Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

banzar bazara k'azama tayi min abinda zan ci domin ban amince da hakan ba."

Ya dinga auna maganganun ta a cikin ranshi yace." Wacece banzar bazara kuma."?

Ba tare da ta kalleshi ba tace." Kafi ni sanin ta ka fad'a mata cewa duk abubuwan da take aikatawa ina da labari amma idan na tashi yi mata hukunci ba za taji da kyau ba."

Maganar ta bashi dariya amma beyi ba, ya kalleta da fadin." Magana muke akan abincin da za kici babu ruwana da banzar bazarar da kike magana ni bukata ta a yanzu kici abinci."


Kai tsaye tace." A bani abunda nake bukata mana."

Ya kai minti biyu yana kallonta kafin ya juya ya fita, ta bishi da kallon takaici! tsaki taja tana sake jin haushinsa a zuciyarta a ganinta duk shine ya bawa yarinyar dama shiyasa take abunda take so, Marakisiyya duk ta sheda mata abunda ta gani da idonta, za kuma ta dauki mataki a kansu ba'ki d'aya."




*Kika futar min da littafi keda Allah! ki ka karanta baki biya ba kema keda Allah!*

*#500via.....0542382124.....Binta umar gtbabk, idan kati zaki turo kiyi min magana ta WhatsApp da wannan number.... 07084653262.....BINTA UMAR ABBALE*
2/18/22, 12:31 - Binta: *GJ*
*73&74*
Yana jin kunyar kiran Asp a waya saboda abunda ya faru a tsakaninsu, yana kuma tunanin yanda za'ayi yarinyar ta samu abunda take bukata, bashi da ra'ayin yawace-yawacen gidan abinci, wannan dalilin yasa yake tunanin kiran abokin nasa koda irin taimakon da zai masa, shi a kankin kansa ya san hakan bai dace ba cewa da abinci da duk abun bukata a gidansa amma ya tafi wani gidan barar abinci, babu shakka ba komai ne ya janyo masa hakan ba face rashin samun nagartaciyyar mace. wacce bata kiyaye cikinta ba ballanatana ta kiyaye nasa da nauyin yake a kanta.

Ajiyar zuciya ya sauke ya yanke shawarar kiran Asp din yayi......Suka gaisa da juna kamar wani abu bai faru a tsakaninsu ba, cikinsu kowanne yay kokarin danne abun a ransa.

Cike da jin nauyi yake sheda masa Uzurinsa.

Asp din yay murmushi da fadin." Haba ai wannan ba'a abun damuwa bane abokina bari na kira Madam a waya yanzu na sheda mata."

Yace." Godiya nake mutumin kirki Allah ya saka da alkairi."

Yana 'yar dariya yace." Umaru bana san yawan godiyar da kake min ai tuntuni na fada maka cewa ni da kai mun zama daya saboda haka don Allah ka daina yawan yi min godiya idan wani abu ya ratsa a tsakaninmu."

Murmushi kawai yayi yana girgiza kai tare da mamakin mutunci da dattakon mutumin tabbas irinsu na da wahalar samu a duniyar nan.


Sashen ta ya nufa a karo na biyu, ya sameta tana waya da Aunty Zeey sai kyalkyala dariya take, aunty zeey din take bata labarin wani maganin mata da tayi amfani dashi wai Asp din kuka ya dinga yi wurjajan! harda majina!! shine fa abun ya bata dariya tace." Nima ina so akawo min irins.........Shigowarsa ta katse maganarta, ta gyara fuskarta da fadin." 'Kawata zan kira ki idan an jima." Tayi saurin kashe wayar domin bata so ya fahimci abinda suke tattaunawa.

Ido suka had'a tayi kasa da kanta tare da dan zumb'ura baki.

Yace." Ke da waye kuke waya haka."?

Cikin shan 'kamshi tace." 'Kawata ce."

Yace." Amma dai tana da matsayi babba duba da irin walwalar da ki keyi."

Shuru tai masa ba tace komai ba.

Yace." Munyi waya da Asp insha Allah za'a kawo miki abunda ki ke bukata daga gidanshi."

Ci kanka ba tace ba, yay jim yana kallonta koda za tayi magana.

Ganin tsayuwarsa a dakin tana nema ta haifar mata da matsala yasa ta kalleshi da fadin." To kayi tafiyarka mana."

Juyawa yayi da nufin fita ta tsirawa bayansa ido! yanayin kayan dake sanye a jikinsa sun ja hankalinta sosai har ta dinga jin bakon abu na ziryar tar gangar jikinta.......Zazzafar ajiyar zuciya ta sauke bayan fitarsa ta kwanta saman kujera da waya a hannunta.

Boyayyan masoyinta ta lalubo text tai masa zuciyarta sai harbawa take ita a kankin kanta tasan abunda take ba daidai bane amma ya za tayi, a halin da ake ciki a yanzu tana bukatar kulawa da rarrashi da kuma soyayya.

Koda ya duba text din murmushi kawai yayi.....Gaisuwa ce kawai da fatan alkairi ba wani abu da tayi wanda ya wuce gona da iri.


Whas'App a shiga ya tura masa sabbin sticks masu hargitsa lissafi mussaman yasa Adewale ya turo masa saboda plan dinshi a kanta.

Bayan ya tura mata sticks din sai ya rubuta magana kamar haka...........

_"Wai shin yaushe ki ka shirya had'uwar mu ne, my love ina cikin tsananin bukatarki na san dai kema kina da wannan bukatar ki shirya had'uwarmu a shirye nake dana gamsar dake zan gwada miki soyayyar da baki ta'ba tsammani ba."_

Tashin hankali kenan, ai ganin zafafan sticks din ya jefa ta cikin mawuyacin hali, gabadaya jikinta ya dinya kyarma tsigar jikinta duk ta tashi wani irin sha'awar namiji take, tana duba sticks din tana lumshe ido 'kasan ta sai wani irin abu yake, pant dinta kam ya riga ya gama ji'kewa.

Lamo tayi kan kujera mararta na wani irin ciwo mara misali still ruwan kasan ta dake fita har yanzu be daina ba.

Idonta ya ciko da ruwan hawaye, wai shin ya za tayi da wannan masifar ne? anya kuwa FARUK mutumin arziki ne? idan ba haka ba mai zai sanya ya dinga turo mata hotonan iskanci yana tayar mata da hankali, kwanakin baya ta gargade shi amma ya be bari ba, tana ganin dole tai wa tufkar hanci tun kafin ya jefeta a wani hali.


Koda Nabila ta shiga ta sameta cikin wani irin yanayi sai hankalinta ya tashi, ta ajiye kayan abincin a gefe, ta karasa har inda take kwance tana kiran sunanta.

Ta kalleta da jan ido kafin tace." Yaushe ki ka shigo."?

Kusa da ita ta zauna cikin kulawa tace." Tun dazu nake sallama a falo shuru sai can mai aikin ki ta fito daga kicin take sheda min kina cikin daki to na shigo ina ta sallama baki amsa ba anya kuwa aunty Zinatu ko baki da lafiya ne."?

Zaune tayi yunkurin tashi tana dan cije baki tace "Bana jin dadi wallahi mara na ke ciwo."

Tace." Ayya ko lokaci ne yayi."?


Girgiza kanta kawai tai ba ta iya magana ba.

Tace." Ko asibiti za muje idan kinci abincin bari na kira Uncle a waya." Tana nufin Umaru domin da Uncle take kiransa kuma ita duk a tunaninta yana gurin aiki.


Da sauri tace." Aa kada ki kira shi rabu dashi kawai zan sha magani."

Jiki a sanyaye ta sauke wayar daga kunnanta, wanda a lokacin ma kiran har ya shiga basu sani ba.


Ganin wayar ta katse ne yasa yabi layin domun sanin wanda ke kiransa.

Ta duba wayar da fadin." Kinga ya ma kira."

Tsaki! taja da fadin." Baki ji abinda nace ba kenan? cewa nayi fa ki kyaleshi shin waye ma ya baki number shi."?


Da yake tuntuni ta san halinta sai tayi murmushi tare da kokarin mayar da al'amarin 'karami tace." Na fara kiran shi na katse saboda abunda ki kace ashe ta shiga ina ganin shine dalilin da yasa ya kira domin yaji waye."

Shuru tai tana wani ya mutse fuska.

Ya sake kira a karo na biyu domin wancan da yayi ya katse bata daga ba.

Jin muryar mace a kunnansa yasa shi mamaki.

Yace." Wacece ne."? Tace." Uncle Fadila ce ina kwana."?

Ita kad'ai ce take kiransa da wannan sunan, shiyasa lokaci guda ya gane ta, ya saki fuska da fadin." Daughter ya kike ina Madam ina fata kuna lafiya."?

Tace."Duk muna lafiya lau Uncle, Nazo kawowa aunty Zinatu abinci ne."

Cike da jin dadi yace." Nagode sosai daughter bari na shigo mu gaisa."

Tace." To Uncle sai ka shigo."

Kashe wayar yayi itama ta kashe tata wayar babu wani abu a zuciyarta tace." Aunty ko na zuba miki abincin ne."?

Kallonta tayi ta watsar taja tsaki ta mike tare da kama hanyar toilet tana wasu tunane-tunane a ranta.

Murmushi tayi tare da bin bayanta da kallo, ita kam ta rasa! wane irin hali ne da ita, duk yanda za kayi don ka kyautata mata sai ta gwasale! bata ta'ba mu'amula da mutum mai irin halinta ba.

Jikinta ta gyara, ta cire pant (wando) ta sauya wani ta fito cike da rashin kuzari a tattare da ita.


Koda ya shigo dakin kallo daya yayi mata ya sheda cewa akwai wani abu dake damunta......Koda yake ya san dole abunda zai faru kenan, shi kansa kallon sticks din ya jefe shi a cikin wani yanayi don dai kawai yana iya sarrafa kansa ne.


Ta dauke kanta daga garesu bakin gado ta zauna tana jinsu suna sake gaisawa sai godiya yake mata.

Tace." Uncle babu komai ai an zama daya ka daina godiya."

Murmushi yayi ya dan kalli gefen da take zaune kamar hankalinta ba'a kansu yake ba, amma kuma duk maganganunsu ta naji tana kuma aunasu akan sikeli, har yanzu ba suyi abunda ya wuce gona da iri ba, sai dai tana mamakin yanda akayi yarinyar take da number wayarsa, koda yake hakan ba abun mamaki bane idan akayi duba da irin sha'kuwar dake tsakaninsa da mahaifinta watakila a gurinsa ta samu number.


Ta mike tsaye tare da gyara zaman hijab din dake wuyanta, tace." Uncle ni zan tafi gida, Aunty Zinatu Allah ya kara sauk'i." bakinta ne ya sub'ce da fadin hakan shaf ta manta maganarsu.


Uffan ba tace ba ballantana tayi mata godiyar hidimar da akayi mata, tana dai jin sa yana mata godiya tare da bada sakon gaisuwarsa ga Mahaifiyarta .


Bayan fitar Fadilan ya k'arasa kusa da ita da fadin." Kin ci abincin ko."?

Girgiza kai tayi alamun A'a."

Yace." Saboda me ki dubi time fa ace har yanzu baki karya ba me yasa kike san zama da yunwa."?

Lumshe ido tayi tare da jin tsunkuli a mararta ta dan ya mutse fuska da fadin." Ba na jin zan iya cin wani abu yanzu."


Yayi jim yana kallonta kafin yace." Me yake damunki domin alamu ya nuna baki jin dadi."


Kallonsa tayi da lumsassun idanuwanta da suke buge da muguwar sha'awa.

Magana take so tayi amma rashin abunda za tace yasa ta mayar da kanta kasa kawai taja bakinta tayi shuru.

Murmushi yayi a cikin zuciyarsa yake ayyana wani abu, wato yanzu ya gama gane lagonta abinda yake saurin ladabtar da ita kenan, bata da juria ko kadan, a cikin kwayoyin idanuwanta kadai zaka fahimci hakan.


Ya zauna kusa da ita sosai kafadarsu ta had'u ba tayi yun'kurin matsawa ba, sai ma wani irin ajiyar zuciya data sauke, burinta kawai taji ta a kwance a faffadan kirjinsa dake mutukar gigita ta.


Ya dan kwantar da murya irin yanda ya saba rarrashinta......"Ki daure ki ci ni zanyi miki maganin matsalarki."

Yanda yake maganar a tausashe yana mata wani irin kallo yasa gabadaya gabobin jikinta suka saki, ta sake shiga wani yanayin, a dan raunane ta kalleshi kafin tace." Ni na fada mata ina da matsala."?


Ya dan kashe idonsa still yana kallonta yace." A cikin kwayar idonki na gani."


Ido ta tsira masa dan so ta tabbatar da maganarsa, a ganinta tayi kokarin ganin ta boye abunda yake damunta ashe hakan bata samu ba.


Ganin ta kasa magana yasa da kanshi ya janyo kwandon abincin ya fito dasu ya dauko plate ya zuba mata funkason uku ya zuba miya a kai, da ido kadai ka kalli funkason da miyarsa sai kayi sha'awa tun kafin kasa a bakinka, kamshin miyar ya cika dakin.

Ya d'ora plate din a cinyarsa kafin yasa hannu ya gutsira tare miyar kai tsaye bakinta ya nufa da fadin." Bude bakin."

Wai! i abun nema ya samu sai ta wani susuce! ta dinga yi masa wani irin kallo tana mamakinsa, ashe dai yana da wayewar kai har haka, ada kallon bagidaje take masa amma yanzu ganin abunda yake irin na goggun 'yan duniya yasa ta 'karyata zarginta.


Da 'kyar ta iya bude bakinta yasa mata funkason da ya jike da miya nan da nan ta cinye yasa mata wani, haka suka dinga yi har sai da ya tabbatar ta k'oshi sannan ya bude mata lemo tare da kokarin sanya mata a baki, girgiza kanta tayi ta nuna masa ruwa.........Ruwan ya dauko ya tsiyaya mata a cup ta kar'ba tana sha tana kallonsa.

Ya kar'bi cup din da fadin." Kin koshi ko.''? kai ta daga kamar wata 'kankanuwar yarinya.

Yace." Alhamdulillhi." Agogon dake daure a hannunsa ya duba......'Daya shaura na rana, yana ganin ba zai tunkari wani abu ba yanzu saboda lokacin sallah ne, ya mike da fadin." Lokacin sallah yayi idan kina bukatar wani abu kina iya kiran waya ta."

Ya kama hanyar fita daga dakin ba tare da ya tsaya jiran amsarta ba........Wani irin kallo ta bi shi dashi ta na jin kamar taje ta janyoshi ta ha nashi fita har sai ta samu abunda take bukata daga gurinsa.

*****

*KUYAN TA INNA!*
Wani 'karamin 'kauye ne a garin kano, Wanda bashi da jama'a sosai sai dai yawan gonaki wanda ake noman rani iri daban-daban, da yawa jama'ar dake cikin 'kauyen suna da rufin asiri ta dalilin noman abincin da suke duba da cewar abinda yake wuya kenan a cikin wannan zamanin...........Tunda suke zaune a garin wani gagarimin tashin hankali bai ta'ba faruwa ba kullum suna zaune lafiya kuma koda ba'ko zai shiga garin zasu kar'be shi hannu biyu su bashi masauki suci dashi kana kuma su jashi gona domin dogaro da kansa.


*UBAN DABA!* Tare da a yarin sa da sukayi shaura a wannan gari suka yada zango..........Da yake da fuskar salihai suka shiga garin yasa jama'a da dama suka kar'be su hannu biyu, wani Dattijo mai suna malam Dauda ya jagorancesu zuwa fadar mai unguwa domin ya san da zuwan su garin.

Mai unguwa ya kar'be su hannu biyu kuma ya bukaci sanin daga wane gari suke.


*UBAN DABA!* ya kada baki yace." Ranka ya dad'e mu din mutanan Maiduguri ne kasancewar garin namu babu lafiya yasa mukayi hijira domin samun tsira da rai da lafiyarmu, muna roko a bamu gurin zama kafin komai ya daidaita mu koma garinmu."


Mai Unguwa Malam Hassan ya girgiza kai yana jimanta al'amarin...........Yace." Kada ku damu insha Allahu kun zo inda za'a share muku hawaye, Najeria Uwa ce domin kuwa tana d'aukar kowa a matsayin d'anta, sannan garin *KANO* Gari ne da ya sha bambam da sauran garuruwa, da yawa akwai mutanan da suka tsallako daga garuruwansu suka zo suka yada zango a cikin wannan gari namu mai albarka suka zauna kafa sassani tare da kasuwanci kana kuma sukayi aure suka hayayyafa, mutukar ba'a fada ba babu wanda zai ce ba 'yan garin bane, wannan yana d'aya daga cikin halin girma da kuma dattako na wannan gari namu, saboda haka ba zamu k'yamace ku ba, tunda har kuka za'bi yada zango a wannan k'auye insha Allah za muyi iyakar bakin kokari gurin ganin mun baku taimako domin rike kanku har zuwa lokacin da Allah zai kawo zaman lafiya a garinku, saboda haka *KANO TA DABO!* Tare dani mai unguwa Malam Hassan mai wakilatar 'kauyen *KUYAN TA INNA!* Muna muku barka da zuwa."

*UBAN DABA!* Ya girgiza kai kamar wani mutumin arziki yace." Ranka ya dade mungode k'warai da wannan karamci Allah ya saka da alkairi, Allah ya baku lada akan aikin alkairin da kuke."

Mai Unguwa ya amsa da ameeen ya Allah wannan ba komai bane a gurinmu babban burin mu ace k'asar mu ta samu zaman lafiya da kwanciyar hankali saboda haka duka ku kwantar da hankalinku, ku zauna kamar kowa a cikin wannan gari."


To a takaice dai mai unguwa da kansa ya basu masauki mai kyau, ya kuma dauki dawaniyar ci da shansu, kafin tafiya tai nisa, wasu daga cikin jama'ar k'auyen suka fara d'aukarsu suna tafiya gona dasu, amma banda shugaban nasu wato *UBAN DABA!* saboda nakasar dake tare dashi, kullum dai yana tare da mai unguwar a fada yana ganin yanda yake gudanar da mulki a garin.



_*SAI MUN HA'DU RANAR MONDAY DA IKON ALLAHj_*_




*Kika futar min da littafi keda Allah! ki ka karanta baki biya ba kema keda Allah!*

*#500via.....0542382124.....Binta umar gtbabk, idan kati zaki turo kiyi min magana ta WhatsApp da wannan number.... 07084653262.....BINTA UMAR ABBALE*
2/21/22, 16:38 - Binta: *GJSR*
*75&76*
Yini tayi cikin wani irin yanayi mara dadi, domin duk yanda taso da ta danne abunda yake damunta kasawa tayi, hakanan ta kwanta kan gado tana birgima tare da shafa kasan mararta, ita a kan ki kanta tasan bata da hakuri da kawar da kai a wannan gurin domin kuwa da ta sanyawa zuciyarta juria da hakuri to da bata jefa kanta wani mummunan hali ba, to ta riga ta sanya al'amarin a cikin 'kokwan ranta ta kuma kwadaita dashi sosai, abunda ya faru a tsakaninsu a ranar da ya dawo gidan shi take k'ulafuci, dan ta ga alamar kamar hakan ba zata faru ba sai ta tagaza wani abun domin dai tunda ya sanya k'afarsa ya fita bai sake shigowa ba ballanatana wani abu ya ratsa tsakaninsu.

Da 'kyar ta samu tayi wanka tayi sallah, don magariba da isha'i ma had'asu tayi tana kokarin tashi daga kan daddumar ya shigo dakin da sallama a bakinsa.

Cikin ranshin kuzari ta amsa ta zauna gefan gado tana kokarin cire hijab din dake jikinta.

Kawar da idonshi yayi sakamakon yanayin kayan dake sanye a jikinta kananu ne masu fitar da sura.

Ya bita da kallon nazari yana mamakin sauyawarta gabad'aya ta zama wata lazy kamar mara lafiya.


Gyaran murya yayi kafin yace." Zan dan je wani guri yanzu ina fatan baki da wata matsala."?

Kallonshi tayi a karo na biyu, ya shirya tsaf cikin dogwayen kaya riga da wando na shadda dark blue da aiki a wuyan rigar besa hula ba amma ya taje sumar kanshi ta tafi tsaf da kyataccan sajen da ya kwata kyakykyawar fuskarsa, yay mata kyau sosai abinda take ji a tare da ita ya sake nunnukuwa.

Lumshe idonta tayi tana sake takure jikinta guri daya.

Murmushi kawai yayi be sake cewa komai ba ya juya da niyyar fita yana raya wani abu a cikin ranshi.

Motsin fitarsa yasa a hankali ta bude ido tana kallonshi har ya fice daga dakin bata dauke idonta daga kansa ba.


Ya fita ya bar mata 'kamshin turaransa wanda ya sake jefata cikin mawuyacin hali, ta kwanta lamo kan gado tana ji kamar ta fashe da kuka saboda rashin yanda za tayi, cikin zuciyarta kuwa tayi wa Faruk Allah ya isa yafi cikin kwando domin a ganinta duk shine silar shigarta wannan mugun yanayin.

Meeting suka zauna wanda ya dauke su tsayin awani uku, sai sha daya na dare suka tashi.


Sha biyu shaura ya shiga gidan.......kai tsaye gurin ta ya nufa domin duba halin da take ciki.

Jin motsin bud'e kofarsa yasa zumbur ta tashi zaune tare da tsirawa bakin kofar ido.


Ido suka had'a tana zaune daram tsakiyar gado babu alamun bacci a tare da ita, jikinta sanye 'yar karamar vest da wandon ta k'arami, gabadaya surar jikinta a waje........ta sanya kayan ne domin ta ja ra'ayinsa.

Ya girgiza mutu'ka! amma kuma sai yayi namijin kokarin danne kwad'ayinsa, ya nufe ta da wata madaidaiciyar leda a hannunshi mai dauke da wani tambari a jiki.

A marairaice take kallonshi tana motsi da bakinta magana take so tayi amma tana jin nauyi.

Gyaran murya yay kafin yace." Baki bacci ba har yanzu."?

Kai ta daga masa alamar "Eh yace." Me hanaki bacci."?

Shuru tayi bata iya ce masa komai ba sai faman lumshe idonta take.

Ya sauke ajiyar zuciya tare da ajiye mata ledar dake hannunsa a kusa da ita yace." Ga tsaraba nan nayi miki ina fatan dai kin ci abinci."?


Kai ta girgiza a sar'ke tace." Ba wannan nake bukata ba."?

Ya kalli idon mara kunya da mamakin furucinta yace." Okey kina da wata bukatar kenan."?

Kai ta daga masa, ya kalli agogon hannunsa da fadin.'' Zanyi wanka yanzu amma kafin na dawo ki tabbatar kinci abinci shine zan saurari bukatarki."

Ta dan sauke ajiyar zuciya tana kallonshi da sassarafa ya kama hanyar fita......Lips d'inta ta dan ciza tana ya mutse fuskarta, itafa a halin yanzu babu abunda take bukata sai soyayyarsa gabadaya ma cikinta a cushe yake


Ledar da ajiye mata ta bude tana dubawa

Manyan biscuit ne da tarin chocolates masu dadi.........leda biyu taci ba biscuits din kafin ta fara shan chacolate din gabadaya hankalinta da tunaninta yana kansa.


Sai da yaci abinci sannan samu damar yin wanka, yana fitowa daga toilet ta shigo dakin........ ya bita da kallon mamaki.

Daburcewa tayi kafin tayi namijin kokarin aro jarumta kawai taje ta zauna gefan gadonshi tana ya mutse fuskarsa, ita kanta mamaki kanta takeyi to ya ta iya da abinda yafi karfinta.......Kafin ma yay magana ta riga shi, cikin shagwaba da so lallai sai ta kare kanta tace." Tsoro nake ji a dakin."

Yace." Tsoro kuma yau kwananki nawa a gidan nan ba kiji tsoro ba sai yau."?

Ta daga kai da fadin." Kullum idan dare yay da kyar nake bacci dalilin motsin da nake ji kawai dai banyi magana ba ne "

Girgiza kansa kawai yay sam bai yarda da wannan maganar ba, kawai ta fadi hakane saboda wata manufarta, sai kawai ya bagarar da maganar da fadin." Yanzu muka rabu da Mutuminki yace yana gaisheki."

Ta d'anyi murmushi da fadin." Ina amsawa."

Shiru dakin yay babu wanda ya sake magana a cikinsu..........Shi yana ta hidimar shirya jikinsa ita kuma ta kura masa ido tamkar kura ta samu nama.

Ya juyo suka had'a ido da sauri ta kawar da kanta tana sauke ajiyar zuciya......Murmushi yay kawai ya kama hanyar fita shi ya san abinda ya shirya mata.


Tsuru! ta zauna ita kadai a dakin tana sake-sake anya kuwa bata tafka wauta ba, ta lura kamar ya fahimci abinda takewa shiyasa yake mata wulakanci.

Taji wasu hawaye masu zafi suna shirin kwace mata, bata ta'ba tsammanin zata dinga bibiyar namiji irin haka ba..................Garin ne ya rikice hadarin dake kwance ya tashi, iska da walkiya har cikin d'akin, da alama ruwan sama ne zai sauka.

Falon ta bishi, nan ta sameshi kwance saman kujera da wayar a hannunsa yana dubawa.......Motsin zamanta a kusa dashi ya sanya shi tashi zaune yana kallonta da fadin.'' Ke har yanzu baki kwanta wai me kike so ne."?


Taji wani 'katon abu ya tsaya mata a wuya, wai me yasa yake so ya mayar da ita wawuya ne........Amma ta san abunda za tayi masa.

Ba tace masa komai ba kawai ta cire hijab din jikinta, yay sauri kawar da kansa tsigar jikinsa gabadaya ta tashi sakamakon ganin zahirin jikinta.


Wayar shi take kokarin k'wacewa yana rikewa tare da fadin." Ke me haka ne? ki tashi ki tafi ki kwanta kin dame ni."

Ta fashe da kuka da fadin." Kasan bani da lafiya ko."?

Kawai ya saki ya baki yana kallonta kafin yace." Yaushe zan sani ke ya kamata ki fada min amma baki fada ba sai yanzu, me yake damunki."?


Ta goge hawaye dake karakaina a saman fuskarta cikin shagwaba tace." Duk jikina ne yake min ciwo muje daki ka min tausa.''

Ya dinga kallonta yana mamakin karfin halinta, wai har shi za tayi wa wayo! yace." To naji sauka daga kaina muje dakin ko.''

Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta sauka daga kanshi amma bata saki hannunsa ba ta rike gam kamar wanda zai gudu.


Jikinsa a mace ya mike tsaye itama ta mi'ke tana sake shigewa jikinsa, duk sai ya rasa nutsuwarsa dan gabad'aya yanayinsa ya sauya shima yana bukatar al'amarin kawai yana daurewa ne.


Tun kafin

Please Login or Register in order to submit comment