Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yake juyawa a gurin, dishi-dishi! take kallonsa har ya karaso inda take zube!

Ya tsugana kusa da ita, sai tayi saurin janye jikinta, ya sha kunu; tare da matsawa jikinta, ta sake janyewa tana watsa masa mugun kallo!

Mahaukaciyar dariya yayi! ya cigaba da lasar lebansa, yana bin sassan jikinta da wani irin kallo na tsantsar sha'awa! Hannu ya kai jikinta, a zabure! ta fitar da hannu ta bashi kyakykyawan mari a fuskarsa! ko gezau! beyi ba sai dai yaransa da suka zabura! sukayi kanta!

Ya daga musu hannu da basu umarnin matsawa baya.

Suka matsa can nesa suka bar shi da ita, zaman dirshan yayi a gabanta ya mika mata tafkekiyar fuskarsa dake cike da kasumba! yace. " Idan hakan yana miki dadi ki sake aikatawa." Ya fada yana sake tura mata fuskar.

Tsaki mai tsayi taja! ta matsa nesa dashi! ya rarrafa kan gwiwarsa ya cimma inda take! kafafunta dake daure da takalmi ya tsirawa ido, babu abunda yafi tafiya dashi irin shara'ban kafafunta, ya kai hannunsa gurin yana shafawa da lumshe ido, janye kafarta tayi da fadin." Allah ya isa!!
Ya bude idanuwansa da suka rikice! da zazzafar sha'awarta!

"Ni kikewa Allah ya isa."? yafada yana nuna kirjinsa.

Ba ta amsa ba, wani irin kallon banza take mai, ya lumshe idonsa ya bude da fadin." Ina sonki saboda kinyi min, ban ta'ba amfani da mace na maimaita ba, amma gani guda da nayi miki naji cewa kece zaki zama mahadin rayuwarta, shekaru sun ja ya kamata ace nima na ajiye k'wai a duniya kece zaki zama uwar 'ya'yana, kinzo hannuna babu wani mahalukin daya isa ya rabani dake."

Maganganunsa suka dinga amsa kuwwa! a kunnanta, ta tsira masa ido tana mamakin furucinsa, kallonsa kawai take ta rasa yanda zata fasaltashi, shi ba mutum ba ba aljan ba.

Ya mike tsaye a kanta! saurin kauda kanta tayi gabanta na lugudan duka!

Blet din dake daure a kugunsa ya fara kokarin kwancewa, tayi saurin tashi tsaye! dariya ya fashe da ita, kafin ya cire blet din ya jefar dashi ya zame wandon............"Innalillahi- wa'ina ilahi raji'un! abinda ta ambata kenan, ta rintse idonta da karfi! tunda take bata ta'ba ganin tsaraicin namiji ba sai a kansa, yanda yake mara fasali to hakama gabanshi yake tamkar na mahaukacin doki!!

Wandon ya mayar jikinsa, yana kyalkyala dariyar hauka kafin ya fizgo kafadarta! fuskarta ya rike a cikin tafin hannunsa, ta rufe idonta gam! bata son kallon mummunar fuskarsa.

"Ina fatan kin shirya zama tare dani! masoyiyata nayi miki alkawarin baki dukkan wani jin dadi na duniya! gwarzo ne ni akowane fanni! na tabbata cewa ba za kiyi nadama da kasancewarki a tare dani ba."

Zuciyarta ta dinga tashi sakamakon warin bakinsa, fuskarta ta fizge! da karfi ta matsa can gefe tana numfarfashi! yawu ya cika mata baki! yana zuwa gurin da take ta fesa masa yawun a fuskarsa!

Ya sanya hannu ya shafo yawun yana lashewa! amma kuma fuskarsa ta rikide da alama yaji haushin abinda tayi masa.

Sai da ya lashe yawun tsaf! sannan ya kalleta, ta tsorata da yanayinsa, sai ta sunkuyar da kanta, a kausashe! yace." Wannan shine na farko kuma shine na karshe kada ki sake maimatawa idan ba hakaba zan ladabtar dake.

Ta cire tsorosa da fadin." Wawa!! kafara ladaftar da kanka kafin ka ladaftar da wani."

"Wawa!! kalmar tayi mai ciwo! sosai a ransa sai kawai ya dingi maimaita kalmar a fili yana zagayeta, ta dinga binsa da kallo duk inda yayi, ya shammaceta yasa mata kafarsa ta fadi a kasan a gurin! turmusheta yayi ya danneta iyakacin karfinsa! bakinta yake kokarin sumbata tana kautar da kai yana bin duk inda ta nufa, be fasa maimaimata maganar ba! suka dunga bugawa! domin duk yanda yaso hada baki da ita ya gagara! ta gumtse bakinta gam!!! sai ya zama kamar mahaukaci sai rawar jiki yake babban burinsa yaji yana shan bakinta.................Ba zato! ba tsammani! yaji saukar kibiya a gadon bayansa!!

Ya gantsare! tare da zabga ihu!! a zabure! ya mike tsaye! ya fizge! kibiyar ya jefar jini ya fara tsiyaya! tashin hankali kenan! waige-waige yake a gurin yana mamakin yanda akayi hakan ta faru.

Cikin zafin nama! ya mikar da ita tsaye sai numfarfashin wahala take, ya rike hannunta katamau! yana sake dudduba gurin!..................!

Wani abu dake daure a hannunsa ya murza! kafin ya kirayi yaran sa! kaf! suka kewayeshi! sai dai ganin jini na tsiyaya a bayanshi ya firgitasu! a garin ya akayi hakan ta faru!
Ya akayi ogansu ya bari aka cimmasa irin haka? a tarihin rayuwarsa kaf babu wani mahalukin da ya ta'ba fitar masa da jini sai zuwan wannan matashin saurayin lallai akwai wani abu da yake shirin faruwa!


Wani irin nishi! yake yana zazzare idonsa! shi kansa yayi mamakin al'amarin, yana da suddabaru! iri-iri! ya akayi har yaron ya samu damar ganin inda yake tare da samun damar harbinsa da kibiya!!

Sai kawai ya fasa ihu!!! ya dubi abunda ke daure hannunsa yana wasu irin surutai! ya sake murza abun! yana sambatu! gurun yayi tsit! babu mai kwakwkwaran motsi a cikinsu, domin sun shiga rud'ani da faruwan wannan al'amarin!!

Sautin muryarsa ne kawai yake tashi a gurin, yana wasu irin maganganu!..............Can kuma sai haushin karnkuna! ya maye gurbin maganarsa, Tsit! yayi gabansa na wani irin fad'uwa!!

Hankalinsu ya kai kololowa gurin tashi!! duk suna tsaye sun kasa tabuka! komai ya zabura! da karfi yace."Tsayuwar me kuke ba zaku ba zama ba har sai ya cimma na."

Da sauri suka rarrabu a cikin dajin suna neman inda yake..

Yana tsaye! a gurin sai kace dasashe! har yanzu kuma hannuta yana rike a hannunsa ya rike tamau!!


Haushin karnukan! suka cigaba da kusantowa inda yake! da saurin gaske ya fara kokarin janta tana turjewa! kawai sai ya dauketa ya sa a kafad'a, ya riketa da kyau! da niyyar neman mafaka! taku daya yayi yaji saukar wata kibiyar! ya gantsare! tare da sakin ihu!! amma duk da haka bai sauketa ba.


*"Ni ne GOJE!!! mugun! makangari sai kuree! Ni cinkun! naci garina kuma ni ke zuwa garin wasu yaki!! kandagarki kurmar dutse! mugun makangari sai kureee!*

Sautin maganarsa ya cika dajin gami da kunnuwansu.

Ya juya gabas kudu yamma arewa! domin hasashen inda maganar ke fitowa, bashi da tabbacin gurin, kawai sai ya umarci sauran wa'inda ke tare dashi cewa su tashi bomb a kowanne sassa na gurin!

Hakan ne kuwa ya faru tashin bomb! sukayi a gurin kowane sassa a dajin ya rikice! da hayaki! wannan damar ya samu yayi dirar mikiya! a gabansa! alokacin da yake kokarin neman mafaka.

Kallon kallo aka fara! Zinat kam ganinsa ya sanyata sauke ajiyar zuciya ta shiga godewa Allah!!!

Ido ya tsirawa! hannunta dake cikin nasa. wata kibiyar kishi ta sokeshi! cikin hargagi! yace."Sakar mata hannu ko na sheka da kai barzahu"!!

Ya tsira masa jajayen idonsa kafin ya fashe! da dariya ya sake rike hannunta da kyau! Yace." Kai ne dan iskan da kake ganin ka isa kayi gogaggaya dani ko.!

Yace" Eh ni ne UMARU! kuma ni zan kawo karshen ta'addancinka."!!!
Kaifaffar wu'kar dake rataye a jikinsa ya cire ba tare da zato! ba ya datse! masa hannu wanda yake rike da nata! hannun tun daga kafada har kan yatsu ya fadi a gurin yana wutsil-wutsil, jini kuwa sai tsartuwa yake! ya durkushe! a gurin, yana wani irin ihu!!!!!!

Kafin kice kwabo! kaf! kowa ya hallara a gurin, ganin ogansu a durkushe! babu hannu ga jini na zuba ya zaburar dasu! sukayi kansa! sai yayi gaggawar soka wu'ka a wuyan ogan nasu!!! *Uban daba!* ya sake rikicewa! domin bai shirya mutuwa ba, da hannu yayi wa yaran sa alama cewa su ajiye makaman dake hannunsa, sukayi yanda ya umarcesu!

Ajiye makamansu keda wuya suka fara jin jiniya alamun jami'an tsaro sun shigo gurin!!!! *Uban daba!* hankalinsa ya sake tashi, babu shakka ya san ya shiga hannun hukuma k'aryarsa ta kare! sai kawai yayi kwance-kwance ya shammaceshi! wani wawan duka ya sakar masa a gwiwarsa!. dukan ya shigeshi! sosai yayi taga-taga! zai fadi wannan damar ya samu ya k'wace! daga hannunsa a sukwane! ya bar gurin cikin wani irin gudu na ceton rai! sauran yaransa suka rufa masa baya...........!

Zubewa yayi k'asan gurin ransa a masifar bace! kwata-kwata bai so hakan ta faru ba, amma ba komai tunda har ya samu nasar raba shi da hannunsa guda, watarana zai samu babbar nasara a kansa!

Tsinin bindiga! yaji a saman kansa! da sauri ya bude idonsa sai kawai yayi arba da zaratan! sojoji da 'yan sanda! sun zagaye shi kowanne ya saita shi da bindigar dake hannunsa.........."Babban cikinsu shine yayi magana ."You under arrest."! Hannuwansa ya daga sama cikin bin umarni, suka d'aura masa zabgegiyar tsar'ka! kafa da hannu suka sa key suka kulle, kafin su mikar dashi tsaye....!



*#500 via 0542382124...Binta umar gtbank, idan kati zaki tura ki min magana ta WhatsApp da wannan number... 07084653262........Mutanan Nijar ku tuntunbi wannan number....*
*22796074090* dala dari katin airtal ko mov.
1/21/22, 12:30 - Buhainat: *GOJE!*ƒ™†_
ƒ™¤`%’]bq _(SADAUKI OMAR RETURNƒ™«aƒ™.c_)

*BINTA UMAR ABBALEĪ]*

*_MANAZARTA WRITERS ASSOCIATIONƒ™ˆg•æ_KqXk*
_____________________




*RASHIN ADALCI A TSAKANIN MATA*
___________
_*Mata da yawa su kanyi kukan rashin adalci da mazajensu keyi a tsakaninsu. maza kuji tsoron Allah kuyi adalci a tsakanin matanku. lallai wajibi ne kuyi adalci tsakanin matayenku ga wanda yake auran mace sama da d'aya dole yayi adalci, ya sani cewa dukkan abinda yake gudana Allah yana sane kuma yana ganinsa, kuma wallahi sai Allah ya tambayeshi akan zaman da yayi dasu a goben kiyama.*_

*Manzon Allah SAW yana cewa." (Dukkan wanda yake da mata biyu sai ya karkata ga daya baya yiwa dayar adalci, to zai zo ranar alkiyama bangaran jikinsa guda a shanye)*

*Malamai sunce karin aure ba wajibi bane, ba mustahabi bane ga wanda yake da ikon ya 'kara amma wajibi ne kayi adalci, idan har kasan ba za kayi adalci ba to kada ka fara neman k'ara auran ma domin k'arin zai iya kai ka zuwa ga halaka.*
*Manzon Allah SAW yana cewa." (Dukkaninku masu kiwo ne kuma dukkan ku abin tambaye ne akan abinda aka baku kiwo a gobe kiyama)*
*Allah a cikin alkur'ani yayi hani akan kada maigida ya karkata gabadaya zuwa ga wata daga cikin matansa ya kyale sauran matan saboda rashin adalci*
*Allah ya baku ikon adalci a tsakanin matayenkuƒ™¹jƒ™Ž_*




FREE PEGE
*25&26*
"Kada ku yarda ku bari ya kubce daga hannunku, mugu! ne macuci! ya jima yana ta'addanci a k'asa! kuyi masa hukunci mai tsauri! domun da bakinsa yake fadin cewa yafi karfin hukuma! yau tsayin kwana shida kenan daya raba ni da iyayena yayi kidnapping dina domin samun makudan kudi daga gurin mahaifina, " Sunana ZINATU ni 'yar asalin jahar kano ce mahaifina kuma shine sarki dake kan kujerar mulki a jahar." Bilhaki da gaskiya take maganar.

Gabad'aya hankalinsu ya koma kanta a lokacin da take wannan maganar, da yawa daga cikinsu ba su lura da ita ba, maganarta ce ta janyo hankalinsu kanta. ganinta a firgice babu sutturar arziki yasa suka gazgata maganarta, babban cikinsu ya kwantar mata da hankali da cewa komai yazo karshe kuma sunyi alkawarin kaita gaban iyayenta idan sun gama gudanar da binkice.

Beyi mamaki da jin furucinta akansa ba, ita kad'ai ce zata bada cikakkiyar sheda a kansa, amma ba tayi hakan ba, to ba zai tsananta ba, ba kuma zaiyi jayayya da hukuma ba, zai bi doka da odar amma ya san ita gaskiya d'aya ce kuma a kanta yake babu gudu babu ja da baya babu shakka! Allah za bayyana mai gaskiya.

Da kansa ya haura ya shiga motar ya zauna, sojoji uku suka zauna hagu da damanshi, ya kalli na hannun damansa cikin nutsuwa yace." Akwai sauran yarana da suke n........ ya katseshi ta hanyar buga masa tsawa da fadin.

"Rufe mana baki ko kai zaka nuna mana aikinmu."? Kansa ya girgiza, yace." To kabi umarnin mu domin shine samun zaman lafiyarka."

Be sake cewa komai ba ya kauda kansa gefe yana hangensu suna ta binkice a gurin...........Can ya hango sun taso sauran yaransa a gaba! suna dukansu! bai dauke idonsa ba har sai da suka karaso gurin, gabadaya sun galabaita domin wasu harda rauni a jikinsu bayan wa'inda suka kone sakamakon bomb din daya tashi, ya tausaya musu sosai, domin ya san shine mujaza! domin da yawa daga cikinsu ba'a son ransu hakan ta faru ba.

Suka dinga turasu cikin motar suna dukansu da wata murtukekiyar bulala irin ta karfe!

To duk iya binkincensu a gurin Allah bai nuna musu dungulmin hannun *Uban daba!* da 'kasa ta turbudeshi a gurin ba, Yana kallonsu suka 'karaci dube-dubensu suka shishshiga mota da niyyar fita daga dajin.

'Bude baki yayi da niyyar magana kawai ya hangota tare da wani soja yana kokarin bude mata gaban mota domun shiga........Yaji wani irin ciwo a cikin ranshi! bakinsa ne yayi nauyi ya gaza furta maganar dake cikin cikinsa har suka fita daga cikin dajin bai dago kanshi ba! wani irin kuttun bakin ciki ya tsaya masa a wuya, tunda yake bai ta'ba ganin butulu irinta ba.

Da yayi motsi zasu saita shi da bindiga! da fadin." Ya kiyaye idan kuma yayi wani yunk'uri na gudu to zasu harbe shi! murmushi kawai yake musu, wanda hakan ke 'kara tunzura musu zuciya.

Labari kaf ya cika garin Katsina da kewayenta cewa A yau 11/3/2007 jami'an tsaro sunyi nasarar kama babban dan ta'addah nan wato *Mashekin daji!* wanda ya addabi k'asa da jama'ar dake cikinta.

Headquarter 'yan sandan kuwa cike take da 'yan jarida da jama'ar gari masu ganin kwal uwar daka.


Koda motocin jami'an tsaron suka shiga headquarter 'yan sandan sai gurin ya hargitse da hayaniya kowa burinsa yayi ido hudu dashi, Mussaman 'yan jarida masu daukar rahoto.

Sai da suka rufe masa fuska sannan suka fito dashi a dadd'aure! Suka rirrikeshi da kyar yake cire k'afa sakamakon sark'ar da tayi masa dabaibayi!

Duk da hakan sai da yan jaridan suka dinga daukar hotonsa tun daga sama har kasan Kafafunsa, da yawa daga cikin 'yan jaridar da jama'ar dake gurin sunyi mamakin ganinsa ingarmar namiji a labari dai sun san cewa ba haka kammaninsa yake ba gajere ne mara fasali ya akayi kuma a zahiri basu ga haka ba.

Har sai da aka shiga dashi ofis din Asp sannan kowa ya watse, jama'ar gari suka tafi da zancan a bakunansu, su kuma 'yan jarida suka fara gudanar da ayyukansu.


****
Cikin tsananin tashin hankali Saude matar Alba ta shiga gidan tana kuka hannunta rike da jarida.

Uwale ta tare ta tana tambayarta abinda ke faruwa.

Jaridar ta nuna mata da fadin." Uwale kin san abinda yake faruwa kuwa."? ta kar'bi jaridar tana dubawa tace." Saude kin san ban iya karatu ba me yake faruwa."

Tace."Ki duba hoton jiki mana Mijina Alba ake tuhumarsu da ta'addanci."

Gabanta ya fadi! tace." Ta'addanci kuma Saude! su da suka tafi farauta mai ya hadasu da ta'addanci inace gobe zasu dawo."

Saude na kuka tace." Uwale kisa kunne da kyau ki saurari jawabin da zanyi miki."

Jiki a sanyaye tace." Ina sauraranki."

"Jami'an tsaro ne suka kama UMARU wato jikanki dashi da yaransa saboda zargin da ake musu na ta'addanci, a yanda na karanta rahoton cewa wai ana tunanin shi UMARU shine wannan d'an ta'addan da ya addabi kasa! yanzu haka dai gabad'ayansu suna hannun hukuma! jama'a da yawa sunyi imani da cewa hukuncin kisa za'ayi musu."

Hankalinta ya tashi sosai sai ta fashe! da kuka ta tsirawa hotonsa ido duk da fuskarsa a rufe take hakan be hana ta ganeshi ba, ta tsirawa kafafunsa ido tana wani irin kuka tace." UMARU wannan ranar nake gudu a gareka, itace rana mafi muni da ba zan ta'ba mantawa da ita ba, ashe tsautsayi ne ya sanya ka tsunduma kanka wannan harkar, ni na san halinka UMARU kuma zan bada sheda a kanka, ka taka sawun 'barawo insha Allah sai Allah ya wanke ka daga zargin da ake maka." Kuka sosai takeyi hawayenta duk ya jika takardar dake hannunta.

Hamra'u ta shigo gidan cikin kuka na fitar hayyaci! tana zuwa ta rugumeta da fadin."Uwale ya za muyi da wannan kaddara hukuma ta kama Yayana da laifin ta'addanci! bayan bashi da laifi Yayana bashi da mugunta baya cin hakkin wani burinsa kullum ya za'ayi k'asa ta samu cigaba, amma ya taka sawun barawo jami'an tsaro sun kamashi dumu-dumu a cikin sansanin da *Uban daba!* yake zaune da jama'arsa, Uwale ya za muyi bamu da kudi bamu da ikon da zamu tunkari hukuma! domin kalubantar zargin da sukeyi akan wanda bai ji bai gani ba."

Tace."Hamrau bamu da komai wanda zamu tunkari hukuma dashi, amma muna da Allah shi kadai zai ne zai mana jagoranci Allah ba azzalimin sarki bane yana tare da masu gaskiya insha Allah cikin hikimarsa zai bayyana mai gaskiya."


Asp Musa Baharu shine shugaban 'yan sandan jahar, kuma duk wani jami'in tsaro a karkashinsa yake, mutumin yana da hankali da nutsuwa gami da sanin makamar aiki, koda aka shigar masa dashi ofis din kallo daya yayi masa ya tabbatar da cewa bashi suke da bukata ba, amma be nuna hakan a zahiri ba, sai kawai ya bawa wa'inda suka shigo dashi umarnin fita, ya rage su biyu kacal a ofis din.

Shi baya ganin komai saboda har yanzu fuskarsa a daure take, amma shi Asp din yana kallon duk wani motsinsa.

K'ira ne ya shigo wayarsa, daga gidan gwamnati , cikin cikin girmawa ya daga da fadin." Ranka ya dade barka da wannan lokaci."

Mai girma governor yace." Barka dai Asp barkanmu da samun nasara! wannan ranar ba zamu ta'ba mancewa da ita ba, yana kuma da kyau ayi rubutu na mussaman domin ajiyewa a kudin tarihi."

Asp ya d'anyi murmushi da fadin." Hakane ranka ya dade, labarin samun nasara ya cika gari da sauran garuruwa jama'a da yawa sun kirayi waya suna yi mana murna! amma ban san me yasa ni nake shakku! akan hakan ba."

Mai girma governor yace." Asp wannan wace irin magana ce? da farko kafin isowar rudunar da muka tura kaine ka kirayi wayata kake sheda min cewa an samu nasara ya za'ayi kuma yanzu kace na shakku akan hakan."

Gilashin dake idonsa ya cire ya ajiye saman tevur din dake gabansa, ido! ya tsira masa yana sake nazartarsa, yace." Ranka ya dad'e ni da kai da sauran jama'ar gari bamu ta'ba ganin *Uban daba!* a zahiri ba, sai dai muna hasashe akansa cewa shi din wani irin mutum ne mara fasali sanin hakan ma ya samo asali ne daga bakin d'aya daga cikin yaransa da Allah ya bamu ikon kamawa a shekarun baya, shine yake sheda mana kammaninsa, a lokacin da al'amarin ya faru, banyi 'kasa a gwiwa ba na samu yaron daya haddace zane ya zana min kammaninsa domin samun sauki gurin binkice a kansa, amma abin mamaki! a yanzu wanda yake gabana a yanzu kuma muke hasashen cewa shine wanda muke nema ruwa a jallo kammaninsa yasha bambam! da wannan hoton zanen da nasa aka zana min a shekarun baya."

Mai girma governor yace." Asp ya akayi hakan ta faru? kana so ka sheda min cewa bashi bane."?

Ya mi'ke tsaye da wayar a kunnasa, kujerar ya janye ya fito daga tsakankanin kai tsaye inda yake zaune ya nufa!.......Yana wayar yana kokarin kwance masa fuska dake d'aure.

Tsaf ya warware d"aurin fuskar, idanuwansu suka hadu guri guda, kujera yaja ya zauna suna fecing din juna.

Ya cigaba da cewa." Gani gashi a halin yanzu kuma yanzu zan dauki hotonsa na turo maka dashi domin ka sheda maganata, amma duk wani binkice zanyi a kansa domin samun tartibiyar magana."

Mai girma governor ya sauke ajiyar zuciya da fadin." Okey to babu damuwa ina tsumayinka." sallama sukayi kafin ya kashe wayar, ya tsira masa ido! shima nasa idon ya tsira masa suka dinga kallon kallo suna nazarta juna, shi Asp din shine ya fara janye idonsa daga kanshi, ya jima kanshi a kasa kafin ya dago ya sake mai da idonsa gareshi yace." Inaso naji cikakken sunanka gami da jin asalin tarihin rayuwarka."?




*#500 via 0542382124...Binta umar gtbank, idan kati zaki tura ki min magana ta WhatsApp da wannan number... 07084653262........Mutanan Nijar ku tuntunbi wannan number....*
*22796074090* katin mov ko airtal.
1/21/22, 14:07 - Buhainat: *GOJE!*ƒ™†_
ƒ™¤`%’]bq _(SADAUKI OMAR RETURNƒ™«aƒ™.c_)

*BINTA UMAR ABBALEĪ]*

*_MANAZARTA WRITERS ASSOCIATIONƒ™ˆg•æ_KqXk*
_____________________


FREE PEGE

*29&30*
Kusan a tare suka d'auke idonsu daga barin kallonta, Asp din yayi magana amma shi uffan bece ba har ta gama harare-harare! ta fita daga ofis din. Ya d'an ja k'aramin tsaki da fadin." Yarinya nan babu tarbiya a tattare da ita duk kuwa da cewa ta fito daga tsatso mai kyau, ba ta gaji dattako da karamci irin na mahaifinta ba, duk da ba a garin kano muke zaune ba muna da labarin dattakon mahaifinta mutum ne mai karamci da mutunci yana aiki da hankali da ilimi yana kuma gudanar da mulki a bisa tsari na isalama."

Beso ya tanka a cikin al'amarin yarinyar ba amma ganin yanda Asp din yake jaddada maganar yasa yace." Akwai irinsu da yawa wa'inda suka dauki mulki wata tsiya idan akace mahaifinsu nada sarauta ko wani muk'ami sai su dauki girman kai su dora a kansu suna ganin babu wanda ya isa dasu, hakane maganarka mutumin kwarai yana iya haifar baragurbi acikin al'umma jarabtace kawai daga Allah.'' Yace." Kwarai kuwa wannan haka yake sai dai kawai mu roki Allah ya shirya mana zuria baki d'aya." Ya amsa da ameeen ya Allah.

Shuru na minti biyu ya ratsa gurin, cikin 'yar tsokana Asp din yace." Akwai abinda na manta ban tambayi *MAI DAWA!* ba."?
Murmushi yayi da fadin." Akwai sauran tambayoyi kenan."? Girgiza kai yayi da fadin." Tambaya daya ce shin kana da iyali kuwa.''?

Girgiza kai yayi gami da dan ta'be bakinsa.........Asp ya dan zare ido da fadin." Kana nufin babu iyali kenan."
Kai ya daga masa still da murmushi a fuskarsa.

Sai kawai ya shiga girgiza kansa da fadin." Gaskiyar magana yanda kake jarumin namiji mata hudu suka cancanta da kai amma ace ma ko daya babu." cike da alhini ya kare maganar.

Sai abun ya bashi dariya ya dan dara kafin yace." Asp matsalar mata nada yawa shiyasa nayi zamana a haka ba wai don bani da bukata ba, kawai nafi bukatar kwanciyar hankalina nayi duk abinda nake so ba tare da wani ya caza min kai ba.''

Yace." To ai hakan nan ake hakuri dasu da matsalarsu Umaru kowane maigida yana da matsalar iyali mussaman idan mace fiye da d'aya yake da ita, dole ba zaka rasa shi da matsala ba, nima matana biyu sai dai kowacce da gidanta kuma yanzu haka ina shirin yin ta uku da yardar Allah sai na cike domin ina da ra'ayin hakan."

Ya girgiza kai da fadin." Kayi kokari sosai kuma ka aikata sunnah Allah ya baka ikon yim adalci a tsakaninsu."

Ya amsa da "Ameen ya Allah ina fatan kai ma kayi koyi dani."

Girgiza kai kawai yai baya tsammanin hakan domin baya san damuwa ba lallai sai ka tara mata a gidanka za'a tabbatar da jarumtarka ba, shi a ra'ayinsa zai iya 'kare rayuwarsa da mace daya, sai dai kuma duk yanda Allah

Please Login or Register in order to submit comment