Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

"oh ni bakina yajamin dama nai shiru na cigaba da kwasar romo na "

Su duka suka fashe da dariya,

Yanda take dariya bakaramin burgeshi yakeba, yayi shiru yana kallonta cikinso da kauna,

Jin yayi shiru itama tai shirun ganin ita yake kallo suka kure juna da kallo dukkansu sunajin feeling like to hug thereself,

itace ta dauke ido, sannan shima ya dawo tunaninshi cikin inda inda yace "I love you cutie "
Ta kalleshi ta sakarmai murmushi tace "I love you more"

Jiyayi kamar yakai mata kisss yayi sauri ya dukar dakai kamar me nazari,

Faseelat na kallon sumar kanshi dake kwance takatse shirun da "where's my angel?"

Ya dago yayi murmushi yana jindadin yadda takeson yarshi yace "tana gida, tana missing naki sosai, wani lokaci takanwa mommynta kuka akaita gum anty ita "

faseelat tai murmushi tace "I'm missing her too, inaga zanje ganinta very soon "

yace "baki tsoron aisha tagane muna soyayya? "

Faseelat ta girgiza kai tace "a, a banajin tsoro, bana tunanin akwai abinda zeban tsoro inde akanka ne, anty nasona nasan zata fahimceni, "

Yace "hmmmm"cikin ranshi yana cewa "bakisan true colors na aisha ba"

Ta katseshi da cewa "komiye de ni inasonta saboda ta dalilinta na sanka, and saboda kana sonta saboda inason duk abinda kakeso "

Ya cije lips yace "really? "

Tace "eh, insha Allah nida anty zamu zauna lpya bawanda zeji kanmu "

Yayi murmushi ya girgizakai yace "I wish so "amman yana ganin wuyar abun,

Sunata fira kusan 40 minutes ya zaro akwatin zoben da yasiya mata ya bude, tace "Wow" tana zaro ido da rufe baki ganin haduwar zoben na diamond me shegen kyau,

Yakara matsawa kusa daita yace "here's our engagement ring,plsss let me put it on your hand"

Tai mai wani kallo tana murmushi ta make kafada tace "nagano wayon naka, so kake katabani hankalinka ya kwanta"

ya kalleta yayi guntun murmushi yace "don't take me wrong Allah my intention is not to do that ,kawai I want to put it on you "

Tace "ban yarda ba "

Ya rufe akwatin ya dora akan cinyarta yace "alright have it "ya dauke kai

Ya tamke fuska tatsaya tana kallonshi feeling sad ya juyo yana kallonta yace "I want to go back home"

Tai fuskar tausayi ta dauki zoben ta dora a kan lap dinshi ta dora hannu kan dayar,

Tana mishi good look tace "feeling happy now? "

Yayi murmushi ya bude akwatin ya zaro zoben ya dago hannunta yanajin wani diffirent soft ya saka mata zoben,

Ta lumshe ido har yasaka mata tanajin nice bazato taji yayi kissing din hannun ta bude ido dasauri jin yarrrrr jikinta,

Idanunsu suka hadu yana mata love looking yace "will you marry me? "

Tanata kallonshi batare data saniba bakinta ya furta "I'm ready to marry you "

Fahad ya Saki dariya yana kallonta tai sauri ta dawo tunaninta ta rike baki not knowing me tace yake dariya,

Ya dago "inasonki me kyau da duk wani abunda kikai "

Tai dariya ta rufe fuska yace "yanzu zankoma, very soon zan aiko parents nawa yanzu mufita inbaki tsarabarki "

Tace "thank you "tana kallon hannunta

Yace "u r beautiful kome kikasa dole yamiki kyau "

Tai murmushi ya bude yafita itama tafito ya bude gidan baya ya dauko ledar ya mika mata,

Ta amsa tace "Nagode "tana murmushi

Yana mata kallon shaawa yace "I'm going "

Tace "bye take good care of yourself for me "

Ya daga kai kurum, taki tafiya yace "just go sekinshiga gida zantafi "tai murmushi ta juya tana tafiya,

Yabi kugunta da kallo da suke sababurna baburna πŸ˜‚πŸ€­ ya lashe lips yanata kara kallonsu, harta kusa shiga gida ta juyo ya sakarmata murmushi ta daga mai hannu tana murmushi ta shiga gidan, ya girgiza kai yana kara cusa lip abaki ya shiga mota yabar unguwar,

Faseelat nashiga gida taga ummi tsaye bakin kofa da hijab a hannu tace "ummi lpya inazaki? "

Ummi ta harareta tace "wace irin fira ce kuke haka har 1 hr Allah da bakishigo ba sede kiganni awajen"

Faseelat tace "yi hakuri ummi bawani abu fa dan Allah kiyarda dani ummi "

Ummi tace "bahaka bane ba rashin yarda bace ai se anayi ana duban bakin gatari ko faseelat "

Faseelat tace "hakane umminmu zan kiyaye, kinsan ummi muje kiga zoben da yabani da kayanda ya siyomun a Italy da yaje "

Ummi tace "hmmmm marar kunya muje nagani "suka wuce ciki,

Suka zauna suka fara fiddo kayan, wasu dogayen riguna biyu da turare da agogo, se dayar ledar sweet ne kala kala tun wadanda ya taba semata,

Ummi tace "kaya sunyi kyau, zobenma yayi yanzu idan abbanku ya dawo se anuna masa "

Faseelat ta kwantar da kai kan cinyar ummi tanajin dadi tana ta kallon zoben hannunta,

Ummi ta kalleta itama she's happy ganin faseelat din na son abun awannan karan,

Anahaka abba ya shigo ummi ta nuna mai kaya yagani,

Yace "naga kaya Amman waye wannan ya sunanshi aina yake, saboda inyi bincike kanshi donke ba budurwa bace da zaaita jan jiki gwara in dagaske yake yafito ayi aure shine "

faseelat kanta duke tace "sunanshi fahad dawood kuma a GRA gidanshi yake "

Abba yace "yanada mata kenan? "

Tace "eh "kanta kasa,

Ummi tabata fuska, "wai wannan yaron da bewuce 30 ba shine yake da mata har yana neman ta biyu? Gaskiya nikam abun ya siremin "

Abba yace "wannan ba matsala bace inde beda matsala, kuma ke faseelat ai kina iya zama da kishiya ko? "

Faseelat tai sauri tadaga kai ummi ta watsa mata harara tace "tashi kiba mutane wuri sakarai ni nan kinganni da kishiya ne? Kike wani murna zaki auri me mata "mtsssw


Faseelat ta tashi ta shiga daki


Abba ya duko kasakasa yace "angayamaki ita irinki ce me shegen kishi "yayi cikin zolaya.




abu a duhu abba wayasani ko itanma hakan take 🀣

ai comments ko infasa auren fahad ehe 😎
[7/12, 11:01 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰




By






*MAMAN MAMY*
*(SHALELE)*




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

✍✍✍✍✍✍✍
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*
✍✍✍✍✍✍✍


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*





4⃣6⃣





*another page for you rukayya haroun(maman nour)* *and erminatou*



Ummi tace "gaskiya alhaji bazan kai diyata gidan kishiya ba "

Abba yace "haba asiya be kamata kina magana irin haka ba, ita ai ba budurwa bace jawara ce kinga mawuyacine tasamu saurayi, dan Allah kibarta tunda tanasonshi karki sage mata gwiwai "

Ummi tace "ni ban iya kishi ba bare ita hakanan kaje aimaka wani mugun abun kana zamanka lpya "

Abba yace "shikenan tunda zancen kikeso bari nabaki wuri inkingama mitar kikawomin fura ta "

Ya tashi yabata wuri, ummi tace "shikenan se inki magana, yanzun intayi auren ko nima hankali na ba kwanciya zeba bare ita, tunda taji tagani shikenan Amman dole na dage mata da gyara na musamman in inaso tai daraja "


Ta tashi ta nufi dakin abba,

Faseelat nashiga daki ta haye gado ta kunna data cikin farin ciki,

Messages nagama shigowa tabude na maman amira wanda yanzu ta meda number ta da my anty , ta bude message nata "wai antyn amira kinmanta danine?ko duk zawarcinne ya boyeki?har munyi tafiya mundawo, in bazaki zoba kibani address naki zanzo ni saboda yarki ta matsamin "

Faseelat tai dariya ta tura mata "zanzo insha Allah zuwa jibi de nima ina missing naku "

Tafita tashiga contact na fahad ta turamishi "masoyi naji dadin kyautar ka, Allah yakara maka budi ya kareka daga sharrin makiya, kanata kara kyau miye sirrin ne?"

Ta turamishi tana murmushi ta kashe datar se barci,

Da laasar fahad ya kirata suka kara shan vedio call sannan sukai sallama,

Se dare ta samu tabude data bayan sunyi bankwana da habibinta, ta shiga message din maman amira "πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌthank se kinzo inanan ina zuba eyes"


Faseelat ta tura mata "don't mind"

Tafita alokacin fahad ya turomata reply kamar haka "amin cutie karki damu da kyauta da namiki bakomai bane danko raina kikeso zanbaki, kinason kisan sirrin?"

Faseelat tace "thanks eh inaso inji "

Cikin zolaya yace "aisha ce sirrin tana kula da service dina duk lokacin dana bukata ana bani "

Faseelat ta tura mishi "😏 To yayi kyau ,tunda ta isheka me zakai dani "?

Yace "I'm joking fa naga kinhau I just test you kinga kema kishinne dake zuwa zakuyi kuyita hadamin zafi "

Faseelat tace "aini bazanyi kishi da anty ba "

Yace "hmmm Allah yasa, gobe inanan zuwa fa, don kullum zanzo sekin gaji dani "

Tace "ai bazan gaji ba kazo yanzu ma "


Yace "kina tsoron nawa da rana ma yaaka kare? "

Tai murmushi ganin ya sauya zancen tace" good night sleep well 😘"

Yanagani yayi murmushi ya cigaba da aikinshi.


Da safe abba yaje yasamu baba babba akan maganar fahad yace zesa amishi bincike akansa,


Da marece faseelat taci gayu sosai tasaka kayan da ya siyomata, tafito ummi tace" kinyi kyau gaskiya ina zuwa halan? "

faseelat tace "fahad ne yace yana kan hanya "

Ummi tace "to waike bazaki ce yarika shigowa ba kullum fira a mota? "

Faseelat tace "to ummi zanmasa magana "

ummi tace "kibada asiyomiki dan juice mana kitafi mashi dashi yadansha "

faseelat tace "to bari nabawa Mubarak "

Ummi tace "sekinfa dage yarinya, don ba khalil bane wannan awaye yake kuma yanada mata "

Faseelat tace "nasani ummi bari naje "

Ta juya ummi tabita da kallo rigar duk tafito mata da shape dukda tanada fadi, kuma faseelat dan mayafin rigar kawai ta yafa,

Karfe 5 yazo ya mata waya tafito, be fito daga mota ba ta cikin glass yake karemata kallo, harta zo tabude marfin motar ta shiga,

Yaja numfashi ya sauke ta kalleshi tana turo baki,

Ya lumshe ido ya bude yace "cutie wannan kwalliyar fa?"

Tace "i did it just for you "tana marmara ido cike da jan hankali,

Yayi murmushi yanabinta da ido yace "thank you I'm happy, kinyi kyau sosai "

Tace "thanks ga ruwa"

ta mika mai water melon juice yana kallon kwalin yace "ni bazansha ba sede kibani a baki "

Ta bata fuska tana hararanshi yace "abinda aisha keyi kenan komi yimin take taimin wanka, tasmin kaya, ta bani abinci abaki, amma ke just kiban drink yagagara "

Ta harareshi tace "kabari kaga muyi auren ba wanka ba har goyonka ma zanrika yi "ya kyalkyace da dariya yace "sure? "

Ta daga mai kai yace "to fara tundaga yau mana mugani inda gaskene"


Ta tunzuro baki gaba tace "open ur mouth"

ya wage baki yana jiran tafara bashi,

Tai dariya ta bude marfin ta dora mishi kwalin abaki, ya dage yayita kwankwada, tai sauri zata janye caraf ya rike hannun alamun ta cigaba da bashi,

Ta dora mai yayi ta sha ta fiddo ido tana kallonshi tasss ya shanye yana meda numfashi ,tana mamaki ta sadda robar Kasa bakomi ciki ta dago tace "amma yau anty batai maku girki ba ko? "

yayi dariya yana goge bakinshi da handkerchief yace "yau nidakaina nashiga kitchen, bawani yunwa nakeji ba jindadin juice dinne yasa na shanye shi duka, kinsan duk abinda ya fito daga gunki dole yayi dadi "
Ya kashe mata ido daya,

Ta rufe fuska tana dariya,

ya dauko waya yace "kigyara nai miki pic, badani zaaiba bare kice danna samu na tabaki ne "

tace "OK, amma zamuyi da kai a wayata "

Ya saki murmushi yanajin dadi,

Ta dan fiddo ido ta matse baki ya dauketa, pic din yayi mugun kyau kalar rigarta purple da baki ,

shiru be dagoba yanata kallon bakinta da ta matse kamar zatai kisss,

Tana kallonshi tace "muyi atare mana "

cikin rashin sanin abinda yake yace "wait for me "

Ta turo baki ta matsa ta leka wayar yayi zooming bakinta yanata kallo ta fashe da dariya,

yayi sauri ya dago cikin dawowa tunani,

tana nunashi da yatsa tana dariya tace "Allah kacika jaraba dubi duk yadda idanunka suka koma "

Yayi murmushi ya jingina da seat ya juya ya kalleta yace "kamar kinsani kima shirya "

Ta canza maganar da matsawa kusa dashi ta dauke su pic,

Tana dauka shiko hankalin nakanta tana samu tadauka ta matsa tana dubawa tace "yayi kyau sosai, kasan wani abu zan dorashi a status da insta "

Yayi murmushi yace "idan kuma bakisaka ba ni zan saka akan nawa "

Ta rufe baki "rufani kasayani ban shirya abinda zancewa anty ba, gobe ma zanzo ganin yata anty ma tace tayi missing dina "

yace "gobe munada special guest kenan Allah yakaimu "

Tace "amin bari natafi se munyi waya"

Yace "ammmmm"ya fiddo 1000 rafas biyu daga gaban motor ya mika mata yace "kibawa yara "

Ta girgiza kai tana murmushi tace,"bana son kudinka kai nikeso"

Yaji dadin maganarta ya lumshe ido ya bude kafin yace wani abu tabude tafita tana mai murmushin dauke numfashi,

ya rumtse ido gam yanajin yadda zuciyarshi ke harbawa saboda tsananin sonta,

sannan ya bude yana kallonta har ta shiga gida, seda ya dau 10 mnt sannan ya tada mota ya tafi,

Yana kan hanya yamata transfer na 500,000,


faseelat mamaki ya cikata da tagani tanata tambayar kanta koshi bejin wuyar fidda kudine oho, ta nunawa ummi, ummi tace

"duk kan gyaranki zasu kare ai"

faseelat tai dariya

Next day tunda wuri faseelat tagama aikinta tatafi super market, ta kwashi kayan kitson yara danginsu beads ,robber band,robar kitso ,Brazil wool dasauransu sannan taje wurin kayan wasan yara,


Wata big teddy me kyau ta baby ta burgeta ta dauka taje tabada ATM suka cire kudinsu kusan 50 thousands teddyn yakama tana dauke daita ta hau napep zuwa gidansu Aisha,

Me napep na ajiyeta ta biya tai knocking ta gaida baba tsoho ta shiga,

Amira na wurin wasanta ta hango faseelat da gudu taje ta rungumeta,

Faseelat na dariya tace"daughter I really miss you "

Amira tai dariya tanakai hannu kan teddy faseelat tabata tace "dama nakine gashinan "ta mika mata amira ta rungume babyn,

Faseelat tace "ina anty? "

Amira hankalinta na kan teddy dukda tana da wadanda suka fisu setaga wannan tafi mata tace "she's inside "

faseelat tace "OK zo mushiga ciki "ta jawota suna tafiya tana kallon kitson kanta da yadan tsufa,

Suka tsaya bakin kofa faseelat ta danna door bell shiru takara dannawa seda akai 15 mnt sannan aisha tazo tabude tana murmushi tace "maraba da anty "tana kallon kayan jikinta,

Faseelat ta shigo tana murmushi,

faseelat ta gaida aisha, ta amsa tana mata kallon up and down tace "a, a! Jawara kinfaso gari kinga yadda kika kara kyau kuwa? "tana dariya

Faseelat tace "anty bawani kyau kina zaulayata ne "


Maman amira tace "Allah kinsauya gaskiya bazawarinki na kula dake "

Faseelat tai dariya tace "anty very soon de zanyi aure nahuta da kirana jawara da kike "

Aisha tace "Allah yakaimu muna murna ai, saboda mune kirjin biki "

faseelat tai murmushi,

Aisha ta mike "baride nakawomiki drinks, inkoma ciki daddyn amira nanan, bacci ma muke kika tadamu "

Faseelat tace "ok"

Aisha tatafi kawo mata drinks ita kuma ta bude jaka ta fiddo kayan kitson amira ta dauki wasu da zatai amfani ta ajiye sauran ta ajesu a kasa, tafara wa amira tsifa,

aisha nadawowa tagansu tace "yau ranar ta amira ce kenan naga harda katuwar teddy aka siyomata "

Faseelat tace "eh dan ita nazo "


aisha tace "to Nagode "ta ajiye mata ta haura sama,

Seda tagama mata tsifa ta danzuba drink tasha, ta daga kai tana kallon benen jin aisha shiru, wani malolo yatsaya mata a makoshi ta daure ta farawa amira Twisting,

Irin manyan nan ne masu guda ukku shaf shaf tagama mata aisha shiru bata fito ba, abun yabata mamaki kusan 1hr,

Cikin dabara ta kalli amira tace "kitsonki yayi kyau jeki gwadowa mommy "

Amira ta gudu tana taka step,

Ba jimawa segasu sunfito Aisha rike da hannun fahad shi kuma ya dauki amira yana tambayarta wa ya mata kitso dan besan faseelat bace har tazo,

Har suka sauko falo ahaka faseelat tunkan bene take kallonsu tanajin haushi,

Fahad na dago ido yaga faseelat,

Tayi kyau tana sanye cikin milk hijab da brown atamfa ya dan dauke ido daga kallonta,

Aisha tace "yaya kaga teddyn da faseelat ta siyowa amira nan gashi harda kitso tai mata "

Faseelat cikin jin haushi tace "inayini "

yace "lpy thanks for your care for our child "

Tai banza dashi ya juya yacewa Aisha "sena dawo "

Ta matsa tai masa kisss a cheek tace "take care of yourself"

Faseelat ta cika tai famm yana satar kallon faseelat ya fita,

aisha tazo ta zauna tajawo amira tana duba kitson tace "gaskiya kinyi kokari har kingama cikin sauri kiyi hakuri nabarki ke daya wlh se yanzu mukai wanka tundazu muna kwance "

Faseelat tace "badamuwa "tana yamutsa fuska tace "tafiya ma zanyi "

aisha tace "tunyanzu kitsaya mudanyi fira mana "

Wayar faseelat tahau ruri ta ciro ta duba taga fahad ne batare data dauka ba ta kalli Aisha tace "jirana akeyi dama nacika alkawari ne kawai "

Aisha tace "to shikenan Nagode kwarai faseelat Allah yabarki da masoyinki naga yanaji dake har iPhone 8s kike riko yanzu "faseelat tai yake,

Aisha tace "bari nakawomiki tsarabarki "

Faseelat tace "dan Allah anty kibarta ina sauri "


aisha tai dariya tace "aikuwa har gida zan kawomiki wasu English dress ne masu kyau nasiyomki naga zasuyi kyau da jikinki dan Allah kima bari nakawomiki daukosu kawai zan yi "

Faseelat tace "tom"

Aisha ta juya faseelat taja tsoki,

Can zuwa aishar ta dawo da ledar ta amsa tai godiya shaf shaf ta fita daga gidan,

Tana fita taga motar fahad awaje tana sauri tai gaba yabi bayanta da motar,

haryakai setin ta ya rage glass yace "kishigo in kaiki "

Tai banza takara sauri,

Yakara binta yana cewa "meyafaru ne wai? Kishigo mutafi "

Takarayin gaba, cikn fushi yakashe motar yafito yabita yajawo hannunta tana ta kokarin kwacewa ya sakata motar yaja yabar unguwar,

Faseelat ta duke tafashe da kuka me cinrai,








kujimin iko seta hanashi soyewa da matarshi 😎



team faseelat de πŸ’‹
[7/12, 11:01 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰



By





*MAMAN MAMY*
*SHALELEπŸ€ΈπŸΌβ€β™€*



✍🏽✍🏽 *GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION*✍🏽✍🏽✍🏽

We are bearer's of so golden a penπŸ–Š
We write assidiously perceiven no pain
So magical
Our creative golden penπŸ–Š
Be hold our words
A product of our penπŸ–Š
Savour our words
For it will cause you no pain.✍🏽


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


4⃣7⃣




Yana tuki yana jiyowa yana kallonta saboda mamakin abinda yasakata kukan kawai yake,

Ta cigaba da kuka tana sheshsheka, cikin jin ciwon kukunnata ya gangara gefen titi yatsaya, ya kifa kai jikin sitiyarin motar zuciyarshi na zafi,


Faseelat batabar kukan ba don wani mugun kishi takeji yanda suka fito tareda aisha says it all sunacan suna soyewarsu ne,

Ya dago yana kallonta cikin jin haushi yace "wai me yafaru ne?hakanan sekita kuka ninasan banmiki komi ba, kifadamin mekikewa kuka "

Ta cigaba da kukanta tana rage volume din,

Ya matsa ya dago fuskarta yana kallonta,

Bata kalleshiba ta cigaba da zubda hawaye,

Yana nazarinta yace "cutie kifadamin damuwarki plsss banajin dadin kukanki "cikin rarrashi,


Ta daga ido ta kalleshi tana ajiyar heart tace "bakome kaina ne ke ciwo "

Ya girgizakai kawai yafara share mata hawayenta da hannunshi sannan yace "kishi ko cutie?"

Taki cewa komi ya kwantar da kanta kan kafadarshi ya jinginar da kanshi jikin seat din motar ya rumtse ido zuciyarshi na harbawa dasauri,


Bayan 3mnt tanata ajiyar heart tadena kukan cikin jin tausayin kanshi yace "faseelat meyasa zakimin haka? yakamata ace kina boye kishinki kefa kikace min bazaki kishi da aisha ba yanzu me kike? Aisha ce fa ,aisharki haba for god sake ni yazan da rayuwata, faseelat akwai kalubale da yawa akaina, kullum cikin tunani nake taina zamfara fadawa aisha wannan batun, momy zata amince koko?ga shawarki data addabeni inason aurenki nankusa na rasa taina zanfara komi ya jagulemin hakanan kike ganina Amman ni nasan me nake ciki, yanzu bazaki temakamin ba ?ki kwantar da hankalinki kicire kishinnan ko nasamu kwanciyar hankalin yin abunda yakamata, saboda inkina fushi dani wlh duk tunani akanki yake tafiya "

faseelat ta daga kanta daga kafadarshi tanajin tasayinshi ta saka hannunta cikin nashi ta damke ya bude ido yana kallonta,

Tace "kayi hakuri plsss bazan sake ba"

Yana ta kallonta yace "yanzu haka zamuyi auren faseelat? I'm not going to take you to somewhere agida daya zaku zauna ya kenan, I want to build a peaceful family,idan kina haka yazaku zauna lpya keda aisha? Itama fa bansan ya zata dauki abun ba fa "

Faseelat tai fuskar tausayi tace "I'm really sorry nadena kishinka are you happy now? "


Ya juyar da kai yace "I'm not, ai bacewa nai kidena kishina ba, cewa nai ki rage ai u have to hide it now "

Ta cire hannunta daga nashi tace "naji nabari, kuma badole naji ciwo ba, nazo kunbarni a palo kuna ciki kuna...... Sannan kunfito harwani kisss zatai maka dan iskanci "

Yayi murmushin takaici yace "to miye aisha cefa maman amira "yaida yana dariya,

Ta harareshi tace "nasan kunayi basekafada minba ai"

Yayi murmushi ze kamo hannunta ta janye tace "kakaini gida ni "

yayi murmushi "ke yarinya kincika wayau time dinda kinason kiji dadin hannu na keda kanki kika rikoni nikuma in inaso seki hana? "


tai murmushi ta rufe fuska tace "kuskure ne akasamu "

Yayi dariya yana tada mota yace "inason irin kuskuren nan,"

yana hawan titi yace "bari muje na kaiki kidanyo shopping ko se nakaiki gida "

Tace "nide kakaini gida kawai banison shopping din "

Yace "I insisted "

Tai shiru yana tuki har suka isa big mall yayi parking ya fita ya budemata tafito suka shiga ciki,

Duk yadda yaso tadauki abunda takeso taki, sede shi yazabar mata kayan makeup da different perfumes dasu kayan tea ,

Yaje yayi payment suka fito suka kama hanyar gida, sunata labari kamar ba yanzu tagama kuka ba,

Suna zuwa kofar gidansu ya tsaya ya kashe motar ya kalleta yace "kigaidamin da kowa se nazo gobe "

Tace "tam Nagode hubby Allah yabiya maka bukatunka na alheri "

Ya lumshe ido ya bude yace "inason adduarki kicigaba damin addua "

Tace "karka damu ahakan bakomai bane akan wacce nakema aduk salla ta"

Yace "thanks Allah ya amsa "

Tai murmushi tafita,

Ya bude back seat din ya dauko ledojin yaji da nauyi yace "muje narage miki aiki banso ki expanding "yana dariya,

Tamai harara irinta masoya ta juya sunatafiya tare har bakin kofar gidan ya mika mata yace "bye"


Ta daga mishi kai kawai ta shiga, yana juyowa abba naiso wa akan mashin,

Fahad ya dakata har abba ya sauko ya zukunna har kasa ya gaidashi,

Abba ya amsa yana kallonshi, sannan fahad ya tashi ya tafi,

Bayan abba yashiga gida suna daki da ummi yace "anyi bincike kan yaronnan"

Ummi tace "to lpy de ko? "

Ya girgizakai yace "akwai matsala gaskiya ,wato shi mahaifiyarshi sun rabu da babanshi da dadewa kuma ba rabuwar arziki ba, shi yataso ne awurin matar babanshi, lokacin da babanshi na raye yahana mahaifiyar shi koda ganinshi saboda wulakanta yaron da tayi lokacin tana neman Saki, yanzu da yamutu tanata bibiyar yaron ya yafemata yaki ,saboda ancusa mishi kiyayyarta,yafison matar babannashi akan mamanshi sannan diyar ita matar babanshi yake aure, kinga akwai matsala kenan ace mutum na fushi da uwa, kuma yana tareda diyar ita wadda yakeso kinga faseelat zatasha wuya ne, kuma bazata hada kanta da kishiyartan ba tunda sunfi mu hali ganinake abun zezo da matsala, nima dazun alhaji ke fadamin Amman yace wannan duk ba matsala bace tunda suna iya sasantawa da ita mamanshin nangaba "


ummi tace "a, a gaskiya ni dama banason gidan kishiyarnan, bare ita wannan da yaruwarshi ce ,wlh da maganar da zanmaka ince kungama binciken ace yaturo dan naga ita faseelat ta haukace kanshi yanzu ma daga zuwa unguwa ta dawo da nikinikin kaya yasiyo mata "

Abba yace "Allah sarki ainima mungaisa yanzu har Kasa ya zukunna ya gaisheni "

ummi tace "ai yanzu sede ta hakura don abunnan bazeyiwuba"


faseelat dake bakin kofar daki kan tabarma tana kwance duk tanajin abunda ake wufff tatashi ta shiga dakin abba ta durkushe gabanshi tana zubar da hawaye tace "dan Allah abba karku rabani dashi, wlh inasonshi ni aganina shi abun tausayi ne, ansa mishi tsanar mamanshi kuma bayada wanda ze nuna mai gaskiya, dan Allah abba kayarda in aure shi kodan na temaka mishi "

Daga ummi har abba sukai kasake suna kallonta saboda mamaki, itako she don't care batamasan kunya ayanayin da take ciki ba ,

abba yace "faseelat karfa ai abunnan azo ana danasanin yinshi"

ta girgiza kai "insha Allah abba baabunda ze faru "

Ummi hannunta kan baki tana zaro ido tace "kajimin ikon Allah dama kina labe kinajinmu kenan, kuma yanzu faseelat tunda kinfara soyayya kin tattara kunya kin aje gefe kina ta zuba rashin

Please Login or Register in order to submit comment