Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kunya, bama agabana ba hargaban abbanku ko? "

Faseelat ta girgiza kai "ummi dan Allah kubari na aureshi "

ummi tace "ahaf tunda kinji kingani ai shikenan Allah yasa alheri iyakar abunda zamu ce kenan "

Abba yana kallon faseelat yace "tashi kije "ta tashi tafita,

Ya kalli ummi yace"mutayata da addua kawai Allah yasa hakan ne alheri"

hannun ummi kan gemu tana mamaki tace "amin ya Allah" tana kadakai dan mamaki,


akan hanya fahad se tunanin yadda yaga gidansu faseelat yake duk da ginin cement ne amma ya tsufa, acikin ranshi yake shawarar canzamusu gida daga cikin gidajenshi,


Se marece ya koma gida, kodayaje aisha batanan tafita, yakada kai kurum dama da mommy takirata inde baya gida tafiyarta kawai takeyi sede ya samu batanan,

Se dare ta dawo amira ahannu tana bacci ,yana cikin balcony ya taso ya amsheta suka shiga ciki se akan hanyar shiga takecewa "mommy ce takirani anty kulsum ta haihu shine muka tafi tundazu muna asibity se yanzu muka dawo ,ta samu baby boy "

Yanata tafiya yace "Allah yaraya "tace "amin"


Tunda tashiga take ta kai kawo tai wanka ta shige salloli,

shiko yana saman bed yajawo computer dinshi yana aiki, yana cikin aikin faseelat ta turomishi pic Data dauka da dayan color da yasiya mata ,ya bude pic din yana kallo rigar is maroon irin robar nan ce irin kayansu na yan can tabi jikinta sosai ta mata dasss kamar dan ita aka yisu ga pic din andauketa from head to toe ta dan juya kadan wanda har hips nata ana gani,

ya kure pic din da kallo yanajin many emotions, yana tunanin kila dan takarasa shi ta turomishi pic din,

Yanata kallon pic din bako kyaftawa gabadaya ya rikice hannunshi biyu adunkule akasan habarshi,

Har Aisha tagama sallolinta taje gaban mirror ta shafa perrfumes dinta tasaka rigar baccinta da wando ta juyo tana kallonshi taga baaikin yakeba tunani ma yake, yadda taga yakure system din da ido dukda bata cika bin aikinshiba amma yasa ta zagaya ta bayanshi tai tsaye tana kallon computer din,


Abinda idonta yagani ne ya tada mata hankali gabanta ya rika harbawa fat fat!!!

Jikinta yadau rawa koina tafara ja da baya tana jawo numfashi da karfi,

Jin nishi nishi yasa fahad ya juya yaga aisha nata kyarma tana ja baya,

Cikin tsoro ya mike yana kallonta ,

Har takai karshen bango tanajinta jikin bango ta zukunna ta dora hannu biyu tafasa tsuwwar da fahad besan lokacin da yakai wurinta ba yariko ta yana "sorry Aisha take it easy please "

Jikinta na cigaba da rawa cikin rarrabuwar harshe tace "fa..fa....see.... Lat.... Ce..... Fa......A...com. ..pu.. Ter...dinKa.... KaKe..... Kallon....pic......nata "tadora hannu abaki tana fiddo ido,

Ya rumtse ido ya zukunna gabanta yahade hannu biyu yace "kiyi hakuri Aisha ki saurareni "

Itako kojinshi batayi tana ta tariyo maganganun faseelat, "harna fara son wani daban , anty soon de zanyi aure nima nahuta dakirana jawara da kike "sune maganganun datake ta tariyowa, that means tun tanada aure suke tare, kuma shine Wanda zata aura.

ya jawota jikinshi yana fadin "listen to me aisha "


Tai kukan kura ta tunkude fahad daga jikinta tai waje da gudu tana kuka , yabita yana kiran "Aisha wait plss kitsaya karkifita dare ne "

Koda yafita har tabar gidn ko takalma babu bare dankwali,

Kusan karfe 10:40 tana fita tasamu mashin ta haye tana kuka da rawar jiki tafada mai yakaita malali quarters ,


mashin na ajiyeta ta dira tafara buga gate din gidansu da karfi tana kuka,

megadi yazo yabude da katuwar gorar shi ahannu,

Tabanka aguje ta shiga cikin gidan,

Me mashin ko kotsayawa amsar kudi beba yajuya, don ya tausaya mata

Kannenta biyu na kallo Tawuce su dagudu tafada dakin mommy, mommy na zaune tana waya kan bed aisha tafada jikinta,


Jikinta na rawa tace "mommy mommy kitemakamin faseelat ta cuceni zata auremin miji... ......"




tohwa ana wata ga wata πŸƒπŸ½β€β™€



inga ruwan comments woooo 🀣🀣🀣🀣🀣



Shalele takuce fansπŸ€—
[7/12, 11:01 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰



By




*MAMAN MAMY SHALELE*




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

✍✍✍✍✍✍✍
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*
✍✍✍✍✍✍✍


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*




4⃣8⃣




*dedicated to firdausi, FπŸ§•πŸΌkinsanme? Inasonki sister😍, kina sona kinga ko dole naso ki hausawa na cewa kaso me sonka,shiyasa nakamu over, fans kutayani son firdausi don nima inasonta, tadamu Dani matuka da zanwuce 9am bana online seta kira taji ko lpya nake, I love you FπŸ§•πŸΌ,my masoyiya*




Mommy tarika kallonta hankali tashe takamo fuskarta tace "ban fahimta ba, ki kwantar da hankali sosai kimin bayani"

Tana sheshsheka tace "mommy yaya aure zeyi kuma kawata ce, wlh faseelat ta cuceni ban cancanci haka daga gareta ba"

Momy tafara tafi tana salati tace "nashiga ukku ni faiza, yanzu yazanyi ne? Ke dan ubanki har wata kawa kikasamu wadda bansaniba? "

Ta daga kai tana kuka tana jijjiga mommy tace "dan Allah mommy kice karyayi aurennan wlh zuciyata bugawa zatayi, nide nashiga ukkuna faseelat ta gama da rayuwata "

Mommy tace "keda harkina da guarantee kan kawa? da har zaki saki jiki daita? To yanzu gashinan de kinaso kijamin asara inyi renon banza, nasaki jiki zansamu kudi Amman kinjawomin tsiya, kafin mahaifin fahad ya rasu ya mallaka mishi gidaje da filaye da gonaki da bansan adadinsuba, su ramlat su ukku bazasu samu rabin gadonshi ba shiyasa nasamu nahadaki dashi kinga komi de nawa ne akarshe Amman kinyi sakaci zekawo wata ta ragemin lissafi "


Aisha tace "mommy kihanashi plsss wlh bazan iya sharing dinshi ba da wata "

Mommy tace "aiko sede ki hakuri sanin kanki ne nariga nasaba mishi da goyon bayanshi akan komi, yanzu innace aa to matsala zaasamu saboda yana iya bijiremin gwara na yarda din yafi "

aisha tafasa kuwwa tadora hannu saman kai mommy ta jawota tana rarrashi tace "ki kwantar da hankalinki diyata baabinda ze faru a aurennan kede kirika bin shawarata sannan kirika fadamin duk abinda ake ciki "


Aisha ta cigaba da kuka mommy nata rarrashi tace "dole ki hadiye kishinnan ki nuna mishi kinason abunnan kinga zeji dadi yakara sonki kuma ko tazo ki kauda kai ga alamuransu seki zauna lpya, inkika yi haka se yakara ganin girmanki fiyeda da "


tana kuka tace "mommy wlh bazan iyaba ni ina kishin mijina sosai bazan iya dannewa ba "


Mommy tace "to hauka zaki tayi duk kisure mishi, ?kowane namiji fa inde zaiyi aurennan seyayi doki, kuma yanada damar auren mata hudu in yaso, kita hauka yadena sonki bahaka kikesoba, kinade gani yanda nazauna da babanshi komi atafin hannuna "

Takara volume na kuka "wlh faseelat setayi danasani inta auri mijina "


Mommy tace "aure kam kamar anyi angama ne, kedai kinyi kuskure, yanda mazannan sukai karanci bare naki da kowa zeso kikabari har tasanshi, kiyi hakuri kinji nasan kome zanyi akai "


aisha takara volume itafa inba auren akace anfasa ba bazataji dadi ba,mommy nata bada baki Amman ina,


Jiki sanyaye fahad yakoma cikin gida yana shiga amira tazo ta rungume tana kuka tana kiran mommy ya dauketa yana rarrashi ya dauko Key yasaka riga suka nufi gidan mommy tunkan hanya amira tai barci, shiko yanata sakesake,

Yana zuwa yayi parking ya sabi amira awuya suka nufi ciki

Yana shiga su sadee suka tashi sukai saman bene da gudu don sunajin kukan aisha su azatonsu ko jibgarta yayi ,

Bedamuba ya kwantar da amira kan kujera yana sauraron kukan aisha daga sama,

Ya kama hanyar benen cikin sanyin jiki, dama yasan bazaa kwashe da kyau ba,

Mommy nata bata shawarwari koji batayi tanata kuka ya shigo dakin, yana kallon fuskar mommy yaga yanayinta ya zauna gefen gadon yafara magana "dan Allah mommy kiyi hakuri bazan kara aurennan bane don inci mutuncin aisha ba, inason yarinyar ne kawai"

Mommy fuska a sake amma deep down tanajin zafi tace "rabu daita dana ai kai mijin mata hudune, ni nagoyi bayanka kaje kayi aurenka karka biyewa Aisha kishine ya rufe mata ido "

Yayi shiru cikin jin nauyi zaaiwa diyarta kishiya Amman bata damu ba ya kalli aisha ya sadda kai kasa,

Mommy tace "gobe nidakai na zanje naiwa kawunka magana ayi komi in time akawo maka matarka "

Yayi shiru bece komiba sede yana jinjina irin son da mommy ke mishi, ya matsa ya rungumo aisha jikinshi yana cewa "kiyi hakuri Aisha, zanyi aure ne kawai amma ketadabance kinada special place in my heart, ki kwantar da hankalinki plss honey"

Mommy na zaune na kallo shiyasa aisha bata fizge ba daga rikon da yamata,

Tana ta kuka taji hannun mommy ta tsunkuleta ta dago ta kalleta mommy tai mata alamun tai shiru da ido,


Aisha tadan rage kukan, mommy tace "kutashi kutafi Allah yamaku albarka diyana, kiyi hakuri aisha kishi jihadin mata ne se andaure "

Ya mike tana jikinshi yace "seda safe mommy "


Mommy tace "ka kara bata hakuri plsss ka kuma hakuri daita har ta sakko "

Yace "Nagode mommy "yanajin sonta da kaunarta yaja aisha sukafita,

Ya dauki amira suka tafi gida,

Aisha naganin amfito takara saka kuka hannuwa biyu saman kai tanayi tana dumumuwa "ni nabani na lalace ni aisha, wayyo Allah na ancuceni an ci amanata "

yana tuki sede yajuya kai ya kalleta yana mamakinta wasu dumuwan dashi takeyi sam bata bashi haushi ba har suka karasa gida,

Yana parking tabude ta banka cikin gida da gudu, ya girgiza kai ya dauko amira ya medata dakinta ya kulle yafito ya shiga dakin aishar,

Ya sameta tana ta wurgar da pillows tana hauka, cikin rarrashi ya rikota cikin kwantar da murya yace "Aisha plss stop all this kar kanki yayi ciwo, faseelat ba kowa bace in zan kwatanta ta dake, inasonki sosai Aisha kuma u knew it ki yi hakuri nasan namiki laifi plss pardon me my love "

Yazo ze kaimata kiss ta kwace daga rikonshi tana kuka tace "ni zakuciwa amana? Ni faseelat zataiwa haka after all I did to her? "

Taja tsokii tai wurin mirror tabude Jakarta ta fiddo waya, yana tsaye yana kallonta ta dannawa faseelat kira hannuwa na rawa,

Wajen 1am ne faseelat tayi barci bata kashe wayar ta ba kiran aisha ya shigo, cikin magagin bacci ta lalubo wayar takara akunne,

ganin andauka aisha tafara balai tace "marar mutunci marar amana faseelat ni zaki ciwa amana? Kirasa wanda zakiso se mijina? Dan kina diyar akuya ko azatona ke diyar arziki ce ashe bansaniba da katuwar karuwa nake tare kinci amanata kuma wlh bazan barki haka ba, kishigo cikin gidan se naci kutumar uwarki jakka yar iska "

Faseelat tuni ta wartsake tafara kuka cikin kukan take cewa"anty dan Allah kitsaya ki saurareni kiji me zance "

Aisha tace "bakida hankali da kike tunanin zan tsaya in saurareki karuwar banza karuwar wofi me bin mazan mutane... "

Kafin taida maganar fahad da kejin kalmar karuwar nan kamar ana zuba mishi wuta ya fige wayar yanajin kamar ya kai mata mari,

Ta riko hannunshi cikin kwaratsi take cewa "kabani waya ta kabani wayata in kara zagin shegiyar can, yanzu daddyn amira ni zakaiwa kishiya? Nice fa aisharka ur honey "

yazo ze rikota tai kasan bene tana kuka ya zauna dabass kan bed ya dafe kai da hannu biyu saboda tsananin sara mishi da yake,


Faseelat najin aisha takashe wayar tafashe da kuka me karfi, ummi da jin maganar faseelat tafito tai tsaye jikin window tanajin abinda aishar ke cewa,

ummi ta tura dakin tashiga tace "ke dama kinsan matarshi ne? "

Faseelat ta daga kai tace "eh inazuwa gidanta "

Ummi tace "amma baki kyauta ba faseelat ai wannan cin amana ne, yakuna tare daita kuma kizo ki auremata miji baki kyautaba gaskiya "

Faseelat cikin jan numfashi tace"ni aganina kowa da yadda Allah yatsara haduwarshi da wani, nita sanadiyarta ne Allah yasa nasanshi be kamata tayimin irin wannan wulakancin ba, saboda banida niyyar cutar daita ko na aure shi, inaganin girmanta bazan manta alherin da tamin ba"


ummi dake tsaye gefen bed tace "to Allah ya kyauta, tundade kinji kingani aishikenan amma kinde fara fahimtar yaki zakijeyi kenan, ita kuma bewar allannan kisamu bayan kwana biyu kikirata kibata hakuri in Allah yasa tayi shikenan, "

faseelat ta daga kai tana kuka, ummi namata kallon tausayi saboda batasan me diyarta zata tarar ba tace "kidena kuka ki kwanta seda safe munyi maganar "

Faseelat ta koma ta kwanta amma takasa bacci tanata tunani ta yanke shawarar gobe taje tabawa aisha hakuri su dedeta,


Duk yadda fahad yaso ya bawa Aisha hakuri taki hakura a karshe ya barta falon tanata wurge wurge ya shiga dakin amira ya kwanta ya jawota jikinshi, tunani be barshi bacci ba yana ta tunanin ita faseelat ya take ciki yanzu,


Se asuba bayan yayi salla bacci ya daukeshi itako aisha tana gama salla ta dawo falo ta zauna har tagaji da kukan sede azabar zafin da zuciyarta ke mata ta mikar da kafa tadan kwanta itama bacci ya dauketa amma ba me dadi ba,


Tun asubar farko faseelat tafito tana aiki ko tarage jin damuwa amma ina hankalinta yaki kwanciya tanata tunanin miake ciki yanzu,


Ummi na dakin abba dan befita da wuri ba,

Faseelat tai wanka tasaka doguwar rigarta orange color tasaka farin hijab ta duba wayarta karfe 9 dede ,batare da ta fadawa ummi ba tai wufff tabar gidan tanufi gidan aisha,

Aisha cikin dan gajeren baccinta taji karar door bell tana yamutsa fuska taje ta bude ,

Ganin faseelat tsaye tai mutuwar tsaye tanajin kamar ta shakota ta daba mata wuka kotaji daman abinda takeji,

Ganin tayi tsaye tana kallonta faseelat ta kutsa kai ciki tana tunanin kila su dedeta, ta zukunna gaban aisha kanta Kasa tace "anty nasan ni me laifi ce agunki dan Allah kiyi hakuri bansan taina zan fara fadamiki bane tuntuni cewar muna soyayya da mijinki....."


Bata bari takara saba cikin tsawa tace "keeee dan uwarki harkin isa kifadamin kina soyayya da mijina, karuwar banza kawai wato tunda kikaganshi kika like masa ko? To ki san dasanin nidake har abada wlh nayi danasanin saninki a cikin rayuwata "

Faseelat tafara hawaye tace "anty kitsaya ki saurareni plsss "


Aisha tace "kimaza kibarmin gida wlh kafin inci ubanki "


Faseelat ta dago zatai magana aisha ta rufeta da bugu ta koina, jikake fas! tab!duf!duf ,

Jin Azaba faseelat tafara ihu, cikin barci yaji ihu, ya farka zaune yakasa kunne inyaji da kyau muryar faseelat ce ,yace "oh my God "ya fita dasauri,

Tunkan bene ya leko yaga yadda aisha tahaye faseelat tana jibga ya kwatsa tsawa "keeeee aisha"

Koji batayi tana ta jibgar faseelat cikin sauri ya sauko daga kan benen ya janye aisha ya dauketa da mari a duka kumatunta, jikake tasss! Tassss,

Aisha ta dafe duka kumatun da hannu biyu tana kallonshi dan saura kirisss ta kife awurin,

Cikin sauri ya tada faseelat tana ta kuka ya rungumota jikinshi yana.........



*inajin dadin comments naku jiya anyi ruwan comments godiya lodi lodi, nima inasonku masoyana*πŸ’‹πŸ’‹


Wani sabon salo har team aisha ke da kwai yanzu πŸ˜‚πŸ€”


Team fahad πŸ’‹
Team faseelat 😘
team khalil bodariπŸ˜‚
Team Aisha 😍

Yayin team team ake saura team hajiya da team jamila πŸ˜‚



luv u always my fans dake koina πŸ€—
[7/12, 11:01 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰




By




*MAMAN MAMY*
*(SHALELE)*




✍🏽✍🏽 *GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION*✍🏽✍🏽✍🏽

We are bearer's of so golden a penπŸ–Š
We write assidiously perceiven no pain
So magical
Our creative golden penπŸ–Š
Be hold our words
A product of our penπŸ–Š
Savour our words
For it will cause you no pain.✍🏽


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



4⃣9⃣



*dedicated to those lovable group's*πŸ‘‡πŸΎ

*RAGGON MIJI FANS*
*RAGGON MIJI FANS 2*
*RAGGON MIJI FANS 3*
*UMMYN YUSRAH NOVELS GROUP*
*MUKARU DA JUNA BY MOMYN SAUBAN*
*NOVELS ZAFAFA BY DR FATEE*
*MY FORUM GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION*
*MOMMY'S NOVELS GROUP BY SHALELE*

*THIS PAGE IS ALL YOURS FRIEND'S ACIGABA DA COMMENTS KAWAI*β›ΉπŸ»β€β™€



*MANZON ALLAH (S. A. W) YACE :-lalle Allah ya rubuta kishi akan mata, da jihadi akan maza wadda tai hakuri acikinsu tana da lada kwatankwacin wanda yayi shahada.*



Yanajin wani irin ciwo a zuciyarshi, jintana ta kuka ya dagota yafara duba jikinta duk yayi ja abunka da farar fata ga gashinta duk Aisha ta yamutse shi cikin jin tausayi yakara rungumeta yana shafa bayanta,

Kwata kwata kuka yaki zuwa ma aisha tazuba mishi ido tana ta kallonshi ganin yadda ya kwakume faseelat kamar ze medata ciki yasa ta sauke hannuwa daga kumatunta tai hanyar kitchen da gudu ko seconds goma baaiba ta fito da sharbebiyar wuka ahannu tai kukan kura zata sokawa faseelat a baya, fahad yayi sauri ya rike kaifin,

Aisha tafara jujjuya wukar tanaso ta kwace ta sokawa faseelat shi kuma ya rike kuma still yana rungume da faseelat daketa kuka,

Dandanan jini yafara diga Kasa kan farar hijab din faseelat, ganin jininshi yana zuba amma yaki sakin wukar Aisha ta saki wukar ta dora hannuwa biyu akunne ta kwara baki ta saki kuka tai saman bene da gudun tsiya,

Fahad ya Saki wukar tafadi kasa ya bude tafin hannunshi yana kallon yankan da ke jiki,

Faseelat ta zare jikinta tana kallonshi cikin tausayi ta duka ta dauki kallabinta dinta ta kama hannun fahad tana nannada mishi tana kuka, shi ko kallon fuskarta kawai yake yana ganin wautar ta na zuwa gidan a yanzu,

Suna haka aisha tafito tana kuka sabe da amira awuya tafita tabar gidan, duk sukabita da ido,

Seda tafita faseelat ta medo kallonta gareshi tana sheshsheka tace "I'm sorry bansan haka anty take ba nazata zata saurareni ne dana sani banzo ba "

Ya riko fuskarta da hannu biyu yana kallon cikin idanunta yace "aisha zata iyayin fin haka, karki sake irin gangancinnan cutie yanzu da bani nanfa? Wlh aisha har kashe ki tana iyayi saboda gabadaya ta haukace,"

Ya riko jikinta "jibo yadda taimiki da jiki"

Faseelat takara zubo da hawaye dan ta jibgu ba karya ,

Ta riko hannunshi tana fadin "it's hurting ko? "ta kalleshi cikin jin tausayi,

Ya rungumota jikinshi yana kwantar mata da gashin kanta yace "it's not idan nahadashi da zafin dukanki da Aisha tayi "

ta kwantar da kai kan kafadarshi tana hawaye,
Yana ta shafa gashin kanta tai breaking hug din tace "zan tafi gida "

Ya jawo hijab dinta da take dauke da drops na jininshi yasaka mata, sannan ya kalli jikinshi daga shi se boxer ya dago ido yace "bari na dauko key na kaiki "

Ya juya ya haye bene few minutes ya dawo cikin jallabiya da keys a hannu ya kamo hannunta suka fito daga cikin gidan ya bude mata motor ta shiga ya zagaya yaja sukabar gidan ,shide baba tsoho yanata kallon ikon Allah yadda yaketa ganin Aisha na ficewa da kuka yasan akwai matsala,


Suna kan hanya yana tuki da hannu daya hannunshi daya kan cinyar faseelat, tunda suka fito take ta kara zubda hawaye,

Ya kalleta ya meda kai kan titi yace "kiyi hakuri cutie ki dena kuka ,Aisha bata isa ta hanani aurenki ba inasonki sosai fiyeda yadda zaki harsaso, ki kwantar da hankalinki aisha zata sauko insha Allah "

Faseelat zuciyarta zafi kawai take yadda Aisha ta wulakantata ga zafin yankan da taiwa fahad da takeji kamar ita akaiwa,
Ta Kalli hannunshi dake kan cinyarta
Tasa hannu ta rufe fuska jin kukan da ya taho mata tafarayi tana jan numfashi,


Fahad ya dauke hannun daga kanta ya shafi kanshi zuwa sajenshi ya fitar da iska me zafi daga cikin bakinshi gabadaya Sun caza mishi kai yace "cutie ya kikeso nayi ne? Yanzu kina ganin zan bari kitafi gida kina kukannan? Kiyi hakuri plsss"

Ta daga kai ta jawo hijab dinta tafara share hawayen dake zubomata tana sharewa wasu na zubowa,

Ya girgixa kai ,har suka kawo kofar gidansu, Ta bude zata fita yace "kode nakaiki asibity ne ko akwai inda ke miki ciwo? "

ta girgiza kai cikin muryar kuka tace "thank you "ta bude tafita ta shiga gida dasauri,

Yakara murmuxa gashin kanshi kanshi na zafi sannan ya tada motar ya nufi gidan mommy,

Faseelat dasauri ta shiga gida ummi da tundazun ta duba bataga faseelat ba ta ga wulgin faseelat dasauri tafito daga dakin abban tabi bayan faseelat da kallo kayan jikinta a cumumuye ga jini saman kan hijab din zuwa kasan hijab din,

Hankalinta ya tashi tabi bayan faseelat, lokacin faseelat ta yaye hijab din tahaye can karshen gado ta hade kai da gwiwa tana kuka,

Ummi ta shigo dakin tana kallon gashin kanta cumimiye tace "kee daga ina kike "

Faseelat ta dago tana raba ido tafara nazarin me zatacewa ummi,

ummi tace "dan ubanki ba magana nake miki ba? "

Faseelat ta fara yarfa hannuwa tana kuka,

cikin zafin rai ummi ta haye kan gadon ta shakarota cikin tsawa take cewa "bazaki fadamin ba ne dan ubanki daga ina kike? "


Abba yafito daga daki jin kakari da fadan ummi yayi sauri ya shiga dakin ummi ganin ta shakare faseelat yayi sauri ya je ya janye faseelat din yana kallon ummi yace "haba asiya kibari mana aibata haka zaki tambaye ta ina tajeba "

Ummi tace "alhaji yarinyarnan harta san takwasa taje wurin saurayi? Yaga ma tumurmusarta ta dawo tana kuka, jibi hijab dinta "ummi tajawo hijab din tana nunamasa tace "duk jinine jiki wlh faseelat ta iskance tunda har taiya bashi kanta kafin aure "

Faseelat ta dago tana zare ido jin abinda ummi ke cewa,

abba cikin mutuwar jiki yakebin faseelat da kallo duk ta harmutse,

ummi tace "nikam nagaji alhaji dan Allah kasamu yaronnan kace ya turo tunkan ta jawo mana abun kunya"

Abba bece komi ba yabar dakin ummi tazo zata kawowa faseelat bugu faseelat ta kauce tana zare ido tace "wlh ummi banyi komi ba, naje bawa anti hakuri ne, shine ta yankeshi a hannu amma wlh baai komi ba "


Ummi cikin rashin yarda tace "gafara can da Allah ni zakiwa karya, ko ni makauniya ce? ke kikasani dan wlh ko aurenki yayi bazaki wata daraja ba sakarai kawai yo miki so hauka ne da zaki je kibashi kanki, kin kyautawa kanki ai "


Fuuu tabar dakin faseelat ta fashe da kuka ta jawo pillow ta danne kanta dashi ta cigaba dayi,



ummi nafita bataga abba ba har yabar gidan takoma dakinta ta buga tagumi zuciyarta na zafi, tundazu maganar da sukeyi da abba akan faseelat ne don yaji abinda yafaru jiya Sunata neman mafita sega sabuwa ta billo,


Aisha nashiga cikin gida takara sakin kuwwa da mommy dasu ramlat sukayo waje, sadiya tai sauri ta amshi amira daga hannunta,

Aisha ta rungume mommy tana kuka,

Mommy tace "wato Aisha bazaki bi shawarata ba ko? Yanzu mi yakawoki da safennan?"

Aisha na kuka tace "faseelat dince wai tazo bani hakuri shine nahauta da duka ina cikin dukanta shine yazo ya mareni shine na dauko wuka zan soka mata shine yarike da hannunshi duk yaji ciwo ahannun "

Hjy tace "wato de bakijin magana ta kenan ko? yanzu da kin kasheta fa? Kema ba barinki zaaiba, nace kiyi hakuri kibar lura da abubuwansu kinki, inaji miki tsoron ya sake ki dan masu irin wannan haukan da saki suke karewa, kinga shikenan se ita wasila take kowa tasami yadda take so"

Aisha tace "wlh bataisa ta rabani dashi ba "ta cigaba da kuka,

Ramlat dake gefe tace "kinyi dede anty gwara da kika ci ubanta da kyau "

Mommy ta banka mata harara tace "tashi kiban wuri "

Ramlat tatashi tabar wurin dama sadiya bata zauna wurinba tunda ta amshi amira ta wuce daita ciki ta kimtsata,

Mommy ta medo hankalinta kan Aisha taja ta tazaunar daita kan cushion tace "haba Aisha inafada miki abinda yakamata kiyi kina kaucewa, kiyi hakuri kibari ayi auren karkimanta fahad a tafin hannuna yake ya daukeni tamkar uwa, ba abinda waccan zata fiki awurinshi inde zakibi shawarata "

Aisha takara saka kuka mommy nata ban baki amma taki denawa,

Seda fahad yafara zuwa hospital akai mishi dressing sannan ya taho gidan mommy,

Yana shigowa ya gansu main pallow yaude fuskar mommy ba walwala dan taji zafi da ya mari diyarta akan wata,

Yazo ya zauna gefen kujera Aisha ta dago ido tana kallon hanninshi da bandage ta cigaba da kuka kanta kan cinyar mommy,


fahad yace "Aisha kiyi hakuri kizo mutafi gida banso na dakekiba "


Aisha batace komi ba mommy na kallonshi tace "inaganin kabarta anan ta danyi kwana biyu tadan samu natsuwa sannan se ta koma don naga duk tafita hayyacinta, kayi hakuri daita da duk abinda zatayi anan gaba, nide namata duk nasihata taki ji "

Fahad gabanshi ya fadi don be tunanin zeiya 2days batare da matarshi ba wannan nema yasa yake tafiya daita duk inda zashi,


Cikin rarrashi yace "Aisha kiyi hakuri mukoma gida, kinsan bazan iya

Please Login or Register in order to submit comment