Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tashi zaune tana rawar jiki.......Me yasa ta kasa samun abunda takeso a jikin rigar! ita a tunanin kaurin rigar ne ya saukar mata da nutsuwa sai taga akasin haka. "Ba rigar bace mai rigar ne yasa miki nutsuwa da kwanciyar hankali."
zuciyarta ce take mata wannan maganar.

Da sauri ta k'aryata zuciyarta ta sake rurrufe jikinta da rigar tana korar abinda zuciyarta ke raya mata, babu yanda za'ayi ta amince da cewa wannan gantallalan ne zai zama garkuwa a gareta.

Daya daga cikin yaranshi ne ya kawo mata ruwa da asuwaki da abin kari. ganin yanda maigidansu yake bata kulawa ya sanyashi gaisheta, bata amsa ba sai wukalantaccan kallon da take masa shida tarkacen da ya ajiye a gabanta. Girgiza kansa yayi baki a cije! ya bar gurun ba don kar ya dauki mataki akan yarinyar ya samu matsala da maigidansa ba, da sai ya fasa mata baki domin yaji ciwon kallon banza da tayi masa.

Har gari yayi haske sosai tana takure cikin rigar har yanzu ta kasa tantance a wane iri yanayi take,

Can ta hangoshi yana zuwa inda take, ido kawai ta tsira masa babu kiftawa sosai take mamakin tsananin kamar da yake da jarumi(Barbahs) tana bala'in son jarumin saboda jarumtarsa da iya soyayyarsa idan yana abu a film kamar gaske, zazzafar ajiyar zuciya ta sauke tana kokarin karyata abinda zuciyarta ke raya mata a kansa.

Tsaf yake cikin shirin fita, ya sauya rigar jikinsa doguwar jallabiya ce browan mai gajeran hannu sai ya sanya dogon wadon jens kanshi nannad'e da bakin yadi yayi gammo sosai! idanuwan nan rad'au! da bakin kwalli! kafad'unshi rakwacam! da tarin kayan farauta, har da irin doguwar bindigar nan, hakanan wuyanshi da damtsan hannuwansa wasu irin abubuwa ne a d'aure.! kafafunsa sanye suke da wani irin takalmi mai tarin igiyoyi a jikinsa.


Tunda ya tsaya a kanta take kallon kafarshi, mamakin kyawun kafar take, bata ta'ba kallon kafarsa ba sai yau, faratanshi tas babu kazanta sai kananun gashi dake kwance saman yatsun kafar.

A tsorace ta dinga sauke ajiyar zuciya tana kokarin kawar da idonta daga kan kafar. taji muryarsa cike da wani irin amo!! "Tashi zaune."

Yanda ya fadi maganar babu wasa yasa ta tashi tana kallon fuskarsa, babu fara'a yace." Zanja ragamar yara na wani aiki a cikin dajin nan, ina so ki kula da kyau! kada kiyi kuskuran barin gurin nan! ki kiyaye! mutukar kina so ki cigaba da rayuwa a duniya.

Kuka tasa tana kallonsa da fadin." Me yasa ba zaka tafi dani ba, saboda tsabar mugunta shine zaka had'a kan yaranka ku tafi ku barni ni kad'ai! bayan ka san dajin bashi da kyau komai yana iya faruwa da rayuwata."

Yace." Nan gurin yana da tsaro bayan haka kuma gurin da zamu shiga yana da had'ari shiyasa na yanke shawarar barin ki anan sai yafi miki kwanciyar hankali."

Ta girgiza kai tana shakar hanci tace."Aa nifa ba zan zauna ba wallahi ko kun tafi sai na biyo bayanku."

Yanda tayi maganar babu alamun wasa a tare da iya yasa yaji shakkar tafiya ya barta.

Ya kalleta a lokacin da take kokarin mi'kewa. "Na fad'a miki abinda yake da akwai kina kuka ko."?

Hannu ta d'aga masa da fadin." Nifa ba zan zauna ni kadai a wannan gurin ba." Tana gama maganarta ta kama tana tafiya babu takalmi a kafarta, ga kanta babu dankwali."

"Ki tsaya nan nace."! Cikin tsawa yayi maganar. taja ta tsaya ba tare da ta juyo ba.

Yaja tsaki tare da komawa baya, takalmi ya lalobo mata tare da wani farin yadi.

Ya karasa inda take da fadin." Kar'bi wannan ki rufe jikinki dashi." ba tayi musu ba ta kar'ba, ta lullube jikinta har kasa. Ya bata takalmi ta tsuguna tana kokarin sawa, ganin tana 'bata masa lokaci yasa ya tsuguna da kansa ya d'aura mata takalmin sosai yanda duk wuya ba zai fita a kafar ba.

Hannunta ya rike a cikin nasa suka nufi inda ayarin jama'arsa suke tsayuwar jiransa, ganinsa tare da ita ya basu mamaki! amma babu wanda yayi magana a cikinsu, yayi gaba suka rufa masa baya.
karnuka wasu a gaba wasu a baya, sai kuma bushe-bushe da gangi! da ya cika dajin!

*Free pege ya kusa 'karewa a hanzarta biyan kudin karatu.*
*0542382124...Binta umar gtbank* a tura sheda ta wannan number...... 07084653262


*Ayi kokari a duba wannana_*
_Mijina baya bani_ kulawa bayan kafin muyi aure yana bani kulawa da duk wata soyayya
___________
*Watakila kece kika janyo faruwar hakan, na farko dai namiji yana da bukatar kulawa, ta kowane fanni, watakila kafin kuyi aure ke din 'yar gayu ce mai tsafta, bakya rabo da kwalliya kamshin turare ako da yaushe, sai bayan auranki kuma ki mayar da kanki jakar mata, da kuruciyar da komai ki shiririce wanka ma sai kiyi kwana biyu ko uku ba kiyi ba mussaman a cikin wannan lokacin, sai kiyi kwaskwarima ki shafa mai akan dauda kina tsamin hammata! to me zai hana namiji bai kyamace ki ba, babu mummunar mace, kuma komai shekarunki mutukar kina da miji to kada ki zauna a lalace domin hakan zai janyo miki bacin rai mai tsanani mussaman idan kina da abokiyar zama to zaki zama koma baya ta kowane fanni, tsafta jigo ne a cikin zamantakewar aure don haka ki kula da wannan abubuwan.*

*1- Wanka sau biyu a rana*
*-2 yawan aske sassan dake fitar da gashi a jikinki*
*4-Zama cikin kamshin turare mai sanyi da sanyaya zuciya*
*3-Kitso duk bayan sati ko kwana goma kuma kafin ayi kitson a wanke kan*
*5-Wanke baki sau biyu ko uku mussaman idan zaki kwanta*
*6- Taraiyaya da iya kalami mai dadi a lokacin da kike tare da mijinki*
*7-Sauya kalolin abinci masu inganci*
*8- Sanya kaya na mussaman domin zuwa turaka*
*9- Shagwaba wata abace mai muhimmanci*
*10- Banda yawan dariya mara ma'ana a gaban miji murmushi zaki yawaita yi masa kina sarrafa kwayar idonki a kansa kina bashi labarai masu dadi.*

_Mutukar kin kula da wannan to zaki kama mijinki a hannu kuma zai baki kulawa ta mussaman_



*#500 via 0542382124...Binta umar gtbank, idan kati zaki tura ki min magana ta WhatsApp da wannan number... 07084653262........Mutanan Nijar ku tuntunbi wannan number....*
*22796074090* Dala dari Katin Airtal ko Mov
1/12/22, 20:33 - Buhainat: *GOJE!*_
`%]bq _(SADAUKI OMAR RETURNa.c_)

*BINTA UMAR ABBALE]*

*_MANAZARTA WRITERS ASSOCIATIONg_KqXk*
_____________________



*Mijina mazinaci ne*
_________
_Mazinacin namiji daban yake a cikin maza, duk irin kokarin da za kiyi a kanshi to hakan ba zai hanashi neman matan banza ba, da yawa daga cikinsu jarabtace daga Allah! amma kuma son zuciya yafi yawa a ciki, 'Yar uwa idan Allah ya jarrabeki da auran mai irin wannan dabi'ar, ba zama zakiyi ba addua zaki tsananta akan Allah ya kawo miki mafita, Allah kuma ya shiryeshi ya gane hanya mai kyau. amma mafi alkairi a rayuwarki rabuwa da auransa domin samun zaman lafiyarki, koda kuwa akwai zuria a tsakaninku rabuwar ita tafi alkairi._

*Ubangiji Allah ka shirya mana mazajenmu ka dauke hankalinsu daga kan haram ka mayar da hankalinsu kan halalinsu, mu kuma Allah ka bamu hakuri da juriar dawainiya da bukatunsu.*


FREE PEGE
*17&18*
*UBAN DABA!*
Ya gagara! yayi shura! a harkar ta'addanci! ya addabi 'kasa da jama'ar dake cikinta, ran mutum abun banza ne a gurinsa, da yawa jami'an tsaro suka shiga sassaninsa, basa fitowa da rai! idan anyi sa'a wasu su fito a raye to za'a samu muggan raunika a jikinsu, shekaru bakwai kenan daya kafa sansani a cikin dajin dashi da jama'arsa, manya manyan bishiyun kuka ciki suka fafake ya zama makwancinsu, duk abunda yake faruwa a cikin gari yana samun labari akwai redio a tare dashi, bayan haka kuma yakan tura yaran sa suyi badda kama su dauko masa rahoton abinda kasa take ciki.

Masana sunyi hasashen cewa Gurin da ya kafa sansani akwai albarkar kasa a gurin, irinsu gold da man fetur da sauransu, wannan dalilin yasa shima ya tsaurara matakan tsaro a gurin, babu wanda yake amfana da albarkar dake gurin sai shi da jama'arsa, duk sanda suka haqo gold din akwai wani hamshakin dan kasuwa dake zuwa ya saya. cikin dare ya kan shiga dajin kar'ba! ya basu kudi da kayan masarufi, sannan a duk sanda sukayi ra'ayi zasu badda kama su shiga cikin gari suyi siye-siyen abunda suke bukata.

*Mashekin daji!* Hatsabibin mutum ne wanda yake da suddubaru! duk sanda hukuma ta tura jami'anta binkice a dajin, basa nasarar ganin sansaninsa amma kuma shi da jama'arsa suna ganin duk irin d'auki ba dadin da jami'an tsaron keyi a kok'arinsu na ganin sun ga mafakarsu, wannan damar suke samu su karkashe wanda sukayi ra'ayi, sai dai a fito da gawarsu.

*GOJE!* Ya jima da jin labarin hatsabibancinsa, kullum tunaninsa ya za'ayi ya kawo karshen ta'addancin daya ke a kasa.

Kafin ya yanke shawarar tunkarar inda yake sai da ya zauna da yaransa domin yaji ra'ayinsu, da yawa daga cikinsu jikinsu ne yayi sanyi domin dai sun san tunkarar mutumin babban al'amari ne! dalili shi akwai kayan aiki a tare dashi da jama'arsa, duk da suma suna da dabaru amma a ganinsu tunda sojoji da 'yan sanda suka kasa samun nasara a kansa to waye zai iya .

Ganin jikinsu yayi sanyi yasa ya karfafa musu gwiwa da fadin." Su cire tsoro a cikin ransu, kada su sanya a ransu cewa *masheki* da jama'arsa zasu samu nasara a kansu, idan sun yarda da kansu cewa sunfi karfi wuka da bindiga to tunkarar inda yake abune mai sauki bayan haka kuma su dauka cewa wannan aikin da za suyi kamar jahadi idan ma Allah ya kaddara mutuwarsu a gurin aljanna ce makomarsu.

Wannan maganar da yayi ya sanya suka samu karfin gwiwa, suka kwanta da shirin tunkarar *masheki* ba tare da k'asa ta san abinda suke shirin aikatawa ba.

Tafiya suke tsakankanin bishiyu da manyan tsaunika, gami da kwazazzabe, gabadayansu, babu alamun gajiya a tattare dasu, tafiyar suke suna bushe-bushe tare da farautar duk wata dabbar data gilma a gurin, ita dashi ne a gaba, yayin da jama'arsa ke take masu baya, tayi masifar galabaita! bakinta ya bushe cikinta in banda qugi! babu abinda yake, ba komai ke damunta sai yunwa,

kallonshi tayi kamar tunda aka halliceshi be taba dariya ba, tunda ya rike hannunta da zasu tafi be sake kallonta ba ballantana magana ta had'asu,

Magana takeso tayi masa amma tana jin shakka! don yanayin sa kadai dole ya baka tsoro! sai taja ta tsaya cakk! tana sauke wani irin numfashi!

Kallonta yayi na minti biyu, kafin ya juya yayi masu magana da ido, sun gane abinda yake nufi, sai suka samu guri suka zazzauna wasu kuma suka fara hawa kan bishiyu suna kad'o 'ya'yan itace.

Kan wani ice ta zauna tana kallonsa sai kai kawo yake a gurun.........."Ina bukatar ruwa da abinci." tafada tana dam hararar bayansa. Yana jin maganarta amma be juyo ba.

"Ina magana fa."! tafada kamar zata fashe da kuka.

" Alba." sunan d'aya daga cikin yaransa kenan. Yayi saurin zuwa gurin, yace."Ka bata ruwa da abinci." Yace." An gama maigida.

Gabanta ya k'araso da wata 'yar jarka ruwane a ciki, ya mika mata da fadin." Kisha yanda kike so"

Cike da k'yan'kyami take bin jarkar da kallo, 'ya'yan wasa sun tashi a cikin ruwan.

Tsaki! taje cikin tsawa! tace."Wuce ka ban guri waye zai sha wannan kazantaccen ruwan."

Maganar ta dauki hankalinsa ya juyo yana kallonta, shi kansa Alba d'in ransa ya baci da jin irin tsawar data buga masa.

Ya kalleshi da fadin." Jeka kawai." Ya girgiza kai, da fadin" Angama." Gurin ya bari. Shi kuma ya juya mata baya, tunda ba zata sha ruwan da kowa yake sha ba sai ta zauna a haka.

Ranta ya baci ganin ya juya mata baya tace." Wai me ake nufi ne."?

Ba tare da juyo ba yace." Ya kike so ayi miki? an baki kince bakya so akwai wanda kike so ya zama ruwa a cikinmu kisha."?

Tace." Ruwan fa bashi da kyau, bayan haka ya za'ayi na hada bakina dana wannan 'kazamin."

Ya girgiza kai da fadin." Sai ki zauna da ishirwarki ."

Kuka! ta fashe dashi! da fadin" Allah ya isa tsakanina da kai mugu azzalimi."!!

Ya juyo da fuskar bacin rai yana kallonta.....Alba dake kokarin zuwa gurin yace."Oga wannan yarinyar fa tana da matsala wallahi! da zaka bani dama sau daya dana koya mata hankali ."

Ya kalleshi na minti biyu kafin yace." Ko bana guri ban amince da hakan ba amana ce a gurina." da sauri yace."Allah ya huci zuciyarka."

Ya gyada kai da fadin ." Wanke lemon ka bata." Da sauri yayi abinda aka umarceshi, ta kar'ba tana yatsine fuska.

Yana kokarin barin gurin yace."Bani wannan jakar ruwan ta hannunka." Ya mika masa, a gabansa ya bude murfin ya zubar da ruwan ciki. Ya bar gurin da ita a hannunsa.

Ita dashi duk suka bishi da kallo yana tsallake manya duwatsu kafin su daina ganinsa, gabanta ya tsananta fad'uwa ganin baya gurin, ta dora idonta kan Alba dake tsaye yana zazzare mata jajayen idanuwansa, saurin sunkuyar da kanta tayi, tsoro takeji kada yayi mata wani abun, sai da ya gama cije-cije kafin ya bar gurin.

Ya kasance sai ita kadai a gurin, sai motsi da maganarsu da takeji a saman bishiyu, ta daga kai tana so ta hangesu, amma ta kasa ganinsu,

Dajin ta dinga bi da kallo, kanta yana juyawa, manya dutsina da tafka-tafkan bishiyun dake gurin sun juyar mata da kai.

Da sauri ta kama hanyar da taga yabi, tana tafiya tana waiwayen bayanta.


Sai da yayi tafiya mai tsayi sannan ya cimma ruwa yana gudana daga kasan wani tsabtataccan dutse gare-gare dashi.........Ya haura wasu manya duwatsu kafin ya samu nasarar d'ibar ruwan.

Yana juyowa kibiyar ta gilma ta gefan fuskarsa, da alama saita shi akayi Allah be bada nasara ba.......Da mugun sauri ya daga kanshi sama, can ya hango su saman wani dutse sun kai su biyar, yayi gaggawar fitowa daga tsakanin ruwan.

Suma basu fasa harbinsa da kibiya ba.
A gaggauce ya fara kurd'awa inda jama'arsa suke baya su cimma inda suke ba tare da shiri ba. sai dai me! biyoshi sukayi suna sakar masa harbi ta ko'ina!!

K'aro sukayi da juna!! ya rike hannunta tamau! bayan wata bishiya suka 'buya, suka 'karaso gurin suna sassare matattatun itacuwan da suke gurin.

Hannunsa dake cikin nata yake kokarin cirewa ta rike da kyau! tana girgiza masa kai! wai kada ya fita, ya sake yunkurin cire hannunsa ta rike! hawaye masu tsananin zafi suka wanke mata fuska, bakinta tasa a kunnansa, a hankali tayi magana "Kada kaje."

Jajayen idonsa ya tsira mata! ta marairaice fuska, tana ro'konshi da idanuwanta.

Tausayi ta bashi ganin yanda jikinta ke wani irin karkarwa, cikin zuciyarsa yace."Ba yanda za'ayi yana ji yana gani nasara ta kufce mai wannan ce hanya mafi sauki da zai tunzura zuciyar abokin gabarsa.


Kafin ta ankara, ya fuzge! hannunsa, ya fice! ta leqa kanta tana hango artabun da suke a tsakaninsu, su biyar ne shi d'aya, amma cikin ikon Allah ya samu nasara a kan mutum biyu ukun kuma suka gudu!.

Ya k'wace wukaken dake jikinsu, da sauran kayan ta addanci, kana ya d'aure musu hannuwa, gaba ya tisa su har inda suka yada zango shida jama'arsa.



*#500 via 0542382124...Binta umar gtbank, idan kati zaki tura ki min magana ta WhatsApp da wannan number... 07084653262........Mutanan Nijar ku tuntunbi wannan number....*
*22796074090* dala dari katin Airtal ko mov
1/21/22, 12:26 - Buhainat: *GOJE!*_
`%]bq _(SADAUKI OMAR RETURNa.c_)

*BINTA UMAR ABBALE]*

*_MANAZARTA WRITERS ASSOCIATIONg_KqXk*
_____________________


FREE PEGE



*19&20*
Cikin tsantsar tashin hankali! da gigita suka gurfana a gabansa kafin su sheda masa abinda yake faruwa.............."Ya wani mike a fusace! tare da mi'ka tafkaken hannunsa wanda yatsun ke cike da zabban zinare da azirfa! wani irin bahagon mari! ya dinga kifa musu kafin ya sanya kafarsa ya tunkudesu duka suka fadi wanwar! a gurin. gabadaya suka
Sunkuyar da kansu, jikinsu in banda rawa babu abinda yake.

Ya takarkare! da karfi! ya kurma uban ihu!!! lokaci k'ank'ani gabadaya kaf yaransa suka kewayeshi! ya goya hannu a baya yana kai kawo a gurun!

Tsit! gurin yayi babu mai kwak'wk'waran motsi a cikinsu.

Lokacin da yake kai kawo a gurin kallonshi nake ina mamakin muninsa! baki ne sosai gashi gajere dab da kasa, yana da katon kai da tafkekiyar fuska, gabadaya hallitunsa masu girma ne bayan gajartar da yake da ita, bakinsa kato haka nan hancinsa kwala-kwala idonsa kadai ya isa firgita yaro! jajawur! dasu, kasumba tayi kaca-kaca a fuskarsa babu kyawun gani!
kallo guda za kayi masa ka tabbatar da rashin imaninsa.!

Cikin kaushin murya! ya fara magana kamar haka." A jinin jikina naji cewar akwai ayarin da suka shirya min! Yau tsayin sati guda kenan idan na kwanta bacci nake ganinsu a idona! babu wani shirinsu da zai firgatani! na shiryawa zuwansu! na kuma yiwa kaina alkawari cewa duk yawansu sai naga bayansu! babu wani mahalukin daya isa ya tunkari inda nake ba tare da she'kashi barzahu ba! nafi karfin hukuma! ballanatana wani dan adam! saboda haka dukkunanin ku na umarceku da cewa ku zauna cikin shiri babu wanda zai fita da rai a cikinsu."! jiki na tsuma! yake maganar yana wani irin huci! gabadaya ya burkice sakamakon jin abin da yazo masa a bazata!


********
Saboda tsabar kwarjin da yayi musu sam sun kasa hada ido dashi, suna gurfane a gabansa, yayin da shi kuma ke kai kawo a tsakaninsu kafin yaja tunga ya tsaya a gabansu, hannuwansa ya goya a baya, babu wasa ya fara magana kamar haka." "Ya sunanku."?
babu wanda yayi magana a cikinsu. Ya sake maimaita maganarsa! uffan basu ce ba.
Ya juya baya yana kallon jama'arsa dake tsatstaye kowanne a cikin shiri.

"Alba bani wannan dorinar." yafada yana kallonsa.
Da saurin gaske ya ciro bulalar daga cikin gidanta, kaurinta ya isa! nayi imanin za ta iya dauke fatar mutum.

Ya gyara rikonta a hannunsa, cikin wani irin hargagi! wanda yasa gurin amsawa! yace."Ba zaku bude baki kuyi magana ba ko."? Duk da sun tsorata da yanayinsa, amma hakan besa sun magantu ba.

Ya zabura! ya juya tare da kiran Alba! yana zuwa ya umarceshi da ya cire musu kayan jikinsu kaf!
Alba yabi umarni!

Ya kai ya kawo ya gurin jikinsa na wani irin karkarwa! tsumin ne ya tashi! ganin haka ya sanya wasu daga cikin yaranshi suka bara buga gangi!!! da bushe-bushe? Ya sake rikicewa! wani irin tafka! yake musu! suna ihu! da birgima a gurin!
Birgima suke a gurin suna gurnani! yana binsu da tafkekiyar dorinar dake hannunsa yana tafka musu, wanda ya janyo tsiyayewar idon daya daga cikinsu.

Hankalinta a masifar tashi taje tana kokarin rike masa hannu kuka take kariris! tana bashi hakuri sunyi bala'in bata tausayi! bata san bashi da imani ba sai yau!

Tureta yayi ta fad'i kasa ta rirrike kafafunsa "Kayi hakuri wannan rashin imani ne, ka zubar masa da ruwan ido ga jini yana fita a jikinsu kada kayi kisan kai." Wannan maganganun nata besa ya fasa abinda yake ba, ya sanya kafarsa ya taka gwiwar wanda yake kokarin gudu! ya murza da karfin gaske! wani marayan ihu! ya saki kafin ya zube a gurin yana karkarwa jiki yace." Yi hakuri kada ka kasheni zanyi ma bayani."

Ba tare da cire kafarsa ba, ya buga musu tsawa! da fadin" Ya sunanka."? baki na rawa yace." sunana Yakubu ." Ya kalli dayan da yake matagugu a kwance "Kai fa."? Yace." Sunana Sulaiman."

Kafarsa ya cire yana wani huci! ya barsu a gurin.......Saman wani icce! ya zauna! wasu daga cikin yaranshi suka bishi! da ruwa...

Wasu na masa fifita wasu kuma na kara kambaba darajarsa!

Nad'in kansa ya warware kafin ya sunkuya tare da bada umarnin a zuba masa ruwa a saman kan.

Ya dago kan yana girgije ruwan sumarshi mai laushi tabi ta kwanta tana digar da ruwa. Alba yasa abu yana tsane masa ruwan.

Har yanxu babu sassauci a tare dashi, idonshi na tsaye a inda suke. tana tsaye a gabansu, magana a suke a tsakaninsu amma basa iya jin abinda suke cewa.

Ranshi ya baci da ganin abinda take, yarinyar ta nema ta lalata masa aiki. mikewa yayi da bulalar a hannunsa ya karasa gurin, kallon mara imani take masa, za tayi magana kenan, a zabure! yayi kanta da bulalar!! ta matsa gefe da sauri! gabanta na bugawa! jajayen idanuwansa ya tsira mata cikin mashahuriyar tsawar data kusa sanyata sakin fitsari yace." Wuce ki bani guri."! kafafunta na rawa ta bar gurin, bai ta'ba firgitata ba kamar yau.

Ya kallesu kafin yace." Ku tashi tsaye! suka yunkura da kyar suka tashi! gabadaya jikinsu ya sauya kama saboda duka! yayi musu wani kallo kafin ya juya da basu umarnin bin bayansa.


Ba tare da iya kallon fuskarsa ba ya fara yi magana kamar haka "Aikinmu shine ta'addanci! rai ba abakin komai yake ba a gurunmu, sannan muna tarewa jama'a hanya cikin dare mu farauci dukkanin guzirinsu, muna rabasu da matansu da 'ya'yansu, mu kwanta dasu, kamar matan auranmu daga 'karshe mu 'kona gawarwakinsu ko kuma mu fito dasu kan hanyar mu yasar! duk wanda ya shiga komarmu bama saurara masa muna da muggan makamai kuma muna da daurin gindi daga sama, kamar yanda ka sani cewa masana sunyi hasashen cewa gurin da muke rayuwa akwai albarkar kasa, to tabbas hakane akwai! amma maigidanmu yaci alwashin cewa babu wani mahalukin daya isa ya amfana da albarkar dake wannan guri sai shi da ayarinsa, yawancin mu musulmai ne magoya bayanshi, amma ya haramta mana ibadah! bama sallah bama salati da duk wani abu da ya cancanta, burin mu ako yaushe mu kashe duk wanda yayi yunkurin shiga gonarmu, maigidanmu yaci alwashi mai zafi! akan duk wanda yayi yu'kurin ganin bayan rayuwasa." Ya k'are maganar tare da sake risinar da kanshi kasa.

Beyi mamakin da jin wannan jawabi ba, hausawa sukace da dan gari akan cin gari, a jawabin da sukayi masa ya fahimci cewa gabadayansu musulmai ne amma suka yarda suka bada goyon bayan ta'addanci a kasa.

Ya girgiza kanshi da fadin." Yakubu-Sule daku aka hada baki wani wawa! zindiqi! mushiriki! ya addabi! kasa da al'ummar dake cikinta, shin me kuke nema a duniya da har kuka mayar da zubar da jini! abin banza? a matsayinku na Musulmai masu amsa sunayen annabawa! shin ya cancanta ku aikata wannan ta'addanci."!

Gabadaya suka shiga girgiza, jikinsu yayi wani irin laushi, yaja numfashii ya fesar! kafin ya cigaba da cewa." Dukkaninku baku cancanta da cigaba da rayuwa a duniya ba domin barin irinku a ban 'kasa had'ari ne."!

Jin abinda ke fitowa daga bakinsa ya firgitasu, a tsoroce! suka shiga bashi hakuri suna kiran sun tuba!!

Wani mugun mari! ya kifa wa daya da jikinsu, 'yar hantsile yayi ya kifa yaci da kasa! tsaye ya mike! yana zagaye a kansu. gabadaya sun tsorata da yanayinsa, su kansu yaran shi basu taba ganinshi a cikin irin wannan yanayin ba, jikinsa in banda tsuma! babu abunda yake, Zinat kuwa addua take a zuciyarta kada Allah yasa ya aikata kisan kai!

Da jan ido ya kallesu, da fadin." *Ni! ne zan kawo karshen ta'addancinsa! *GOJE!!* *Nake mai maganin wani takadiri! Nayi tawa! nayi ta wasu! wannan haka yake! ba'a zubawa dani a kwashe lafiya! *Billahil-lazi hurramanu!* *nayi wa kaina alkawarin ganin bayansah"!* Yanda yake maganar yana zazzare ido shi tabbatar da abinda yake cikin zuciyarsa hakan yake babu 'karya!

Shar'bebiyar wukar

Please Login or Register in order to submit comment