Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta fiddo waya ta kira maman amira,

Maman amira da ke wajen saloon ta dauka tace "momyn amira yaushe zaki zo ne? Ko kintaho?"

Faseelat tace "anty gani nazo "

Maman amira tace "ayya wlh bansan zakizo da wuri ba nazata seda marece, gashi ni ina wurin saloon, zaaimin da wankin kafa, ita kuma amira ai mata kitso "

faseelat tace "to bakomi anty bari natashi natafi se bayan salla in Allah yakaimu "

Maman amira tace "au kina ciki kenan, ashe daddyn amira ya dawo, to tunda kina ciki kijira ni mana daman dan kar in shanyaki waje, ki bani 30 to 40 minutes inazuwa "

Faseelat tace "Tom anty se kindawo "
Ta yanke kiran dan koda 2 hrs maman amira tace tozata iya jira saboda ko kamshin turaren fahad kawai da ya mamaye falon yasa ta tsaya bare ga kyakykyawar fuskar shi tana kallo,

Tunda tafara waya yake kallonta se lokacin ya samu amsar tambayarshi wato kawar aisha ce, he wonder ina ta samo wannan, ya meda kanshi kan aikinshi cikin ranshi yana cewa "she has sweet voice too"

Faseelat tai zaune dukda de adarare take amma she love the moment, a dan sace take samu tana karemishi kallo, yana sanye cikin white shirt blue trouser, yayi kyau sosai ta cigaba da satar kallonshi she don't think ta fishi da wani abu dan inma fari ne har ya fita ,

Suna zaune ahaka shima suna musayar ido da wannan ya dauke nashi se wannan ya soma,

Can de fahad yameda hankalinshi kacokam kan system nashi,

Faseelat ta rasa abinyi zaman yafara isarta seta jawo waya takira aisha, maman amira na dauka faseelat tace "anty I'm feeling hungry "

Maman amira tace "ayya I don't think zaki samu abinci amma ki bude fridge na hanyar dining ki samu ko snack ne da drink kici "

faseelat tace "ayya anty ni abinci nikeso fa "

Maman amira tace "no be problem kishiga kitchen ki dafa abunda kikeso kafin na dawo "

Faseelat tace "OK I'm waiting "

Ta kashe kiran ta tashi tsaye ta ajiye Jakarta takama hanyar kitchen fahad yabi bayanta da kallo hijab din jikinta roba ce ta dan fito mata da shape kadan,


tana shiga kitchen tabude freezer wow ga freez chicken nan ga fish, liver and kidney ga chicken breast nan ma na company "

Ta danyi tsaye tana tunanin mi zatayi, can zuwa tace "le me do yam porridge and toastedchicken "

Ta fiddo kaza da sauri da ice fish ta wanke tasa kasu a oven on law heat don Ice din dake jikinsu tayi melting,

Ta fiddo kayan miya tai blending tadora tukunya a gas tafara soya su,

Ta fiddo kazar da fish din har sunfara zafi ta ajiye tai grettin tarugu da albasa tazo tai hadin kazar ta shafa mata ta kai fridge don tayi marinated ta cigaba da aikinta for like 20 mnt ta fiddo ta ,ta saka a foil paper takara hada mata spice tasaka a oven,

Ta koma ta cigaba da hada faten doyanta for like 30 mnt da shigarta kitchen yaji kamshi yana kawowa inda yake,


40 mnt dede ta gama komi ta dan zuba wanda zata ci a plate ta zuba nasu a hotter takai dining,

Yana zaune yaga tafara zarya dining to kitchen yatashi ya dauki system dinshi ya haye sama, faseelat na fitowa bataganshi ba,

Tasaki murmushi "kagama duk wani jiji dakanka zaka shigo hannu ne "tafada saboda karfin hali,yo karfin hali mana🀣

Ta zo ta zauna tana cin nata hankali kwance tana gamawa takira maman amira, tana dauka tace "anty har yanzu kusan 1hr fa kenan da zuwana "

Maman amira tai dariya "sorry gamu kan hanya "

Takashe kiran tana magana da amira "zakiga momy ko? "

Amira ta daga kai tana murna,

Faseelat na zaune amira ta shigo da gudu ta rungume faseelat, faseelat ta dauketa tana jindadi, aisha ta shigo tana faraa tareda cewa "sorry I keep you waiting "

Faseelat tai dariya "bakomi anty "

Ta cigaba da wasa da amira,

Maman amira ta haura sama, ta samu fahad nata aikinshi tafada jikinshi tana fadin "washhh! "

Tace "yaya I'm very tired "tana shige mai,

Ya matsar da laptop din ya kara jawota sosai kan cinyarsa yana Shafa kanta "kinyi kyau sosai honey "

Aisha tai Far da ido tace "thanks you my heart beat "

Ya na mata kallon bukata yadora hannu kan boob's dinta yana matsawa yace "I want to have you ..."

Ta katseshi "but not now yaya kaga fa inada bakuwa plss kabari na sallameta sannan "

Yayi murmushi yace "who is she to you "

Tace "just a friend "

Yace "good"

Ta tashi tsaye "let me attend her karta ga na dade "

Kallo kawai yabita dashi har tafita, tana fita yasa hannu ya na shafar sajenshi tareda furta "ahmmmmm"


aisha na fita ta hangi warmers akan dining tayi gun ta bude tace "wow so delicious "

Ta rufe tafito tana zama tace "faseelat har wahala kika bawa kanki? "

Faseelat tace "a, a bawata wahala anty "

Aisha tace "thank you yau zamuci ur delicious cooking gaskiya kin iya girki "

Faseelat tai dariya tana cewa amira "my angel kitsonki yayi kyau, anty nima fa naiya kitso ni zanwa faseelat na salla "

Aisha tai dariya "kinada kokari gaskiya Allah yakaimu, da inayin kitso da har ni zakiwa to sede bana kitso daddinta bayaso ya fison ganin gashi haka "

faseelat tai murmushi ta dubi agogo to 2 ta mike tsaye "anty bari nayi salla nawuce "

aisha tace OK, "ga toilet nan daga kofar fita kitchen, bari nakawo miki carpet "

Faseelat ta juya ta tafi tayo alwala ta dawo tai salla suka dan yi labari ta tashi zata tafi maman amira tamata kyautar perfume, ganin zata tafi amira tafasa ihu wanda yasa fahad lekowa daga saman bene,

Amira tana kuka tace "i want to follow you mommy "da maganarta da bata ida gogewa ba, ta rikewa faseelat hijab,

Faseelat tana rarrashi aisha nayi faseelat har suka fita, fahad na Sama yana kallo su basuma san yanayi ba, suna fita ya saki murmushi,


Faseelat tabar gidan sannan aisha ta dawo tanata wa amira wasa har ta samu tai shiru, sega fahad ya sauko tace "yaya muje muyi lunch I'm hungry "

ya amshi amira yana fadin "my blood what do you want ?"

Aisha tace "rabu daita ta cika rigima "

Har kan kujera ya zaunar da amira ya zauna aisha tai sarving dinsu ta zauna tafara ci, spoon daya tayi ta rumtse ido tana fadin "yummy"tana juya kai,

amira tuni take ta kai spoon baki tanacin abincin yana zaune yanata kallonsu, baya tunanin waccan insane girl din zatayi wani abun kirki,

Can zuwa ya daure ya kai spoon baki, wani dadi ya ziyarci kwakwalwarshi ya rumtse ido, inda akabar aisha baya kenan ba ruwanta tana ma iyayin sati batai musu abinci ba sede suje waje suci ko yayi musu da kanshi, tun tana gida mommy ta shagwabar dasu komi se me aiki ce keyi baruwansu sede charting bacci da kallo,

fahad yaji taste yakara dauko spoon yakai baki besan lokacin da yace "wow" idonshi rumtse,

Aisha har ta dau spoon zata kai baki ta meda ta ajiye wani haushi da kishi suka taso mata, taja plate din gabanshi "girrrrr "
Ta medoshi gabanta,

Ya bude ido yana kallonta idanunta har sunyi ja tatashi tafara hada abincin cikin cooler har da wanda amira keci,

Yana kallonta idonta tab da kishi yace "aisha plsss mana kibari muci abincinnan yamin dadi "

Ta watsa mishi harara hawaye na neman fito mata tace "wlh baba tsoho zan kaiwa shi bawanda zeci abincin nan "

Ta cigaba da juye abincin, yahade hannu wuri daya yana kallonta, ta gama juyewa ta rufe kular ta dauka,

Amira tafasa kuka "daddy talk to mommy to bring my food back "

aisha tawatsa mata harara tai waje,

Yabita da ido ya girgiza kai, ya jawo amira yana tapping dinta yace "it's okay bari muje restaurant muci kinji? "

amira ta cigaba da kuka, yana cikin rarrashinta aisha ta shigo tana ta hade fuska ta hau step din bene har takusa hayewa ya kira sunanta "Aisha! "

ta juyo fuskarta da hawaye tana kallonshi......
[7/12, 11:00 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰



By



*MAMAN MAMY*





https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

✍✍✍✍✍✍✍
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*
✍✍✍✍✍✍✍


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*



3⃣2⃣





*Bismillahirrahmanirrahim*



*dedicated to yan amana 🀣*




Se yaji badadi ganin hawaye fuskarta yayi alamar tausayi da fuskarshi, bata jira shiba ta haye sama, yayi murmushin takaici ,bega wani laifinsa ba ita ta gayyato shi cin abincin honestly speaking abincin yayi dadi b4 yafara santi she's the one that begin, ya juya kan amira yace " angel muje mu rarrashi momy she's angry with us "

Yaja amira suka haye sama, suka shiga dakinta aisha tahaye saman bed tana rusa kuka yanaganin abinda take ya dafe goshi, yaja hannun amira suka fita yakaita dakinshi yabata game ya fito ya koma gun aisha,

Tana kwance tana shan kukanta yazo yazauna kan bed din yajawota jikinshi, ta cigaba da kuka don wani katon abu taji yatsaya mata a wuya,

Yana rungume daita tana cigaba da kuka yace "ya Allah"yana rumtse ido dan jin kukanta yake har cikin zuciya,

Magana yafara mata "aisha plss stop this crying, kukan ki na tabamin zuciya,nayi lefi kiyi hakuri plss, bansan zakiji zafi ba da bance abincin yayi dadi ba "

Ta dago ido tana cigaba da kuka tace "i love you yaya bazan iya hakurin abinda kayi ba inajin ciwo a zuciya ta sosai "

Ya fara share mata hawaye yana cewa "it's okay haka baze kara faruwa ba, nifa nakine ke daya sweety dan haka just wipe your tears and stop this crying "

Ta dago ido tana kallonshi yace "plss mana ko kinaso nima nayi kukan? "

Ta girgiza kai yace "toki hakuri my one and only "

Yana kashe mata ido daya, batasan lokacin da murmushi ya kufcemata, yayi murmushi shima yace "that's my girl "ya kai mata kisss, ya riga yasan aisha akwai kishi amma tana da saurin hakuri,

Yasamu ya rarrasheta sannan suka tafi Chinese restaurant cin abinci,


Faseelat tana isa gida tai ta juyi itakadai tarasa ina zata saka kanta don dadi finally yau de taganshi ,

Ta zauna kan kujera ta jawo wayarta ta tura mishi "kayi kyau sosai "

Ta ajiye wayar tai shiru tanajin haushin kanta yadda tai da ta ganshi.

Ko da khalil ya dawo da daddare take ce masa maman amira nagaidashi kuma tabata turare,

Yace "Allah sarki tanada kirki sosai gaskiya "


Lokacin da fahad yaga message din faseelat dariya ma abun yabashi yana tunanin yadda yaganta a tsorace, se ya tura mata smiling face, tana gani ko seda taji dadi.


Ana haka aka shiga watan azumi, tunda aka fara azumi shikenan khalil ko romance din ma yadena yi da yayi bude baki ze cigaba da jan cazbi daganan yawuce masjid suyi isha da tarawih ya dawo da yagama cin abinci ya cigaba da laziminshi itakuma taita charting dinta da friends,


Har akayi azumi 15 wani problem da faseelat ke fuskanta azumi ake amma ita shaawar karuwa take dan ko baccin rana takeyi mafarki take,

shi ko khalil gajiyar azumi da aiki ce tahanashi katabus,

Abun ya damu faseelat ta rasa ina zata saka kanta taji dadi, atleast ma tasamu wanda tafadawa zata rage wani abu,


Yau bayan ya dawo daga tarawihi ya zauna yana lazimi, ita ko faseelat sede ta juya ta kalleshi tayi tsoki kasa Kasa "waishi khalil miyake nufi ne?akace masa su uztazan basa bawa matansu lokacinsu ne? Basa wata fira me tsayi be taba cewa yana sonta ba sede aukin santi in yana cin abinci,

Hakanan taji tana son sharing problem dinta da maman amira, akai saa tana online faseelat ta tura mata "anty ansha ruwa lpy? Anty ina cikin matsala, shaawa tamin yawa, mijina be damu dani ba "

Maman amira na karantawa taji badadi tai mata reply "subhanallah, abu beyi dadi ba kiyi hakuri "

ta tura mata "anty shawara zakibani"

Maman amira tace "shawarata kije ki sameshi ki masa maganar, mijinki ne fa ba wata kunya tsakanin ku, ki masa maganar ku zauna kushawo problem din"

Faseelat tace "to Nagode anty "

maman amira tace "bakomi ai anzama daya "


Faseelat ta sauka online tana tunanin ta ina zata fara, don gaskiya hakurinta ya tafi karewa,

Har Sun kwanta takasa mishi maganar can de tai ta maza ta fara kiran sunanshi ya amsa yana saurarenta,

Tace "khalil banajin dadin yadda muke having sex"

Tana inda -inda tace "ni se nake ganin kamar baka lpya ya kamata kanemi magani "

Yayi shiru yana nazarin maganarta ya jawota jikinshi yace "I'm sorry faseelat,amma ni lpyata lau banaso na fara shaye shayen magani nafiso ki saba dani ahaka, faseelat bantaba koda rike hannun mace ba seke bantaba muamala da mata ba nike ganin shiyasa abubuwannan suke faruwa haka kiyi hakuri zuwa gaba komi ze dedeta "

Tai shiru ya dan matse ta cikin wasa yace "kinji "

Ta daga kai, yace "kuma cikin azuminnan wlh agajiye nake aiki yamin yawa shiyasa ko feeling banaji amma kiyi hakuri bayan salla komi will be normal "

Tace "to "tanajin haushi aranta itade tagama yarda da zuciyarta bashi lpya,ya zaai yace rashin sabo ne wata 7 ba kwana bakwai bane, suna haka bacci ya daukeshi while ita ko bacci batai ba,


Bayan kwana biyu de abun na cigaba da damunta ta rubuta tambaya ta tafi daita wajen tafsir, ta saka a akwati,

Kaidar malamin seya fara karanta questions sannan afara karatu tana zaune aka karanto tambayarta,
"Aslm inama malam fatan alheri Allah ya shirya zuria yakara ilimi, malam munyi wata 7 da mijina amma be taba kusanta ta ba ,da abun ya daman namasa maganar yace min lpyarshi lau inyi hakuri dashi ahaka, malam ina cutuwa sosai, har ya kai matakin da bazan iya hakuri ba ina neman shawarar malam "

Bayan yagama karanta tambayar yace "bewar Allah kina cikin jarabawa daga cikin jarabawoyin duniya akwai shaawa, saboda tana saurin halakar da mutum, shawarar da zanbaki ki hakuri ki cigaba da kame kanki, sannan ki kai maganar ga magabata tunda kinmishi be gyara ba,inaba maza shawara kuji tsoron Allah kurika sauke hakkin matanku na aure saduwa shine banban ginshikin aure bazaka ajiye mata dan kabata ci da sha da sutura ba kace kagama mata komi, a, a akwai hakkoki da suka rataya akanka daga ciki harda kawar mata da shaawarta, da zama daita kuyi wasa da dariya bata labari da debe mata duk wata kewa da zata hanata ganin wani namiji awaje, dan wasu mazan iyakarsu sex shikenan ba dariya ba magana me dadi, mata suna bukatar kulawa sosai saboda masu rauni ne, muna miki fatan zaku dedeta da mijinki Allah ya dedeta tsakanin ku, idan kuma anfada wa magabatan be dena ba kina iya neman ya sakeki, saboda auren ya haramta tunda akwai cutarwa ciki Allahu aalam "

Faseelat tunda taji an amsa tambayarta memakon taji sauki se ma tashin hankali da tashiga wa zata samu da maganar 'ummi? Gaskiya baxata iya ba gwara de ya sawwake mata yafi, tai shiru tana tunanin khalil gaskiya yana matukar sonta kuma yana da halin kirki sede tarin kayan haushin shi, tai shiru tanajin tausayinshi,


tana komawa gida takira maman amira awaya dan itakadai ce tasan matsalar kuma itama bata fada mata gaskiya ba tunda bacewa tai be taba kusantar ta ba,

Maman amira na dauka jiki badadi faseelat ke bata labarin tambayar da tayiwa malam da amsar da yabada,

maman amira cikin jimami tace "kiyi hakuri faseelat komi zewuce "

Tace "nagaji ne maman amira haryanzu zuciya ta takasa sonshi har nafara son wani daban "

Maman amira tace "subhanallah gaskiya be dace ba tunda de kinajin bazaki iyaba ki rokeshi ya sakekin"

Faseelat tace "to anty Allah yatemakeni ya yarda"

Takashe kiran ta zauna dabass kan kujera tanajin tausayin khalil,


bangaren fahad ko yanzu sunfara charting da faseelat don yafara meda mata reply shima hakanan yakejin wani feeling akanta saboda pic datake ta turomishi any how,
Kuma sosai yakejin dadin adduoin da take mai saboda bayada me mishi addua, mommy batayi befi tace mishi good luck ba a wayance, haka maman amira sede tace mashi best of luck, ko safe trip ko something de,


Faseelat sosai tasha kuka saboda batajin dadi kwata kwata hakanan taji bazata iya tarar khalil da maganar ba,

Aranta tace "kayi hakuri khalil dole se nayi abubuwan da zesa ka sakeni "

Anya ko khalil ze iya sakin faseelat πŸ€”
[7/12, 11:00 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰






By




*MAMAN MAMY*





https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

✍✍✍✍✍✍✍
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*
✍✍✍✍✍✍✍


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*




3⃣3⃣






*Bismillahirrahmanirrahim*




*Kad aflahal muuminuun...... wallazinahum anil lagwi muuriduun*





*Dedicated to golden pen writers, ko nima zansamu aban matsayin gimbiyaπŸ˜‚πŸ€­ kuzabe ni plss ni nacancanta abawa, 🀭ina maku gaisuwa da rokon iriπŸ‘πŸΌπŸ˜‚*




Wajen karfe biyu khalil ya dawo gida don dukda ana azumi yakan dawo da rana ya dan huta, har lokacin faseelat na zaune tana faman kuka da sake sake yana shigowa yaganta zaune idanu jawur da sauri ya isa wurinta ,ya durkusa ya dafa cinyoyinta yace "faseelat lpya meyafaru? "

Faseelat naganin yanda ya rude ganin tana cikin damuwa tana sheshsheka tace "bakomi kawai azumin ne ke bani wahala "

Yatsaya kallonta don be yadda da maganar ba,

Can zuwa yace "faseelat karya bataimiki kyau ba, saboda baki sabayi ba kifadamin meke damunki plsss" yariko hannunta .

wani kukan ya kufcemata cikin kukan tace "wurin waazi ne akai waazi akan azabar da akewa yan wuta shine ya firgitani"

Ya dubi hijabinta dake gefenta don tunda ta dawo take nan ya rumtse ido ya bude yakara damke hannunta yace "idan anji waazi ba kuka akeba komawa ake ga Allah ta hanyar kaucewa aikata duk wani sabo da kara kaimi wurin aikata alheri, ke mi zesa ki daga hankalinki, kina karkashin inuwar aure, manzon Allah (S. A. W) yace duk macen da ta mutu kuma mijinta ya yarda daita zata shiga, akwai hadisin da kuma yace idan mace takiyaye sallolinta biyar, ta kiyaye azuminta da farjinta da hakkin mijinta to zata shiga aljanna ta kofar da taga dama, me ze dameki kina min biyayya bamu taba samun sabani ba kuma kina da yawan ibada, ki shakuruminki ni dake duk yan aljanna ne gabadaya in Allah yaso, "

Ta kureshi da ido tana jinjina maganganunsa,

Ganin takure sa da ido ya sa hannu yana sharemata hawaye yana cewa "ki kwantar da hankalinki mata ta yar aljanna "

Tai shiru tana zazzare idanu wani mugun tsoro nakara shigarta.

Ganin tayi shiru sannan ya tashi," bari naje na dan kwanta kitashi kiyi salla "


yawuce cikin daki, har bayan 15 mnt da shigar shi faseelat takasa tashi, dakyar ta mike ta shiga don yin salla,

Bayan tafito ne wayar ta tafara ringing ta dauka tana dedeta maganarta ishak yace "yaya kin sauke? Ni har nafara ta biyu "yana murna

Faseelat tai dariya tana tabe baki "lazy boy dani kakeso kaja? Hhhh dasauranka ni kaga nakusa sauke na biyu, ina ummi tayi ta farko ma? "

Yana dariya yace "ummi najin azumi fa ta de kusa yin rabin sauka "


Faseelat ta babbake da dariya "kafadamata se ta taho "

yayi dariya "anti kina kokari asamu a addua "

Tace "karka damu ka gaida kowa, kuma kafadamasu se suntaho "

Takashe wayar tana dariya, wato su yar rige sukeyi a sauka cikin azumi wanda ya wuce kowa ummi na mashi kyauta ta musamman,

Ajiye wayar tayi tafara karatu seda akai laasar ta shiga kitchen,


bayan ansha ruwa khalil ya tafi masjid ita kuma har tagama tata tarawihi ta dauko wayarta, tana Bin chart dinta da fahad, duk reply dinshi bewuce thanks, ameen, i love it, ko u look pretty good, tai dariya tana jindadi, ta rumtse ido tana tuno yanda yake ta aiki a tsanake ranar nan yanzu muryar shi kawai takeson ji, zataso taji ya voice nashi tasan jinta kadai zesa tai bacci cikin farin ciki,

Batare da jinkiri ba ta bi numbers tai dialing my hope,

Fahad dawowarshi kenan daga masjid yana cikin mota ko fita beba wayarshi tafara vibrate,

yana ganin number yagane number insane girl dinshi ce,

Ya dauka yayi shiru jin andauka faseelat tai Kasa da murya tai sallama, ya amsa yana lumshe ido tareda dora kanshi kan seat,

Faseelat wani irin dadi muryarshi tai mata jitai kamar ba muryar namiji ba tsabar dadi,

Tadanyi jimm sannan tace "inafatan kasha ruwa lpya? "

Yace "yeah "yana mamakin yanda yakejin wani abu namasa yawo

tace "Allah ya karbi ibada, ina anty da my meera "

Yace"they're all fine "

tace "naji dadin jin hakan, Inajin muryarka kamar honey or sweet ,nakirawo ne naji muryar ka ko nasamu peace of mind, daddin amira tun ranar da naga pic naka i fall for you "

yayi shiru cikin ranshi yace, "u have nice voice too "


jinshiru tace "I'm sorry na takura maka it's your love that make me gone crazy,im sorry for all my disturbances, "


Yayi murmushi me sauti wanda yasa taji wani abu na zubo mata yace "why do you force me to start loving you, yeah you force me to fall for you ,u know what? I love everything about you, ur smile ur voice , ur duas for me ur cooking and your beauty, I love everything about you"

Saboda dadi faseelat batasan lokacin da ta mike tsaye ba, sautin muryarshi nata kaikawo a brain dinta,

Wata irin dariya ce marar tsayi takeyi me cike da mamaki tana rufe baki tace "did you? ....."

Takasa karasawa, kamar yasan me zatace yace "yes I love you, I love you beauty "

Dadi yakashe faseelat da karfi tace "thank you so much I love you too "

Ta datse kiran tana tsalle ,can zuwa takwara baki tace "I love you "

Saboda zafin da ake tsakar gida take sallan, khalil tsayuwar mashin dinshi kenan yaji maganar ta da karfi tana fadin I love you,

ya shigo gidan don bude gate, tanajin karar kofa tai tsaye wayarta rungume da kirji,

Yana mata kallon mamaki yace "kedawa kike waya kike daga murya haka? "

Tana inda inda tace "ya omer ne munkwana biyu ba mugaisa ba shine yamin albishir nakejin dadi "

Yajuya kawai ya bude gate din yafita, tasaki ajiyar zuciya tana zaro ido waje ta shige daki,


Fahad jin yanda take murna yakara sashi cikin wani Yanayi, Ya rumtse ido shikadai yasan yanda yakeji gameda ita, brain dinshi tana hasko mishi irin murnar da takeyi yace "be happy always my cutie,
Ya samu yashige gida ya je ya sauke duk abinda yakeji gun aisha.



tundaga ranar kullum se faseelat ta mishi barka da shan ruwa kuma suna chart suna fadawa juna zafafan words da suke kara narkar da zuciyoyinsu.



Salla saura 5 days maman amira ta fadawa faseelat zasuje dubai acan zasuyi salla, faseelat kamar tai hauka takira fahad, he was busy doing office work be dauka ba seta turamishi message "zanyi kewarka my heart, inamaka fatan nasara akowane abu da Kasa agaba Allah ya ya kaika lpya ya medoka lpya "

Seda aiki ya lafa yaga miss call nata da message yana gama karantawa yayi murmushi ya tura mata "why did you fell sad, we will continue chatting with each other and I will call you time to time stop worrying your self we will only spend 10 days only going to miss you too "


ya turamata tana ganin message din tai murmushi,

ko minti biyu baaiba yakirata yana rarrashi yace taturamasa account number dinta ta tura masa nan take taji alert din 200,000.


kusan zaucewa tayi tanata kara karanta zero zeron taga ko de bata karanta dede ba.



Manage it πŸ€¦πŸ»β€β™€
[7/12, 11:00 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰







By







*MAMAN MAMY*




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

✍✍✍✍✍✍✍
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*
✍✍✍✍✍✍✍


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*



3⃣4⃣





She's very happy, his gift is the best gift for her, can kuma setaji murnar duk ta tafi she don't want his money she want him ,not the money he own, bayan 15 mnt da turomata ta kirashi ya dauka yana driving to home, yace "menene kuma cutie? "

Tai murmushi "naji alert a account dina, bazance banyi murna ba saboda kyautar will always be the

Please Login or Register in order to submit comment