Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

maybe, ba zata yi halin Ramata, Ameerah ko Raheemah ba. Kila ita za ayi zaman mutunci da ita!.








K'arshe!


'THE GREATEST HAPPINESS OF LIFE IS THE CONVICTION THAT WE ARE LOVED; LOVED FOR OURSELVES, OR RATHER, LOVED IN SPITE OF OULSELVES!'.
VICTOR HUGO






*☆⋆Epilogue⋆☆*





Bayan Shekaru Biyar...


"Ni abinda yake daure min kai shine, babu fa abinda na mishi, kawai daga sama kamar saukar aradu naji maganar, ya sakar min ita aka kamar tashin bomb!".
Janan take fada cikin tsananin kunar zuci.
Ni kuwa me zanyi in ba shekewa da dariya ba? Na dinga kya-kyatata kamar ba zan daina ba. Tana gefena tana jefo min bama-baman harara ita kuma. Sai da nayi ta isheni, na gyara zamana ina kwashe kwallar data zubo min.

Tayi kwafa, "baki da kirki wallahi Na'ilah. Saboda ke kina da kishiya, shi yasa kike sheka min dariyar mugunta nima don za'a min?".

Na daga kafada, "tunda na dandana, kowa ma ya dandana mana. Ke dalla ki kwantar da hankalinki, ki daina wani daga hankalinki akan abinda bai taka kara ya karya ba. Ita fa kishiyar nan, wallahi gane mata ne mutane basu yi ba saboda kawai sun riga sun fadawa kansu ba abokiyar zama bace, amma da gaske abokiyar zama ce. Ke ni yanzu wallahi Abban Maama ko ta uku da hudu yace zai karo, zamana zan gyara kawai ince Allah ya shigo dasu gidan lafiya. Ga fili ga mai doki, to ma wai, a kaina zasu zauna ne? Wasu ayyukan ma zasu rage min karewa. Ko ba komi, kin samu rarar kwanakin girki, kin samu abokiyar tayin ayyuka da hira, kin samu yar tayin raino da hidimar gida, sannan at least, wulakancin namiji ba sai kare a kanki ke kadai ba, ya dinga rabawa biyu yana bata rabi itama".

Janan ta kame baki, tace "Innalillahi! Na'ilah, kece kuwa ko dai wata ce mai kama dake?".
Nayi murmushi nace, "shafa ki ji!".

Ta jinijina kai, "Allah kenan! Kuma rayuwa kenan, babu abinda ta bari. Idan wani yace min akwai rana da zata zo ki tausar da wani akan zama da kishiya, wallahi ba zan taba yarda ba".

Na gyada kai a hankali, ko ni kaina ina mamakin kaina.

A shekaru biyar ko shida da suka wuce, idan wani ya fada min cewa zan zauna in fadi wani alkhairi game da zama da kishiya, hakika da idan muka fara fada dashi babu wanda zai iya raba mu dashi sai Allah.
Ban taba zaton akwai lokacin da zai zo, in so kishiya ba, in kuma kaunace ta, ban taba ba.

Duk a zato na, kishiyar bala'i, masifa ce, wadda zata kawo maka rashin zaman lafiya da kowa naka, wadda zata kawo maka bakin jini ta sanya maka cuta a cikin jiki da zuciyarka. Ashe duk rashin fahimta ce ta kawo hakan.
A zato na, bata nufar kowa da alkhairi sai sharri. Nayi zaton tana shigowa tunanin fitar dani daga cikin gidan aurena zata fara yi, sai naga banbanci.
Tabbas Anty Sailu tayi gaskiya, da tace ba duka aka taru aka zama daya ba. Duniyar Allah mai fadi ce, ba'a rasa mutanen kirki a cikinta. Kamar yadda ba'a rasa abokan zama na gari a cikinta.

Ina ga ni nayi dace ne sosai, Allah ya hada ni da wadda ban taba zaton zan hadu da ita ba.
Koma dai menene, ta dalilinta sai gashi ina kallon abokiyar zama da wani ido daban, in a different way, in a different light.
Ta saka ni fahimtar cewa, tsanar kishiya dana taso ina yi, saboda banyi dacen haduwa da mai halin kirki bane, wadda take kaunar zaman lafiya da zaman aminci da amana.
Ramata dama can halinta mara kyau ne, irin mutanen nan ne da dama can tun asali basa son wani daban ya rabe su ko wani nasu, sun fi son komi ya kasance nasu ne su kadai, basa son cigaban kowa sai nasu. Saboda haka ne suke yin duk abinda suka ga zasu iya, don su ga cewa sun kawar da duk wani abu da zai yi threatening dinsu da cigaban su. Saboda haka ne su son kishiya ko diyanta, baya cikin lissafinsu, me yasa zaka so abinda kasan cewa ya fika matsayi a inda kake so kaga cewa kafi kowa matsayi?.
Haka Raheemah, haka ma Ameerah.

Na fahimci cewa su irin wadannan mutanen, son zuciya da son kai ya musu yawa. Shi yasa basa tunanin komi, kuma basa tunanin kowa sai kansu.
Ita kuma duniyar yanzu, cike take da mutane masu son kai da son zuciya, yan kalilan ne masu son farincikin wasu da cigaban wasu.

Duk ban fahimci hakan ba sai a dalilin zaman da nayi da abokiyar zama na, Hajara. Yanzu zan iya fada da alfaharina, cewa ita ba kishiya ta bace, 'yar uwa ce. Ta dalilinta idanu na suka washe sosai, har nake iya dauko uzurirrika akan dalilin da yasa wadanda na zauna dasu a baya suka dinga yin abubuwan da suka yi din, sai naji na dan fahimce su. Duk da cewa naga rashin wayonsu, tausayinsu yafi rinjayata.
Dama sun bi ta wata hanyar da ba wannan ba.
Dama basu biyewa rudin duniya, shawarar abokan banza, da bakar zuciyarsu ba.
Dama sun bi ta hanyar data dace, dama sun sowa wasu daban irin rayuwar da suke sowa kansu.
Watakila da yanzu muna tare dasu cikin aminci kamar yadda muke zaune da Hajara.

Kwanaki naji cewa Ameerah ta samu tayi aure da kyar, bayan manema kusan shida na fitowa suna guduwa saboda zancen dalilin da yasa ta bar gidanta na farko da suke ji. Sai daya zama kamar ma kyautar da ita ma iyayen suka yi. Gidan mata uku aka kaita, itace cikon ta hudu. Ga tarin 'ya'ya. Hakan yasa ni zama wani tunani, duk wata kauna da iyayenki zasu nuna miki a matsayinki na 'ya mace, ta dan lokaci ce. Dole dai gidan aure nan ne gidanki na har abada. To ko meye amfanin shiga cikin rayuwar auren 'ya'ya da iyaye suke yi? Bayan sun san cewa, daga ranar da ka karbi sadakinta, duk wani hidima nata da komi nata ya tashi daga karkashinsu ya koma kasan wanda ka aurawa? Yakamata iyaye su bude idanunsu, su kuma kula da cewa shiga cikin rayuwar auren 'ya'yansu mata da suke yi suyi babakere, har su dinga karfafa mata gwiwa akan sabawa miji, hakan baya haifar da komi, sai zubewar darajarsu a idon yaransu da mazajensu, wanda hakan zai iya kawo rabuwar aurensu daga karshe. Kunga anyi biyu babu kenan. Tunda ba kowa bane zai iya zama ya iya jurewa a dinga yi mishi wasa da rayuwar aure.

Na sauke ajiyar zuciya a hankali ina kallonta, nace "baki kula da juyin da aka samu bane? Lokacin da za'a min kishiya nima fa haka kika zaunar dani kina min nasiha da bada shawarwari".

Ta gyada kai tana murmushi, "kwarai anyi haka. Sai dai ni ban taba zaton idan nawa lokacin yazo ba, zaki maidawa kura aniyarta ba".

Na hau karewa falonta kallo, hotunanta dana mijinta da 'ya'yansu, Abdul-Azeez kusan sa'an Muhaaseen, da dan kaninshi Sultan, sun mamaye falon. Shekaru uku da suka wuce aka wa mijinta Al-Mustapha canjin wajen aiki, suka dawo Abuja. Tun daga nan muka kara hadewa, kanmu a hade yake sosai. Musamman da wajen aikinmu ya zama daya, tare da ita muka yi masters dinmu anan wata private university. Hajara ma ta shigo cikinmu. Idan ka ganmu kamar wasu 'yan uku, babu mai cewa ita din kishiyata ce.
Kulsum ma ta auri wani dan kasuwar kayan masarufi, tana Kaduna abinta da danta Suleiman.

Nace "rayuwar kenan, haka take zuwar ma mutum a bai-bai, cike da ban mamaki da tu'ajjibi". Ta gyada kai.

Nace "to yanzu ya ake ciki ne?".
Tace "ni fa dama can ban hana shi yin auren shi ba, ce mishi nayi Allah ya sanya albarka. Kawai ina ta tunanin ta inda na gaza ne da har zai yi tunanin kinkimo min kishiya ya kawo min. Naga dai babu abinda na rage shi dashi. Gyaran jikin nan duk karshen wata yin sa nake, watarana ma kafin karshen watan yayi nayi. Ke karewa ma, VIP ce ni a Tee-Tee's Care. Ki duba fa yadda fatar jikina take taushi da laushi da komi!". Ta karasa fada tana nuna min hannunta.

Na matsa gefe guda ina harararta cikin dariya, "dalla can matsa Malama. Wai ke an fada miki wadannan abubuwan suna hana maza karo aure ne idan suka yi niyya? Kawai dai nasan suna kara miki wata daraja a idanunsu musamman idan ita wadda aka kawo miki din bata san sirrin gyaran nan ba".
Ta gyada kai.
Hakan ta tuno min, lokacin da Hajara ta haifi Suhaima, sai data kusa yin yaji saboda yadda Yaya ya dinga mata. A cewarta, ce mata yayi gabadaya ta canza, yace ta same ni in gaya mata yadda ake gyaran jiki idan aka haihu. Wanda hakan shi ya bata mata rai. Ni kaina naji na tausaya mata, sai dana sameshi kuma na fada mishi hakan babu dadi, kuma bai dace ba.
Saboda tsananin gyaran dana samu lokacin dana haifi Muhaaseen, sai da Yaya yayi min kyauta mai girma. Su Anty Haleemah kuwa da su Fatsu sun sha godiya tafi cikin daro.
Sai dana zaunar da ita na fahimtar da ita muhimmancin irin abubuwan nan, duk da hakan ma dai tana dan yi ne kawai. Su ainihin yan boko ne, irin wadannan abubuwan babu su a cikin dictionary dinsu. Lokacin data fada min haka, ba karamar dariya na sheka mata ba. Kitso da kunshi ma, musamman ma dai kunshin, sai idan zamu je ni da Janan muke jan ta muje.
Mawuyaci ne kaji fadan mu ni da ita, idan ma kaji, ba akan son zuciya bane fadan, abu ne ziryan tsarkakke, ko kuma kawai sabawa da zaman tare yake kawowa. Wannan kuwa is natural, fada ce kuma ta ma'aiki, duk zaman da za ayi shi babu ire-iren samun sabanin nan, akwai alamar tambaya a cikinshi.

Nace "ke dai kawai sai dai muyi fatan Allah ya hada mu dana kwarai ne kawai, amma fa wani gyaran jikinki da wasu karairayar ki, babu abinda zai sa balle ya hana wallahi".
Tace "gaskiya ne, Allah dai yayi mana zabi mafi alkhairi, ya kuma bamu ikon zama dasu lafiya. Allah yasa mu cike ibadunmu lafiya".
Nace "ameen".

Tashi tayi ta shiga kicin tana fadin bari ta duba abinda ta dora akan wuta. Ni kuma na dauki wayata na turawa Yaya da yake kan hanyarshi ta dawowa daga kasar Germany, sakon Allah ya kiyaye hanya. Shekara guda kenan da aka maida shi Manajan gidan jaridar Daily Trust. Alhamdulillah, budi ta ko'ina muke samu. Tuni na haura matsayin da zan jira ayi min wata hidima komi girmanta kuwa, sai dai in yiwa wasu. Ko babu aikin da nake yi, Yaya Bilal ya kasance mijine mai tsananin kula da duk wata hidima ta iyalinshi.

Janan ta fito da kwaton bowl a hannunta, tun kafin ta karaso kamshin daddawa da tafarnuwa ya min iso, naja miyau na hadiya mukut!. Cikin da nake dauke dashi mai kimanin wata uku, ya sanya min tsananin son kwadayi da son ciye-ciye.
Ta ajiye farfesun kayan ciki dana sameta tana dafawa a gabana. Na shaki numfashi, dadin kamshin yana ratsa min har cikin kwanyata.

Nace "kyawunta abinnan ace har 'yar uwata zata samu".
Janan ta zauna a kusa dani tana zuba farfesun a cikin madaidatan plates, "ai fa, komi 'yar uwa, 'yar uwa. Na ajiye mata nata a microwave, don nasan kalar mitar da zan sha idan ban ajiye mata ba".
Nayi dariya, "kin kyautawa kanki kuwa", na karbi plate din data miko min na fara ci.

Ina cikin ci wayata tayi kara, hoton Hajara da aka dauka rungume da Muhaaseen ya bayyana, nayi murmushi, "kinga yar halas din ba", na dauka.
Fada min tayi ta tashi daga wajen aiki, zata biya makaranta ta dauko yara sai ta biyo nan ta daukeni, nace mata sai tazo.
Muna yan hirarrakinmu, har suka iso gabadayansu. Yaran suka zo suka rungume ni, na dauki Suhaima da take rarrafe na dora ta akan cinyata.
Janan ta zubowa Hajara da sauran yaran, suka fara ci. Yaranta sun riga su Muhaaseen samun hutu, suna Kaduna.

Suna gamawa muka fara haramar tafiya, Al-Qaseem da muke kira Papa, yarona mai kimanin shekaru uku da rabi, ya dauki Suhaima ya fita waje da sauri yana cewa bari ya riga mu. Duk muka rufa mishi baya muna dariya.
Janan ta raka mu har gaban motar Hajara, dankareriyar Maybach GLS 650, shigen tawa ce. Ba'a jima ba da Yaya ya canza mana su, ni tawa ruwan maroon ce mai duhu, tata kuma ruwan hoda mai haske. Na shiga gidan gaba, ina zama Papa ya dora min Suhaima akan cinya data mishi tumbud'i, yana yatsinar fuska yana mitar shi fa shiyasa baya son daukarta. Ni da Hajara kam dariya muke ta mishi. Janan ta karbi tissue a hannun Hajara data yago, ta goge mishi gefen riga. Daga nan dai muka daga mata hannu muka harba kan titi.

Muna isa gida, muka tura yaran daki akan su je su shirya kafin lokacin zuwa islamiya yayi. Mu kam shirin tarbar maigida zamu shiga yi.
Hajara tace "Yaya, idan mun gama zan nuna miki wasu sababbin kayan daki, kila wadannan suyi naga suna da kyau".
Nace "to shikenan".

Bikin Maryam yana ta matsowa, wannan shekarar zata gama degree dinta akan chemistry a ABU, tana gamawa kuma za ayi aurenta ba da jimawa ba. Ni da Yaya Mudatthir aka dorawa alhakin kayan dakinta, hakan bai dameni ba ko kadan, hasalima naji dadin hakan. Ko babu komi an nuna mana cewa muna da wani gurbi a wajensu.
Shi yasa ni kuma na daurawa Hajara aikin nema mana kayan daki har ma da wasu daga na kicin, masu kyau na garari, tunda fanninta ne. Tana aiki da wani babban kamfani ne anan Abujar, sukan zana abubuwa iri-iri, kayan daki ne, gidaje ne, makarantu, masana'antu, da sauransu. Akwai ainihin kamfaninsu dake Saudi-Arabia, shi yake kera ire-iren abubuwan da suka zana din, a sayar.

Tuni magriba ta fara kawo kai lokacin da muka gama. Muka yi wanka, muka cancada kwalliya kamar masu zuwa fashion show. Dole Hajara ta koya min zana gira da yafa eyeshadow, haka nan nake shafawa duk da ba ko wani lokaci ba. Amma kuma duk lokacin dana yi din na kan sha yabo da kirari wajen wanda aka yi domin shi din. Suma yaran muka shirya su bayan sun dawo daga makaranta. Daga nan zuwa kowane lokaci Yaya zai iya dirowa, tun dazu Balarabe ya tafi dauko shi.
Muka zauna akan manya-manyan leather seats din dake cikin falon da muka canza, muna duba kayan dakin. Har dai muka tsaya akan wasu jajaye da farare da suka mana, tace zata saka su cikin oda, nace mata to. Daga nan muka koma dakinmu muka yi sallah. Tun kafin in gama na fara jiyo hayaniyar yara, hakan ya tabbatar min da cewa maigidan ya karaso kenan. Banyi gaggawar fita ba sanin cewa ba nice da girki ba. Nasan zai fara yin wanka ne kafin ya wuce masallaci sallah.
Ina dakin a zaune ina karatun Kur'ani ya shigo, na mishi sannu da zuwa muka gaisa, ya wuce masallaci.

Sai bayan sallar isha'i muka hadu gabadayanmu a falonshi muka ci abinci. Ni da Hajara muka fara jidar kayan muna maidawa kicin bayan mun gama, Papa da Muahaaseen kuma suka tafi daukowa Abbansu takardunsu na makaranta ya gani.

Na zauna a gefen Papa da yake gaban Abbansu yana duba nashi takardun cikin gyada kai, da yake yaron tubarkallah akwai ilimi, mawuyaci ne suyi jarabawa yaci kasa da casa'in a cikin dari.
Bayan ya gama dubawa, ya janyo yaron cikin jikinshi yana shafa kanshi, yace "good boy, kayi kokari sosai Baba na. A cigaba da kokari ko?".
Yaron ya gyada kai cikin murmushi, yace "that's my boy", tare da bashi peck a kumatu.

Yaron ya wani yatsina fuska, Yayan yana dagawa yasa bayan hannu yana goge kumatunshi, yace "ewww Abba!". Ni dasu Yayan me zamu yi idan ba dariya ba? Yaya ya kama kumatunshi duka biyun yana ja, yace "Babana har yanzu baka daina jin kyankyami na bane?".
Na shafa kan yaron ina murmushi, haka Allah ya halicce shi da son jiki da kyankyami.

Ya maida hankalinshi ga Muhaaseen da tayi shiru a zaune tana kallonsu cikin dan murmushi. Ita kuma kunya da kawaici ne da ita kamar me, abinda wani lokacin nake cewa mai sunanta ta biyo.
Yace "Maama fa, ya ake ciki ne?".

Awa daya da kusan rabi yana ta hira ne da yaran nashi, ya dauko tsarabar su ya kunce musu, kowa aka bashi nashi. Daga nan ne suka mana sai da safe, kowa ya nufi dakinshi. Suhaima kuwa tana kwance akan cinyar Yayan tana barci.

Bayan tafiyar su ne muma aka kunce mana tamu tsarabar. Kaya ne na ado iri-iri, dogayen riguna, takalma flats da heels da kayan su jikkuna masu kyau da burgewa, turaruka da sauran tarkace. Muka hau mishi godiya sosai, Hajara tace "Abban Maama mu kam kana shagawaba mu da yawa wallahi, mun gode, Allah ya saka da alkhairi Ya kara budi mai amfani".

Yace "ai ban muku komi ba cikin abubuwan da kuke yi min, hadin kanku ma kadai ya isheni, balle kuma tallafawarku a gareni da kulawar da kuke bani. Allah dai yayi muku albarka, Allah ya kara hade min kanku gabadaya".
Duk muka amsa da "ameen", a tare.
Abinda ke kara mana kwarin gwiwar kyautata mishi kenan, Yaya baya kyashin yabonmu a ko'ina ne, a kuma gaban ko waye sai dai idan bamu yi abinda ya burge shi ba.

Bayan mun zauna, yace "yaushe yara zasu samu hutun makaranta?".
Nace "nan da sati hudu muke sa rai".
Yace "to ku shirya, umara zamu je gabadaya har yaran".
Muka kalli juna ni da Hajara, kafin muka saki ihun murna muka dira jikinshi muna ihun murna da godiya. Aikin hajji kam mun je shi babu iyaka, mun fara zuwa ni da Yaya, muka koma har Hajara. Haka su Malam ma shekarar data wuce suka je suka sauke. Shi dama Baba yaje ya kai matanshi.
Ranar har wajen karfe sha daya da rabi muna falon ana ta hirar yaushe gamo, kafin na mike tsaye ina musu sallama.
Hajara ta kwashe kayanta ta kai daki bayan ta kai Suhaima ta kwantar a dakin Yaya, Yaya ya taya ni kwaso kayana muka kai dakina.

Yana zube kayan akan gado ya juyo ya janyo ni jikinshi, ya nutsa kanshi a cikin gashin kaina, nayi yar dariya tare da zagaye hannuwana a bayanshi.
Yace "ya kike, ya babynmu, hope baya matsa miki ko?".
Nayi dan murmushi, "dukkanmu lafiyarmu lau. How was your trip?".
Yace "Alhamdulillah, mun samo fiye da abinda muka je nema".
Nace "to madallah, haka ake so".

Mun dan jima a haka, kafin na dago kaina na kalleshi, "kada fa ka tsaida Hajara da jira, nasan itama tayi kewarka, sai da safe ko?".
Yace "wato har kin gaji da ganina kenan?".
Nayi dariya ina kama baki, "ni har na isa in ce na gajii da kai? Ban ki mu dawwama a haka ba. Amma bana so mu shiga hakkinta ne ko kadan".

Yace "to shikenan, sai da safe".
Nace "sai da safe, ku tashi lafiya".

Ya wuce gaba na bishi a baya, a bakin kofa ya juyo ya manna min sumba a goshi, sannan ya juya ya tafi. Nayi murmushi kawai tare da girgiza kai, na maida kofar na rufe tare da murza makulli.
Shirin kwanciya barci nayi, na kashe wuta na bi lafiyar gado.









*_...Alhamdulillahi Rabbil-Aalameen. Masha Allah La Quwwata Illah Billah!_*
*Da haka muka kawo karashen littafin 'A Zato Na'. Ina fata Allah yasa mu fi karfin zukatanmu, Allah yasa kuma mu amfana da sakon da wannan littafi yake dauke dashi. Kurakuran dake ciki, Allah ya yafe mana, ameen.*



*Ina mika sakon dumbin gaisuwata da fatan alkhairi ga daukacin jama'ar ZAB, bamu da bakin yi muku godiya da baku hakuri amma duk da haka zan kwatanta. Mungode, Mungode, Mungode, Allah ya kara dankon zumunci. Bamu so abubuwa suka kai har haka ba, mun gode kwarai da hakuri da tarin uzurirrika da kuka mana, bamu da abin cewa sai Allah ya kara dankon kauna kawai. Fatan alkhairi gareku bakidaya! Jeedderh Loves you all!* 😘 ♥ ♥ ♥

Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels


Please Login or Register in order to submit comment