Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba in sukaji wlh har bugu na baba zeyi"

Khalil ya cire wayar daga aljihu yana mata kallon mahaukaciya yace "saboda hauka sekije bata hakuri mtswww mental tokice mata me? "


"Nide zanje nabata hakuri wlh in su mama sukaji fushi zasuyi dani "

Yakara jan tsoki "wai saboda hauka jamila kije wurin hjya ido da ido kifada mata magana, hmmmm yanzu nariga na mata karya nace iskokai ne dake in ta hakura shikenan inbata hakura ba kau akwai matsala, kuma kisani hjy ita ta haifeni tai duk wata dawainiya ta itace duniya ta itace lahira ta tafi duk matan duniya awurina ita nafi so fiye da komi idan har kinason zama dani dole kiyi hakuri da yadda take in bazaki iyaba sena sawwake miki, kamar yadda kike tsoron fushin iyayenki haka nake tsoron fushinta fin tunaninki ma kuma duk abinda zesa ta farinciki zanyi kokarin yi mata shi,kuma dole kirika girmamata inkinason zaman lpy dani useless girl kawai "


jamila ta cigaba da kuka, ya fita yabar mata dakin ya koma dayan dakin ya kwanta, shima yakasa bacci , rabin son da yakewa jamila duk ya tafi se tunanin faseelat da yadawo mashi sabo yadda take kula da mahaifiyarshi kafin taso rabuwa dashi, ya gyara kwanciya ya rungume pillows yana tuna yadda takeyin kasa da fuska saboda kunya da murmushinta idan sukaje gun hjya,sonta se yadawo mashi sabo ya rumtse ido zuciyar shi na zafi

yace "hjya duk ke kikajawo hakan ko alhakin faseelat baze barki ba nasan kema dole zakiyi kewarta, I love her so much babu wacce zanso kamarta tana da duk qualities na mace tagari amma saboda son zuciyarki hjya kikai abinda dole ta sauya hali kinja na rabu daita gashi har yau nakasa cire tunanin ta araina nikan tuno duk wani abu me kyau nata cute face, cute body, cute skin,white lulu eyes good structure ,long hair obedient tasty food and drinks shyness more over light heart and her beautiful smiling "

Ya kara matse pillow ya rumtse ido yana tuno yadda yakejin natsuwa idan ya rungumeta hawaye masu zafi suka zubo mishi ya bude ido yace "I love her I will surely die with her love, ko tana ina yanzu? "(niko nace mishi ai tayi aure 🤣)

"inafatan ki kara zama Matata akaro na biyu saboda inasonki nine nafi kowa sonki"

Jamila tagaji tai shiru cikinta se juyi yakeyi setaji kuma tana regretting abinda tayi, she love khalil so much bazata iya rabuwa dashi ba, tasan ta bata mishi rai sosai tunda har yayi mata hijira agado ta sauko daga kan bed din tabude fridge tasha ruwa kamar barauniya tana sanda ta nufi dakinshi,

Yana ta kallon silin ta turo dakin ta shigo ta durkusa kasan kujerar da yake kwance tace"dan Allah yaya kayi hakuri wlh duk sharrin shedanne da na zuciya I promise you bazan sake ba kayafemin "

Beko kalleta ba yakira sunanta "Jamila! "

Ta kura mishi ido yace "kin matukar batamin rai da kika nuna mahaifiya ta bakomi take agunki ba nayi zaton zaki bata girma fiyeda nikaina amma bahaka ba, wlh rabin son da nike miki duk ya tafi tunda har kika iya wulakanta min uwata kitashi ki tafiyar ki dakinki tunda kin fadi ta cikinki aise kije ki bacci "

Jamila ta riko hannunshi dasauri hankali tashe tana zubda hawaye tace "Dan Allah kayi hakuri karka dena sona wlh nafison ka fiyeda komi ka dawo da duk sonda kakemin zan gyara kuskurena"

Yaja tsoki a zuci yace madness its true fa jamila kanta da motsin dukda yarinta da kuma hauka,

Tace "plssss wlh zan gyara namaka alkawari zanso ta kuma zan bata girma bazan kara yin korafi akanta ba "

Yayi shiru taita risgar kuka yagaji yace "Dan Allah karkisa dodon kunnena yayi ciwo naji inasonki na kuma hakura shikenan? "

Tace"se kuma kadawo da son nawa da kace ya tafi "

Abun de na yarinta yace "to ya dawo shikenan kije ki kwanta "

Ta share hawaye da bayan hannu tace nima anan zan kwana tare da kai "

Ya dafe goshi yace "OK tashi mukoma dakinki kar jikinki yayi ciwo anan "

Ta kamo hannushi ta tashi suka tafi dakinta suka kwanta

ta matsa ta rungumeshi sosai tana kara bashi hakuri shiko tunaninshi ya tafi akan gobe yadda zasuyi da hjya,

yayi shiru yanaso tasamu bacci ne kawai saboda cikin ta,

wansafe fuska ba yabo ba fallasa yake shirin fita,

jamila tagama breakfast ta shigo ta sameshi tai zaune tana ta kallonshi so take takara bashi hakuri kuma tana tsoron ya dawo yi mata fada,

Jiki amace tace "ga breakfast dinka "

yana saka hula yace "banci ki dauke abinki"

tafara hawaye tace "kacemin ka hakura ni kawai kabarni har ita inje nabata hakuri "

yace "karki kuskura ki kara taka kafa waje bada izinina ba kinga jiya na shareki amma next time wlh sena gwadamiki nawa kalar haukan, ki kwashe kayan abincinki wurin hjya zanje nayi breakfast dina "

Ta dora hannu akai "nide nashiga ukku ni jamila "

Yace "bakwai kika shiga ba ukku ba, mental "

yazo ze fita wufff ta kamo gefen rigarshi tarike tana magiya" dan Allah yaya khalil kayi hakuri na yarda banda hankali, wlh nayi nadama bansan meyahau kaina ba "

ya kalli rigarshi ya kalleta yace "cikani "

Taki Saki ya bige mata hannu ya nufi kofa,

beko samu cikinta ba ta dafe ciki ta duke tafara ihu "wayyo Allah cikina wayyo ya khalil"

da gudu ya dawo wurinta ya duka yana fadin "lpy meyasameki ko mutafi asibity ?"

ta rika yarfa hannu" yaya cikina zaya balle marata "

hankalinshi ya matukar tashi tuni tausayinta ya mantar dashi lefin yace "sannu yi hakuri bari na samo mota mutafi asibity sannu "

ya juya yafita dasauri, ta cigaba da kuka tana kuka tace "inba haka naiba bawai hakurin zeba "

bayan 10mnt ya shigo tai shiru kanta Duke akushin ya wuce ya dauko abaya yazo ya rikota zesa mata sutafi hospital tai fuskar yaushi tace "yadena ciwon ai base munje asibitin ba "

Ya kalleta yace "a, a mutafi likita ya dubaki"

ta girgiza kai tace "kabarshi na warke"

yayi shiru yana kallonta na seconds ya tashi ya fita ya sallami me motor da ya taro,

Yadawo wurinta still tana nan daga tsaye yace mata "lpy lau de ko don fita zanyi "

ta dagamai kai tace "amma kayi hakuri bazan iya cin abinci ba in baka yafemin ba "

Ya yamutsa fuska yace "to naji na hakura ai kici abincinki nima ki ajiyemin nawa zandawo naci "

Tai murmushi ta share hawaye tace "nagode yaya "

Ya kalleta ya fita, bawai dawoma abincin zeba dan kawai tade ci natan shi bata abinci yake ba yasamu ya gama da hjya tukun,

da shigarshi gidan hjya yaganta fuskarta kumbure ,ya duka gaisheta"hjy ina kwana? "

tace"bawannan ba saki nawa kaimata?"

yayi shiru ya sadda kai gabanshi na faduwa,

Ta daka mai tsawa "bada kai nake ba shin baka saketa ba kenan?"

yayi shiru kanshi kasa de yana durkushe, tace"wlh khalil ka rako maza duniya, sammm bakai kama da namiji ba, matarka ta zagi mahaifiyarka ka kasayin komi akai da wani ne wlh seya ci ubanta sannan yatura ta gidan ubanta"

"katashi kaje ka saketa tunda sena koya ma yadda ake nuna bacin rai "

cikin kaskantar da kai yace "hjya dan Allah kiyi hakuri wlh yarinyar nan baita kadai take ba tana da iska, tunda ta dawo dede nabata labari take kuka tanaso tazo ta baki hakuri kiyi hakuri dan girman Allah"

Hjya tai banzar dariya "hehehe he! khalil nifa na haifeka nafika sanin duniya nawa kake yanzu, to wannan karyar batai ba sakarai solombiyo bawan mata, katashi kaje ka saketa saki ukku zaka mata ringissss dan kai daita har abada wlh"

yayi shiru ranshi na zafi tabbas jamila batai ba amma he love her kuma tausayinta yake dagayin aure se saki, kuma shi yatsani ma saki kuma bayason yabawa wata danshi ko diyarshi dan baya da tabbacin zata rike shi amana tundade jamilar yarinya ce kuma tanasonshi maybe ta gyara, yanajin tsoro kar yakuma samun wadda tafi jamila hauka shide yasan yayi missing yayi missing mace me tsada,

Murya sanyaye yace "hjy ayi hakuri de aduba ajanye maganar sakinnan she's very young kuma kiduba baatashi yi mata aure ba amma akabani ita, iyayenta bazasuji dadi ba, kiyi hakuri hakan baze kara faruwa ba ,kiyi hakuri kodan cikin jikinta taci albarkacin shi Allah mafa yatsani Saki hjy "

hjya ta zaro ido "Allah ko ustaz alaramma ash sheik khalil, toni ina ruwana da iyayenta aida nasan basu yi mata tarbiyya ba da bazanje ba, tobari kaji wlh tallahi seka saketa dole karabu daita ko kazaba koni koita shasha "

Khalil ya dago fuska Yakalleta yace "haryanzu hjy baki lura ba? Baki fahimci abinda ke faruwa ba, ni bawani so na musamman nakewa jamila ba,akan wanda nakewa faseelat hjy ki tuna baya mana yakamata ace kin dau darasi Dan Allah kiyi hakuri karki matsa na saketa kinga fa siyama na wurinsu abun ze zama matsala, zanwa jamila magana zata zo tabaki hakuri kuma bazata kara ba "

Hjy tace "aikoni nadauki darasi amma nariga nagama daukar shi daga gun jamila de, kuma su sako min siyamar seme shikadai ne autan maza kai seka saketa fa seka Saki jamila dole yarinya mayya marar tarbiyya me zaai daita yo wlh danma cikin jikinta ya tsufa da se abarar dashi dan gudun hada zuria da mahaukata "

Hawayen bakin ciki ne suka zubowa Khalil ya share hawayen yace "nide hjy kimin uzuri akan wannan kimin alfarma kibarni daita,dan Allah "

Ta tabe baki ta dora hannu a gemu tace "to ita kazaba kenan to Allah yayi maka albarka kayi dede katashi kabarmin gida katafi can gun matarka karka sake dawomin anan inde ba sakinta kai ba "

Ta juya ta shige daki khalil yabita da kallo, sosai yaji tausayin kanshi yasa hannu ya share hawayen fuskarshi ya mike ya bita daki yana zuwa ze shiga da karfin tsiya tace "karka shigominnan ka koma can wurin matarka kada insake ganin ko meka ma dakai anan"

Yayi tsaye cikin rashin abunyi, itako ta shige bedroom, yayi kusan 15mnt a tsaye sannan ya juya ya fita jikinshi a mace,

Tuki yake yana neman mafita koda yaje school kasa komi yayi dole ya koma gida, ya samu jamila nata kokarin yin girki his favorite shinkafa da wake da salad da yaji,

Beko tsaya amsa sannu da zuwa da take mishi ba ya shige daki ya haye gado,

Wani mugun zazzabi ya rufeshi yaja zanen gado ya rufa,

Jamila ta biyoshi tazo tai tsaye murya sanyaye tace "yaya baka lpy? Me yasameka? Inkawo maka magani kasha sannan ka kwanta"

ya yaye zanen yanajin haushinta yace "ba dama haka kikeso ba to ga irinta nan seku kasheni ku duka ku huta "yakoma ya rufa

Ta fiddo ido waje "yaya bangane ba fa mekake nufi "


yamata banza tagaji da surutu ta koma kitchen,

masassara yake amma tunanin mafita yake tunani yayi yaje yasamu kawu manu suyi maganar yaje yabawa hjya hakuri maybe adace,

Dan gaskiya beyiwa iyayen jamila adalci ba in ya saketa daita kanta jamilar saboda tana da gaskiya itama,da wannan shawarar ya tsaya anjima ze koma dukda de yasan ba saurarenshi zatai ba amma ze gwada saa,


atanadar min barka da salla ta fan's 🤣zan zuba ido jiran jin alert ran salla jibi... 🤗😁
➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰






By








*MAMAN MAMY*
*(SHALELE)*








https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~*



7⃣0⃣






*Dedicated to my lover (Mrs Ibrahim)* *I love you badly😍,Allah yabawa teeman mu lpy*






Hankali tashe yayi zaman dirshan agabanta ya rungumota jikinshi wasu tsokoki yagani a gun ya saki kara yana kuka yake girgizata "faseelat dan Allah karkimun haka karki bari cikinnan ya fita "

Faseelat ko batasan halin da take ciki ba don hankalinta ya dade da barin gangar jikinta ya cigaba da kuka yana kara ya kuma rungumeta tsam a jikinshi difff numfashin faseelat ya dauke wanda shi besani ba,


Aisha jin karar shi tayi yawa yasa ta dakata da chatting da take ta zaro ido waje tace "innalillahi karde ya kashemusu diya? "ta ajiye wayar ta fita daga dakin da gudu ta nufi dakin faseelat, tana zuwa ta murda handle ta tura kofar, abunda tagani seda hanjinta suka motsa jinin har yakusa kawo bakin kofar dakin ga faseelat zindir rungume a jikinshi yanata rusa kuka da ihu,

Aisha ta zaro ido ta rufe baki da hannunta dake rawa tai tsaye takasa shiga ciki ,

Amira naganin Aisha ta gudu itama ta biyo bayanta tana tafiya ahankali saboda tsoron da takeji zuciyarta nata harbawa da karfin tsiya,

Fahad yana ta kuka besan ma Aisha ta shigo ba yakasa temaka wa faseelat ya kaita asibity don baya cikin hayyacin shi,

Bazato Aisha taga jini gabanta, se sannan ta kara zaro ido tai cikin dakin dasauri ganin jinin daketa zuba, ta bude wardrobe din faseelat ta zaro shirt da single zane ta iso wurin da suke jikinta nata rawa tace"yaya kasa mata kayanta ka kaita asibity jininta ze kare "

Fahad ya dago face duk hawaye yace "Aisha ta mutu ko? Na kasheta wayyo Allah na "

Aisha ta dafa shi tace "bata mutu ba yaya kasa mata kaya mutafi asibity jininta na zuba "ta mika mai kayan,hannunshi duk jini yana rawa ya amsa ya rikesu ya dago fuskar faseelat yaga ko numfashi batayi yakara rikicewa yana kiran sunanta da karfi,

Aisha na tsaye hannunta yakasa barin bakinta duk ilahirin jikinta nata rawa kunsan jini beda kyan gani bare wannan da yayi yawa,

Amira tana dari dari ta shiga dakin ganin abinda ke faruwa yasa ta firgita ta fiddo ido waje zuciyarta takara gudu wanda har kirjinta yake dagawa sama,

Kamar ance ta kalli kasan ta, ta ga jini har yazo kafanta ,ta sulale wurin a sume,

Aisha batasan da shigowar amira ba tana ta kallonsu ,kamar ance ta kalli kofa ta hango amira kwance cikin jini,

Aisha tafasa kara da gudu ta isa wurin amira tana kuka ta tallabo ta ta rika tapping face dinta "amira! Amira !! "shiru amira bata amsa ba idanunta a rufe,

Aisha na kuka ta dauketa batako kara waigen su fahad ba tai waje ko mayafi bata tsaya dauka ba se key data dauka akan kujera tafita ta shiga mota tabar gidan takama hanyar asibity, tana tuki tana kuka,

Karar da Aisha tayi ne ya medo fahad tunaninshi sauri sauri yasawa faseelat riga ya dora mata zanen ya daukota ya fito yasata a mota gidan baya ya shiga ya figi motar, megadi bema ida bude gate dinba fahad ya fita da motar da speed up,

tuki ne kawai yake amma hankalinshi baya tare dashi da temakon Allah suka isa alhayat prvt hospital,

Ya bude motar yana kuka ya dauko faseelat dake lifeless tana ta bleeding ya shiga daita da gudu,

nurses suka tarbeshi aka dora ta akan gado aka tukata zuwa emergency room, fahad ya zube akan gwiwowinshi ya rufe fuska da tafukan hannaye yana kuka me ban tausayi da karya zuciya,

Itama Aisha a asibitin takawo amira dan akwai specialist doctors a asibitin suna kokari sosai wurin gudanar da aikinsu, anbasu room ansawa amira ledar ruwa an kuma yi mata alluran bacci don ta samu hutu, Aisha na zaune gefenta tai tagumi lokaci to lokaci hawaye na zubarmata ,


ya omer yana da wani friends da suka hadu a facebook tun yana Niger da yadawo Nigeria sun zama friends sosai dan suna kawowa juna ziyara akai -akai tun yana Niger yake dora pics dinshi da faseelat a facebook page nashi, friend din seda ya taya omer yafada mishi matar aure ce sister dinshi ce , duk da haka friend din yayi saving din pic din saboda sun burgeshi sosai ,shima yakan dora pics din kuma omer nagani sede ya mishi godiya,


a asibitin yake aiki karamin likita ne ya kanyi dressing small injures allurai har da magani yakan bada, ya fito daga office dinsu yaga anwuce da faseelat akan bed gashi awarwatse fuska a kumbure ga jini duk ajikinta, inda besan ta sosai ba baze iya gane ta ba ,
Hankalin shi ya tashi ba tsayawa ya fiddo waya ya dannawa omer kira,

Omer da yagama waya kenan da fadilarshi kiran abokinnasa bello ya shigo wayar, ya dauka da murmushi kan fuskarshi yace "likita manyan gari yau antuno dani kenan"

Doctor bello da becika hayaniya ba kamar de omer sede har ma yafi omer shiru shiru, muryarshi very cool yace "hold on, yanzunnan naga ankawo wata patient me kama da sisternka tana ta bleeding I don't know ko idona ne se naga kamar ita "

omer dake kwance ya tashi zaune kanshi na sarawa gabanshi na faduwa yace wa bello "waya kawota mace ko namiji? "

Bello yace "namiji wani dogo fari kyakkyawa yana da saje, shima de hankalinshi a tashe dan se kuka yake"

omer ya bata fuska kamar ze kuka zuciyar shi a cunkushe yace "itace wlh dan Allah kadubamun room da zaakai ta gani nan zuwa yanzunnan"

difff yakashe kiran ya dafe kai yanajin kamar yayi kuka kamar an tsikareshi ya tashi yayi dakin ummi dasauri da key dinshi a hannu ,

ummi na zaune da baki dake zuwa mata murna ya shigo dakin kallo daya ta mishi tagane ba lpy ba, muryarshi na rawa yace "ummi faseelat bata lpy yanzu haka suna asibity "

Ummi tace "subhanallahi miiyasameta ne? "

Idanunshi jawur yace "inaga tayi miscarriage ne "

matan dake dakin suka taya ummi sallallami ummi ta mike jikinta har rawa yake ta dauko hijab tace "mutafi asibitin naganta "

omer ya fita ummi na bayanshi Suka shiga mota suka kama hanyar hospital din,


acikin emergency room anyiwa faseelat allurar tsayarda jini jinin ya tsaya akamata allurar bacci akasa mata ledar jini don sunada jini a blood bank, sannan aka fito daita,

Fahad na durkushe yaci kuka har yagaji aka fito da faseelat ya tashi jikinshi na bari ya bi bayansu aka shigarda ita awani daki suka kwantar daita yayi tsaye yanata kallon fuskarta da ta kumbura gashi har yanzu bata dawo hayyacin ta ba ,

nurses nagama shiryata suka juya suka fita adakin fahad yakarasa bakin gadon yayi kneeling ya dora kai jikin gadon yana zubar da hawaye yana sambatu "nacuceki faseelat na rabaki da farin cikinki nayi sanadiyyar zubewar gudan jini na ihate myself kiyafemin plssss..."

Dukda saurin da omer keyi ummi gani takeyi kamar baa tafiya dandanan ta tambaya baaisa asibitin ba?

Har suka isa sunata sauri su dukan burinsu suga halin da take ciki,

omer yakira bello yazo ya samesu suka tafi ya nuna musu dakin yana jimami, be iya shiga dakin ba ya juya,

su ummi suka tura dakin suka shiga, fahad na durkeshe suka shigo ya dago face duk hawaye ya kallesu seda gabanshi yafadi ganin su awurin adede wannan lokacin,

Dasauri ummi takarasa kan bed din ta zauna gefe fahad ya matsa yabata wuri kanshi kasa, ganin halinda faseelat ke ciki ta fara salati jikinta nata rawa fuskar faseelat kamar ba tata ba ga jinin da yake jikin zanenta daba a sauya ba, ummi ta juyo ta kalli fahad tace "wai miyasameta ne accident tayi komi? "

Fahad yayi shiru kanshi kasa, ummi tace "I'm asking u meyafaru? "

Fahad yace "accident ne"Muryarshi a sarke


ummi hannunta na rawa ta kaishi bisa kan faseelat ta shafoshi hawaye suka gangaro mata,

omer tunda ya shigo yaga halin da take ciki ya rungume hannayenshi zuciyarshi awuya se cije lips yake dan ya riga yagama observing abinda yafaru,


Suna haka for some minutes har lokacin fahad na zukunne se amira tafado mai arai yadda Aisha tafita daita batako numfashi ya dago kai dasauri,

ya yunkura ya tashi jikinshi a mace yabar dakin ,ya nufi office din doctor okato,

Omer yakara matsawa gaf da gadon ya kurawa fuskar faseelat ido besan lokacin da hawaye suka zubomishi ba,

Ummi da take dafe da kanta tana hawaye ta waigo da kanta tace "omer kaina ya kulle wane irin accident ne wannan?jibarta duk yadda takoma lokaci daya kamar ba faseelat dita ba"

Omer jijiyoyin kanshi awaje yace "bawani accident ummi duka ne ya meda diyarki haka tun kafin bikinsu yafara marinta amma faseelat sonshi be bari taga laifinshi ba namata magana seta nunamin bazata iya barinshi ba, ki dubata sosai ga wasu tsoffin tabo nan ajikinta wanda nasan ba dasu tayi aure ba "yaida maganar dakyar kamar ze kuka,


Ummi tajuya wurin faseelat tafara kallonta daga sama zuwa kasa duk ga sashin belt nan a wuyanta be ida bacewa ba, ga wasu jikin kafafunta, bata damu da omer dake tsayeba ta dage zanen jikin faseelat sama nanma duk sashin belt ne, hawaye suka gangarowa omer,

ran ummi bace ta kalli omer tace "zoka zaremata wannan jinin dake shiga jikinta ka dauketa mutafi wani asibitin inason diyata ban bashi ita don yakashemin ita ba "

Ta matsa ta bashi wuri omer ya zare jinin ya sargafe shi ya dauki faseelat suka fita daga dakin sunata sauri,

sede bello yaga sunfito daita yabisu yana wa omer magana "ina zaku kaita kubarta plsss tana cikin hali "

Omer ko jinshi bayayi bello nabiye dasu saboda ganin bello securities basu Hana ba suna zaton an sauya musu asibity ne har bakin mota ummi ta bude mishi yasa faseelat itama tashiga ya kulle kofar, ya juyo wurin bello ya dafa kafadarshi yace "karkadamu zamu kaita better place thanks for your help "

ya wuceshi ya shiga motar yajata da gudu suka fita asibityn,

bello ya dafe kai yace "what I put my self into?"



daga alhayat specialist hospital suka wuce turai yaraduwa daita, anan ma a emergency aka amsheta ba jimawa aka fara dibar jinin omer akasa mata, kuma ana bukatar leda biyu,




fahad wurin likita ya shiga doctor yace mishi ya zauna yaki yace yanason sanin dakin da akai admitting amira,

doctor ya fadamishi dakin, fahad yafita ya nufi dakin ,

Yana turawa Aisha da tai tagumi ta dago ta kalleshi shima ya kalleta.





Insha Allah angama samun tsaikon posting bazan ko numfasa ba se na kai karshe mahakurci mawadaci ,kungama hakuri insha Allah 😍matsala tazama labari.
➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰







By







*MAMAN MAMY*
*(SHALELE)*




✍🏽✍🏽 *GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION*✍🏽✍🏽✍🏽

We are bearer's of so golden a pen🖊
We write assidiously perceiven no pain
So magical
Our creative golden pen🖊
Be hold our words
A product of our pen🖊
Savour our words
For it will cause you no pain.✍🏽


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/





7⃣1⃣





*Dedicated to maman nour, soupnass, ikra rukayyat, maman 4H,hauwa lawal,kucigaba da comments*💓





Jiki a mace ya shigo dakin tabishi da ido tanata kallonshi mamaki kawai yake bata yasha jibgarta amma bai taba yi mata wannan jina jinan ba, kenan itama watarana yakan iya yi mata haka,

Bakin gadon amira yaje yayi tsaye yanata kallon fuskarta da yadda take nishi zuciyarshi takara cunkushewa yanajin tsanar kanshi ,ya dade tsaye yana kallon amira Aisha batace mishi komi ba yajuya yafita daga dakin tabishi da ido,

Office din doctor ya shiga yaja kujera ya zauna yana yamutsa fuska yace "me ke damun amira? "

Doctor dake duba wani buk ya dago face yace "she's very scared and shocked abun ya girmi brain dinta ,that force her to fainted ,amma she'll be okay, "

Fahad yace "what about my wife? "

Doctor okato yakara gyara zama yace " sakamakon dukan da akamata sosai tayi miscarriage sannan taji ciwuka sosai tana bukatar kulawa da lokaci kafin tasamu lpy "

Fahad ya daga kai ya hadiyi miyon bakin ciki,

Doctor yace "as ur family doctor I want to advise you, dukan mata baya taba kawo gyara sede yabata, mata wani lokaci they're crazy se ana kai zuciya nesa ana kaucemusu amma duka bedace dasu ba saboda they're weak , ina maka jajen rashi da kukayi Allah ya bata lpy"
(wani lokaci sekaga Christian da soft heart kuji yadda yake bawa fahad shawara)

Fahad yace "thanks you"

yatashi yafita yanajin duk duniyar tamishi zafi,


omer yakira abba yafada mashi suna asibity kuma ana bukatar jini ba bata lokaci segashi asibityn aka dibi nashi dana abul, aka cigaba da sawa faseelat dake kwance tana nishi,

Duk kansu hankalinsu tashe abba yakasa yadda da abun da yake gani,

ummi dataci kuka tagaji tacewa abba "wlh seya saketa yata bazata zauna da meduka ba, wannan shine karshen zamansu"

abba yace "kiyi hakuri asiya amma kidena rantsuwa cikin bacin rai, amma ni kaina bazanso takoma gidan shi ba"


ummi tace"hmmmmm"!


fahad dakin da akai admitting faseelat ya nufa

Please Login or Register in order to submit comment