Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da zagayen da yake.

Falon ya dauki shiru kamar babu wasu halittu da suke numfashi a ciki.

Yace "ban san ko daga ina matsalar nan take ba, amma wannan ba hujja bace. Me kike tunani, kin tsani ganinta ne har haka ko me? Hasbunallahu wa ni'imal wakil!".
Da alamu ya. kasa iya wrapping kanshi akan wannan matsalar, nima hakan take a wajena.

Yace "kwanaki munyi ta cin karo da matsalar yawan gishiri yaji, tsami, da sauransu a duk ranakun da Na'ilah tayi girki, it was so suspicious I can't help but wonder, kina da hannu a haka?".

Ta dago rinannun idanunta da suka rine suka yi jawur saboda tsabar kuka, suka yi clashing da nashi rinannun da tsananin bacin rai, shock da tu'ajjibi suka haifar mishi. "Bab...", ta daga baki zata fara magana yayi gaggawar katseta, "cut it! Tambayarki nayi don haka amsa zaki bani ehh ko a'ah?".
Tayi kasa da kanta a sanyaye, "kayi hakuri".

Ya rumtse idanunshi yana girgiza kanshi kamar yana shaking wani abu daga ciki, "cikin da kika yi b'ari fa kwanan nan?".
Nan ma wani shirun ya ziyarce shi kafin bada hakuri ya biyo baya.

Shirun daya biyo bayan nan was deafening.
Magana daya Yaya ya iya yi a wannan lokacin, "kin cuce ni Ameerah!". Wadda daga jin yadda muryarshi ta lullube da zallan bakin ciki da sararwa, daga gani babu tambaya abin data aikata ba karamin girgiza shi yayi ba. Sai dai ni kaina abin ya girgiza ni, sosai ba kadan ba, wa ma zai taba tsammanin haka daga gareta? Da iliminta, da wayonta da komi. Rashin dabara ce ko kuwa tsananin jarumta?.

Daga lokacin da Yaya ya yanke shawara, na fahimci abinda yake shirin aikatawa, niyyarshi a bayyane take, idanunshi sun rufe da takaicin abinda tayi.

"That's it Ameerah... Kije na..."

Ban san lokaci ko dalilin daya sanya ni mikewa tsaye da sauri ba ina mai ambatar sunanshi, dalilin daya sanya shi dakatawa kenan, ya tsaya yana kallona cikin nuna alamun tambaya.
Nace "Yaya, kada ka aikata abu cikin fushi kazo daga baya kana dana sani, don Allah ka fara nutsuwa tukun".

Ya kalleni, ya juya ya kara kallonta, ya daga baki kamar zai yi magana, ko kasa yin maganar ma yayi? Kawai juyawa yayi ya fita daga cikin falon da sauri.

Ameerah tayi tsaye a nan inda ya barta, kusan minti daya, kafin ta lallaba ta fada cikin dakinta. Na koma cikin kujerar dana tashi na sake zama. Ba ni na aikata abin ba, amma har yanzu ilahirin jikina rawa kawai yake yi. Ita Raheemah na tsaye a inda take, bata da niyar motsawa. Allah kadai yasan iya lokacin da muka dauka a haka, bayan rawar da jikina yake yi, wani irin sanyi jikin nawa ya dauka ta yadda ko yatsar hannuna kasa motsawa nayi.

Zuwa can sai muka ji karar bude kofa, muna daga kai sai muka ga Ameerah ta dora gyale a kafada, ta ratayo jaka a daya kafadar, makullin motarta a hannu. Babu wanda ta kalla a cikinmu bare muyi tunanin samun karin bayanin inda ta nufa, ta kara gaba. Muma babu wanda yayi gigin tararta bare ya mata magana. Tana fita Raheemah ta juya ta koma dakinta.
Na ci gaba da zama a falon ba ko motsi, ina kallon waje daya kawai; inda Ameerah take tsaye yan mintuna da suka wuce.

Shiru Yaya zai dawo yanzu, amma babu alamun shi. Ba karamin mamaki nayi ba lokacin dana daga kai na kalli agogo naga goma saura. Sai a lokacin ne nayi kokari na koma dakina ina hada hanya. Sallar isha'i na fara yi. Ko bayan na gama sallar, zama nayi akan abin sallar ina kara neman tsarin Allah daga sharrin zafin kishi, kishi wanda zai iya sanya ni aikata mummunan abu ko kwatankwacin wanda Ameerah ta kwatanta yi yau.
Wani irin kishi ne wannan? Wane irin so ne da zai sanyaka aikata abu kamar sanya guba, da sunan son yin framing din wani, kawai don ya bar maka gida? Anya mata zamu so ganin haske a cikin rayuwarmu kuwa?.

Abin bai taba zuwa kaina ba a cikin rayuwata sai yanzu. Nasan nayi kishi, na kuma san na tsani kishiya, sai dai ko da wasa, ko a cikin mafarki ban taba tunanin zan iya aikata abu irin wannan ba. Sai dai dana zauna na kara yin tunani, sai naga ai tun daga farkon fari, abinda ya sanya ni kin kishiyar kenan. Tsoron juyewa in zama abinda ba ni bace yasa, tsoron kishi ya sanya ni aikata abinda zai zo ya zame min abin nadama nake yi, ina tsoron aikata ire-iren wadannan abubuwan ne.
Na kara rokon Allah akan ya kiyaye zuciyoyinmu daga sharrin sake-saken shaidan, da bin shawarar mugayen kawaye, har ma da yan'uwa.

Sai wajen karfe sha daya sannan Yaya ya dawo gidan, lokacin gidan yayi shiru, ko karar tv baka ji a lokacin balle na mutane, har lokacin kuma ina zaune anan inda nake.
Kirana yayi a waya yace in same shi a falonshi. Na tashi na fita, yana zaune akan kujera da ledoji a gabanshi. Sai lokacin na tuna ban dauke kayan abincin ba ma. Ya miko min nawa, buyin kuma yace in mika musu, da alamu bai san Ameerah ta bar gidan ba.
Dana fada mishi Ameerah bata gidan, bai ce komi ba, kai kawai ya gyada tare da tashi ya fada dakinshi.

Na kwashi ledojin na tsaya ta kofar dakin Raheemah na buga mata kofa, ta leko na bata. Bata ce komi ba ta amsa ta maida kofar ta rufe. Sauran kuwa sai kicin na kaisu na ajiye don babu abinda zai iya shiga cikina a lokacin. Na kwashe kayan nan gabadaya na zubar da komi, har lokacin ganin komi nake yi kamar a mafarki, na kasa yarda ya faru.

Sai wajen karfe goma sha biyu nayi sallama dakin Yaya. Yana kwance akan gado, amma ba barci yake yi ba. Na zauna a gefen gadon ina kallonshi, bai yi ko motsi ba.
Zuwa can nace mishi "ba zaka ci abincin bane? Ko zan sama maka wani abu ne?".
Ya girgiza kai. Sai ban takura shi ba, na tashi na kashe wutar dakin na koma na kwanta.

Nasan yana bukatar lokaci kafin ya samu komi ya zauna mishi a kai. Ko ni kaina abin ya kasa zaunar min, balle shi, da suka kwashe lokuta masu tsayi da ita, to think that zata iya betraying dinshi ta haka, abu ne mai wahala. It must be a big blow. Daga ni har shi babu wanda ya tankawa wani, muna ta sake-sake. Ranar kam barci sai barawo.


*

Washegari karan wayar Yaya ne ya tashemu daga barcin da muka koma bayan sallar asuba. Kaina har juyawa yake yi saboda tsabar ciwo da rashin barci.
Sai da tayi kara sau kusan uku babu kakkautawa, a raina har ina mitar wane mai gajen hakuri ne wannan da bai san ya kira sau daya ya hakura ba? Karfe bakwai da rabi ma bata karasa yi ba lokacin.
Sai da kira na uku na katse, yana katsewa kuwa na hudu ya sake shigowa. Sannan Yaya ya kai hannu ya dauka.

Murya shake da barci ya fara da yin sallama, sai dai da alama mai kiran wayar bai damu da sallamar tashi ba, ya tare shi da "Me Ameerah ta maka ka turota gida tun da sassafe?". Da alama Babanta ne.
Kasancewar a kusa dani yake, ina jin maganar da ake yi a daya bangaren.

Tashi zaune yayi yana gaida shi, wannan karon ma bai amsa ba, ya kara maimaita mishi tambayar daya mishi. Tashi yayi cimak ya fita daga dakin, na bishi da kallo.
Sai can kusan bayan minti sha biyar, sannan ya dawo dakin. Ya zauna a kan sofa tare da dafe kanshi cikin hannuwanshi. Ganin haka yasa na tashi zaune a tsakiyar gadon.

"Lafiya?". Na tambayeshi a sanyaye. Yanayinshi bai yi kama da wanda yayi tattaunawar arziki da surukin nashi ba.

Ya girgiza kanshi kafin ya dago kai ya kalleni, "ban sani ba nima, kawai dai Ameerah taje musu gidan da safiyar yau, wai tunda taje take kuka bata ce komi ba. Yanzu dai Babanta yace zai zo nan ya sameni, zamu hadu anjima kadan a Will's Park".
Na dan zaro ido, kafin na gyada mishi kai.

Nasan ko na koma na kwanta ma babu wani barci da zanyi. Don haka na tashi kawai na shiga bandaki na dauraye bakina. Na tafi na dora girkin safe.

Abincin sai tsakurar shi kawai aka yi. Karfe daya Yaya ya tafi ganin mahaifin Ameerah. Bai dawo ba sai gab da magriba. Fuska babu yabo babu fallasa haka ya shigo gidan. Ameerah da take girki, ta mishi sannu da zuwa ta bishi zuwa dakinshi.

Sai da dare muna falonshi mu duka, sannan yake bamu labarin abinda ya faru.
Mahaifin Ameerah dai yaki yarda, ko kuma ince yaki daukar laifin da diyar tashi tayi. Daga karshe ma sai ya koma accusing din Yaya kan cewa dama baya kula mishi da diyarshi yadda yakamata, ya maidata ta zama koma baya a cikin dangi. Tafi-tafiya ma sai yace yana bukatar takardar sakinta kawai. Duk yadda Yaya yayi wajen ganin cewa ya fahimtar dashi, abin yaki yiwuwa. Shi a ganinshi abin bai kai ga haka ba, sai ya gangaro yace idan bai sakar mishi diyarshi ba zai iya maka shi a kotu. Sai da ya rubuta mata saki daya sannan ya warci takardar ya kara gaba.

Daga ni har Raheemah babu wanda bai jijjiga da jin haka ba. Muka jinjina maganar sosai, daga karshe nayi fatan Allah yasa hakan shi yafi alheri.

*

Kwana biyu gidan shiru, ita kanta Raheemah ta kame kanta ta kai gefe. A hankali komi yazo ya wuce, ya zama tarihi a wajenmu. Rigima bata kuma tashi ba, kamar hakan ya zamewa Raheemah abin tunatarwa da darasi. Tsakanina da ita sai kallo kawai, ba uhm ba uhm uhm. Habaice-habaice da bakaken maganganu da take yawan jifa na dashi a kullum rana ta Allah babu gajiya, muddin muka hadu sau daya ko sau goma a rana sai an jefo shi kamar wani abin arziki, yanzu ta daina kamar anyi ruwan sama an dauke.

Ko lokacin da tafiyarmu umara yayi, bayan sati biyu da tafiyar Ameerah kenan. Lokacin mun kai azumi na hudu kenan. Yaya yayi mata maganar zamu tafi ranar da aka dauki azumi na takwas, mu tsaya mu kwana a Kaduna, washegari mu wuce Katsina mu kwana. Ranar da aka kai azumi na goma zamu wuce Umra. Daga fari nayi zaton zata hau yin kalar dibar arzikin da tayi kamar da, amma ga mamakina maimakon tayi wani abu, kawai sai gyada kai da tayi ta mana fatan a dawo lafiya.
Shi kanshi Yaya sai da ya nuna alamun yayi mamaki, kafin ya girgije. Yace to tayi list din abubuwan da zata bukata kafin mu dawo. Nan ma tace babu komi.

Wannan karon kam sai da mamakinshi ya fito fili, yace "babu?".
Tace "to duka-duka ko sati daya fa ba'a yi da kawo kayan provision ba. Bamu yi wani amfanin azo a gani da kayan ba".
Yaya yace "to shikenan".

Ranar da zamu tafi, haka ya dauko naira dubu dari cif ya dire mata a gaba. Yace tayi hidimar sallah. Tuni dama tare aka kawo mana kayan sallah da kayan kamun azumi. Manyan atamfofi da leshina, ya kuma hado mana da kudin dinki. Iyayenmu suma haka ya aika musu atamfofi da shaddoji har da kudin dinki. Hatta su Malam ma sai daya aika musu.
Duk da nima sai dana aika musu, da su kayan kamun azumi. Suka yi ta mana godiya da sanya albarka kuwa.

Kamar yadda yace, Kaduna muka tsaya muka musu shan ruwa. Janan ma ranar a gidan ta sha ruwa da yake Almunta baya gari. Muka yini muna hirar yaushe gamo. Da dan yaron cikinta ma kuwa, duk da taki yarda da zancen tana ta min kwana-kwana.
Su dukansu sunyi mamakin abinda ya faru da Ameerah. Abu ne na Ala wadai, amma su dukansu babu wanda yayi mata addu'ar banza ko yayi wata maganar da bata dace ba, sun dai jinjina abin, kafin suka yi addu'ar Allah ya kara shiryata da duk sauran ire-irenta.
Da yake da kayan sallah ta na taho, washegari kafin mu wuce zuwa Katsina, muka je wajen telarta ta auna ni, muka bar kayan dinkin anan.
Muna komawa gida muka wuce Katsina.






*☆⋆48⋆☆*




A gida muka sauka, da yake tare da Balarabe muke, Yaya ya tsaya suka gaisa da Baba, anan ma suka sha ruwa tare da Baban da Balarabe, sannan suka wuce masauki.
Tarba mai kyau muka samu wadda ban yi zatonta ba, ba daga Baban ba, ba daga matan nashi ba, ba daga yaran ba, kowa ya nuna farincikinshi da ganinmu har abin ya bani mamaki.

Sai bayan tafiyar Yaya sannan na fahimci cewa da wani abu a kasa. Tunda muka je, Aliyu da Ramata suna daki, tun lekowar da suka yi suka mana sannu da zuwa suka koma daki, basu kara lekowa ba.
Yanayin yadda na ganta ya tsorata ni, tayi wata irin rama, sai girman shekarunta ya kara fitowa.
Bayan mun kebe a dakin Maryam inda nan na saba sauka, na tambayata abinda yake faruwa da masu gidan. Abinda ta fada min ya girgiza ni.
Wai Aliyu aka kama yana saida ganyen Iblis. Jiya yan sanda suka zo unguwar aka kama gungun yan unguwar da suke shaye-shaye, ga namakinsu sai aka hada dashi. Har wajen karfe ukun dare suna police office din wai, da kyar aka bada shi.
Na kama baki ina jinjina kai kamar zanyi ihu, "garin yaya haka?", na tambayeta, "ban sani ba", itace amsar data bani.

Muna nan a dakin nata muna maida magana, Awwal ya leko yace in je dakin Baba yana kirana. Na dauki hijabita na saka na tafi. Shi kadai na samu a dakin nashi. Na zauna a kasan kujera, muka sake gaisawa dashi a nutse ba kamar ta dazu ba da aka yi ta a tsaitsaye.

Kafin ya daga baki ya sake magana, sai ga Alawiyya da Ramata sun shigo dakin kusan a lokaci guda, duk suka samu waje suka zauna. Na kurawa matar da tunda na mallaki hankalin kaina ta hana ni shakar numfashi mai dadi a rayuwata. Akwai wani lokaci a can baya, da ko sautin muryarta naji tana tashi, sai naji faduwar gaba ta ziyarceni. Akwai wani lokaci da zan mata kallo daya, inji babu abinda nake so da kaunar sake gani kamar in daga idanuna in ga gawarta shimfide a kasan.

Sai dai a yanzu da nake sake dubanta sai naji babu wannan tsoron, babu wannan tsanar, sai tsananin tausayinta daya lullube ni. Hakan kuma baya rasa nasaba da yadda naga ta makure a gefe kamar bera a gaban mage, kanta a kasa yake tunda ta shiga dakin, bata yi gigin daga ido ta kalli kowa ba.
Ba'a jima ba, sai ga Aliyu ya shigo shima, ya nemi waje can kusa da Ramata shima ya makure.

Sai da kowa ya nutsu sannan Baba yayi gyaran murya. Hakan yasa duk muka maida hankulanmu gare shi.
Ya fara da cewa "Ke Na'ilah ke da baki gida, ke kadai ce anan da baki san abinda yake faruwa ba...", nan ya zayyane min duk abinda Maryam ta sanar dani.
Baba ya cigaba da cewa, "saboda haka na yanke shawara, ba zan cigaba da zama da tantirin yaro kamar Aliyu a gidan nan ba. Ba zai lalace ba, kuma daga baya yazo ya lalata min yara, ba zai yiwu ba. Don haka nace mishi ya fita ya bar min gida na tun a jiyan. Ban fada maka kada ka kuskura in dawo gidannan in gan ka ba?".

Aliyun bai ce komi ba sai kara lafewa da yayi a jikin Mamanshi yana shesshekara kuka, yayin da Ramata din take share hawaye itama.

Alawiyya ta wurwusa ta matsa kusa da Baba, tace "Alhaji kayi hakuri da wannan magana da zanyi, amma matakin daka yanke kwata-kwata bai dace ba, ina ga da dai ka sake shawara".

Baba yace "shawarar me zan sake? Zubda kimata da mutuncina yaron nan ya riga yayi, yanzu duk cikin unguwar nan kowa zancen yake yi. To zai zauna yayi min a gida kuma? Ba zan iya ba, ya tarkata nashi-i-nashi ya bar min gida kawai".

Sai lokacin na samu kwarin gwiwar yin magana, nace "Baba kamar yadda Anty tace, wannan fa ba shawara bace. Zancen zubewar girma da sauransu, duk bata taso ba, tunda abinda dai ya faru ya riga ya gama faruwa, kuma ba'a dawo da hannun agogo baya. Abinda ya faru ya riga ya faru, sai dai a tari na gaba kawai. Amma korar Aliyu daga gidannan ba mafita bace, Allah ya gani. Baka tunanin idan ka kore shi din, maimakon ya saduda, sai hakan ya kara sanya shi yabi wata hanyar daban kuma? Duk kuma dai abinda zai yi nan gaba kana da alhaki akai, kuma duk inda zai je ya dawo dai, nan da shekaru goma ko dari, dole ya dawo gareka saboda danka ne, tsatsonka ne. Shi hannunka ai baya rubewa ka yanke ka zubar".

Baba yace "sai dai in hannun baya damuna. Amma tuni zan yar da dan banza in huta. Tun yaushe Aliyu yake bata min rai? Makaranta baya zuwa daga ta boko har ta islamiyar, bai san komi ba sai daukar magana a cikin unguwa. Yau ya zagi wancan, gobe ya bugi dan wancan, shi kadai ranshi yabi ya addabi mutane ina dalili?".

Nace "hakuri dai za ayi, shima ba zai kara ba".

Baba ko in ce iyaye da dama, suna da wani hali na sangarta yaransu, to the extent that sangartawar zata wuce misali. Yara zasu lalace, su daina ganin kan kowa da gashi, wani abin dariya ko tausayi shine yadda hatta da iyayen nasu ma zaki ga basa jin maganar su. Sai labari ya sha banban, yaro yaje ya dauko magana, sai kuma anan iyaye suzo su ce basu san wannan ba. Su zo su kori yaran. To me kenan aka yi? Ihu bayan hari kenan. Maimakon tunda da sanya hannunka hakan ta faru, ka tsayawa yaronka ya koma gagara-badau, lokacin da yayi tashen tsageranci da rashin da'a ka tsaye mishi, maimakon idan sun dauko maganar da tafi karfinsu su sake tsaye musu, a'ah, sai suce sun janye hannunsu daga garesu.
Sun manta lokutan da suka tsaye musu suka dinga yin abinda suka yi din, har suke ganin babu wani ko wata wadda ta isa sai su.
Don bana manta lokuta da dama da mutanen unguwa zasu kai karar Aliyu wajen Baba, akan wani abu da zai musu, muma mun sha kaiwa ba sau daya ba, ba sau biyu ba, amma bai taba daga baki yace mishi don me? Ko kul ba.
To yanzu idan iyaye basu dauki responsibility din laifukan 'ya'yansu ba, wanda idan aka yi duba tun tali-tali suna da kamasho a ciki, wa zai dauka?

Bayan doguwar muhawara da jeka-ka-dawo, da kyar muka samu ni da Anty Alawiyya Baba ya sassauto. Duk wannan abu da ake yi, Ramata da Aliyu na gefe in banda sharar hawaye babu abinda suke yi.
Daga karshe dai yace ya hakura, akan sharadin idan makamancin haka ta sake faruwa lallai zai kore shi. Ni dana kasance zabiya, ni nace naji na amince. Nan ya sake hada mu yayi mana nasiha mai shiga jiki, yace ya sallamemu.

Ina tashi, Ramata ta kamo hannuna. Kuka take sosai kamar wadda aka yiwa mutane, godiya take jera mana kamar harshenta zai fado kasa, "nagode, nagode, Na'ilah! Yau da ba don ke ba ban san yadda zanyi ba, Allah yayi miki albarka, nagode!!".
Ni kam na ma rasa abinda zan ce mata, jiki a sanyaye na dinga binta da kallo har sai da tayi radin kanta ta sake ni, sannan na juya na fita daga dakin.

Kai tsaye dakin Aliyu na wuce, na same shi a gefen katifarshi a zaune. Zama nayi dirshan a tsakiyar dakin, magana muka yi mai tsayi ni dashi game da abinda ya faru. Ba karamin mamaki na ci ba lokacin daya fada min wai kudi yake bukata shi yasa ya fara saida tabar saboda yaga abinda yaran unguwar sa'anninshi suke yi kenan, kuma suke samun kudi.
Nace "kai kuwa me ka nema ka rasa haka?".
Yace "to Baba baya bamu kudi, yanzu ko Mama baya bata. Kudin makarantarmu kusan term biyu bai biya ba, sai da aka koro mu. Kuma Mama bata da lafiya, in taje asibiti aka bata magunguna, Baba baya sai mata. Ya zamu yi?".

Wannan a halin Baba kam ba abin mamaki bane, haka yake. Duk wadda baya dasawa da ita a cikin matanshi, to ba ita kadai ba, har 'ya'yanta ma sai sunji a jikinsu. Na gani a kaina, hakan kuma ta faru akan ido na. Ina ga ina bukatar mu sake zama na musamman da Baba. Yana bukatar wani ya fahimtar dashi irin wannan rashin adalcin nashi, ba abu bane mai kyau. Sai dai dana sake tunanawa, sai naga ba hurumina bane hakan. Watakila Yaya dai zai iya shiga cikin maganar tunda duk cikinmu, baya jin maganar kowa kamar tashi.

Nan na zaunar da Aliyu, na fahimtar dashi cewa hakan fa ba mafita bace, sai jefa kanshi daya kusa yi a cikin halin k'ak'a-ni-kayi. Na tunatar dashi muhimmancin hakuri, da cewa ita rayuwar duniya ba lallai bane sai ka mallaki abinda kake so ba. Tunda ba duka kake samun komi ba, kuma idan kace kai sai ka mallaki komi to kai zaka kwana ciki kuwa. Na jima sosai a dakin nashi kafin na tashi na koma dakin Maryam.
Ina zuwa na tadda Kulsum, nan muka hau hirar yaushe gamo. Tana nan har an sanya musu ranar aure da wani lakcaran su. Sai da za'a rufe gida sannan ta mana sallama ta tafi.
Bayan munyi shirin kwanciya, na dauki waya na kira Yaya Mudatthir na zayyane mishi duk abinda ya faru. Yace Baban ya mishi waya a jiyan, amma bai sanar dashi hukuncin daya yanke ba. Mun jima muna tattaunawa dashi, daga karshe muka yi sallama dashi akan cewa cikin satin zai zo. Bayan mun kashe wayar, Yaya na kira muka raba dare muna hira. Muna gamawa ko barcin minti talatin banyi ba, na tashi sallar tahajjud.

Da asuba muka tashi ni da Maryam muka dafa abincin sahur. Bayan munyi sahur, Mazan sun tafi masallaci, mu kuma muka yi tamu sallar a daki. Na dauki Al-Kur'ani mai girma na fara karantawa.

Gari ya fara yin haske lokacin da Ramata ta fado dakin kamar an jefota, ni da Maryam duk muka bita da kallo cike da mamaki. Ta tsaya a bakin kofa muna kallon-kallo da ita. Maryam ce ta tambayeta, "Mama lafiya?".

"Na'ilah kiyi hakuri!". Itace kalmar data fara fita daga bakinta. Tsabar mamakin jin kalmar yasa na saki baki hangangan ina kallonta kamar wata sabuwar halitta.

Bata damu da kallon da nake jifanta dashi ba, ta fara cewa "nasan cewa bani da hurumin baki hakuri akan duk wasu abubuwa dana miki, nasan na aikata abubuwa da dama na rashin kirki a gareku, amma wallahi na aikata hakan ne cikin tsananin jahilci wanda kishi ya haddasa min. Amma yanzu na gane, na kuma dawo cikin hayyacina, don Allah ku yafe min abubuwan dana aikata muku".

Har lokacin bakina a bude, bansan abinda yakamata in ce mata. Strangely, sai naji wata fahimta ta shige ni. Wani fannin na raina ya fahimci abinda tayi din. Ban sani ko hakan yana da nasaba da halin da nake ciki a yanzu bane. Zama tsananin mata irin Ameerah da Raheemah, zai sanyaka ka fahimci abubuwa da dama kamar halin da muke ciki yanzu da Ramata dai.

Akwai lokuta da dama, da tsabar kishi, son zuciya da zugar shaidan suka sha taso ni a gaba da wasu irin shawarwari da muggan sake-sake. Wadanda tsabar tsananin tsoron Allah da abinda zan tarar idan nayi abinda Ramatan tayi ne kawai yake dakatar dani, don haka ne na dage da rokon Allah akan ya yaye min irin wadannan abubuwa. Allah kuwa maji rokon bawanshi ne, a hankali naji duk wadannan sake-saken na daina yin su.

Nasan Ramata tabi zugar shaidan ne da son zuciya. Son zama da tauraruwar da haskenta bashi da wani tasiri balle hasken azo

Please Login or Register in order to submit comment