Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dake rataye a kafad'arsa ya fizgo! daga gidanta, wani masifaffan ihu! ya kurma!!! kafin ya fara dadura! wukar a wuyansa!!
Tashin hankali kenan! gabad'aya gurin ya kacame! dan yaran sa ma manyan wukake! suka fito dashi suna gurzawa a kowane sassa na jikinsu! . shi kuwa a wuyansa yasa wukar ya zage karfi sosai! yake gurzawa.!

kuka wiwi! ta dinga yi tana kallon badakalar dake afkuwa, ita tsoronta kada su kashe kansu, ta rasa ya za tayi da rayuwarta a cikin wannan mashahurin dajin!

Tana kuka na fitar hayyaci ta karasa inda yake gabanta na lugudan duka! hannu na karkarwa take kokarin rike damtsan hannunsa, "Ka bari don Allah! ka daina! ka umarci yaranka su daina kada ku kashe kanku."!!
Ko sauraranta beyi ba ya cigaba da abinda yake, jikinta na wani irin rawa ta rumgumeshi tsam! tana kuka tare da dukan bayanshi. wannan ya janyo sadudarsa! ya cake! wukar! a gurin tare da danneta da tafin hannunsa!
Numfarfashi kawai yake gumi na yankowa daga kowane sassa na jikinsa!

Tsit! gurin yayi sakamakon umarnin da ya basu, suka mayar da wukaken jikin jikinsu.

Har yanzu tana manne a kirjinsa ta kam'kamshi shi da yayi wani motsi zata kai masa duka! kuma bata fasan kukan ba.

Hannu yasa ya d'ago fuskarta, suka tsirawa juna ido! ya jima yana kallonta kafin yasa hannu ya goge mata hawayen da suke ta zuba! yayi namijin kokarin cireta daga jikinsa! ta sake kokarin rungumeshi! duk a kokarinta na hanashi aikata wani abun.
Hannu ya daga mata da ido! ya gargade ta, sai ta sunkuyar da kai! amma har yanzu bata dawo daidai ba.


Ya kalli Alba da fadin." Bani abun rubutu."

Da sauri ya fito da takarda da biro! ya mika masa.
A takaice ya rubuta."


_*(KA SHIRYA YAKI DA MAKASHINKA!!!)*_


Wanda yake da d'an sauran kuzari ya mikawa takardar da fadin." Sa'kona ne wannan kana isa ka bashi, cewa daga ni *MAKASHIN MAZA!*

Da kyar! ya mike ya kama hanya yana tafiya tare da waiwayen d'an uwanshi dake kwance cikin halin rai da rayuwa!


Koda ya karanta wasikar sai kawai ya fashe! da wata mahaukaciyar dariya! da mike tsaye tare da dukan! girkakken dutsen dake gabansa!

Hannuwansa yasa ya tallefe 'keyarsa! tare da sunkuyar da kanshi kasa!

Ya jima a haka kafin ya d'ago yana kallon yaranshi dake kewaye dashi, gabad'ayansu suma jikinsu yayi sanyi da wannan al'amarin.

Ya kalli Nuhu dake rakube! gabadaya kammaninsa sun sauya saboda wuyar da yasha, ranshi ya sake 'baci! kawai ba tare da kowa ya ankara ba, ya fille wuka! tana! walwali a wuya ya burma masa! a take ya fara shure-shure a gurin jini sai tsartuwa yake, kafin wani lokaci rai yayi halinsa!

Ya juyo kansu a sukwane! yana kallonsu da kwala-kwalan idanuwansa! Sun tsorata mutuka gaya da ganin tashin hankalin maigidansu.

*"Cike da cin laya yace."Kamar yanda na soke! wuyan wannan shashashan! to haka zan soke! wuyan wannan marakunyar yaron daya tunkari inda nake! Ni! nayiwa kaina wannan alkawari!! saboda haka zamuyi kwankwance! kafin mu afka inda suke da yak'i."*

Suka hada baki gurin fadin."Yanda kayi shine daidai maigida muna goyon bayanka ako wane yanayi."

****
Tun bayan tafiyar Nuhu! babu wani abu daya gilma, hakan besa sun saki jikinsu a gurin ba, sai da duhun dare ya shiga sannan suka fara neman abinda za su ci.

Ita dai 'ya'yan itacuwa kad'ai ta iyaci, tana zaune tana kallonsu sun tada wuta sai gashe-gashe sukeyi da kallon ikon Allah! da kudirarsa, ace wai mutum ya gasa majici gafiya da sauran dabbobi marasa kyau yana ci a cikinsa.

K'auri da karni! duk ya cika gurin! dole ta tashi domin sauya gurin zama, domin mutukar tana shak'ar hayaki da kaurin dake tashi agurin zata iya amayar da abinda taci.

Ido ya bita dashi! be dauke ba har sai da ta samu guri ta zauna can nesa dasu, inda Allah ya takaita akwai hasken farin wata a gurin.

Ta jima a zaune a gurin tana sakawa da kwancewa! sai yanzu ta san ya rayuwa take, ta taso cikin kulawa da gata da komai na jin dadin rayuwa, tunda take bata ta'ba tsammanin cewa akwai ranar da za tayi rayuwa mai muni irin wannan ba! babban tashin hankalinta rayuwa da d'an ta'addah! irin wannan, duk abinda yake a kanta bai janyo masa 'kima da mutunci ba, domin kuwa shine mutum na farko wanda yayi sanadiyar tagayyara rayuwarta, hakika ta tsorota da rayuwa da duniyar ma gabad'aya, A yanzu babban burinta ta samu ku'bta daga cikin wannan dajin, sannan tayi wa kanta al'kawarin ganin ta jefa rayuwarsa cikin kunci da tashin hankali kwantankwacin yanda yayi mata.


Saukar wani abu taji saman wuyanta, da sauri tasa hannu ta buge! ta mike tsaye! wata lafceciyar tsutsa ce ta fado daga saman bishiya.

Rintse ido! tayi tana kiran sunan Allah! kafin taji zirrrrrr a kan kafarta, tayi tsalle ta matsa gefe tana kallon gurin, ashe gabadaya gurin tsutsutsine suke yawo.

Jiki na wani irin rawa ta bar gurin, tana isa inda suke ta iske sunyi shimfida sun gatange gurin da itacuwa tare da rufe gurin da Net!

Tsayawa tayi a gurin ta kasa shiga, domin gabad'ayansu mugun haushinsu takeji! daga nesa ta hangoshi ya nufo gurin, d'auke kanta tayi tare da jan tsaki a cikin zuciyarta.


Koda ya iso gurin bece mata komai ba, ya kama hannunta! kallonshi tayi kamar za tayi magana sai dai tayi shuru, jan hannunta yayi suka shiga gurin.

Guri guda ya zaunar da ita, muryar rarrashi da kwantar da hankali ya aro yace." Ki kwanta anan gurin nayi miki alkawai cewa babu abinda zan bari ya sami rayuwarki."

A maimakon hakan ya faranta mata sai kawai taja masa tsaki! ta kawar da kanta tana zumbura baki!

Hakan da tayi ya bata masa rai amma sai ya danne! be dauki mataki ba ya fara kokarin barin gurin, ta bude baki da fadin." Mamugunci! insha Allah sai naga karshenka."

Maganar ta bashi mamaki mutuka! sai ya juyo da wani irin murmushi a fuskarsa ya nuna kirjinsa da fadin." Me yasa kike so ki kaga bayana."?

Ta zabura! da fadin." Saboda kai din azzalimi ne macuci.!!

Ya jima yana kallonta da mamakin furucinta" Saboda kai din azzalimi ne macuci."! to wai shin da take kiransa da wannan sunayen wane irin zalinci yayi mata tun farkon had'uwarsu?

Still murmushin ya sake kafin ya furzar da iskar bakinshi, cikin gaggawa ya fita ya bata guri domin yana ji idan ya kara second a gurun zai iya nakastata.

Ya jima yana fesar da hayaki kafin ya samu sassauci a zuciyarsa, zazzafar ajiyar zuciya ya sauke! yana me sake jin sautin muryarta na amsa kuwwa! a kunnanta a cikin kunnuwansa, tunda ya taso lokacin kuruciya da girma gwargwamaya yake da *Maza!* bai ta'ba sanya mata a cikin al'amuranshi ba, saboda sanin hallayarsu! yana da tausayi mussaman akansu amma baya yarda da raini daga garesu, mace daya ce yake jinta a cikin zuciyarsa, domin duk ta tara abinda yake da bukata, hankali nutsuwa ilimi tarbiya da sauransu, ita kad'ai! yake ji a zuciyarsa zai rayuwa mai tsayi da ita, ya kai ma'kura a gurin iskancin da yarinyar nan take masa, yana tausaya mata amma ya lura ita bata gani ta daukeshi a matsayin macuci! to yana ganin zai fita daga harkata domin ya samu zaman lafiya. tare da gudanar da aikin dake gabanshi.


*#500 via 0542382124...Binta umar gtbank, idan kati zaki tura ki min magana ta WhatsApp da wannan number... 07084653262........Mutanan Nijar ku tuntunbi wannan number....*
*22796074090* dala dari katin Mov ko airtal
a
1/21/22, 12:28 - Buhainat: *GOJE!*ƒ™†_
ƒ™¤`%’]bq _(SADAUKI OMAR RETURNƒ™«aƒ™.c_)

*BINTA UMAR ABBALEĪ]*

*_MANAZARTA WRITERS ASSOCIATIONƒ™ˆg•æ_KqXk*
_____________________


*MIJINA BAYA IYA GAMSAR DANI*
________________
*_Wannan ba sabon abu bane, da yawa mata suna kuka da hakan cewa duk sanda za suyi rayuwar aure da mijinsu basa samun gamsuwa, matsalar daga shi mijin ne daga zarar ya biya bukatarsa zai tashi, bai damu da damuwar matasa ba, wannan kuskure ne babba! idan kasan baka da cikakkiyar lafiya to kayi hanzarin neman magani domin kana aikata kuskure! mata suna da kawaici da hakuri mussaman a wannan bangaran, duk macan data bud'e baki tafadi wannan maganar to ka tabbata tura ta kai bango! shi aure na mutum biyu ne to kai d'an uwa bai kamata ka ajiye mace a gida don kana ta'kama kana ci da ita ka tauye mata hakkin aure ba, wannan abun shine ginshikin aure domin daga ranar da akace babu shi to matsala ta dinga afkuwa kenan, saboda haka d'an uwa kayi hattara daga ranar daka fahimci cewa ka gaza gurin sauke hakkin matarka, to ka tashi tsaye ka nemi magani, idan kuma kasa taurin kai kace kai lafiyarka lau ba zaka sha magani ba to babu shakka! komai yana iya faruwa..... ke kuma 'yar uwata, kada ki yarda shaid'an ya rimbaceki ki aikata wani mummunan aiki ta sanadiyar wannan matsalar, domin da yawa daga ciki akwai matan da suka famtsama kansu harkar banza, saboda rashin samun kulawa daga mazajensu, akan ki aikata hakan gwara ki rabu da auran ki roki Allah ya baki daidai da rayuwarki_*


FREE PEGE


*21&22*
Hakika baka sanin amfanin mutum a rayuwarka sai ranar da wata musiba ta sameka, ya taimakawa rayuwarta, ita kuma ta daukeshi a matsayin abokin gabarta! tayi masa mummunar fahinta duk da irin taimakon da yake akanta, ni a ganina idan shi din macuci kamar yanda kullum take kiransa ba zata kai labari ba, domin da tuni ya keta mata haddi ya yasar da gawarta a dajin. koda yake kowane dan adam da irin tunaninsa, har yanzu ita tana shakku akansa cewa bashi ne ya sato ta daga gaban iyayenta ba.

Kwanciyarta da kamar minti goma mugun k'aikaiyi ya tasheta, ashe tsutsar data sauka kan kafad'arta tana da dafi! kuma ta cijeta a gurin har ya kumbura sai tsuko! yake mata, yatsunta biyar tasa a gurin tana aikin sosawa amma kamar 'kara angiza kaikaiyin take, fatar gurin tayi jajawur! saboda susa duk ta kwaile.
Hawaye kawai take tana jan hanci! daga wannan sai wannan! ciwuka a jikinta iri-iri! sosai take kuka tana kiran innalillahi-wa'ina ilaihi raji'un!


Ya rage shi kadai a waje yana kai kawo a gurin, har yanzu zuciyarsa taki aminta da gurin, yana ganin kamar idan yaje ya kwanta wata matsalar zata faru! zagaya gurin yake karnukansa na binsa duk inda ya nufa sai koke-koke suke.........Alba ya cimma inda yake tsaye cikin girmamawa yace."Maigida yarinyar nan fa tun dazu ta ishi mutane da kuka."
Yace."Me kukayi mata."?
Da sauri yace."Wallahi maigida babu abunda mukayi mata kawai dai munji tana kuka shine nace bari na sheda maka."

Ya girgiza kansa da fadin." Jeka gani nan zuwa." da sauri ya juya ya tafi.

D'azu ta 'bata masa rai! ya hakura ya shanye amma baya tsammanin yanzu zata kawo masa shiririta ya saurara mata.

Ya sameta sai gursheken kuka take gabad'aya ta cire rigar dake jikinta sai breziya sai soshe-soshe take.

Ganinta a haka ya 'bata masa rai! rashin kamun kanta yana bashi haushi, idan ba hakaba ta san da cewa ita kadai ce mace a cikinsu mai yasa ba zata suturta kanta ba, kullum shike k'okarin ganin ya suturta ta a matsayinsa na namiji amma ita a cikin maza! saboda rashin sanin darajar kai take bude tsaraicinta.

Tsaki mai karfi yaja ya juya yana kallon gurin da ya yaransa ke zazzaune! akwai tazara a tsakanin inda take, baya kuma tsammanin zasu hangeta saboda kafin ya fita sai da ya katangeta.

Murya a sama! yace."Mayar da rigarki." ido gaja-gaja da hawaye! ta kalleshi, ya murtuke fuska! ko alama bata bashi tausayi ba, ya bude mata dukkanin idanuwansa! umarni ya sake bata, a dashe tace." Ka daina yi min tsawa! ko ka san abinda yake damuna."?
Yace"Babu abunda ke damunki sai hauka! da gidadanci! idan ba haka mai zai sanya ki cire riga cikin maza."

Wani abu mai nauyi ya tsaya mata a wuya! wai ace wannan gantalallan ne yake kiranta da mahaukaciya.

Nauyin abunda ya tsaya mata a wuya ya hana ta magana sai uban hawayen dake tsere a saman fuskarta, abu biyu ne suka dameta a halin yanzu.

"Mtswwww! tsaki mai tsayi yaja kafin ya fita da gurin, ya dawo da fitila a hannunsa sai da ya rage karfinta sannan ya tunkari inda take.

Ta sake takure jikinta tana kallonsa yana dube-dube a gurin, rigar ya mika mata da fadin." Kar'bi kisa ko kuma yanzu nayi abinda ba kiyi tsammaninsa ba."

Ta tsira masa ido! da jin shakkar maganarsa, ganin babu alamun wasa a fuskarsa yasa tasa hannu ta kar'bi rigar amma bata sanya ba, ta rike kawai a hannunta tana cigaba da sosa gurin dake mata ciwo.

Ya haskata da fadin." Cire hannuki a gurin! da sauri ta cire! tsigar jikinsa ta tashi! ganin yanda gurin yayi jawur! har da kumburi! zuciyar musulunci, duk sai jikinsa yayi sanyi haka kawai baya so wani abu ya cutar da ita, burinsa bai wuce ya kaita gaban iyayenta lafiya lou ba.

Sassauta murya yayi yace."Sannu yaushe hakan ya faru."? a maimakon ta bashi amsar tambayarsa sai kawai ta sake rurucewa da kuka!!

Yatsansa yasa saman bakinsa da fadin." Shiiiiii." kukan bashi da amfani kiyi shuru zan taimaka miki."

Ba tayi shuru ba kuma bata daina kallonsa ba, yace."Kina bukatar hakan ko."?

Kamar wata sakarai ta daga mai kai!

Yace."To ki zama jaruma! ki daina yawan kuka bashi da fa'idah."!

Taji kamar ta kai masa duka! ta'ina zata iya daure wannan azabar!

Fita yayi da kamar minti biyar ya dawo da magani a hannunsa. yayi zaman ra'kuma a gabanta cikin muryar da ya saba rarrashinta ya mi'ka mata maganin da fadin." Jarumata! kar'bi maganin ki shafa a gurun zai daina miki ciwo."

Maganin ta kar'ba ta lakato a yatsanta, can bayan kafad'arta gurin ciwon yake ta daga hannu sosai tana kokarin shafawa hannunta ya gaza kaiwa!
Ganin haka yasa ya kar'bi maganin daga hannunta ya lakato kan yatsansa, ya kalleta da fadin." Kin bani izini."?
Shuru tai masa.

Ya sassauta murya yayi da sake maimaita maganarsa.

Kai kawai ta iya daga wa gabadaya jikinta ya mutu! ya lalubi gurin yana shafa maganin a hankali yana sake kwantar mata da hankali da cewa gurin zai daina ciwo insha Allah!

Ido kawai ta lumshe tana jin maganganunsa sama-sama a cikin kunnanta, har ya gama shafa maganin fuskarta ya dan kalla sai yayi sauri ya janye idonsa jin yanayinsa na neman sauyawa, gefe ya matsa tare da sassauta murya ya kirayi sunanta............ *GIMBIYA!* a kasalance ta bude idonta! tana kallonshi , tana masifar son taji ya kira ta da wannan sunan. yace."Sannu ki kwanta ki huta na shafa miki maganin." Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta zame ta kwanta tana tattakure guri daya, Shima ajiyar zuciya ya sauke kafin ya lalubi wani zani mai kauri ta fara k'okarin rufa mata a jiki akayi rashin sa'a gwiwarsa ta zame ya fad'i kanta! fuskarsu ta hadu! da sauri yayi gaggawar rabuwa da jikinta yana bata hakuri! uffan ba tace ba asalima lokacin da hakan ya faru idonta a rufe yake.

Ganin tayi shuru ba tace masa komai ba yasa a gaggauce ya fita yana auziyya a zuciyarsa, be san me yasa ba kullum zuciyarsa take kwadaita masa wasu gurare na jikinta, a duk sanda zasu kasance a guri daya yakan rasa nutsuwarsa.

Itama anata bangaran hakane, har yanxu idonta a rufe yake ta rasa abinda yake mata dadi! yanda yake sassauta murya yana rarrashinta yakan karya mata garkuwar jiki, tana jin dadin hakan sosai, a rayuwarta tana masifar son namiji wanda ya iya soyayya, bayan haka kuma bata san lusarin namiji tafi son tsayayye shiyasa wasu lokatan yake birgeta domin dik ya tara abubuwan da take bukata.

Ajiyar zuciya ta sauke tare da jan zanin daya rufa mata ta rufe gabadaya jikinta harda fuskarta, addua take a zuciyarta Allah ya sa bacci ya dauketa. Cikin ikon Allah kuwa bacci mai nauyi ya dauketa................

Kamar a mafarki! ta dinga jin ihu!!! da hayaniya tare da kukan karnika! da karar wu'ka'ke! a firgice ta tashi tsaye! tana bin gurin da kallo, babu kowa duk sun fice! yanda 'kura! da guguwa! take shigowa har gurin da take shi tabbatar mata da cewa babu lafiya!

Fitowarta daga gurin yayi daidai da tashin bomb! gabadaya gurin ya kacame! ya hargitse! da hayaki! da rarrafe ta koma katangaggen gurin ta takure guri daya tana kiran sunan Allah.

Ta jima a haka kafin ta dago kanta, still tana jiyo hayaniya da kuwwa! tare da kukan karnika! ga wani irin b'akin hayak'i! da ya turnuke! a gurin!

Hannu tasa ta toshe hancinta tare da sake takurewa a guri daya jikinta in banda rawa babu abunda yake, bakinta sai motsi yake adduar yaye masifa takeso tayi amma bata iya ba, sai kawai ta dingi nanata innalillahi da karfin gaske!

Hakan ya janyo hankali d'aya d'aga cikin yaran *uban daba* wanda yake shawagi a gurin...........Gurin ya shiga yana zazzare ido! ita kuma ganin b'akuwar fuska yasa ta sake rikicewa! shi kuwa murmushin farin ciki yayi ya nufeta da saurin gaske!

Hannunta ya fizgo! ta turje! tana rirrike itaccen dake katange da gurin, kuka take tana rokonsa yayi hakuri, ya d'auke fuskarta da mari! da tafkeken hannunsa!! a take hancin ya fashe! ya dinga tsiyayar da jini!

Jaýÿÿÿ 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~nta yake tana turjewa da bashi hakuri cewa bata da laifi itama sato ta sukayi, ya sanya kan k'otar lafceciyar wu'kar dake hannunsa ya dinga bubbuga mata a gwiwa, lokaci guda ta galabaita! ta zube a gurin! d'aukarta yayi ya sa'ba a kafad'a ya fito da ita. kai tsaye mafarkarsu ya nufa da ita a kafad'arsa.............


Tashin hankali kenan! lokacin daya hangeta sa'be a kafardar gardi! sai da wukar hannunsa ta subce! ta kusa fad'uwa amma yayi muzzakaracin riketa da kyau a hannunsa!! Wani uban ihu! ya kurma! wanda ya razana! abokan fad'an nasa suka ranta ana kare, amma ina! basu samu nasara ba, sai da ya kama su, ya sanya wata narkekiyar igiya ya daure musu hannuwa da kafafu!

Gabad'aya gurin ya hargitse! sakamakon bomb din da ya tashi, yayi sanadiyar kona biyu daga cikin yaran shi, suna kwance magashiyan! rai a hannun Allah...... Duk da cewa sune suka samu nasara amma beso wata matsala ta afku da yaran sa ba..

Ya kallesu gabad'aya kammaninsu ya sauya hatta da fuskokinsu sun rine! da baki! sakamakon tashin bomb din, wannan ce hanya mafi sauki da abokin hamayyar ya samu nasara a kansa!

Ya kallesu da fadin." Yayi imani! da cewa idan ya tunkari inda muke da wu'ka ko wani abu makamancin haka ba zai samu nasara akanmu ba, wannan shine dalilin daya sanya shi jefo mana bomb! ba tare da munyi tsammanin hakan ba, to Alhamdullhi duk da hakan be samu nasarar da yake bukata akanmu ba, yanzu kalubalan dake gabanmu tunkarar sansaninsa domin gwabzawa a tsakanimu, babu yanda za'ayi mu tafi mu bar masa wannan yarinyar da yayi nasarar dauke mana ita, duk da cewa tsintar ta mukayi akan hanya bamu san daga ina take ba, hakan ba zai sanya mu bar masa ita ba, duk yanda za'ayi sai mun samu nasara a kansa."

Da yawa daga cikinsu sun tausaya mata, amma wasu sun kalubalanci maganarsa! bai ta'ba sanya kara sun tsallake ba, amma da alama akwai wa'inda za suyi masa tawaye a cikinsu.

Ya dinga kallonsu yana nazarin yanayinsu, yace." Babu wanda zan tursasa! cewa ya take min baya! a cikunku. zan iya tunkarar sansanin ni kadai! ba tare da kowa ba! saboda haka wanda yake ganin zai bi bayana bisimillah." Yana gama maganarsa sai yayi gaba, wasu suka bi bayan shi da sauran karnukan! dake raye, wasu kuma suka tsaya suna surutai da mai da magana a tsakaninsu!


*Free pege ya kusa karewa a daure a biya kudin karatuƒ™¹jƒ™Ž_ don Allah idan kin san ba siyan littafin nan zaki ba kada ki dauki number ta kiyi min magana*


*#500 via 0542382124...Binta umar gtbank, idan kati zaki tura ki min magana ta WhatsApp da wannan number... 07084653262........Mutanan Nijar ku tuntunbi wannan number....*
*22796074090* dala dari. katin airtal ko mov.
1/21/22, 12:28 - Buhainat: *GOJE!*ƒ™†_
ƒ™¤`%’]bq _(SADAUKI OMAR RETURNƒ™«aƒ™.c_)

*BINTA UMAR ABBALEĪ]*

*_MANAZARTA WRITERS ASSOCIATIONƒ™ˆg•æ_KqXk*
_____________________


FREE PEGE

*23&24*
*Biyu da rabi na sulusin dare!*
Cikin firgitaccan yanayi ta tashi zaune tana kiran sunan Allah! hakan ya janyo farkawarsa dama can bashi da nauyin bacci, zaune ya tashi kafin ya rike hannunta dake wani irin rawa, yace."Menene Aysha."? Sai kawai ta fashe da wani irin kuka ta rungumeshi tana girgiza kai da fadin." Zinat ce ranka ya dade yarinyar nan na cikin mugun yanayi Allah ya nunan hakan a mafarkina."

Sake rungumeta yayi a jikinsa cikin sigar rarrashi yace."Aysha mafarki ba gaskiya bane kada ki gazgata abinda ki ka gani, bana tsammanin cewa mafarkinki zai tabbata, jikina yafi bani cewa yarinyar nan tana a raye kuma daf take da ta dawo garemu da ikon Allah."

Kallonshi tayi hawaye na tsere a saman fuskarta tace.''Ranka ya dade koda Allah ya nufa yarinyar nan ta dawo gida bai zama lallai a sameta da cikakkiyar lafiya ba ka san dai yanda duniyar nan ta lalace da rashin gaskiya wannan shine babban tashin hankalina."

Ya sauke ajiyar zuciya da fadin." Kada ki fadi haka Aysha! zuciyarki ta dinga halarto miki alkairi akan yarinyar nan! adduarki a gareta karbabbiya ce a gurin Allah, kada ki yarda zuciyarki ta yarda da wannan mafarki ki dauka cewa k'anzon kurege ne, a yanzu abinda zakiyi ki faranta min shine ki tashi kije ki dauro alwala ki gabatar da nafila a gaban ubangiji kana ki mika masa kukanki."

Ta sauke ajiyar zuciya da jin sassauci acikin zuciyarta, a hankali ta zame jikinta daga nasa ta sauka daga gadon ta nufi toilet domin daura alwala.

Tana fitowa shima ya tashi ya shiga ya daura alwalar ya fito, lokacin har ta tayar da sallar, jallabiya da gajeran wando ya sanja kana ya gyara dadduma shima ya tayar da tashi sallar.


******
Tun bayan daya sa'ba ta a kafad'a suke buga artabu a tsakanisu, rikon tsauri! yayi mata yana gudu tare da tsallake manya-manyan dutsina da ita a kafadarsa! tayi duk wani kokari gurin ganin ta ceci kanta abun yaci tura! domin mutumin mugun basamude! ne wanda cizo da yakushi basa shigarsa! dukansa take tana cizo duk ta dauke masa fata amma ko ajikinsa, ya riketa katamau! yana gudu! burinsa kawai ya kaita gaban ogansa ya san hakan zai faranta masa rai.

Hakan ne ya kasance kuwa, Ogan nasu yana cikin bacin rai! mai tsanani sakamakon rashin samun nasara! bai ta'ba fuskantar irin hakan ba sai a wannan lokacin, kai kawo kawai yake gurin ya rasa abinda yake masa dadi! ............Amma zuwan babban yaron sa da yarinyar ya faranta masa rai! mutuka, sai kawai ya kwashe da wata 'yar iskar dariya kafin yayi wani irin tsalle! da juyi na jin dadi, ya zuba mata kwala-kwalan idanuwansa!

Bakinsa kawai yake lasa, jikinsa na wani irin tsuma! komai na yarinyar yayi cif da cif! bata da makusa, cikakkiyar mace irin wacce ya jima bai kwanta da irinta ba!

Gurin ya tsit! gabad'aya yaransa sun zagayeta motsin kirki ta kasa, kanta ne ma

Please Login or Register in order to submit comment