Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kikeji kibari na dubaki"

Ya dauketa cak ya dora saman bed yayi tsaye yana kallon yadda jikinta duk yaji ciwo faseelat ta kauda fuska tana hawaye, ya juya ya fita adakin, yaje dakinshi ya dauko pain killer tablet pcm da ibuprofen da abonike ya dawo dakinta,

Tana nan kwance yadda ya barta ya bude fridge ya ciro cocktail ya hau gadon ya balli maganin ya tada ta zaune yace"kisha magani zaki ji sauki"

Faseelat ta kwaci maganin daga hannunshi ta shanye sannan cikin fada tace "niba wani sauki da zanji, yadda ka wulakanta ni gaban anty "

Yace "nace kiyi hakuri haba honey nine fa hero dinki"


Ta daga ido ta kalleshi ya marairaice fuska "kiyi hakuri plss pardon me "


Jin shiru be fito ba Aisha ta tashi ta haura sama ta duba baya dakinshi tai dakin faseelat ta tsaya bakin kofa ta kasa kunne,

Ya jawota ya bude murfin abonike ya fara shafa mata, tarika fidda numfashi saboda zafi tana fadin "ashhh, uhmmmmm"

Cike da tausayi yake shafa mata yadda take ta mommotsawa tana magana yasa shi jin shaawa ta taso mishi yafara shafarta cikin salo ,

Daga shafawa faseelat taji ya sauya salon,

Faseelat ta daga ido ta ballamai harara,cikin gajiyawa yace "I'm sorry please wai so nawa zan baki hakuri ne amma kinki kiyi nace kiyi hakuri insha Allah hannuna baze kara taba jikinki dasunan duka ba "

Faseelat tace "bazanyi hakurin ba dole ne senayi? katashi kabarmin daki kuma ko nankusa karkai tunanin zankara amincewa da kai"

Fahad ya tsura mata ido haryagaji da bata hakuri se yau yakara ganin hakurin da Aisha takeyi dashi can zuwa yace "faseelat ni kike kora daga dakinki ?saboda slice mistake kuma nabaki hakuri ai yakamata ki hakura, mijinki ne nifa dukda na zalunceki amma ai seki hakura Allah nason fa masu hakuri "

faseelat tamai wani kallo cikin tausayin umma tace "kai kana da hakurin ne ?ummanka tana ta zarya baka hakuri amma kaki hakura abu shekara da shekaru se yaushe ne zaka yafemata wai ko se tabar duniyar sannan ,this is what I want you to understand dole ne amaka laifi kuma dole kaima kayi ma wani seka yafemishi tunda kaima kanason a yafemaka"

Fahad yayi shiru yana tunani faseelat tace "think good,yesterday umma was crying asking for ur forgiveness tana tunanin kaine ka dauki wayar "

Fahad yayi shiru yace "OK I will think about it yanzu de ki yi hakuri kinji? "

Tace "bazanyi ba seka wa umma hakuri itama Ka yafemata just a single slap ne kaketa magana kanshi nifa u slapped me and beat me togather"

Fahad brain dinshi nakara tuno mishi abubuwan da umma ta mishi yace "ba marin ya fimin zafi ba bari na datayi nida mahaifina ta zabi wani shine yafimin ciwo "


Faseelat ta kama hannunshi tana kallonshi cikin kwantar da murya tace "it's ur fate, ko dayaushe musulmi yakamata ya rika daukar kaddara me kyau da Marar kyau kayi hakuri haka Allah ya kaddara ze faru "

"yanzu kayafema ta?"

Yayi shiru yana kallonta tace "idan ka yafemata ba karamar lada zaka samu ba, nima kuma na hakura duk da wannan likimon da kamin "ta Kalli jikinta

Fahad ya yamutsa fuska seda ya hadiye miyau yace "na yafemata amma saboda ke "

Faseelat tai murmushi ta rungumeshi tace "Nagode hero can I ask a favor? Again "

ya daga mata ido tace "please karika sauraranta in ta kira ka, koda na minty biyu ne hakan zemin dadi "

Ya cusa fuska cikin gashinta yace "I didn't promise you about that "
Ya fara mata kisses,

Aisha na bakin kofa labe tanajin su ,jikinta na rawa da tsananin kishi ta shiga dakinta tai dialing number mommy,

Mommy ta dauka tace "lpy kira goman dare? "


Aisha tace "ba lpya ba mommy wai yarinyar can daga zuwanta shekaran jiyar nan har tafara communicating da umman yaya, yanzunnan naji tana rokon ya yafe ma ummar abinda ta mishi "

Cikin jin haushi mommy tace "to yayafematan ne? "

Aisha tace "yace ya yafematan har ma rokonshi tayi wai ya rika daukar wayarta inta kirashi yace beyi alkawari ba"

Mommy tai dariya tace"ko ya yafemata rukayya bazata fini ba agunshi saboda hannuna ya taso reno nane, don haka ki zuba musu ido kawai, ya gidan naku yake dazun ya shigo gaisheni a harmutse"

Aisha tace "hmmmm anty salma ce tazo daga fitar ta naje na amshi amira tarike ta wai itama diyarta ce muka fara cacar baki wlh mommy sede naji mari a fuska ta, ashe yana kallo aikuwa yazo ya dauketa da mari yace tabani hakuri taki shine ya jibgeta ya fita "


Mommy tace "good yayi dede amma Aisha kidena yarda ko cacar baki tana hada ku saboda raina ki zatayi kibar shiga harkarta kuma kinsan inde ta salma zakibi kema jibgar zakitasha kinsanta batada tunani da hakuri ko kadan ki kama kanki kar in kara jin hakan tafaru"

Aisha tace "naji mommy "

Mommy tace "to seda safe ki kula da kanki "ta kashe kiran,


Aisha tai zaune tana tunanin baya, waifa faseelat ce yarinyar da take mata biyayya itace ta mareta, ta dafe kunci tana kara jin zafin marin,



Faseelat ta rike fuskar fahad tace "hero yau ba dare na bane ur heartbeat is there waiting for you, katashi ka tafi tunda dama a kagauce kake "


Yayi murmushi yana tuno dazun dan taji kishi kawai yayi haka don ya rama abinda tayi jiya, besan yadda ze kwatanta mata ba cewar besan tana waya da maza ba kosu dangintan,

Yaja hancin ta yace "korata ma kike ko? "

Ta girgiza kai tace "baniso anty taji badadi yadda kadade nan gwara katafi nasan tana can tana jiranka "

Yace "OK amma plsss kidena biyewa Aisha ki daure kirika bata girmanta ki mata biyayya kuma kiyi hakuri daita , banson tashin hankali a rayuwata "

Faseelat tace "insha Allah hakan baze kara faruwa ba, gobe zanma bata hakuri, a kullum bazan manta alherin da anty tamin ba yau ma bacin raine ya rufemin ido, itada yayarta suncimin mutunci bayannan anty tazo zata amshi amira awurina wai kada nabata mata tarbiyyar diya ni me bin maza da aure na, nafada mata kuskurene hakan da nayi amma me yahada haka da amira se cewa tai wai kila awurin ta gida na koya, naji zafi sosai da takirani mebin maza kuma tahada da mahaifiyata, wlh hero bantaba ko yin saurayi ba ,soyayyarka ce tarufemin ido har na manta auren dake kaina "


Fahad ya lumshe ido yanajin ciwon maganar da Aisha ta mata yace "naji kuma zan mata magana amma kiyi kokari kuhada kanku shine farin ciki na kuma kwanciyar hankali na"


Faseelat tace "insha Allah katashi katafi seda safe ,zanyi kewarka "

ya taba wuyanta "har yanzu da zafi jikinki fa "

Faseelat tace "ai ni na warke tunda ka yafewa umma, fatana de Allah ya dedeta tsakanin ku "


Yace "himmmmm diyar umma kenan "


Faseelat tai dariya ya mata good night kiss sannan yafita,


Dakinshi ya wucewarshi yana shiga yaga Aisha zaune tayi tagumi, bece mata komi ba ya haye gado ya kwanta ,

Aisha ta tashi tsaye kanta kasa taje bakin gadon ta zauna murya sanyaye tace "Dan Allah kayi hakuri yaya akan abinda ya faru baze kara faruwa ba "

Ya tashi zaune ya kalleta yace "meyasa zaki zageta eyeee, saboda neman fitina? inkin lura faseelat tana sonki son da take miki nema harya shafi diyarki ,laifine dan tana koyawa amira karatu? inda batason ki da bazata jata jiki ba ko da muna tare, kisani raini ne kike jawowa kanki kina zubda wa kanki girma awurinta duk biyayyar da take miki tadena"

Cikin ran aisha tace shegiyar fada maka abinda yafaru tai kenan ,ta jinjina tace "kayi hakuri yaya bazan sake ba, kuskure ne nayi "

Yana kallonta yace " Allah yasa amma kinbata min rai sosai"

Ta matsa ta haye saman cinyarshi tarika shafa sumar kanshi tana kashe ido da gantsaro kirji tace "ayya I'm sorry my sweetheart Allah yahuci zuciyarka" tarika lasar lips,

Yaja numfashi saboda yadda joystick dinsa ta motsa ya sa hannu yafara sabule mata riga,



yana fita faseelat ta shiga toilet tayo alwalan bacci tazo ta kwanta da temakon maganin datasha bacci ya dauketa,


ana kiran farko ta tashi jikinta duk yayi tsami sede fever din ta sauka, tana ya mutsa fuska ta shiga toilet ta gasa jikinta tafito ta balli maganin ta tsiyayi warm water a dispensa ta sha tazo ta kabbara sallar rakaatanil fajr,

Shima fahad yanajin kiran sallan ya tashi da yake Sun kwana suna jindadi yasa dole yayi wanka yayi salla ya nufi masjid da counter dinshi a yatsa,


faseelat nagama salla ta tafi dakin amira ta tada ta tai salla suka fara karatu,

kasancewar Monday ce amira zataje school yasa Aisha bayan tayi salla ta shiga kitchen tafara hada breakfast,

Yau dawuri fahad ze fita don basugama tattaunawa da bakinsu ba hakan yasa bayan yadawo masjid ya shiga dakin faseelat ganin suna karatu ya fito, yadanyi aiki a system ya tashi ya shiga wanka,

Bayan sungama karatu faseelat ta wa amira wanka tana saka mata kaya tace"me mommy tafi dafa miki kitafi school dashi? "

Amira tace "tafi soyamin indomie da kwai , amma ba sosai ba sede natafi da cornflakes golden moon, cupcake,snacks da dudu milk, amma mommy tanayo dambun nama takawomin ina zuwa dashi sosai "

Faseelat tai dariya tace "ke mi kikafiso?"

Amira tace "inason tuwon shinkafa sosai mommy bata mana tuwo "

Faseelat ta zaro ido tana dariya tace "tuwo kuma princess? "

amira tace "eh anty friends dina suna zuwa da diffirent food a school,amma ni nafi shaawar tuwon "

Faseelat tana gyaramata maballi tace "yau ko zaki ci tuwo "

Turo dakin da akayi ne yasa suka kalli kofar Aisha ce tai tsaye tana kallonsu zuwa tai ta shirya amira ta samesu haka ,

Faseelat ta sadda kai tace "anty ina kwana"

Aisha tace "lpya "ta shigo dakin ta shafi kan amira tace "tunda kinshirya muje kiyi break daddy ya saukeki don shima fita zeyi "

Taja hannunta suka fita akabar faseelat a zukunne, bayan Sun fita faseelat ta girgiza kai ta tashi ta shiga daki don kimtsawa,

Bayan tafito wanka tai makeup tana saka riga fahad ya shigo dakin fuskarta nata sheki ,

Faseelat ta sakar mishi murmushi shima da murmushi a fuskarshi yazo ya rungumeta ta baya tsamm,

Tace "washhh" saboda ciwon ta da ya fama,,
Ya saketa ya Kalli jikin nata da haryanzu yake jawur ya dafe goshi,

Faseelat tace"ina kwana? "

Yayi shiru cikin jin tausayi yace "ya jikinmu?"

Faseelat ta kalleshi tace"lpya ta lau hero inafatan ka samu sallar asuba "

Yace, "nasamu ai naji dadin yin sallar a cikin mutane, shiyasa nayi setting alarm na tashi "

Tace "shiyasa nake sonka sosai "

Ta ida jan doguwar rigar kasa,

Fahad yayi karamin murmushi yace "muje muyi breakfast ko? "

Faseelat tace "inazuwa zansameka kasan "
Ya kalleta ya juya, ta sauke ajiyar zuciya tariga tasan idan suka fita tare basu kyauta ba,

Seda sukayi nisada cin abinci tafito tazo ta zauna tai sarving kanta pepper meat tafara ci,

Tunda ta zauna hankalin fahad ya koma gunta ta burgeshi sosai yadda batai zuciya da amira ba kuma ta hakura dukda seda yasha fama sannan , se kallon yadda take taunar naman bakinta cikin kwanciyar hankali yake, ya gangaro da kallonshi a wuyanta zuwa saman rigarta da breast suka turo sama ya lashi lips dinshi,

Aisha ta kalleshi ta kalli inda yake kallo cikin haushi tace "yaya zakuyi lati fa it's to 8 "

yaja numfashi ya kalli amira yace "mutafi princess "
Ta sauka Aisha rike da jikar laptop dinshi ta rakasu suka shiga mota tana masu waving suka fita daga gidan,

Ta sauke numfashi ta koma ciki ba tsayawa ta haye sama tafara gyaran dakinta,

Seda faseelat ta koshi ta kauda kayan ta shiga gyaran gidan 9:30 tagama ta koma daki ta kwanta duk abinda take dauriya ce kawai take amma batajin dadin jikinta tunkafin ma ya jibgeta, tana ta tunani aranta har bacci ya dauketa,

Karfe 12 :40pm ta farka ta shiga toilet tai fitsari ta fito ta sauka kasa ta shiga kitchen Aisha na girki faseelat tace mata "sannu anty ko da akwai abinda zan kamamiki? "


ko waiwayo wa Aisha batai ba tace "babu"atakaice

Faseelat tace "to shikenan amma Dan Allah anty kiyi hakuri abinda yafaru jiya sherin shedanne "

Aisha tacigaba da aikinta tace "naji "

Faseelat tai shiru tana kallon bayanta jin yadda take ta amsa maganar kamar dole, batakara cewa komi ba ta koma dakinta ,tai kwanciyarta ta kunna data,


da daddare faseelat ta amshi girki da dauriya tai musu tuwon shinkafa miyar egusi ta shiga toilet tai wanka ta dawo tai simple makeup,

Fahad duk yabi ya zuzuce wurin kallonta dakyar yafita ishai yana dawowa sukai dinner,

Ya riga kowa tashi saboda he's eager yajishi cikinta,

gaban faseelat har faduwa yarikayi dan kar ta takurashi da tabarwa Aisha kwanan saboda batajin dadin jikinta samm,

bawani shirin bacci tana shigowa yafara romancing dinta tafara hawaye besani ba seda ya tubeta yakara ganin jikinta dake jawur sede kumburin ya sabe, seyaji yakasa yin komi ya jawota jikinshi yana rarrashi itako tafara kuka, dakyar ya rarrasheta ,ya ciro waya yakira doctor ya mata bayani tafada mishi sunan magani biyu daya tablet daya cream cikin daren yafita ya siyo su kafin ya dawo faseelat ta kwafe number umma wadda har yanzu tana nan a tsohon sunanta bad woman, awayarta tai saving da my in-law ,ta shiga contact na fahad ta sauyawa number umma suna da umma ta,

Yana dawowa ya shafa mata na shafawa yabata nasha, faseelat da kanta tace yaje wurin Aisha yaki suna rungume da juna sukai bacci can cikin dare shaawarshi ta motsa ya tashi yabar dakin ko 15mnt baaiba faseelat ta gane baya dakin ta bude ido, kasa kasa tanajin duminshi yana sabbatuwa Aisha,


Bayan 4 day's faseelat ta warke simul sede cream na bacewar tabo dataketa shafawa don ta samu tabunan su bace ,

Har yau fahad be daukar kiran umma kuma koda yaga sauyin suna yasan aikin faseelat ne se yabarshi ahaka,

Ranar jumaa ce tunda safe yafada masu karfe 3pm zai kaisu gaida mommy,

Bayan sunyi lunch suka shiga suka shirya yana zaune yana aiki Aisha tazo ta zauna tana sanye da riga da sket na lace da gyale a kafada, itakuma faseelat ta sanyo riga da sket atamfa da gyale sede ta yafashi ne tundaga saman kai, hannunta rike da amira dake sanye da doguwar riga,

Ya dago ya kallesu su duka ya meda kallonshi gun faseelat kayan Sun mata shape sosai komai awaje gyalen yayi shara shara ,ya meda hankalinshi kan computer dinshi sannan yace "honey queen kije ki sauya kaya "

Faseelat ta Kalli kanta tundaga sama har kasa ta kalli Aisha tace "hero miye illar kayan jikina? nagafa anty irinsu ne jikinta "

Ya dago yana mata wani kallo cike da kishi yace "eh iri daya ne amma ita be fito mata structure ba kije ki sauya "

Aisha ko kallonsu batai ba hankalinta na kan chatting,

Faseelat ta haye sama can zuwa ta fito ta doro Arabian hijab saman kayan,

Fahad ya dago ya kalleta, rigar tai kwance kan breast dinta, yace"kije ki sauya dressing nace"

Faseelat ta turo baki ta koma ta sanyo gownt da bakin gyale shi kuma cotton amma karami, ya kalleta ya Kalli hips dinta yace "basuyi ba"

Cikin haushi takoma ta sako English wears da t
Dubai hijab ,ya dago ya kalleta sunmata mugun kyau yace "go and change them "

Ta koma ranta cunkushe ta sanyo riga da single zane ta dora after sama ta fito, tundaga saman bene ya dago ya na kallonta breast dinta sunyo waje motsin da take wurin saukowa suma motsi suke tun kan ta sauko yace "ki koma ki sauya kaya kiyi decent dressing "

Faseelat ta duka ta kalli kayan jikinta ta koma ta sako doguwar riga tasa gyale sama tafito fuskarta kumbure tazo ta tsaya ya dago ya kalleta sama da kasa suma tayi kyau ciki, cikin jin kishi yace "wai ina hijabobinki na gida kije kisa su"

Faseelat tace "ni duk nabada su kuma bakasaimin irinsu ba "

Yayi shiru ya rufe laptop din ya tashi tsaye ya zaro tissue paper daga kan center table yazo ya goge lip gloss da faseelat ta shafa da dan maroon eye pencil da ta zizara, faseelat ta kalleshi tai tsaye,
Ya juya ya fita Aisha ma ta tashi tafita tanajin zuciyarta na tafasa,

faseelat taja hannun amira suka fita suma harsu fahad Sun shiga mota Aisha direct baya ta bude ta shiga, faseelat tazo ta shiga gaba ta rungume amira,

Ya kalli wuyanta dake bude da breast dinta da gyale ya rufe suna tsaye ,

faseelat na niyyar rufe kofa batare da ya kalleta ba yace mata "ki koma baya Aisha ta dawo gaba"

Ya Kalli Aisha ta madubi datake ta kyafta ido da yacika da hawaye,

Faseelat tanai mai wani kallo tace "amma ai yau girkinane kuma se laasar tayi yake komawa kanta "

fahad da kishi ya rufewa ido yace "ba abinda ya damen ki koma baya kuma daga yau ke zaki rika zama baya Aisha a gaba "


faseelat tai murmushin da yafi kuka ciwo ta sauke amira ta zaunar daita gefe ta bude murfin motar ta fita batako tsaya kulleshi ba tai cikin gida dasauri,

Fahad yaja tsoki ya bude motar yabi bayanta cikin zafin rai,

Aisha tace "aikin banza ai tunda tagama gano kana jindadinta shikenan kuma, mutum ya kwana ihu kamar mahaukaci mtswwwww "taja tsoki,

Amira ta juyo tace "mommy anfasa zuwa ne? "


Aisha tace "I don't know "tai shiru dan mugun haushin amira takeji yadda take likewa faseelat ta mata warning so baadadi amma kullum tana manne daita kamar cingam,itada ubanta duk sun haukace ,.



jumaat Kareem
[8/5, 6:12 PM] +234 815 712 7134: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰







By






*MAMAN MAMY*
*(SHALELE)*





https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*




*~We are bearer's of so golden pen🖊~*

*~we write assidiously perceive no pain~.*

*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*

*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*





6⃣3⃣




Dedicated to my fan's




Faseelat na shiga ciki tai zaman dirshan a kasan tyles ta rufe fuska da tafin hannuwa ta saki kuka, ba jimawa ya shigo fuskarshi tamau ya ganta zaune kasa rai bace yace "kee me kike nufi ne kitashi ki wuce mutafi"

Faseelat ta sauke hannuwa fuska jagab da hawaye ta Kalle shi tace "ba inda zanje kuyi tafiyarku"


Yace "are you crying? Kukan me kike? "

Murya na sarkewa tace "ba dole nai kuka ba, hero duk yadda zaka batamin rai sekayi miye laifina da har zakace wai kullum anty ce zata rika zama agaban motarka? Ni I don't care da zaman motar daga yau bazan kara shiga motar ba shikenan ko "

Yayi tsaye yana kallonta zuciyar shi na ciwo wai meyasa bazata gane ba?jikinta yana kyau da duk dressing shi kuma bayason wani ya ganta yayi shaawa,

Ta tashi zata haye sama jiki sanyaye ya riko hannunta batare da ta waiwayo ba ya kalleta yace "banason bacin ranki, kisani farin cikinki shine nawa banyi haka don ranki ya baci ba, banaso ne kowa yana ganinki I love you very much ina tsananin kishinki ne honey don Allah kidena sa wani abu a ranki "

Faseelat ta juyo ta kalleshi idanuwanshi jawur yace "kiyi hakuri mutafi mommy wants to see you, she's the one that ask me to take you there "

Yajawota jikinshi yasa handkerchief dinshi dake fidda sassanyar kamshinshi ya fara share mata hawaye yana kallon fuskarta yake cewa "kiyi hakuri ki zauna bayan kinji zansa ayo miki hijabs daga yau shikenan, amin hakuri kar zuciya ta tai ciwo kinji gimbiya? "

Ta daga ido ta harareshi ta danyi dariya yace "that's my sweet wife, mutafi to kije ki gano mommy ta matsu ta ganki "

yajata suka fara tafiya tana jikinshi faseelat tuni tafara tunani tana matukar mamakin yadda fahad keson mommy she don't think umma zata taba samun irinshi koda Sun dedeta ,

Fahad ya mintsili bayanta ta daga kai ta kalleshi yana dariya yace "I'm happy da kukan ki saboda ya temakamin wurin bata kwalliyar da kikai "

Faseelat tai dariya tace "bazan sake yi ba tunda bakaso "

Sunata murmushi a makale sukazo zasu shiga mota Aisha data hangosu haka tace "ji bassu wawaye kawai "

Yazo yabude wa Aisha gaba ya kalleta yace "Aisha come to the front seat "

Ta tashi tana ya mutsa fuska ta koma faseelat ta zauna baya amira ta tashi takoma bayan ya shiga yaja suka tafi malali quarters,

Suna shiga cikin gidan Aisha tai saman benen, faseelat ta zauna kan kujera ta dan Kalli yanayin gidan, ramlat dake zaune palo ta tashi tai room dinsu tana tabe baki ganin yadda fahad da faseelat suka zauna a kujera daya, amira ma bin bayan Aisha tayi tana kwalawa big mommy kira,

Acan ciki Aisha na shiga dakin mommy, mommy ta tashi zaune tace "aa har kunzo kenan "

Aisha tace "eh gashi can ya taho da matar so wai ta gaidaki "

Mommy tai dariya tace "ni nace yakawota ai, ai diyata ce yakamata nadamu daita,abinda nakeso yagane keda ita daya ne guna "

Aisha tai dariya tace "mommy bakida kirki wlh ni zaki hada da waccan banzar I hate her well the way I hate my death "

Mommy tace "ihmmm bari nafita ni harma kyauta zanmata don nakara samun shiga "ta tashi tsaye

Aisha ta fashe da dariya har da rike ciki tace "wlh ina mugun sonki mommy kin iya kissa da tuggu "

Mommy tace "abinda ake koyamiki kenan kin kasa fahimta daace kina nuna kina sonta ina tabbatar miki da sekinfi haka agunshi amma kinki"

Aisha ta tabe baki mommy tafita, sam Aisha bata iya acting,betrying ba in tanason abu to tana sonshi in taki abu kuma ko afili zata nuna,

Mommy tana taka step tana faraa gab zata sauko tace" maraba da diyata "

faseelat ta kara masgwadawa nesa da fahad ta sunkuyar da kai ,

Har mommy tazo ta zauna faseelat tace "mommy inawuni "

Mommy fuska sake tace "lpy lau diyata ya bakunta? "

Faseelat tai shiru mommy tai murmushi ta kalli fahad daketa kallon faseelat kamar ze medata ciki tace "fahad kabarsu nan zuwa dare seku tafi bayan kunyi dinner don nakara gaisawa da ita "

Yayi murmushi yace "tom mommy bari natafi akwai Wanda ke nema na "ya tashi ya fita,

Mommy tabi bayanshi da kallo ta yatsina fuska Batasan cewa faseelat na kallonta ta cikin gyale ba ,acikin ran faseelat tace "Allah sarki mijina ka dauku da soyayyar wadda bata sonka Allah ya medo hankalinka awurin daya dace, umma ce kemaka son gaskiya ba mommy ba datake acting "

Mommy ta kira jummala jummala tazo dasauri mommy tace "ki kawomata pepper chicken din da drinks"

Jummala ta tashi mommy tadan zauna tana latsar waya, bayan jummala ta kawomata ta tashi tahaye sama ta samu Aisha suka hada kawuna suna tattauna wa ,

Faseelat ta dau exotic ta tsiyaya tasha ta fiddo waya tana latsa,

Can zuwa sega ramlat tafito tazo ta zauna tana bankawa faseelat harara, so daya faseelat ta dago ta kalleta ta meda hankali gun wayarta,

Ramlat taja dogon tsoki ta tashi ta haye sama, faseelat ta dago tabi bayanta da kallo ta girgiza kai ta cigaba da abinda take,


faseelat nanan zaune anan tayi salloli, bayan ishai fahad Ya dawo lokacin kuma duk su mommy sundawo Palo suna kallo sunata dariyar daso da suke kallo acikin wani film tana cewa "ke ni namiji beisa yasani ciwon kai ba yo miye namijin?ban taba bawa namiji amana ba kinganni nan aure na 5 dukkansu dan ubansu ni na sake su da kaina basu suka sakeni ba yo MI akai akai namiji "

itakam faseelat abun haushi ya bata ,

yana kallon fuskar faseelat yazo Ya zauna faseelat ta sakar mai murmushi ya meda mata ,

Sukayi dinner sannan suka tashi zasu koma gida, mommy ta dauko turare me tsada dake a leda tabawa faseelat, faseelat ta amsa tai godiya suka tafi, sosai fahad yaji dadin kyautar da mommy taimata da kuma yadda ta tarbeta,

Suna shiga gida kowa Ya nufi dakinshi amira na like da faseelat ta mata wanka ta kwantar daita sannan ta shiga toilet tayi nata ta fito ta shafa humra dasu roll on ta saka sleeping dress dinta ta haye gado,

Tana charting fahad Ya shigo da katuwar leda a hannu ta tashi zaune tana gyara zaman rigarta,

Yazo Ya zauna gefen gadon idonshi akan breast dinta da

Please Login or Register in order to submit comment