyarka ta hasala! kawai saboda na kiraye shi da macuci alhalin sunan daya cancanta dashi kenan."

Yace."Kin san Allah ba zan matsa daga gurin nan ba har sai kin sheda min irin cutar da yayi miki da har kike kiran sa da wannan sunan."

Ganin yanda ya kafe ta da idanuwansa yasa jikinta mutuwa, me zata ce yayi mata bayan alkairi, ta san ya taka muhimmiyar rawa a kanta amma haka kawai take jin haushinsa! a yanzu duk abinda zata fada a kansa sharri ne!

Ya katse tunaninta da fadin." Ke nake sauraro na fada miki ba zan bar gurin nan ba har sai naji dalilin da yasa kike tsaneshi."


Bakinta ya sub'ce gurin fadin"Saboda ya keta min haddi sakamakon kad'aicewar mu a dajin."

Ya zuba mata ido da so ya tabbatar da maganarta......."Ya keta miki haddi kamar yaya."?

Ko kunya ta sake lailayo wani sharrin......"Fyad'e yayi min." Tafad'a babu nadama a cikin maganarta.

Ya jima yana kallonta da mamakin furucinta kafin ya girgiza kai da fadin." Wannan shaci fad'i ne ban yarda zai aikata hakan ba."

Murmushin takaici tayi da fadin." Ai dama ba zaka yarda ba saboda jarumtarsa tana burgeka a matsayinka na babban mutumin mai rik'e da mu'kamin Asp bai kamata ace kana mubaya ga wannan k'azamin mutumin ba."

Maganarta sai ta bashi dariya, ya tsaya ya dara kafin ya mike yana duba agogon dake daure a hannunsa yace." Lallai yarinyar nan da gaske kike amma babu damuwa, wannan maganar kuma ba zan barta ba sai mun tattaunata da mutumin naki." Shuru tayi ba tace komai ba, har ya bar gurin, tana zaune a gurin suka fito tare da madam d'inshi dirarriyar mace kyakykawa da kyawun jiki sam ba za kace ta haifi 'yar shekara ashirin ba, hannunta rike da 'yar jakarshi ta rakashi bakin mota ta nayi masa fatan alkairi.
Koda ta dawo a falon ta zauna suna hira jefi-jefi ta d'an saki jikinta sakamakon mutunci da karamcin matar wanda ya janyo mata 'kima da mutunci a idonta......Sai dai kwata-kwata jininta bai had'u da Nabila ba, haka kawai ta tsani yarinyar alhalin babu wani abu da tayi mata na laifi........daidai gwargwado tana bata girma tunda ta fahimci cewa ta d'an girme mata sai take kiranta da Auntyna. hakan yana sake sanyawa kanta ya kara girma domin akwai ta da son girma, gata dai a gidan ubanta amma mulkar yarinyar take, da yake ita din mai saukin kai ce bata damuwa, domin bata mance ingantaccen hadisin nan da yake cewa "ka girmama bakon ka, wannan dalilin yasa take mata duk abinda take so, wanda ita kuma anata 'bangaran take ganin kamar ta isa ne! shiyasa take mata biyayya.....!




*#500 via....0542382124.....Binta Umar gtbank, idan kati zaki tura kiyi min magana ta WhatsApp da wannan number.......07084653262....Mutanan Nijar ku tuntubi wannan number.... 22796074090....Dala dari katin airtal ko mov*
1/25/22, 11:15 - Buhainat: *GOJE!!ƒ™†_*
ƒ™¤`%’]bq _(SADAUKI OMAR RETURNƒ™.cƒ™«a)_

*BINTA UMAR ABBALEĪ]*

*MANAZARTA WRITER'S*
*ASSOCIATIONƒ™Ndƒ™ˆg•ýÿ*
____________________

_Mijina kazami! ne! to ni kam sai dai nace kiyi hakuri 'yar uwa domin akwai su a cikin maza amma ba duka ba, kuma bake kadai kike da matsala irin wannan ba, amma ki sani ke da kanki kina iya gyara abinki, da wayo da dabara, zahirin gaskiya kazamin namiji nada wuyar sha'ani! duk macan da take fuskantar wannan matsalar daga gurin mijinta akwai hanyoyi masu sauki da zata bi domin gyara masa dab'iu kamar yanda takeso ya kasance!_



FREE PEGE
*33&34*
Police barrack nan ne mafi akasarin ma'aikatan tsaro suke zaune da iyalansu, a nan gidan Asp yake, haka zalika ma anan ne mai girma Governor ya mallakawa UMARU gida tazarar su da Asp din babu yawa gida biyar ne a tsakaninsu, tsarin ginin gidan mai kyau ne, plate ne mai dauke da bangare uku, kowanne 'bangare a shirye yake tsaf da dukkan abinda za'a bukata na yau da gobe, abinda kawai ya rage a gidan mace, don a ranar da ya tare a gidan ma 'yan uwa da abokan arziki surutun da suke masa kenan, cewa a yanzu Allah yayi masa komai na rayuwa, abinda ya rage masa mace domin duk cikar mutum da kamalarsa mutukar bashi da aure to darajarsa dole tayi 'kasa..........'Kwarai hakane a yanzu ya san cewa cikar mutumcinsa shine aure, wannan dalilin ya sanya yaji sha'awar auran a cikin zuciyarsa, sai dai kuma babu wanda ya amsawa cewa zai auri 'yarsa a cikin wa'inda suke kawo masa tallan 'ya'yansu, da kansa zai duba wacce ta kwanta masa a ransa ya aura.

B'angare d'aya ya dauka Uwale da Hamra'u sai suke amfani da daya, Uwale ganin ba zata iya zama a gidan ita kadai ba yasa tace Hamrau ta ta zauna domin ta taya ta zama, hakan yayi mata dadi mutuka domin dama tana neman hanyar da zata kusanta kanta dashi.

Itace ta d'auki ragamar kula da gidan, ta tsaftacce ko'ina har sashensa idan zai fita take 'karbar key a gurinsa ta shiga ta gyara masa ko'ina tasa turare idan taga ya cire k'ananun kayanshi a toilet ta wanke masa tas ta shanya idan sun bushe ta ninnke tasa masa a wardrobe, kullum idan ya dawo daga gurin aiki tsaf-tsaf yake samun gurinsa yana kamshin turare na mussaman, kafin yayi wanka ya fito ta shirya masa abinci da duk wani abinda zai bukata, k'wazon yarinyar da yanda take kulawa dashi da kakarsa yana burgeshi! ba tun yau ba ya gane inda ta dosa a kansa, zai iya auranta saboda kyawawan dabi'unta dama wannan shine abin dubawa a cikin lamarin aure.

'Bangaranta kuwa shawarwari take da zuciyarta kan cewa ta sheda masa tana sonsa ko kuwa ta bari ya furta mata da bakinsa, a ganinta yanzu tunda yayi kudi yafi k'arfinta shiyasa kullum take jin tsoron tunkararsa da maganar gudun wulakanci, sai dai duk sanda masifar sonsa ta isheta daki take shiga taci kukanta ta koshi, kafin ta roki Allah ya za'ba mata abinda yafi alkairi a rayuwarta, amma tayi mamakin yanda akayi Uwale tayi shakulatun 'bangaro da maganar wanda ada can baya har kayan lefe take tarawa burinta bai wuce tabbatuwar auran ba, amma yanzu kwata-kwata bata maganar, ballanatana ta bashi umarnin auranta kamar yanda tayi alkawari a can baya.

Kamar yanda gwamnati ta mutuntashi ta kuma karramashi, shima haka ya mutunta yaransa ya karramasu yayi musu alheri sosai, domin duk rabin alherin da ya samu ya sadaukar musu, a cewarsa suma suna da hakki duba da irin muhimmiyar rawar da suka taka, hakan ya sake janyo masa kwarjini da farin jini a gurinsu da sauran jama'ar gari.

*******
Yau satin sa guda kenan da fara gudanar da aiki a ofis dinsa na mussaman, Uniform dinshi ma na mussaman ne, amma yayi kamanceceniya dana Asp amma kuma akwai bambanci sosai!

Da yake yana da hikima da nazari babu wani abu da ya shige masa duhu, aikin yake kamar wanda ya shekara yana aikin tsaron lafiyar al'umma!

Wasu takardu yake dubawa kira ya shigo wayarsa dake saman tevur din dake gabansa.

Ya ajiye takardun cikin nutsuwa ya daga wayar da fadin.'' Ranka ya dade barka da aiki."

Daga daya bangaran Asp ya amsa da "Barka dai *Jan wuya!* da yake sunan da yake kiransa dashi kenan, ya cigaba da cewa." Gobe ne fa tafiyar nan."

Yayi jim! yana tunanin maganar kafin ya dan ja siririn tsaki! ya manta shaf da maganarsu ta zuwa garin kano domin kai marakunyar yarinyar nan gaban iyayenta........Yace."Ogah me zai hana ka sata a mota ta tafi ai ita din ba yarinya bace zata kai kanta gida."

Ya girgiza kai da fadin." A'a mutumina ba za'ayi haka ba, ni nayi wa mahaifinta alkawarin cewa dani da kai zamu kai masa ita, sannan kuma ba haka dokar aikin take ba, dalilin da yasa ma tuntuni ban shirya tafiyar ba, saboda na fi bukatar yarinyar ta murmure na 'yan kwanaki hakan zai farantawa iyayenta rai su kuma ji dadin ganinta cikin koshin lafiya, to alhamdullihi yanzu naga tayi kyau sosai babu rama ko wani abu wanda ya danganci haka daga gareta."

Ya sauke ajiyar zuciya da fadin.'' Ranka ya dade don dai kawai ka shirya tafiyar nan dani ne amma da sai dai nace kaje kai kad'ai kawai dalili bana bukatar abinda zai sake danganta ni da yarinyar nan wallahi.''! Cike da takaici ya 'karashe maganar.

Asp na 'yar dariya yace." UMARU ban san me yasa kai da yarinyar nan bakwai jituwa ba, itama yanda kake jin haushinta haka take jin haushinka kullum bata da magana sai taka."

Da sauri yace." Tana zagi! na ko."? Asp din yasa dariya da fadin." In kaji zagi! ma d'aya kenan! shin ka san kuwa maganar da mukayi da ita kwanaki a kanka."?

Kai ya girgiza a k'untace yace." Sai ka fad'a." Jim yayi kafin yace." Na san sharri kawai tayi maka ba zaka aikata hakan ba, duk da dai zuciya bata da 'kashi kuma a lokacin hakan na iya faruwa saboda kusancinku da juna wanda dama shi shed'an burinsa kenan mace da namiji su kad'aice shi sai ya zama na ukunsu."

Tsaf ya fahimci inda maganar ta dosa, murmushin takaici yayi kafin yace." Banyi mamakin jin wannan maganar ba domin duk mutumin da yake 'kin ka, to babu irin k'azafin da ba zai yi a kanka ba, Asp wallahi tallahi! da naso keta haddin yarinyar nan da ba zata kai labari a hannuna ba, saboda na samu dama iri-iri a kanta amma sam ba wannan ne a gabana ba, burina shine na kubtar da ita, sai kuma sharri! ya biyo bayan alkairi."

Yace." Kwarai kuwa shiyasa a lokacin da take maganar na 'karyata ta domin na san ba za ka aikata hakan ba, kawai dai tana neman hanyar da zata tozartaka ne."

Yace."Shiyasa ai nace kayi tafiyarka kawai Asp wallahi kaji rantsuwar musulmi ba naso na sake ganin fuskar yarinyar nan."

Yace." A haba dai kada ka tsananta da yawa abu ne mai sauki wannan ki
'kiyayyar da kukewa junanku ta rikide ta zama soyayya irin wacce take da wuyar samu hakan na iya faruwa.

Ranshi ya 'baci da jin haka tevur din dake gabansa ya buga! murya a sama yace." Allah ya kiyaye Asp bana fatan Allah ya jarrabeni da soyayyar wannan yarinyar, kawai kayi min fatan alkairi ba irin wannan ba."

Asp din yayi mamakin yanda maganar ta fusata shi, sai ya sassauta murya da fadin." Colm dwon mana ka samu nutsuwa, wannan maganar dana nake maka a yanzu ba wai nace lallai hakan ya tabbata ba, kawai a jikina nake jin kamar akwai wani abu da zai ratsa tsakaninka da yarinyar domin anyi irin haka ba sau daya ba, ba kuma sau biyu ba, kiyayya ce ake wacce tafi wannan daga karshe kuma sai ta rikide ta juya matsananciyar soyayya."

"Mtsssssw!!!! Yaja wani dogon tsaki kafin ya kashe wayar ya jefar saman tevur tunda ya had'u da Asp bai ta'ba 'bata masa rai irin yau ba........Shi kuwa Asp din sakin baki yayi da wayar a hannunsa yana mamakin al'amarin.


Da takaicin maganganun Asp ya isa gida, takalmanshi kawai ya iya kwancewa ya kwanta saman kujera ba tare da ya cire inform din dake jikinsa ba, rungume hannunsa yayi a kirji ya rufe idanuwansa yana hasaso kammanin yarinyar............. 'baka ce ba sosai ba, idan be manta ba tana da tsayi gami da cikar kirji da fadin kwankwanso, 'kirar jikinta kenan, tana da manyan idanu da d'an k'arami hanci wanda ke tsatstsafo da gumi ako da yaushe, wannan sune kad'ai abunda zai iya tunawa a game da ita!

Yaja tsaki! tare da gyara kwanciyarsa, har yanzu maganar ce take cin zuciyarsa! shi kam a rayuwarsa me zai yi da yarinyar da ta nuna masa tsantsar 'kiyayya irin haka, hanyar jirgi daban ta mota daban.

Sallamarta ce ta katse tunaninsa, ya bude idonshi tare da tsareta dasu, be tashi zaune ba yana daga kwance ya amsa mata, still idonshi na tsaye kanta, sai tace tunda suke bai ta'ba yi mata kallon kurrullah irin haka ba, duk sai ta tsargu dama ta shigo ne domin ta duba taga ya dawo ta kawo masa abinci, jikinta duk sai ya mutu sakamakon kafe ta da yayi da kaifin idanuwansa.

A sanyaye tace." Yayana sannu da zuwa ashe ka dawo."?
Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya yun'kura ya tashi zaune yana kokarin b'alle botiran gaban rigarshi, yace." Na dawo my dear nagaji ne shiyasa ban leka gurinku ba, ina so nayi wanka na huta tukkuna."

Cike da kulawa tace." Sannu ya aikin? bari na had'a ma ruwan wanka ko."? yana kokarin cire rigar daga jikinshi yace." Godiya nake Allah yayi miki albarka." Cike da jin dadi ta amsa, kafin da sauri ta kama hanyar dakinsa, ido ya bita dashi har ta shiga dakin ya girgiza kai a fili yace." Wannan itace matar aure mai cikakkiyar tarbiya nutsuwa sanin ya kamata yayi imani ko zuria ya had'a da wannan yarinyar ba zaiyi kaico ba.

Ta fito falon ta sameshi daga shi sai vest wacce ta matse shi da gajeran wando domin ya cire gabadaya kayan jikinsa, da sauri ta sunkuyar da kanta kunyar had'a ido take dashi, ganin haka yasa yayi murmushi ya tashi ya bar gurin, da sauri ta dauki inform din ta kai masa daki ta rataye masa kafin ta bude wardrobe ta dauko masa 'kananun kayan shan iska, ta ajiye saman gado da sauri ta fita daga dakin. tana jin wata annushuwa a cikin ranta, yau ta d'an fara ganin alamun sonta acikin 'kwayar idanuwansa....



*Free pege zai 'kare a pege 40 ga masu bukatar wannan littafin suyi payment domin karanta littafin cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, kada mugunta!/hassada!/ ganin k'yashi! ya hana ku biya, ku jira na sata ku karanta, wallahi tallahi hakkin wani masifa ne! bala'i ne! muyi kokarin nesanta kanmu da haram! duk kankantarta!*


*#500 via....0542382124.....Binta Umar gtbank, idan kati zaki tura kiyi min magana ta WhatsApp da wannan number.......07084653262....Mutanan Nijar ku tuntubi wannan number.... 22796074090....Dala dari katin airtal ko mov*
1/25/22, 11:27 - Buýÿÿÿ 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~hainat: *GOJE!!ƒ™†_*
ƒ™¤`%’]bq _(SADAUKI OMAR RETURNƒ™.cƒ™«a)_

*BINTA UMAR ABBALEĪ]*

*MANAZARTA WRITER'S*
*ASSOCIATIONƒ™Ndƒ™ˆg•ýÿ*
_______________



*35&36*
Cikin 'kananun kayan data ajiye masa ya shirya jikinsa tsaf, ya fesa turaranshi mai sanyi da sanyayya rai, ya kimtsa tsaf dashi, kai tsaye b'angaran nasu ya nufa cikin yanayin tafiyarsa ta gwarazan maza!

Uwale kawai ya samu a falon ta zubawa tv ido tana kallo, ya shiga da sallama a bakinsa tayi saurin kallon bakin kofar ganinsa yasa ta sauke ajiyar zuciya ta amsa sallamar tare da maida hankalinta kansa har ya k'araso inda take zaune.

Tibin ya d'an kalla kafin ya zauna kusa da ita da fadin." Kallo kike ne."? Ta gyara zama da fadin." Gashinan dai Ina kallonsu da ido amma bana fahintar komai, yanzu nake cewa Hamra'u ta kai min tashar Arewa 24 nafi fahimtarsu duk da cewa su din ma wani sa'in suna da abun haushi."

Ba tare da yace komai ba ya dauki romot ya canza tasha sunnah tv ya kai dai-dai lokacin da marigayi malam Ahmadu B.u.k yake tambihi akan hadisan Annabi Muhammad (SAW) tace." Allah ya jikan wannan malami yayi wa addinin Allah hidima." Yace."K'warai kuwa ba iyalinsa ne kadai sukayi rashi ba duk duniya ne muna rokon Allah ya jadadda rahama a gareshi." Cikin alhini ta amsa da ''ameen ya Allah."

Gurin yayi shuru gabadaya hankalinsu na gurin sauraran malamin, har Hamrau ta 'karaso gurin kafin tace."Yayana na kawo maka abinci nan ne."?

Hankalinsa na gurin malamin yace." Eh ki kawo min nan." Da sauri taje ta shiryo masa abincin a tire ta ajiye masa a gabansa, kasan kafet ya sauka ya tankwashe kafafunsa, yana kokarin bude kwanakun abincin tayi saurin zuwa ta bude cikin nutsuwa ta zuba masa towon farar shinkafa tas dashi lailaye a leda da miyar zogale wacce taji kayan hadi tayi kyau sosai sai kamshi ne yake tashi, ya kalleta da murmushi a fuskarsa yace."My dear wannan miyar wace kala ce.''?

Tana kokarin magana Uwale tace."Miyar zogale ce, ni nayi sha'awarta nace a maimakon taushe tayi mana ko baka so ne."?

Girgiza kai yayi da fadin." Ai ko bana so tilas naci domin farin cikin ku, na san kuma miyar za tayi min dadi kamar yanda nake bukata."

Hamra'u farin ciki ya lullubeta, murmushi tayi ta tashi daga gurin taje ta samu kujera ta zauna.

A nutse yake cin abincin yana yaba nutsuwa da nagartar yarinyar, duk inda ake tunanin mace ta kai, komai Allah yayi mata nutsuwa tarbiya uwa uba iya girki na zamani dana gargajiya, tunda yake cin abincinta bai taba cin karo da kuskure ba, komai yana masa dai-dai wannan dalilin yasa yake zagewa ya cika cikinsa ba tare da wata fargaba ba, ya cinye wanda tasa masa tas ya 'kara wani yaji dadin miyar sosai da sosai.

Koda ya kammala cin abincin, sai ta kwashe kayan ta nufi kicin dasu domin wankewa........Ajiyar zuciya ya sauke bayan barin ta gurin, ya janye idonsa daga hanyar da tabi, Uwale ta kalleshi da fadin." UMARU ni kuwa ina labarin wannan yarinyar."?

"Wace yarinya kenan."? Yafada idonshi a tsaye a kanta.

Tace." Yarinyar da ka taimaka mata wacce ake maganar 'yar sarkin kano ce."

'Bata fuska yayi da fadin'' Tana nan Lafiya." daga haka sai yayi shuru da bakinsa.

'Yar dariya tayi irin ta tsaffi ta dauki goro ta gutsira kafin tace."Haka kawai nake maka sha'awar auranta"

Ya kalleta da mamakin jin furuncinta, da kyar yace."Me yasa kike min sha'awar auranta bayan duk ga 'yan mata nan masu hankali da tarbiya''

Shuru tayi na minti biyu kafin tace."To UMARU kaine ai kamar mara lafiya duk macan da akayi magana maganarta sai ka 'bata ranka abinda yasa nayi maka maganar yarinyar domin naji abinda yake
zuciyarka na d'auka ko akwai alakar soyayya a tsakaninku."

Girgiza kansa yayi da fad'in" Babu kuma ki cire hakan a ranki, halin da ake ciki a yanzu shine ina binkice akan yarinyar da zan aura."

Fuskarta a sake tace." To masha Allah, nayi farin cikin hakan, amma UMARU ya za kayi da wannan yarinyar Hamra'u ta jima tana sonka don Allah kada ka watsa mata 'kasa a ido"

Murmushi yayi kafin yace."Ai ita zan aura da ikon Allah." sai ta wangale baki tana kyalkyala dariyar farin ciki ta dafa kansa da fadin." Kai masha Allah naji dadin wannan al'amari UMARU Allah ya tabbata da alkairi ya nuna min lokacin da zanga zuriarka, amma ina alfarma a gurina."

Ya kalleta da fadin." Wace alfarma kuma"? tace." Bana so aja dogon lokaci ayi komai a gama a lokaci k'ankani." Yace."Kada ki damu insha Allahu daga na dawo daga training za'ayi komai a gama da yardar Allah." tace." to Allah ya tabbatar mana da alkairi" ya amsa da ameen ya Allah."

*****
A daran ranar Asp ya umarce su ita da Nabila yace su shirya zasuje unguwa, ba a son ranta ta shirya ba, suka fito harabar gidan a tare sai cika take tana batsewa tana ya mutse- ya mutse, ita kuwa Nabila kamar koda yaushe fuskarta a sake kamar gonar audiga sa'i da lokaci ta kan yi mata magana, idan ta kama, sai taga dama take amsawa, a bayan motar suka zauna Asp din ya zauna kusa da direbansa.

Babban super market suka nufa, ya kalleta da fadin." Duk abinda kike da bukata kina iya dauka." Uffan ba tace masa ba tayi gaba tana zagaye gurin, girgiza kansa kawai yayi ya matsa can gefe tare da fito da wayarshi.

Abokin nashi ya kira, don yanzu UMARU ya zama abokinsa duk da ya girme masa, amma abota suke tamkar tare suka taso aiki yasa sun shak'u da junansu,

Cike da girmamawa ya daga wayar suka gaisa kafin Asp din yace." Ka tsammaci zuwana gurinka yanzu."

Cike da mamakin hakan yace." Ina fatan ba wata matsala bace." Yace." Alkairi ne zamu tattauna wasu batu masu muhimmanci" Yace." Okey to shikkenan sai ka shigo din" sallama sukayi kafin kowa ya kashe wayarsa.


Turaruka kawai ta iya dauka sai kayan za'ki data jida sai kace shazumamu! haka take da shan zaqi kamar me a cikin hakoranta ma akwai wanda suka dan samu matsala duk ta dalilin shan zaqi.

Tana gama tsintar abunda take bukata ta mi'kawa Nabila kwandon kayan, ita kuwa ta kar'ba ta had'a na da na hannunta, kai tsaye gurin total ta nufa da kayan, ita kuma ta fita daga gurin.......Tun kafin ta k'arasa bakin motar direban ya bude mata ta shiga ta zauna har yanzu babu sassauci a fuskarta.

Ganin fitowarsu yasa tayi saurin dauke kanta babu wanda ya tanka mata, direban ya bude masa mota ya zauna, kafin ya kar'bi ledojin hannun Nabila ya bude boot ya zuba, ba ta jira ya bude mata motar ba, ta bude da kanta ta zauna tare da bisimillah a bakinta.

Koda suka shiga barrack din direba na kokarin parking ya umarceshi da cewa ya zarce dasu gida mai lamba shida(number 6) kai tsaye can ya nufa yayi parking a inda aka ta nada kafin ya fito da sauri ya bude musu mota.

Tun sa'ilin da Asp din ya kira wayarsa ya sheda masa zuwansa ya fito ya tsaya domin tsumayinsa sai dai ganinshi tare da yarinyar ya d'an sosa zuciyarsa, amma be nuna hakan a fuskarsa ba, cikin wani irin taku na gwaraza! ya isa bakin motar gabadaya hannuwansa goye a bayansa.
Hannu ya mika masa sukayi musabaha ga juna, Nabila da saurin gaske ta gaisheshi har tana kiran shi da Uncle, ya dan saki fuskarsa ya amsa shima ya darajata kamar yanda tayi masa ya 'boye asalin sunanta ya maye gurbin sa da daughter ina godiya." Murmushi kawai tayi tana sunkuyar da kanta.............Kamar yanda ya watsar da lamarinta ita itama haka ta watsar dashi, ta dinga cika tana batsewa tana banka musu harara! tabbas da ta san gidansa ne da tuntuni ta sauka a hanya domin bata bukatar abinda zai had'ata dashi.

Asp ya juyo cikin tsare gira ya kalleta da fadin." Ku shiga ciki ku gaisa da mutan gidan, sannan ke Zinatu sai kiyi mata bayanin kanki."

Ta kalleshi da niyyar caccakarsa, yanda ya sha kunu! yasa ta d'an ji shakkarsa domin ta fahimci shima dan had'in takaici ne mybe tana iya magana ya buga mata tsawa! a gaban mak'iyinta wannan dalilin yasa

Please Login or Register in order to submit comment