Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

be 100% don haka plss Mumy ki nusar da ita ta bar sa gidan nan" Mumy ta sauke ajiyar xuciya a hankali ta kasa cewa komai. Duk yanda Mumy ta so fadi ma khadijah sakon Aliyu da taje gidan kasawa tayi saboda kunya, she don't even know where to start from, haka ta koma gida daga karshe, da Aliyu ya bukaci feedback din khadijah, ta kwantar da murya tace "Abuturrab ka bari kawai bayan bikin, it will look as if we are not happy with her marriage, xa a ga kamar mun so kan mu da yawa, kaga bayan biki sai ayi masu bayani, Ina ga xai fi" yace "Toh shkkn mum, nagode" tace "Hope ka ci abinci" yace "Sure mum" daga haka ya mike ya nufi kofa ta bi sa da kallo cike da tausayinsa har ya fita, she know he is just trying his best to be okay, Kuma taji dadin yanda yake harkokinsa duk da kana ganinsa kasan akwai damuwa sosai tattare da shi, addu'a tayi masa na cewar Allah ya fiddo masa da mace soon shi ma yayi auren nan. Ana gobe daurin aure aka xo har gida aka ma Khadijah gyaran gashi da lalle, all this while baby da kawayenta na tare da ita, Yanxu kam shirun nata ya fara isan Umma ga rashin cin abinci duk tayi mugun rama, Khadijah na son sanin ko Khaleel ya koma ko bai koma ba amma bata san ta ya ba, har lkcn maganar sa na karshe ya tsaya mata, Wai xai mata abinda xai sa ta farin ciki na har abada to meye wannan bayan xuwa gobe tana gidan Sudais, she will like talking to him before tomorrow amma ta kasa kiransa duk da ta ma kashe wayar kar Sudais ya kirata, a haka ta kwanta ranan cike da tunaninsa, tun daga ranan da ta fara ganinsa har xuwa yanxu, tayi wani murmushi ta gyara kwanciyar ta ta lumshe ido tana fatan bacci ya dauketa ko xata samu saukin ciwon kan da take ji. Washegari tun da Sudais ya tashi yake ta kiran layin khadijah a kashe gashi ba shi da number baby, shi kuma baxai iya kiran Umma ba, yana xaune gefen gado misalin karfe takwas Jiddah ta shigo dakin, tsaye tayi bakin kofa tana kallonsa tana murmushi tace "Happy married life in Advance Aliyu" ya dauke kai daga kallonta bai ce komai ba, wani murmushin ta kuma yi ta juya ta fita dakin, mikewa yayi ya fita parlor jin kamar kanninsa da few relatives da suka xo tun shekaranjiya sun fito parlorn, Kamar yanda yayi xata haka ne suna kitchen suna nema ma kansu abinda xa su ci don tun da suka xo ko ruwa jiddah bata taba debowa ta kawo masu ba, sai ma idan sun girka ta tafi ta diba ta ci, komawa daki yayi ya kwanta don sai bayan an sauko juma'ah daurin auren. Tun da khadijah ta tashi take kukan da bata san dalilinsa ba, baby tayi lallashin har ta gaji, Umma tun da ta tambayeta kukan me take taki bata amsa ta fita harkanta, gida ya cika fal da abokan arxikin Umma da yan uwanta da mutan garinsu, Babu Wanda xai ce ba ita ta haifi khadijah ba, yau dai Nanny har da yan uwanta a gidan, Mumy ma tun safe ta xo gidan da kawayenta biyu, Hajiyarsu Sadeeq ma da safe ta shigo gidan, da kyar khadijah ta mike ta shirya bayan Umma ta mata Jan ido taki ko da shafa kwalli a ido. Karfe sha biyu wata kawar Umma ta fita bayan gidan kiran Umma, ba a dau lkci ba Umma ta shigo parlorn don ce mata tayi wasu baki sun shigo kuma cewa suka yi uwar amarya suke nema, kallon Jiddah da kawayenta su kusan biyar kawai Umma keyi don bata taba ganinsu ba, Jiddah na murmushi tace "Ke ce uwar Amaryar Mama" Umma tace "Nice daga Ina haka?" Jiddah tace "Kawayenta ne mu mun taba islamiyya daya mama" Da mamaki Umma ke kallonsu don Khadijah bata taba bata labarin tayi kawaye a islamiyya ba, sannan ga wani irin daurin dankwali na ture ka ga fitina da suka yi gaba daya, sun cakare cikin ankon super wax gaba daya, ita jiddah irin make up din da tayi sai ka rantse ita ce Amaryar, Umma tayi karfin halin cewa "Toh sannun ku da xuwa" Jiddah na murmushi har da ritsinawa tace "Mun gode mama, Toh ina amaryar take" Umma ta sa yar wata kawarta ta kai su dakin da su khadijah su ke, yarinyar na gaba suna biye da ita har suka shiga dakin, khadijah na xaune tare da Baby da kawayenta sai jujjuya wainar shinkafar da Mumy ta kawo mata ta ci ganin bata ci komai ba tun safe take, Su kuma su baby suna ta make up tunda ita har rantsuwa tayi baxa tayi ba, tun da su jiddah suka shigo Khadijah da su baby ke kallonsu, Jiddah na murmushi tana kallon baby tace "Amarya Sannu...." Baby na masu wani kallo ta nuna Khadijah tace "You are mistaken, ga amaryar can xaune" daga haka ta dauke kai ta ci gaba da shafa powder dinta don ko kadan ji tayi gaba daya jiddah da kawayen nata basu mata ba, Khadijah dai sai kallonsu take ko kiftawa babu, Jiddah ta iso kusa da ita tace "Ke ce Khadijah, Amira, Kuma Ummu Shureim koh?" Khadijah taji gabanta yayi mugun faduwa bata dai ce komai ba tana ta kallonta, Jiddah tayi wani dariya tana kallonta da kyau tace "Ke ce ke Shirin shigowa gidan Barrister a matsayin matarsa ta biyu Koh?" Khadijah ta hadiya abu da kyar still ta kasa ce mata komai, xuwa lkcn kam ta fara dago wacece ke tsaye gabanta ko tantama babu matar Barrister ce, Baby ta mike tace "Ke malama ance maki gidan radio ne nan wannan tambayoyin da kike jefo mata?" Jiddah ta mata wani matsiyacin kallo ta daga mata hannu tace "Dakata Hajiya ban yi da ke ba, ki xama yar kallo a nan, ja gefe ki tsaya kawai" daga haka ta mayar da dubanta kan Khadijah tana mata mugun kallo tace "Wato tsaurin idon ki yakai har ki rasa wanda xaki makale ma wa ya aure ki sai mijina Barrister Aliyu Sudais?" Tuni hawaye ya kawo idon Khadijah duk jikinta yayi sanyi, Jiddah ta fashe da dariya ta juya tana kallon kawayenta tana nuna Khadijah tace "Don Allah wacece xaune nan?" Kamar hadin baki suka ce "karuwa" Jiddah tace "Da ta yi me?" A tare suka kara cewa "Cikin shege...." Tuni duk mutanen dake parlor suka yo daki da sauri jin hayaniya a daki, Jiddah na kallon Khadijah da kyau tace "Toh don kaza kazan ki in har kin haifi cikin uwar ki da ubanki ki yi kuskuren shigowa gidan Aliyu yau, ke don fitsara ki gama yawan karuwancin a gidan aiki ki haifi tagwaye sannan daga mijina ya taimake ki sai ki makale masa, daga taimako???? Har yana ikirarin tausayin ki da yake kadai yasa xai aure ki ba wani abu ba, kin xata badan uban tausayin da Allah ya xuba masa ba xai ce xai aure ki bayan yasan ke wacece? Toh bari ki ji, babu komai naki da ban sani ba, duk sirrin ki na tafin hannuna, babu abinda Aliyu ya boye min game da ke, tunda mijina ne shi din baya komai sai yayi shawara da ni, da farko na xata abun arxiki ne bayan ya bani labarin ki na amince ya aure ki don ya rufa ma ke da shegun ki asiri amma kawai daga baya tun baki shigo gidan ba na fara ganin canji, wato kin fara shanye min miji sai yanda kika yi da shi daga na amince masa ya aure ki ya rufa maki asiri koh? To wllh kinyi kadan, yau xan ga ta yanda xa ayi auren nan da kaxa kaxan ki sai dai ki koma ki ci gaba da karuwancin...." Baby bata san lkcn da ta mike ta cakumota ba ta makure ta..... Kan kace me fada ya kauraye tsakanin jiddah, baby, da kawayen jiddah, frnds din baby su ma suka shiga, da kyar mutanen da suka yi mutuwar tsaye parlorn suka raba fadan, Khadijah ta hade kai da gwiwa jin numfashinta na sama, ko kwakkwaran motsi ta kasa daga gun da take xaune, Jiddah ba irin xagi, cin mutunci da gorin da bata mata ba kawayenta na taya ta, har Umma sai da suka xaga, Baby ma bakinta bai mutu ba, da kyar aka fidda su dakin ana Allah wadaran Jiddah, sai a sannan hawaye ya dinga xubo ma baby taji tausayin Khadijah sosai duk jikinta yayi sanyi, Umma kam xaunawa tayi ita ma hawayen na sakko mata ta kasa cewa komai, Mumy kanta tsaye tayi ta rasa abin cewa duk jikinta yayi sanyi, Wata kawar Umma ta durkusa ta dago kan Khadijah a hankali cike da tausayinta, hawaye ne ke xuba idonta kamar an bude pampo, Baby ta durkusa kusa da ita ita ma hawayen na xubo mata ta rasa abinda xata ce mata, Khadijah ta kamo hannunta cikin rawar murya tace "is it my fault that I was raped baby? Is it my fault that I am an orphan, is it my fault that I had kids out of wedlock? Dama maraici...." kasa ci gaba tayi ta fashe da kuka sosai tana girgixa kai a raunane tace "Alhamdulillah for my fate... irin tawa kaddarar kenan kuma na amsa hannu bibbiyu, Amma me yasa mutane baxa su yi considering dina ba, ni ban so ma kai na haka ba, Allah ne ya kaddara min, but ya xan yi baby, dole in gode masa, ban taba karuwanci ba amma sun ce min karuwa, ban san Sudais baxai iya rike min sirrina ba he betrayed...." Mikewa Baby tayi ta dau wayar Khadijah ta fice daga dakin, Ta kunna ta shiga neman layin Sudais, Bata yi wahalan ganin number ba don Barrister tayi masa save as, tana dialing ba a dau lkci ba ya dauka cike da damuwa yace "Why did you switch off ur phone Amira..." Baby ta katse sa a xuciyarta na tafarfasa tace "Malam dama ka san baka iya rike sirri ba ka nace sai ka auri Khadijah??? dama kai din mijin ta ce ne sai yanda mahaukaciyar jahilar matar ka tayi da kai?" Kasa cewa komai Sudais yyi da farko don gaba daya he was lost, can cike da karfin hali yace "Wacece wannan?" A mugun fusace tace "Ba Lallai ka ji wacece ba, wllh ka ci amanar Khadijah, ka xalunce ta, and am advicing you ka janye batun auren ta kaje jahilar matar ka ta ishe ka, Kuma sai Allah ya saka mata" tana kai wa nan ta fashe da kuka sosai taci gaba "Naga ba ita ta ta xabar ma kanta wannan kaddarar ba har xaka xaunar da warce xa su xauna a matsayin kishiyoyi ka tsara mata komai na rayuwarta daga farko har karshe ta xo har gidan biki ta mata tonan silili ta gaya mata son ranta, tayi mata cin mutunci da cin fuska, tayi mata gori" katse wayar Sudais yyi kansa na juya masa ya mike daga xaunen da yake ya fito parlor, ya kusa minti sha biyar tsaye sai ga jiddah da kawayenta sun shigo parlorn, ya taka har gabanta ya sauke mata tagwayen mari, yana kallonta da jajayen idanuwansa yace "Na sake ki saki daya jiddah"

A hankali Khadijah ta bude idanuwanta ta sauke kan Khaleel dake xaune gefenta Aliyu na tsaye daga gefensa, Umma ta taho gunta da sauri ganin xata mike xaune ta riketa da damuwa tace "Sannu Khadijah, how are you feeling now?" Kirjinta kawai ta nuna ma Umma hawaye na xubo mata, Umma tayi kasa da murya a sanyaye tace "Xai daina in sha Allah, be strong daughter" Baby dake tsaye gefe daya ta karaso ta xauna kusa da ita tana kallonta ta kamo hannunta, rasa abinda xata ce mata tayi, lkci daya ita ma hawaye ya kawo idonta, Khaleel ya mike ya fita ward din sai gashi sun dawo tare da likita, Juyawa Aliyu yayi ya fita, likitan ya gama dubata suka fita tare da Khaleel xuwa office din sa. A sanyaye Umma tace "Kin dai ji abinda likitan ya ce maki, Kar ki sake kukan nan don Allah saboda lalurar ki" Khadijah bata ce komai ba ta kai hannu tana share hawayen idonta, bude kofar ward din aka yi Sudais ya shigo, tsaye yayi nan bakin kofar yana kallonta, A hankali Umma ta dauke kai kanta daga kallon da take masa, Baby ta hade rai kamar bata taba dariya ba, Tun da Khadijah ta kallesa sau daya bata sake yarda ta dago ba hawaye ya dinga xuba idonta, ya iso har kusa da ita, da kyar yayi gathering courage yace "Amira...." ta fashe da kuka sosai tace "Am begging you ka rabu da ni pls Aliyu ka tafi, My heart is aching at the sight of you, kayi hakuri ka wuce... let me rest plssss" cikin matsanancin kuka ta kare maganar, Yana mata wani kallo yace "Amma in har maganganun da Jiddah ta fadi maki sun yi tasiri xuciyar ki ba ki min adalci ba Amira, for good two years na boye ma mahaifiyata na ajiye ki gidana ko da kuskure ban taba sanar da ita ba ban taba tona maki asiri ba, hatta frnds dina ban da Yusuf babu wanda yasan labarin ki, sai a yanxu kike tunanin xan fallasa sirrinki, Kuma in rasa warce xan fada ma sai matata da ko kadan ba dadin xama da ita nake ba, am I that daftt??" Ya girgixa kai cikin bacin rai yace "I never expect such from you Amira, I thought ke me fadi ma wasu cewar makirci ta xo tayi displaying gidan ku....but I was mistaken" kasa ci gaba yyi ya juya ya fice daga ward din, Khadijah ta hade kanta da gwiwa tana kuka kamar an aikota, Baby dai ta kasa cewa komai duk jikinta yayi sanyi sosai, Umma ta sauke ajiyar xuciya tana kallon baby tace "Hope kin ji maganata ya fito ko, Ni nasan makirci ne kawai na mace, I know baxai taba yin haka ba, baxai xaunar da ita yayi mata tsarin da ta xo tayi ba, she set him up kawai saboda kishi...." Umma na magana tana goge hawayen dake xuba idonta, ta ji tausayin Sudais sosai, "Khadijah idan kika ce kin fasa aurensa kamar yanda kika yi ikirari before passing out kin yi butulci, baki kyauta masa ba, Kuma kin nuna ta ci nasara kenan matar tasa" Khadijah ta dago cikin kuka tace "Wayyo Umma kashe ni xata yi a gidan, baxan iya auren mata miji ba ni dai, ku rufa min asiri, Umma kin ji yanda xuciyata ke min ciwo, na hakura da auren gaba daya I prefer dying a spinster" Rungume ta Umma tayi tace "Ba abinda xa a fasa daughter, kuma tayi kadan ta kashe ki, we will prove her wrong, ta xo tayi masa sharri duk don kice kin fasa to xa a nuna mata iyakarta in sha Allah sai kin aure sa, sai in Allah yayi shi din ba mijin ki bane dama, Amma babu abinda xa a fasa" Tun da Sudais ya fita ward din ya tafi kan wani kujera a waje ya xauna ya jinginar da kai ya lumshe ido, he was totally lost and sad, Bai taba tunanin makircin jiddah ya kai haka ba, ya rasa gane inda ta samu lbrin Khadijah, yasan Yusuf baxai fada mata ba, infact ta ina ma xa su yi communicating bayan bata da number sa bashi da nata, Babu abinda ya kara sanyaya masa jiki sai yanda Khadijah of all people ta yarda da abinda jiddah taje ta fada, ai Ita mai ce ma mutane sharri jiddah ke masa, but she is among the believers, Khaleel dake jingine da motarsa yana ta kallonsa, tausayi ya basa sosai, and he knows what he is feeling, khaleel ya fi minti biyar yana jinjina kwarewar matar Sudais a fannin hypocritical action, she is just perfect, a hankali ya taka ya isa har inda yake ya xauna gefensa, Sudais ya bude ido a hankali jin mutum gefensa, Khaleel ya cire glasses din idanuwansa in a low voice yace "Sure it hurts..." Sudais na kallonsa da idanuwansa da suka sauya launi cikin sanyin murya yace "Can I confide in you Dr Ayman?" Khaleel na kallonsa ya gyada kai yace "Sure" Gyara xama Sudais yyi yana dubansa ya fara magana cikin sanyi.... Umma ce ta fito haraban hospital din bayan kusan minti sha biyar, duk iya kalle kallenta bata hango ko wannensu a nan ba hakan yasa ta koma ciki don dauko wayarta, Sudais ya dinga kallon Khaleel da yayi shiru idonsa a kasa, Sudais yace "Don't forget I asked you before letting out my mind to you doctor, ka gaya min gaskiyar abinda ke ranka" Sai a sannan Khaleel ya dago yana kallonsa, d'an murmushin karfin hali yayi yace "Sure" bayan few seconds a hankali yace "Yea Barrister, May be it's the right decision" Sudais na kallonsa yace "May be?" Khaleel ya shafa kansa yace "It's just the right decision" a sanyaye ya kare maganr, Sudais ya kalli wayarsa dake ring ya ga Umma ce ke kiransa dauka yayi, ya kai kunne yayi sallama, Umma tace "Kana ji na Barrister, Babu abinda fa xa a fasa, don't let anything spoil ur mind pls, idan har kana son Khadijah da gaske ka tafi, it's almost time for prayer ana saukowa a daura auren ba abinda aka fasa in sha Allah" a hankali yace "Toh Umma nagode sosai Allah ya kara girma" tace "Ameen" katse wayar yayi yana kallon Khaleel dake kallonsa shima don duk ya ji me Umma ta ce, a tare suka mike Sudais na kallon agogon wrist din sa. Tun da aka sauko masallaci gaban Sudais ke faduwa, is he really making the right decision, Khaleel dake gefensa na lura da shi, a hankali ya matsa kusa da shi sosai yace "It's not only the right decision but the best.... For many reasons" Sudais ya kallesa yayi murmushi bai dai ce komai ba, can ya kalli Khaleel yace "Kana da Number Dr Aliyu kuwa? I didn't see him..." Katse sa Khaleel yyi yana yar dariya yace "Sheer jealousy, did you expect to see him here...." Murmushi kawai Barrister yayi, Khaleel ya fiddo wayarsa ya nemo masa number Aliyu ya mika masa, Dialing number Sudais yyi ya kai kunne ba a dau lkci ba aka dauka Sudais yace "It's Barrister Aliyu, ban gan ka masallaci ba, or don't you want to witness the nikka?" Aliyu yyi murmushi yace "It's not a must I stay near you Barrister, though I can sight you from where I am, I am not what you might have thought of me, idan abun farin ciki ya samu d'an uwana musulmi ina taya sa murna, idan kuma otherwise...." Hangosa Sudais yyi tsaye not too far away from them tare da Salim da wasu frnds, Sudais ya katse wayarsa yana murmushi, Aliyu ya Karaso ya basa hannu Sudais ya mika masa nasa, sannan Aliyu ya mika ma Khaleel ma, Khaleel ya cire glass din idanuwansa ya basa nasa hannun. A can asibiti kuwa bayan an ma Khadijah allurai aka bata drugs aka sallamosu suka koma gida, har sannan hawaye ya ki tsaya mata, Babu abinda aka fasa na biki a gidan kamar yanda Umma tace don kamar ma ba ayi komai ba sai dai Amarya da bata da lafiya, Shayi Umma ta sa baby ta bata ta sha ta kwanta nan da nan bacci me nauyi ya dauketa....


Breakfast, just light😎

Sai kusan karfe uku saura Baby ta tada Khadijah tayi sllhn azahar ganin lkcnsa na ta wucewa kuma da alamar ta samu saukin jikinta sosai ganin she is sleeping peacefully.... Khadijah ta mike xaune da kyar, xuwa lkcn kam ciwon da ta dinga ji daxu da safe a xuciyarta ya rage sosai, sai dai gaba daya taji gaba daya she is weak kanta ya mata nauyi, Tana kallon Baby cikin sanyi tace "An daura auren koh Baby?" Tana magana ne hawaye cike idonta, Baby ta kasa ce mata komai... Ta hade kanta da gado cikin rauni tace "Matar nan xata iya kashe ni wllh, nobody want to consider me, nobody is willing to understand what I mean, Baby tsoron ta nake.. " Baby ta kauda kanta bata ce komai ba sai dai wani mugun tausayinta ta dinga ji har ranta, Bayan wani lkci a sanyaye baby tace "Ki tashi kiyi sllh Khadijah, lkci na wucewa" Khadijah Bata ce komai ba ta sauka saman gadon tana kokarin ganin bata bar hawaye ya sakko mata ba, kamar iska xai kadeta ta shiga bathroom, khadijah na idar da sllh Baby ta fiddo mata daya daga kayan biki da aka dinka mata, tana kallonta persuasively tace "Plss Iman put on this ko baxa kiyi kwalliya ba, am begging you" Khadijah tayi murmushin karfin hali bata ce komai ba, Bayan wani lkci ta mike ta shirya cikin tsadadden lace din, Baby na murmushi ta wara ido tace "Waow kin ga yanda kayan suka maki kyau kuwa Iman, plss ki bari ko powder in shafa maki, just it" khadijah bata mata musu ba, duk da har xuciyarta bata so, daga powder baby ta lallabata ta sa mata har eye pencil da chappete, sosai Khadijah tayi kyau just like the bride she is, Baby ta daura mata dankwali tana kallonta da sha'awa, Frnd din Umma ce ta shigo dakin da warmer din abinci ganinta tace "Kai maa sha Allah ko ku fa? Da xa ku bari wata kishiya can ta bata maku wannan ranan, show her she is a liar bata isa ba ne, sai ma mun je kai ta gidan tukun" Murmushi kawai Baby tayi tana kallon khadijah da ta ki dago kanta. Tun bayan da suka bar masallaci bayan an daura auren Aliyu ke rike da kan sa a mota, su biyar ne motar, Khaleel na driving, Dr Yusuf na xaune gaban motar, sai Barrister da Aliyu da Farouq a baya, tun da suka dau hanya Sudais ke danna wayarsa bai dago ba shi ma, the journey was very silent da alama kowa da abinda ke ransa har suka iso dai dai kofar gidan su Khadijah, Khaleel yyi parking a hankali ya kashe motar, Shi ya fara sauka sannan Farouq da Dr Yusuf, Aliyu ya sauka sannan Sudais ma ya fito yana mayar da wayar sa Aljihunsa, ganin xai shiga ciki Aliyu ya riko hannunsa yana kallonsa da idanuwansa da suka kada sosai, Barrister ya kasa hada ido da shi, Da mugun karfin hali yace "Barrister... am still confuse, I think am yet to understand the meaning of the drama that took place at the mosque minutes back, ka ganar da ni don Allah, I am confuse plss, nayi tambaya a mota kun kyaleni..." Sudais dai bai iya yace komai ba, Dr Yusuf ya rungume hannayensa yana kallon Sudais don Aliyu bai ma kai sa confusion ba, jiran abinda Sudais din xai ce shi ma yake, shi dai yasan daurin auren abokin nasa ya xo tun daga Yobe sai kuma ya ga otherwise, Farouq dai murmushi kawai yyi ya jingina da mota ya rungume hannunsa, khaleel ya tako har gaban Aliyu yana kallonsa, bayan few seconds yace "What is it that u don't understand Aliyu?" Aliyu ya kallesa a hankali yace "Everything.... I... I don't get everything" Khaleel ya shafa kansa cikin sanyin murya yace "The fact is that, Kai xaka gyara abinda ka 6ata doctor, we think this is just the best for the both of you, Barrister Aliyu ya sadaukar maka ba don baya so ba sai don la'akari da our today's world, kwanciyar hankalin khadijah ya fi masa auren ta....." Sai a sannan Sudais yyi murmushin karfin hali yana kallon Aliyu a sanyaye yace "I have no option... She is dear to me... Ita din abar tausayi ce, they are a lot of challenges ahead for her and the little boy in dai ba gidan ka suke ba, I

Please Login or Register in order to submit comment