Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

rabinsu ke waje, yace "honey ga hijabs din ki bada wadancan plsss "

Tace "karkadamu nima nafi jindadin hijab din akan wadannan "

Ya tashi Ya haye gadon Ya dora hannu saman breast dinta dake waje yafara shafawa yana lumshe ido,

faseelat tai murmushi ta kalleshi yadda idanunshi duk suka kankance ta janye mai hannu ya kuma medawa,

Faseelat tace "katashi ka tafi plsss banason haka "

Ya ware ido akanta yace "me ke bakiso? dan Allah kibari nadan yi wasa da babies dina wlh bana gajiya dasu bayan hq naki dake zoy ba abinda nafiso se su plsss let me suck them before leaving" Ya tura hannu cikin rigar yafara matsasu

faseelat ta lumshe ido ta bude tana matukar jindadin yadda fahad ke juyata Ya kware wurin rikita mata tunani ta daure ta zare mishi hannu ta kalleshi jiki mace tace "ni taka ce hero komai nawa is urs kuma zakaiya samun su kowane lokaci dan kullum cikin shiri nake amma ba yanzu ba, saboda zaka shiga hakkin wata ni kuma banason karika kauce hanya don inason mugudu tare mu tsira tare kabari gobe ne fa"

Ya lumshe ido yace "bazaki gane ba kwana dayan inajinshi kamar shekara "

Tai dariya tace "se hakuri, gobe inason natafi gida kasan jibi su ummi zasu tafi saudi shine nakeso inje muyi bankwana"

Nan take fahad Ya bata fuska yace "se dare zan kaiki tunda bankwana ne zakije"

Faseelat ta saki baki tana kallonshi ta marairaice fuska tace "haba hero wurin ummi ne fa wlh I'm missing her "

Ya kara tamke fuska tuno yadda take shagwaba wa omer wai tayi missing nashi ya sauka daga gadon Ya zuba hannuwa a cikin aljihu yace "ko kuma kinyi missing yayanki ba "

Faseelat ta kalleshi cikin mamaki tace "yaya kuma to mi yakawo yaya acikin maganar nan "


Yace "karki rainamin wayo zakisa bansan kina waya dashi ba, ki zauna kita mashi shagwaba wai kinyi missing dinshi "

Faseelat tace "haba hero yaya fa uwarmu daya ubanmu daya be kamata kana kishi dashi ba, kuma aiba laifi bane dan nace nayi missing dinshi saboda he love me so much he's gentle and caring, mun shaku sosai shima nasan yana missing dina dan Allah kabari natafi da safe da marece sena dawo saboda mugaisa da yanuwana ina missing dinsu all "

Haushi maganarta tabashi yace "dan iyayenku daya shi ba namiji bane seki zauna kita shashanci gabanshi yayi ta kallonki yanajin dadi,nafada maki se dare zamu tafi "

Ya juya yabar mata dakin

Faseelat tabishi da kallo tace"bangane abinda mutuminnan ke nufi ba fa "

Da safe suna dining fuskar faseelat ahade shima tashi ahade ta gaidashi ya mata banza amira ta kalli fahad tace "hero anty nagaisheka "

Faseelat ta zaro ido tana gumtse dariya, fahad fuska ta mau yacewa amira "I don't heard Her well just eat ur food "

Aisha haushi Ya cikata ta kalli amira tace "kar nakara jin wannan sunan he's ur dad call him daddy kina jina? "ta zare mata ido

Amira ta bata fuska tace "mommy ni inajin dadin sunan da anty ke kiran shine"

Aisha tazo zata tashi fahad Ya riketa tana hararar faseelat ta koma ta zauna,

Faseelat ta tabe baki ta tashi tafara gyaran gidan dan tunda tazo gidan Aisha bata kara dora ko da mofa ba da sunan gyara sede faseelat tayi,

tana gamawa tai wanka amira tazo suka fara bita ,

Shiru har azahar ba faseelat ba labarinta ummi tace bari nakira de naji ko lpya, ta dauki waya takira ta,

Faseelat ta dauka tana magana Ahankali,

Ummi tace "wai amarya bazaki zo mana bankwana ba inata dubar hanyar ki tundazu "

Faseelat tace "ummi Ya hana wai se dare "

Ummi tace "to ai ba matsala duk daya ne Allah yakaimu daren kiyi hakuri kinji "

Faseelat tace "to ummi "

Ummi takashe kiran, ba jimawa kiran umma ya shigo dan yanzu suna magana faseelat so biyu tana kiranta,

Faseelat ta dauka tana faraa tace "umma ina wuni "

Umma tace "lpy lau diyata Ya kuke? "

Faseelat tace "lpy lau umma "

Umma tace "alhamdulillah, dama cewa nai bari nakira ki dan kina debemin kewar fahad, ga kannenki duk sunason su ganki "

Faseelat tace "Nagode umma nima inason nagansu "

Kanwar fahad ta ukku Mansura (lady😉) tai sauri ta karbe wayar daga hannun umma dama kanta a jikin umma yake itada 2 sisters nata sun zagaye umma don sosai sukeson danuwansu amma su dashi sede suga pic dinshi a media ,tace "anty muna sonki sosai yaushe zamu ganki?"

Faseelat tace "koda yaushe nima inasonku sosai kuma ina gayyatar ku gobe dafatan zaku zo "

Mansura tana farin ciki tace "zamu zo anty insha Allah "

Faseelat tace "to se kunzo ina gaida sauran sisters nawa"

Su Mansura suka fara surutu suna fadawa umma abinda tace faseelat tai dariya takashe kiran dan murna basuma san basu kashe kiran ba,

Duk yinin fahad be leka dakin faseelat ba da Maghreb tai masu dinner takoma daki tai wanka, bata ko shafa mai ba bare powder tade shafa humrah ta saka riga da sket material lace orange color ,

Tana zuge zip fahad Ya shigo bata ko kalle shi ba,

Yana shan kamshi yace mata "ki saka hijab mutafi na ajiye karfe tara zanzo daukarki "

Batare da tai mishi magana ba ta ida zuge zip din ta juya tabude wardrobe ta dauko hijab dinta, fahad yabi bayanta da kallo sket din Ya mata cif dammm ta saka hijab cikin jin haushi fahad yace "idan kinje karki cire hijab dinnan kuma karki amfani da hannun hijabin "

Hawaye suka cika mata ido ta kalleshi kamar zatai kuka tace "wace irin rayuwa ce wannan? Shikenan bazan kara sakin jiki a gidanmu ba dannayi aure? A cikin gidan na taso tun yarinta har girma na, yaya de kake magana kanshi har kashi ya wanke mun, kuma duk cikin gidan muharramai na ne ko kamutu ba aure tsakaninmu miye na damuwa kode kanason matsa ma rayuwata ne? "

Taja numfashi tace "to shikenan bazanje ba bazan kara zuwa koina ba tunda bakaso ko yaushe zan kasance mai maka biyayya "

Tafara zare hijab din jikinta,

Fahad ya rike mata hannu murya sanyaye yace "kiyi hakuri da hali na faseelat wlh bansan koda kuda namiji ya tabaki, duk sonki ne yajawo haka kimin uzuri,"

Ya jawota jikinshi Ya gyara mata hijab yace "mutafi muyiwa su ummi bankwana kinji my honey"

Tai kwance jikinshi suka fito, amira tace tana zuwa suka tafi tare,

Atare suka shiga shima Ya gaidasu ummi yabawa ummi 200k Ya tashi Ya fita,

faseelat murna kawai take ta yaye hijab ta matsa wurin ummi, ummi ta kalleta taga duk ta rame sede tai haske dan gangariyar madarar da fahad ke zuba mata lol.

Ummi tace "ya gidannaku Ya kishiyarki? "

Faseelat tace "muna lpy ummi "

Ummi tace "senaga kamar kin rame "


Faseelat tace "hakanan ne kurum "

Ummi tace "Ya naga kamar baki baki a wuyanki da gefen hannunki? "

Faseelat tafara inda inda tace "konewa nayi ummi wlh Allah Ya temakeni daddyn amira Ya siyomin wani cream nake shafawa shine Ya koma haka "


Ummi tace "to Allah yakyauta gaba ga wani tsimi nan na siyo miki kishashi yanzu ga wasu nanma a leda kitafi dasu kin kusa shanye wadancan ko? "

Faseelat tace "eh saura kadan ai ummi bani sanya"

ummi ta rike gemu tace "Allahu Akbar Allah abin godiya "
Faseelat ta rufe fuska, ummi ta mika mata tace "gasunan ki kara himma to "

Faseelat ta dauka ta shanye tsumin tass suka cigaba da fira bayan isha Ya omer Ya dawo murna kamar zata kasheta shima haka sukaita labari su ishak su abul su Mubarak kamar zasu cinyeta,
Abba Ya dawo taje suka gaisa yanata sa mata albarka,

Karfe tara fahad ya kira ta ta tashi tasa hijab ta sabi amira dake bacci ummi ta taho yi mata rakiya zuwa bakin kofa,

Faseelat suna isa kofar ta ta juyo ta kalli ummi tace "ummi zanyi missing naku Allah yasa ayi karbabba dan Allah ummi kimin addua Allah Ya amshi adduoina "

Ummi tace "insha Allah diyata Allah Ya kara baku zaman lpy"

Tace "amin Nagode ummi Allah yakiyaye"


Mubarak yazo Ya amshi amira suka fita, abayan mota Ya kwantar daita ya masu se da safe ya koma gida,

Tunkan hanya faseelat tafara rikita fahad saboda tsumin da yafara aikinshi,

Tana ta shash shafa shi tana Yi mai kiss yana driving, se lumshe ido yake dakyar suka isa gida shi Ya dauki amira ya kaita dakinta Ya koma suka cigaba da rikita juna,

Da daddare faseelat kasa bacci tayi hakanan taji farin ciki Ya dabaibayeta na zuwan sisters nashi , har fahad yayi bacci Ya barta tana ta kallonshi tai masa kiss's ta tashi tayo wanka ta kabbara salla tana ta adduar Allah Ya gyara mata mijinta ya sulhunta tsakaninshi da yan uwanshi ,



Tun asuba bata zauna karatu ba tai sauri ta gyara gidan sannan tai masu simple breakfast,

Ko sleeping dress bata cire ba ta zauna sukai breakfast fahad se kallonta yake yadda take ta murmushi ita kadai, Ya lumshe ido ya bude Ya saki ajiyar zuciya cikin ranshi yace "honey kaunar ki zata kasheni "

Shaf shaf ta samu ta karya ta wuce kitchen tafara aiki zatai wa umma meat pie da spring roll su Mansura su kai mata,

Fahad na daki kasancewar weekend ne shiru bata shigoba har 12 na rana shi kuma yanason yayi ninkaya Ya tashi ya nufi kitchen,

Kitchen din nata kamshi yayi tsaye yana kallonta tanata aiki dasauri, ta juyo ta kalleshi jin kamshin turaren shi,

Ya harde hannuwa yace "wai yau shirin mi kike? "

tana aikin tace "wlh hero baki zanyi kuma they're special and dear to me "

Fahad yayi murmushi yace "lalle kinaji da bakinnan tow Allah yakawosu lpy but ni antakura ni "


Faseelat tace "haba ga anty nan just go to her tunda ni ina busy "

Yana mata kallon mamaki yace"keda kanki kike tura ni, yau ko dan kishi na bakiyi"

Faseelat tai dariya tace "bahaka bane hero dan kasamu natsuwa nace kaje wurinta amma ai ina kishin ka sosai "

Yace "ai kece natsuwa ta, any way natafi kar na hanaki aiki "

Tai murmushi ya juya Ya tafi wurin Aisha ,


Agidan umma su Mansura da safiyya da ummu salma shiri suke tayi sunata doki,

Umma tace "kai yau faseelat se kanta yayi ciwo nasan "

Mansura tace "umma dan Allah kizo mutafi tare, daganan kiga yaya kuma nasan anty zataji dadi da zuwanki"

umma tace "ni tsoron ma ganinshi nake sede inason naga daughter eye to eye wlh inasonta yarinyar kirki ga daa gaskiya Allah yana son fahad da yabashi ita,bari nafadawa daddinku se na shirya mutafi "

Ta shiga tafada mishi yace ba matsala don shima sosai yakeson su shirya da danta,

Karfe 1 tagama komi har abinci ta masu ta wuce daki a gaggauce tai wanka tasaka gownt light purple atamfa tai simple makeup,


Karfe 1:15 su umma suka fito umma na driving su kuma sunata labari suna jindadi, Mansura takira faseelat, faseelat na cikin shiryawa ta dauka,

Mansura tace "anty gamu a hanya kinsan me? Harda umma saboda takagara taganki azahiri "

Faseelat tace "amazing I'm very happy se kunzo kuyi sauri dan Allah "

Mansura tace "OK anty "

Ta juyo ta kallesu tana dariya tace "kunji fa anty tace ai sauri "

Karfe 1:30 suka isa kofar gidan sukai horn megadi Ya bude suka shiga ciki,

Suka firfito sunata kallon gidan sukaje bakin kofa suka danna door bell,

Da gudu faseelat taje ta bude,

Ta gansu tsaye dukkansu sunyi kama da fahad more especially Mansura, tarika murmushi,

Duk sunkare umma,

faseelat tace "ina umma? "

Suka fashe da dariya suka bata wuri, faseelat ta fada jikin umma kamar sun dade tare tanajin matukar dadi itama umma dadi takeji ,

Su Mansura abun Ya birgesu yadda faseelat taiwa ummansu,

faseelat tai breaking hug din tace "umma kushigo sannunku da zuwa "

suka shiga suka zazzauna faseelat ta zauna gefen umma tace "ina wuni umma Ya hanya "

umma tace "lpy lau Ya ta Nagode da karramamu da kikai"

Faseelat tace "umma kidena min godiya ai kamar uwa kike aguna "

Umma tai murmushi su Mansura se kallonta suke kamar su hadiye ta tashi ta kawo masu abunsha ta zuzzuba musu ta dawo ta zauna,

Suka dauka suka sha,

Sunata kallon gidan duk pics din su fahad da Aisha pic daya ne na faseelat,

Kamar sundade tare suka matsa suka fara hotuna harda umma fuskarsu dauke da farin ciki,

Suna haka fahad Ya fito zai fita har yayi wanka Ya na sanye da blue shirt white jeans, tundaga step yagane ko su waye bakin faseelat, Ya daure fuska Ya cigaba da saukowa yana kallonsu da mamaki a fuskarshi,

Jin ana saukowa suka meda hankali gun step din, ganinshi duk suka sha ruwan jikinsu,

Fahad yaida saukowa yana harararsu yaja tsoki yawuce ze fita,

Umma ta mike tsaye tace "son Dan Allah kayi hakuri ka yafemin nida yanuwanka duk muna da bukatar ka "

Fahad yaja wani dogon tsoki, faseelat ta zaro ido jin yawa umma tsoki tai zumburr ta mike tsaye ta buda murya sosai tarika cewa "innalillahi wainna ilaihi rajiun,innalillahi wainna ilaihi rajiun"!!!

Fahad yayi sauri ya juyo saboda seda hanjinshi ya juya saboda yadda take maganar zuciyarshi ta rika bugawa da karfi he is expecting something bad happened to her, Ya ganta tsaye se juya kai take tana hawaye tace "ina tausayin ka mijina saboda sanin idan ka mutu yanzu akwai azabar dake jiranka, hero ka dawo hayyacinka ,ka rika tuna lahira ba duniya kadai ba,umma ce wannan mahaifiyarka data dauki cikinka tasha wuyar nakudar ka ita kake wulakantawa baka tsoron azabar Allah ne? Manzon Allah S. A. W yace

عن ﺃﺑﻲ ﻫﺮﻳﺮﺓ ﻋﻦ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﷺ ﻗﺎﻝ: ‏« ﺭﻏﻢ ﺃﻧﻒ، ﺛﻢ ﺭﻏﻢ ﺃﻧﻒ، ﺛﻢ ﺭﻏﻢ ﺃﻧﻒ ﻣﻦ ﺃﺩﺭﻙ ﺃﺑﻮﻳﻪ ﻋﻨﺪ ﺍﻟﻜﺒﺮ ﺃﺣﺪُﻫﻤﺎ ﺃﻭ ﻛﻼﻫﻤﺎ ﻓﻠﻢ ﻳﺪﺧﻞ ﺍﻟﺠﻨﺔ ‏» . ﺭﻭﺍﻩ ﻣﺴﻠﻢ.

_An Kar6o daga Abi-Hurairah, Daga Annabi Yace: *“An Turmusa Hancinsa a Wuta. An Turmusa Hancinsa a Wuta. An Turmusa Hancinsa a Wuta. Wanda Duk Ya Riske Iyayensa da Girmansa, Dayansu Ko Duka Biyun; Sannan Be Shiga Aljannah ba”*.

Tana haki ta cigaba da cewa "se yaushe hankalinka ze dawo jikinka ne? umma na raye bata mutu ba shin bazaka nemi aljannarka ba se lokaci Ya kure maka sannan, kabude idonka sosai ka duba da kyau hawaye ne a fuskar umma kai baka da tausayi ne ga kannen ka nan duk suna kuka saboda yadda kake wulakanta masu uwa, amma duk da haka suna sonka kana gudunsu"

fahad yabisu da kallo duk sunata hawaye musamman umma da suketa zuba akan gyalenta,

dole asamu tausayi ko kadanne a tsakanin uwa da da saboda bond dake tsakaninsu kuma haka Allah yasaka akowane kirjin Dan Adam so da tausayi tsakanin da da mahaifiya, fahad bema taba tsayawa sauraren umma ba be ko kallonta bare ta bashi tausayi yanzu da yaganta haka duk jikinshi yayi sanyi fuskar umma kasa tana ta faman share hawaye,

Be aune ba yaji hawaye suna bin fuskarshi jikinshi yafara rawa,

Faseelat tace " Dan Allah ka mance baya ka kama mahaifiyar ka ka jikanta kai mata duk kyautatawa ,tanason ka, tanason ta rika jin duminka ajikin ta, hero "

Kuka ne yazo mishi lips dinshi suka rika rawa hawaye nata zarya ,, ido rufe yatafi ya rungume umma ya saki kuka me kashe jiki,

Umma ta rungume danta tanajin kamar andawo mata da wani sashin jikinta data rasa,

su Mansura suna kuka suma suka tafi suka rugumesu suka cigaba da kuka,

Saboda tsananin farin ciki kafafun faseelat suka gaza tsayuwar takoma ragab zaune saman kujera ta rufe fuska da hannuwa ta saki kuka me sauti,
[8/5, 6:12 PM] +234 815 712 7134: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰







By






*MAMAN MAMY*
*(SHALELE)*






https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*




*~We are bearer's of so golden pen🖊~*

*~we write assidiously perceive no pain~.*

*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*

*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*






6⃣4⃣




*Hohoho semu yan golden 🤸🏼‍♀,this page is for you golden pen writers,taurari masu haskawa, marubuta masu amfani da iliminsu da brain dinsu wurin seseta tunanin makaranta ta hanyar fadakar dasu ilimantar dasu da kuma sasu nishadi, mun zama taurari mune ke haskawa*💃🏼

Dole ne nadanmaku baitoci ko biyu ne dan jindadinku 😉

*gangata zan dukawa yan golden forum,, waka ce zan raira maku kuyi sauraro, rawa muke da juyawa mu munzam taurari,, murna muke munzam sha kallo muke haskawa*🤸🏼‍♀

*lokacinmu ne munyi gaba mun wuce yan baya,, semunyi mun rage in mun saura wadansu ke koya,, munfice a cikin marubuta😂mu aketa bida dubayya,, mata hada da maza gaurayya,, masoya muna maku maraba💃🏼😂*



ku cigaba da gashi kawai up up up golden 💋💋💋💋💋💋






Dukkansu kuka suke bame rarrashin wani acikinsu, wani dadi ne da farin ciki yake ziyartar zuciyoyinsu, more especially fahad da yakejin kamar yau aka haifeshi a duniya,

Aisha dake daki tarika jin hayaniya ta fito daga upstairs take kallon abinda ke faruwa ta tabe baki tanajin haushi,


Ahankali kukan faseelat ke ragewa sede hawayen da suka ki tsayawa, ta bude fuska tana kallonsu ta rika murmushi hawaye na cigaba da zuba mata,

Su Mansura suka koma suka rungume faseelat sunata farin ciki,

Kuka fahad keta yi Ya dago fuska yana kuka yake cewa "umma ki yafemin na yarda ki nayi nesa dake na miki duk wulakanci ki yafemin ummana "

Umma ta rike fuskar shi tana hawaye ta rika girgiza kai tace "I forgive you my son stop crying please yau ranar farinciki ce nadade ina rokon Allah ya gwadamin wannan rana da zaka dawo wuri na yau gata tazo ,ina cikin farin ciki son Nagode da kayafemin I love you "

Tarika mai murmushi yace "I love you umma very very much "

Ta saka hannu tana share mai hawaye shima yana sharemata,

Yakara komawa Ya rungumeta, umma ta juya tana kallonsu ta mikawa faseelat hannu faseelat ta tashi taje ta rungumesu tana share hawaye,

For some minutes sannan faseelat ta janye tana ajiyar zuciya tace "umma ku zauna "

Fahad ya rike umma suka koma suka zauna ,

faseelat tana farin ciki tana kallon su ta daga hannu sama tace"Allah Nagode maka da ka dawo da hankalin mijina jikinshi kadedeta shi da mamanshi da yanuwanshi ya Allah kaKara masu dankon kauna da zumunci a tsakanin su kakara masu son juna"

Dukkansu murmushi fuskarsu suke kallonta ta shafa tana sauke ajiyar heart suma duk sukace "amin" suka shafa

Fahad idanu jawur Ya kure faseelat da ido yanajin kaunarta na circulation acikin jijiyoyin jikinshi,

Umma tace"nagode miki diyata da jajir cewar ki har dana yadawo guna Allah yamiki albarka "


Faseelat tace "amin umma "ta sunkuyar da kai

Umma ta Kalli fahad tace "son kayi dacen mata, tana da tarbiyya da kyawawan halaye "

Fahad hankalinshi na gun faseelat cikin subucewar baki yace "she's beautiful as well "

Sisters dinshi suka fashe da dariya, Ya bude ido yayi dariya shima,

Amira data tashi bacci ta sauko kasa ta taho wurinsu, ummu salma tai sauri ta dauketa tana ta kallonta yadda suke kama ta mata kiss tatafi wurin sauran sukai ta daukarta daga karshe umma ta amsheta ,

Aisha ta koma daki tana yamutsar fuska ta dauko waya ta kira mommy saboda tsananin kishi da yadda taga faseelat nataso ta anshe gidan tanajin kome zata iyayi ta juyo hankalin mijinta wurinta mommy bata komi kulum sede tace hakuri, hakuri de hakuri de, gabadaya halinta Ya sauya ,

Mommy ta dauka tace "daughter Ya akai ne? "

Aisha taja tsoki tace "hmm mommy yau gidannan fa drama ake sosai,faseelat de ta sasanta yaya da ummanshi yanzu haka suna down stair sunata murna "

Mommy dake shan banana milkshake ta ajiye cofyn hannunta tace "shegiyar yarinya wato tana amfani da damar ta yanzu ne lokacinta kuma tana amfani dashi, uhmmmm nayi mamaki kuma na wa rukayya murna"

Aisha tace "haka ma zakice mommy? "

Mommy tace "to Ya zance ni bantaba shiga maganarsu ba so bani ciki sasan tawarsu baze hana fahad kulawa dani ba ai "

Aisha tace"ni ta taba zuwa na barta waje, yanzu Ya zaayi ne kuma ni banason sisters dinshi masu kama da aljanu suyi ta zarya anan "

Mommy tace"marar wayo kawai Mace tazo wurinki aiseki saurareta inta tafi shikenan ai, amma ki barta waje don shashanci wlh ba abinda kika bari na yan fari mtswwwww kina jina? "

Aisha ta turo baki gaba tace "eh "

Mommy tace "just pretend like bawani abu da ya faru baya kitashi kije ku gaisa"

Aisha tace "to "

Mommy takashe kiran, Aisha taja tsoki tace "wlh mommy batai ba ita komi yaya ya yayi Dedene bata wani daukar action hmm"ta fita tana tafiya Ahankali har ta sauka duk falon hankalinsu Ya koma kanta, taje ta samu seat ta zauna ta Kalli umma tace "ina wuni"

umma na faraa tace "lpy lau Aisha "

Sisters dinshi suka rika gaidata "mommyn amira ina wuni "

Ta danyi yake tace "lpy lau "in short

Kusan 2:30 time din suka tashi suka hau sama,

Dakin faseelat suka wuce sukai alwala sunata nan nan da faseelat,

faseelat taja su salla harda umma,

Shi kuma fahad ya tafi masjid dukda time din salla yawuce he decide to go there saboda samun ladar tafiyar,


Aisha dukda bata salla ta tashi takoma daki abinta,

Bayan sungama Suka fito faseelat ta tashi tafara kawo kuloli tana ajiyewa Mansura data fi shigemata kuma itace babba ta tashi tana kama mata, umma sede ta Kalli faseelat tai murmushi don jinta take sosai arai ,

fahad Ya dawo daga masjid suka zauna faseelat tafara sarving dinsu vegetable white rice with chicken stew and coslow,

Duk suka dukufa suna cin abincin suna santi, fahad be iya barin umma tarika ci da kanta ba shi Ya matsa yasa hannu ya rika bata abaki ita ma tana bashi,

Mansura baki cike da shinkafa tace "anty zanzo ki koyamun irin girkinnan medadi kai gaskiya yaya kayi dace komi perfect "

Ya harari Mansura yayi murmushi,

Haka suka gama cin abincin ana fira gwanin dadi,

Seda sukayi laasar sannan suka fito zasu tafi dukkansu suka fito yi musu rakiya amira na hannun safiyya Aisha nabinsu ne kawai ,

Suka isa bakin mota fahad ya budewa umma ta shiga suma suka shishshiga sunata jin badadi faseelat ta sa ledar spring rolls da meat pie da tayi aciki , Mansura ta shiga ta jasu sunata ma juna waving sukabar gidan ,

Suna tafiya Aisha taja amira suka nufi wurin shan iska,

Faseelat ta juya ta shige gida dan ta kimtsa inda suka bata,

Fahad yabi bayanta sede taji tsam andagata sama ana juyata,

Suka rika dariya, sannan ya ajiyeta, ta juyo ta turo mai baki taimashi hararan masoya,

Fahad Ya kamo bakin ya rika tsotsa kamar ze cinyeshi ,

ta zaro ido tafara tureshi, seda Ya sha bakin sosai Ya cire bakinshi in cool voice yace " I love you honey queen ,kin min komi arayuwata tunda kika nunamin hanyar samun rahma wurin ubangijina Nagode miki, bansan yadda zan kwatanta miki farin cikin da nake ciki ba,me kike so daga gareni niko namiki shi? "

Faseelat tana ta murmushi tace " nothing kuma wata kyauta zakamin aini ce zan maka kyauta dan nafika farin ciki, shiyasa na ta nadar maka special gift "tai fari da ido

Yana lashe lebe yace "Allah? "

Tace "yeah zo muje ka amsa tana sama kyautar "

Tafara tafiyar jan hankali tana jujjuya buttock tana hawan step,

Fahad ya Saki murmushi ya shafi keyarshi yace "ya rabb I can't ask for more "

Yabita dasauri dan yariga yagama gano kyautar da zaa bashi,

Sosai faseelat ta rikita shi har seda Ya mance awace duniya yake. Lol


Se 6:30 suka fito fahad yakama mata suka gyara gidan,

Aisha ce keda girki tana kitchen tana hada masu abinci,

Suna gamawa ya fita masjid, faseelat ta koma tai salla ta fito ta shiga dakin Aisha amira na kwance kan cinyarta faseelat tace wa amira "princess kizo muje muyi karatu "

Amira ta tashi faseelat taja ta suka fita,seda taje zatai wa amira karatu ta tuna bata kira ummi ba tai sauri ta kirata,

Ummi ta dauka da sallama , faseelat tace "Wslm ummi kiyi hakuri ban kira ba tun dazu ina busy ummansu hero ce tazo inafatan kun isa lpy?"

Ummi tace "lpy lau muka sauka a jidda mukai azahar ma, "

Faseelat tace "ummi albishirinki Hero sun dedeta da ummanshi"

Ummi tace "kai alhamdulillah naji dadi Allah yakara hada kansu "

Faseelat tace "amin ummi, inasonta wlh she love me alot itada yaranta kinga yadda suke nan nan

Please Login or Register in order to submit comment