Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Muka cigaba da takawa har muka fita bakin titi. Shatar keke-napep kawai muka yi saboda lokaci daya fara kurewa.

Allah ya taimaka muka isa akan lokaci. Kasancewar duk practicals ne muka yi, kuma abubuwa basu fara yin nisa ba, yasa bamu jima ba muka taho gida. Karfe biyu ma bata karasa ba muka dawo.
Wannan karon ma napep muka hau. Muna sauka, wata hadaddiyar Range Rover tana shiga gidan. Muka bita a baya muma muka shiga gidan. Ganin ta gangara can bangaren Yaya Jameel, yasa na kalli Janan, "Anty Sarah ta sake mota kenan?".
Tace "da alama, ko kuma ta gidansu ce. Tunda ko yau da safe motar bata nan".

Wadda muke maganar a kanta ta bude gidan gaba ta fito. Matar Yaya Jameel ce. Saratu da muke kira, ko ince ake kira da Sarah, cikakkiyar yar gayu ce, wadda tasan fashion, kodayake kamar akan abinda naji ance tayi karatu kenan, ko kuma dai wani abu mai kama da hakan. Daga yanayin yadda take shigarta, takunta da gudanar da al'amuran rayuwarta, zaka tabbatar da cewa wayayyiyar mace ce, wadda ilimin boko ya ratsa ta. Gidansu gabadayansu yan boko ne. Kai ita kanta a kasar Germany naji ance taje ta hado degree dinta. Matsalarta daya, rashin shiga mutane. Zaku iya kwashe sati cikakke baku hadu da junanku ba, ni da yake dama ba zuwa gidan nake yi sosai ba, zan iya cewa na kwashe watanni fiye da biyar ban ganta ba.

Muka karasa wajen da take, daidai lokacin da diyarsu mai kimanin shekaru biyar, Ruqayyah wadda suke kira Mimah, ta fito daga daya gefen mai zaman banza dauke da jakarta da lunch box.
A lokaci daya muka gaidata ni da Janan, ta amsa tana kama hannun Mimah da take kokarin isowa gareme, jininmu ya hadu da ita sosai. Halin mahaifiyarta na shiga part dinta ta rufe ta kuma hanata fitowa yasa bamu haduwa da ita sosai, sai lokaci zuwa lokaci.
Tana gamawa amsawa ta latsa key tasa motarta a lock, taja hannun diyarta suka tafi.

Duk da haka sai da Mimah ta juyo tana daga mana hannu, mu duka muka daga mata hannun muna murmushi har suka shige part dinsu, ta rufo. Ni da Janan muka kalli juna muka sake yin murmushi, kafin muma muka shige nasu part din.

Adi, da Haleemo suna kicin lokacin da muka shiga, Raheemah kuma tana zaune tana sana'ar kallo, ban san ina Salama ta shiga ba tunda bamu ganta ba. Mu dai muka musu sannu, muka shige daki ba tare da mun damu da kallon banza da aka bimu dashi ba.

Bayan la'asar muka fita waje ni da Janan muka sayo fruits a bakin titi. Muka zo muka hada fruits salad da kayan shan ruwa. Muna cikin soya yam balls, Salama ta shigo kicin din. Babu wanda ta yiwa ko sannu a cikinmu, ta dauki plate kawai sai ganin tana zuba yam balls din a plate din muka yi. Ta debi iya wanda zata dauka, ta fita daga kicin din. Duk kallo muka bita dashi har ta fita. Maimakon abin ya bani haushi, sai ya ma bani dariya. Na girgiza kai kawai, a zuciyata ina furta 'Allah ya kyauta!'.

Sai bayan mun sha ruwa sannan na kunna wayata. Messages, missed calls, voice mails, messages din whatsapp da voice notes babu iyaka daga Umar, duk abu daya yake tambaya, 'don Allah in daga wayata', na harari wayar tawa kamar shine a gabana, in daga wayata in ce mishi me?!











*☆⋆09⋆☆*





Har washegari Umar bai daina kiran wayata ba, nima kuma ban daga ba. Zuwa lokacin missed calls dinshi sun fi a kirga.
Da safe ina browsing din wasu procedures a wayata lokacin da nake jiran Jan ta fito daga wanka, don na rigata shiryawa. Wata bakuwar lamba ta min sallama ta whatsapp. Daga farko nayi zaton ko Umar ne, sai dana bi ta cikin description dinshi sannan naga kwata-kwata komi nashi bai yi shige da na Umar ba. Na farko dai Umar daya zauna ya zubo miki layi biyu a rubuce, ya gwammace kuyi awa biyu akan waya kuna hira. Shi yasa yanzun haka voice notes dinshi ne suka cika min waya.
Kamar wanda yake jira, ina amsawa ana maido da amsar ya nake? Fatan na tashi lafiya?.
Nace lafiya lau, ko wanene yake magana?
Sai aka turo, 'ba lallai ki sanni ba gaskiya, amma ni na sanki farin sani. Ba tun yau ba nake ta so in miki magana, sai yau Allah ya yarda. Sunana Muhammad'.

Na rubuta, 'to Malam Muhammad ko zaka iya sanar dani inda ka sanni? Don bana tunanin nasan wani Muhammad anan inda nake'.
Yace 'in shaa Allah zaki sanni nan ba da jimawa ba, na miki wannan alkawarin. Magana ta gaskiya yanzu bana gari shi yasa, amma da zarar na shigo zan zo in same ki, nasan lokacin kuna shika'.

Na daga gira cikin mamaki, ta alama mutumin nan ya sanni fiye da yadda nayi tsammani. Nace 'ta yaya aka yi kasan haka?', ina tura mishi amsar Jan tana fitowa daga bandaki, na kashe datar na sauka daga kan WhatsApp din ina kallonta. Zama tayi ta gama shirinta a nutse. Tana gamawa muka ci pancake da muka yi da ruwan shayi, da muka gama muka dauki sauran da muka yi muka kai kicin muka wuce.


*

Yau sai yamma likis muka dawo daga asibitin. Da yake yau a bakin titi muka sauka, akan kafafunmu muka gangaro zuwa gidan Yaya.
A kofar gidan, Umar ne tsaye ya jingina da motar shi. Na danyi turus da ganinshi, gabana yana faduwa, kafin na dake muka cigaba da tafiya.
Da sauri ya tari gabanmu, "Na'ilah, sweetie, don Allah ki dakata, don Allah ki saurareni, wallahi na tuba, don Allah....".

Jan ta kalleni, yadda na hade fuska kamar naga wani dan aiken mutuwata, yasa ta fara raba idanu tsakanina da Umar. Yaci gaba da zuba magiya yayin da na zagaya ta gefenshi na tunkari kofar gidan gadan-gadan. Janan ta riko hannuna, na juya ina kallonta, tace "meye haka Na'ilah? Ban san ki da wulakanta mutane ba sam".
Nace "kiyi shiru Janan, baki san abinda ya faru ba, don haka kada kiyi kokarin shiga cikin wannan fadan".
Umar yayi tsulum da bakinshi, "don Allah ki saurareni Sweetie, please...".

Na kare mishi kallo, duk da kokarin dannewa da nake yi, da nuna kamar ban damu ba, amma nayi kewar shi. Kwana daya da yini daya kacal, amma nayi kewarshi.
Na kalli Jan data tsaya tana kallonmu, nace "ki wuce abinki kawai, zan shigo in same ki". Babu musu ta shige cikin gidan ta barmu a tsaye.
Na harde hannu a kirji ina kallonshi, "me? Yanzu kuma mai kake bukata ne? Kana so mu kebe wani waje ne ko kuma ka kama mana daki ne a hotel?".

Ya dafe kai, "Subhanallah, haba Na'ilah me ya kawo wannan maganar kuma? Kuskure ne nasan dana riga na tafka shi, amma ina neman afuwarki don Allah. Wallahi ban san abinda ya hau kaina ba, ok, na sani. Gajen hakuri ne irin nawa, amma wallahi na gane kuskurena, ba zan kara ba, don Allah ki bani dama Na'ilah, na miki alkawarin hakan ba zata sake faruwa ba".
Naji zuciyata ta fara yin sanyi da jin hakan, nace "how sure are you? Ta yaya zaka tabbatar da cewa nan gaba ba zaka sake tare ni a cikin mota, trying to touch me inappropriate ba?".

Ya hau girgiza kai da sauri, "I assure you hakan ba zata sake faruwa ba, na miki alkawarin ba zan kara taba ki ba tare da izinin ki ba har auren mu!".
Nace "idan kuma hakan ya sake faruwa fa?".
Yayi shiru yana kallona, nace "magana daya ce Umar, idan abu makamancin haka ya sake faruwa, we are over! Dama kasan hakan ta taba faruwa, yazo ya sake faruwa yanzu, to babu na uku. Idan kuma muka rabu, mun rabu kenan, ka yarda?".
Ya gyada kai, "it's not as if zan sake maimaitawa, but yeah, na yarda. Fushin ki ba abu bane da zan yi marmarin sake gani ba koda wasa. Yanzu dai kin yafe min?".
Nayi jim ina tunani, na yafe mishi? Ya riga yayi convincing dina, kuma yayi alkawarin hakan ba zata kara faruwa ba, saboda haka meye aibun yafe mishi a ciki? Don haka na gyada kaina, ya saki murmushi a tausashe wanda ya sanya ni sakin murmushin nima, "oh thank God! Wallahi baki ji yadda na damu ba, God, I miss you wallahi".
Nayi murmushi kawai, yayin da naji wani sanyi yana kwaranya a cikin raina. Ban sani ba, na yafe mishi din da nayi ne, ko kuma na dawowa gareni da yayi bane. Kafin in sake daga baki inyi magana, muka ji kiran sallah, ya kalleni yana murmushi, "bari in wuce masallaci to, zan kira ki zuwa anjima".
Na gyada mishi kai tare da shigewa gida.

Bayan mun ci abincin dare a dakin Janan, ta zauna a gefen katifa suna waya da Al-Mustapha saurayinta, ni kuma na shiga whatsapp chatting. Sakon mutumin nan na dazu shine abinda na fara gani, ni na ma manta dashi.
Amsar tambayar dazu dana mishi da safe ce ya turo min, "kamar yadda na fada miki, na san ki farin sani. Kuma ina matukar kula da lamuran wadanda suke very special a gareni, don haka ba wani abin mamaki bane".

Na maida mishi da amsar 'haba? Ta yaya aka yi na zama very special a gare ka?'.
Babu jimawa sai ga reply ya shigo, 'oh, you are very very special in fact! Idan nace zan miki bayani zamu jima a haka, to cut it short, ina jin ki a cikin raina fiye da yadda kike tsammani'.
Haka kawai na tsinci kaina da darawa. Wani abu game da mutumin is very fascinating, yet so familiar. A karo na kusan biyar tunda muka fara chatting dashi yanzu, da naji a jikina duk yadda za ayi mutumin nan ya sanni fiye da sani na, kuma nima ko yaya ne na san shi. Sai dai duk hakan bai dameni ba, yadda naji hira dashi ta dauke min hankali, shine abinda ya bani mamaki ya kuma daure min kai a lokaci guda. It's a first.

Mintunanmu talatin kacal muna hira ta hanyar musayar rubutattun kalmomi, sai gani kwance rigingine a tsakiyar daki, ina kallon fankar dakin dake juyawa, waya a hannu ina ta faman rubutu, yayin da lokaci zuwa lokaci sautin dariya zai fito daga baki na, walau na sani ko ban sani ba. Hakan ya kan sa Jan, da har lokacin tana kan waya, zata juyo ta kalleni cikin alamun tambaya, amma bata tambayeni ba.

Zuwa lokacin da yayi min sallama akan wani aiki da zai tafi yayi, ba ni kaina ba, hatta zuciyata da gangar jikina naji sun aminta da mutumin. Wanda hakan a karan kanshi ma abin tambaya ne, na farko ban san mutumin ba, babu abinda na sani dangane dashi sai sunanshi, yana aiki da wani kamfani da yake sarrafa takardu, shikenan. Dana tambayeshi yana da mata? Sai yace ba ga ki nan ba? Hakan yasa naji sautin bugun zuciyata kamar zai tsaga tsakiyar kirjina zuciyar ta fito.
Tsakanina da Allah ban so muka yi sallama dashi ba, na tabbata idan zamu kwana muna chatting dashi ba zan taba damuwa ba a cikin raina, kai a takaice ma zan so hakan ba kadan ba. Muka yi musayar sai da safe, ya tafi bayan ya turo min 'sleep tight!', ya Allah, ban taba jin dadin ganin kalmomin nan daga kowa ba a rayuwata sai a yau din nan.
Yana sauka naji gabadaya chatting din ya fita daga raina, don haka nima na sauka.
Na lalubo jakata na ciro littafai daga ciki na fara karatu da bibiyar practicals din da muka yi yau.

Sai wajen karfe goma Jan ta gama tata hirar da Almunta, (yadda take kiranshi). Ta juyo ta kalleni tana murmushin tsokana, "fadan masoya hutu, wato saboda kun shirya shine kike wannan glowing?".
Nayi murmushi kafin na jefa mata harara, "ni kada ki min sharri wallahi".
Tace "wani sharri? Ga abu nan a fuskarki, kin kuwa ga yadda kike ta zuba murmushi sanda kuke chatting dinnan? Har wani dariya kike yi, irin soyayya tayi dadi dinnan!".

Na danyi frowning ina kallonta, a hankali nace "ba da Umar nayi chatting ba dazu".
Ta hangame baki cikin mamaki, "wasa kike yi ko? I mean, idan ba Umar ba, waye to? Yanzu da kika fadi haka sai na tuna Umar baya dogon chatting, wanene muka samu??". Ta karasa fada tana daga min gira cikin alamun tsokana.
Na jefeta da littafin hannuna, ta cafe tana dariya, "fada min mana!".
Na mike ina tattara kayan dana baza a wajen na maida su cikin jaka. Bandaki na fada kai tsaye na barta tana ihun, "ko shekara zaki yi a ciki sai kin fito kin fada min wanene yarinya!". Dariya kawai na saki mai sauti. Nasan kafin in fito ta manta da zancen.

Har mun kashe wutar daki bayan mun kwanta, Janan ta kira sunana, na amsa a dan gajiye da kuma barci daya fara cin idanuwana, tace "wai me ya hada ki da Umar ne da?".
Nayi sighing a hankali, "abinda ya faru ya riga ya faru Jan, mun riga mun shirya dashi, that's all that matters. Tone-tonen abinda ya riga ya faru, babu abinda zai mana, don haka ki manta da maganar".
Tace "of course sugar, baki da matsala dani".
Kaunarta naji tana kara ratsa zuciyata, fahimtarta da goyon bayanta a kullum suna kara sa inji ta can cikin zuciya da ruhina. A hankali nace "nagode Jan".
Ina jin sautin murmushin data saki cikin duhun dakin, "sai da safe Na'ilah!".
Nima na maida mata martanin murmushin duk da nasan ba lallai ta gani ba, nace "sai da safe Jan!". Na juya barin damana, tare da rufe idanuna.

Daren ranar mafarkai nayi masu yawa, da yawa daga cikinsu sun kunshi wani mutum da yake ta nanata kalmar, "ke ce Matata!," kamar waka.



-Afuwan, in shaa Allah gobe zan turo mai yawa, wannan dinma aradun Allah da kyar hannuna da idanuna suka bada hadin kai nayi typing dinsa. Thank you all.








#F.W.A










.




.







*☆⋆10⋆☆*





A gabadayan tarihin rayuwata, ban taba, ko a cikin mafarki kuwa, tunanin akwai wata rana da zata zo da zan kwanta in kuma tashi da tunanin abu daya a cikin raina ba, musamman idan abinnan ya kasance d'a namiji. Amma yau sai gani na tashi cike da tunanin wannan bawan Allah da ko sunan shi ban sani ba. Har nayi wanka, na shirya, muka karya, muka dauki hanyar asibiti, tunaninshi ne a cikin raina. Daidai da sakan daya bai bar cikin raina ba.
Muna kan hanya, text message dinshi ya shigo cikin wayata. Na zaro wayar daga cikin jaka na daga, kawai cewa yayi,
*'salam, just wanted to say hi... Ban sani ba ko kinyi tunanina tunda kika tashi, ni dai nayi. Anyway, have a nice day!.'*
Ji na nayi kamar wadda aka wa kyautar kujerar makkah. Garin bai ma gama wayewa ba, amma wannnan text din kadai made my day already.
Na shiga cikin contacts dina nayi saving number da, 'Mysterious'. Wannnan a karan kanshi abin tambaya ne ga wadanda suka sanni farin sani, domin haka kawai bana saving lambar mutane a cikin wayata, musamman wanda na sani na rana daya kacal, abu ne mai matukar wahalar yarda a wajensu.

Yau ma da wuri muka dawo gida. Yau gidan babu kowa, muka dauki makullin gidan a wajen da suka saba ajiyewa muka bude muka shiga. Bayan sallar la'asar muka shiga kicin ni da Jan, muna cikin girki sai ga Haleemo ta fado kicin din, bamu ma ji lokacin data shigo gidan ba. Ta mana sannu muka amsa, tace "don Allah wayar wa take da sauran canji a cikinku ta taimaka min inyi kira?".
Jan tace ta baro wayarta a daki, ni kuma da wayata take saman cupboard muna sauraren kida da ita, na dauka na bata. Tayi godiya ta amsa ta fita.

Janan ta kalleni bayan fitarta, "da alama kuna shiri da Haleemon nan".
Nace "tafi sauran yan uwanta kirki da rashin rawar kai shi yasa".
"uhmmm, don dai kawai ba a gabanki take yin abubuwa bane, amma kada ki bari shiru-shirunta ya kwashe ki wallahi, duk ta fisu rashin mutunci".
Na kalli kofar da tabi ta fita cike da mamaki, "amma kuma yanayinta sam bai yi kama da irin nasu ba".

Tace "dama idan mutum bashi da mutunci, rubuta shi yake yi a goshi ne? Ai ba tambari gare su ba, lokacin da suka buga miki shi ne zaki ji kamar kiyi kuka". Na kyalkyale da dariya.
Ta girgiza kai, "wato dariya ma na baki? Zaki yi bayani ne yarinya!".

Haleemo ta dawo kicin din, ta miko min wayar tana murmushi, "yauwa, nagode Na'ilah". Na jinjina mata kai ina dan murmushi kawai, na karbi wayar na maida na ajiye.
Ta leka kanta cikin tukunyar da muke girki da ita, "sai kamshi mai dadi yake tashi, me kuke dafawa ne?".
Nace "shinkafa ce da miya". Tayi murmushi, "ki ce yau dadi zamu ci? Amma nasan sai zuwa dare don yanzu kaya zan dauka, wajen kamun bikin wata cousin dinmu zamu je".
Ni da Jan dai "humm!" kawai muka ce mata, ta fita daga kicin din. Bayan ta dauko kayan ma, sai data biya ta mana sallama sannan ta wuce. Mu dai muka samu muka gama girkin. Muka zuba musu a cikin manyan kuloli, mu kuma muka dauki namu muka wuce daki.

Da dare Umar yazo, mun jima dashi a gefen gidan muna hira dashi, fir naki shiga motarshi. Ko yanzu ma hirar da muka yi dashi cikin dari-dari muka yi ta. Tun yana korafi har ya koma magiya, ya dawo ban hakuri. Nace mishi yayi hakuri, amma na kasa sakin jiki dashi, a haka dai muka yi sallama.

*


Ranar assabar yini muka yi a daki. Yaya ya dawo daga Abuja, amma da yake a gidan Anty Ameerah ya sauka, kawai dai ya biyo ne muka gaisa. Ina bandaki lokacin daya dawo a jiyan da yamma, har ya tafi bamu gaisa ba. Naji Jan tana cewa sai yau da yamma zai dawo nan.

Tunda muka tashi wajen karfe goma na safe, brush kawai muka yi muka fita falo. Da alama mutanen gidan suna daki don babu kowa, muka shiga kicin da niyar dora abinda zamu karya dashi. Ga kaya nan baje a kicin din, da alamu anyi amfani da kayan ne amma ba'a wanke ba. Abinda suke mana kenan tunda nazo gidan, kodayake nafi kyautata zaton sun riga sun saba yin hakan ne tun ma kafin in zo gidan. Idan suka yi amfani da abu, anan zasu watsar dashi sai dai mu mu gyara. Hatta da su plates din da suka ci abinci, yawanci anan tsakiyar falo suke barinsu sai idan mun je gyara sannan zamu dauke shi.

Yanzu ma tattara su kawai muka yi, bayan mun dama kunun tsamiya, Janan ta soya mana kosai muka shiga daki muka ci.
Muna cikin ci muka ji anyi knocking a kofar dakin, muka kalli juna ni da Jan, kafin ta tashi ta bude kofar. Ina ji ta fara cewa "Yaya ina wuni?", nayi sauri na lalubi hijabi na dora a saman kaina, nima na tashi lallaba na raba ta gefenta na durkusa nima na gaishe shi. Ya amsa hankalinshi akanta.
Dadina da halin Yaya kenan, yana da kulawa, sai dai yana da kame kai matuka. Bai cika sakarwa Janan fuska ba, amma kuma ta acts dinshi kadai zaka san da cewa yana matukar son ta, kuma yana kulawa da ita matuka.

Ya kara zuro kanshi cikin dakin yana shinshinawa, "meye haka kuka ci yake neman tado min yunwata?".
Janan tayi dariya, ni kuma na sunke kai a cikin hijabi ina dan murmushi. Tace "kosai ne muka yi, ko zubo maka zanyi?".
Idanunshi suka dan bude sosai, kamar alamun hope ko dai wani abu mai kama da haka, "kun girka da ni ne dama?".
Tace "mun dai yi da dan yawa ne saboda munyi tunanin zamu iya cinyewa saboda yunwa sai kuma muka yi saura."
Yayi yar dariya, "watarana zarinki zai janyo miki yin kibar da baki so. Ni dai tunda Allah ya taimakeni ya tsaga da rabona, ki zubo ki kawo min ina falo. Dama ban karya ba wallahi.... Mutanen gidan basu tashi bane?," ya tambaya yana juyawa yana kallon falon kamar mai duba wani abu.
Janan tace "bari in kawo maka kunun", ba tare data amsa mishi tambayarshi ta karshe ba. Ya juya ya fita yayin da ta bi bayanshi ta dawo da plate da kofi a hannunta, ta zuba mishi ta cicciba ta fita. Ina jiyo sautin tashin muryarsu, suna hira, don haka na janyo wayata na jingina da bango na tsokano My mysterious Man, kamar yadda sunan nashi ya koma yanzu cikin wayata.

Cikin yan kwanakin nan, mun kulla wata irin abota mai karfi dashi. Bai taba kirana a waya ba, kullum daga text sai ta chats kawai muke hira dashi, duk da cewa Allah kadai yasan yadda nake iya cijewa rashin jin muryarshi da ban taba yi ba, ban taba kokarin gwada kiranshi ba. Amma ina kwadaituwa da hakan. Ina yawan tunano yadda muryarshi zata kasance, yadda shi a karan kanshi zai kasance in person. I really want to see him. Amma dai na daure, ina jira in ga iya gudun ruwanshi.

Har Janan ta dawo, ina kan waya ina chatting dina. Ina jinta tana korafin watarana sai ta dauke wayata, ko kuma ta goge whatsapp da duk chats dina, sai dai kasancewar hankalina yayi nisa ko jin abinda take cewa bana yi sosai. Sai da aka kira sallah muka hakura.

Bayan azuhur, zaune muke a tsakiyar dakin, nayi matashin kai da cinyar Jan din tana warware min kalbar da tayi min. Saboda tsananin santsin kaina da tsayi, ban cika yin kitso ba. Idan ma nayi, baya daukar kwana uku yake warwarewa da kanshi. Jan take zaunawa ta min kalba, watarana sai ta sanya rubber bands kanana a karshen kowane kitso sannan yake dan yin kwanaki biyar zuwa sati. Shi yasa ban cika yin kitson bama sam.

Littafin 'Always a Fighter' nake karanta mana a fili, lokaci zuwa lokaci zan saurara mu dan dara idan na karanta abin dariya, ko kuma mu dan tattauna akan wani abu daya ratso.
Muna cikin haka sai b'ammm!! Karan turo kofa kamar za'a balleta, gabadayanmu sai da muka zabura muka tashi zaune a firgice.

Mimah ta afko dakin a sukwane, kai tsaye bayan labule ta shige ta kame kamar wadda mutuwarta ta biyota. Cikin mamaki nace "Mimah lafiya? Ke da wa?".
Kafin ta amsa, an sake turo kofar dakin dai an shigo, muka maida hankalinmu ga kofar gabadayanmu. Anty Sarah ta fado dakin, tana karewa dakin kallo, da alamu Mimah ta biyo.
Sai data karewa dakin kallo tsaf, sannan ta jiyo tana amsa mana gaisuwar da muke mata, ta kara da, "Mimah bata shigo nan bane?".

Muka kalli juna ni da Janan, ni ce na fara cewa "a'ah, bamu ganta ba". Daga haka ta juya ta bar dakin. Tana bada baya muka hade kawuna ni da Janan muka kwashe da dariya, tace "baki da kirki wallahi, mutum da diyarshi?".
Nayi dariya nace "kika san ko laifi tayi zata bata kashi? Sannan yarinyar nan tana bukatar fresh air da hasken rana, na tabbata rabonta da waje tunda aka dawo da ita daga makaranta jiya", na maida hankalina wajen inda Mimah ta boye, "Mimah fito, ta tafi".

Ba musu ta fito daga bayan labulen, da gudunta tazo ta haye kan cinyata, na shafa kanta ina murmushi, "meye na gudowa daga gida, laifi kika wa Mommy hala?".
Ta girgiza kai tana dariya, "naa, naki zuwa ta min wanka ne wai zamu raka daddy unguwa, ni kuma Uncle nake so, yace zai kaini wajen granny".
Muka yi dariyar yadda take maganar ni da Jan, na kamo kumatunta ina ja cikin wasa, "uhhhh Mimah, soooo adorable. Amma yi hakuri ki tafi kafin Mommy tayi fushi, ki bari idan kun dawo daga unguwar, sai Uncle din yazo ya kai ki".

Yadda ta dago da sauri, idanuwanta manya, farare tas cike da murna yasa naji zuciyata tayi rashin dadi akan turbar da zan dorata tunda nasan ba lallai hakan ta faru ba, tace "da gaske?".
Na daga

Please Login or Register in order to submit comment