Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tun ma kafin in samu damar daga idanuna in kalleshi, in ga wani hali yake ciki, naji saukar lebenshi akan bakina.

Abin ya daukeni a ban shirya ba, na dan yi sak na yan sakanni kafin na biye mishi na kara kawata abin. Lokaci mai tsayi, kamar ba zai bari ba, kafin ya sakeni a hankali tare da sake dagowa ya kalleni. Hannuwanshi biyu yasa ya tallabo kumatuna, "baby...!", kadai ya iya furtawa cikin wata irin murya dana kasa tantance idan tashi ce, kafin ya sake lalubar bakina. Wannan karon hannunshi yasa cikin gashin kaina yana yamutsawa. Ban tantance ba naji an daga ni sama cimak, anyi kan gado dani.

Wani abu a tattare dashi yau ya banbanta da sauran lokutan da muka kasance tare, bai taba zurfafa wasanninmu irin na yau ba, ban taba jin intense abu irin na yau ba. Haka kawai naji zuciyata ta hau bugu, babu kakkautawa.
Daidai lokacin da naji an saki ruwan sama mai karfi, lokacin na jiyo ana jan wata certain addu'a, kafin in gama tantance ainihin abinda yake faruwa, wani irin zafi da ban taba jin kamar shi ba ya ratsa ni, na dan saki ihu, a lokaci daya yatsun hannuna suna lumewa cikin fatar bayanshi cikin azaba....



.......






(Ehhhemmm!!).




*☆⋆40⋆☆*




Karfe biyu ta gota lokacin dana farka daga barcin daya daukemu. Yaya yana gefena, kaina yana kan hannunshi daya, dayan kuma ya zagayo bayana dashi yadda na shige jikinshi sosai. Yanayin garin yayi sanyi mai dadi sosai, saboda ruwan da aka gama yi.
Nayi dabara na zame a hankali ba tare da nayi motsi mai karfi da zai tashe shi ba.
Zanin sallata dake ajiye a gefen gadon na dauka na daura, na shiga bandaki.
Duk da ciwon da nake ji a jikina, amma ba wani sosai dinnan bane da zai hana ni tafiya. Yaya Bilal was very gentle.
Na hada ruwan wanka, na shiga ciki nayi duk abinda ya kamata. Na dauro alwala na fito Zuwa yanzu kuma normal nake jina, duk gajiya, ciwon jiki da wani zafi ya tafi sai dan kadan wanda zan iya manejin shi.

Har yanzu yana kwance yana shakar barcinshi. Nayi zaton motsina zai tashe shi, amma har na gama dauke kayana da aka watsar dasu can gefen gado, na linke nashi, na dauko wasu kayan na sanya, bai ma san ina yi ba.
Na zauna a gefen gadon, na fara daddabar filon da yayi matashin kai dashi a hankali, ina kiran sunan shi.

A hankali ya fara motsi, ya bude kyawawan idanunshi suka dira a kaina. Murmushi ya saki mai taushi, "baby. meye haka nake gani?".

Nima na saki murmushin, "lokacin sallah ya wuce". Abinda nace mishi kenan, na mike tsaye.
Ya fara kokarin tashi zaune shi kuma, ina ganin haka na juya da sauri kamar zan kifa, na wuce inda na shimfida abin sallah na tada kabbara. Ina jin sautin dariyar daya saki a hankali yana wasu maganganu da kunnena bai jiyo ko menene ba, kafin ya shige bandaki na.

Kafin in gama sallah har ya fita zuwa masallaci.
Ina gamawa na yaye zanin gadon dake kai, na jefa shi cikin washing machine na shimfida wani, sannan na fita da hanzari domin in dora abincin rana. Duk da dai yanzu kowa yana dafa abincinshi na rana ne, na kanyi kokari a ranakun da muka samu hutu ko weekends in hada abincin gidan gabadaya.

Ina fitowa daga dakina, Raheemah ta fito daga nata dakin. Tayi tsaye hannu a kirji tana kallona ina kokarin rufe kofar dakina da mukulli, har na gama na wuce ta gefenta, sannu kawai nace mata wadda ban tsaya naji ta amsa bama na wuce.
Cikin sauri na hau yanke-yanken abubuwa, na fara sanwa.

Ina cikin yin girkin Yaya ya dawo, kai tsaye kicin din ya fado don ta karamar kofa ya shigo kamar yasan a kicin din zai sameni.
Ina tsaye ina kada miyar kubewa a cikin tukunya. Ya rungumoni ta baya, kanshi yana sauka a gefen wuyana. Na fara kokarin zamewa daga jikinshi, amma ko motsi bai yi ba.

Yace "bai kamata ace kina aiki ba yanzu, in fact kamata yayi ace yanzu kina kwance ne kina hutawa. Are you okay?".

Kunya ta rufo ni kamar kasa ta tsage in shige, nayi kasa da idanuna tare da daga kai.
Murmushi yayi, "ni fa kada ki fara min wani sadde-sadden kai, don ba zan laminci hakan ba. Zaki iya yin girkin? Idan ba zaki iya ba kinga ki barshi, bari in tura yanzu a siyo mana".

Nace "ni fa lafiyata lau, kuma zan iya yin girkin. Yanzu kawai kaje ka zauna, ko kaci gaba da wasu ayyukan naka, yanzu abincin zai sauka".
Maimakon ya sake ni, sai ma kara janyoni jikinshi da yayi, "na ki wayon".

Nace "Yaya...".
Kafin in karasa fadin abinda zan fada, muka ji anja wani irin tsaki, duk muka juya muka kalli Raheemah dake tsaye a bakin kofar kicin din.

Fuska a murtuke take kallon Yaya, "wallahi an dai fadi babu nauyi, girma kuma ya fadi. Ban da tsabar jaraba ma da masifa, da tsakiyar ranar Allah Ta'ala ma ba za'a daina jaraba ba? Mu dai bamu saba ganin wannan jarabar ba, idan ma ta wanke ta baka ka sha ne, to Allah ya tsare ka".

Ni baki a dage nake kallonta, me yasa matar nan ta saka min idanu ne a cikin rayuwata? Kada dai ace... ta san abinda ya faru yanzu? Na kalleta cikin zare idanu.
Yaya ma bai ce mata komi ba, sai ma kara nutsa kanshi da yayi a wuyana yana peppering wajen da kananun sumba, kamar bata wajen.

Ta sake doka wani tsakin, "wallahi an dai ji kunya, ya biyewa yarinya karama suna shirme a cikin gida!". Ta fita daga kicin din tana cigaba da mita da zazzaga masifa.
Na ture shi daga cikin jikina a hankali, wannan karon ya ja da baya ya tsaya yana kallona, cikin turo baki nace "don Allah ka tafi dakinka ka huta, yanzu zan kawo maka abincin".

Ya shafa sumar kanshi, "but ke ce yakamata ace kin huta baby ba ni ba!".
Abin nashi ya fara kokarin yin yawa, cikin sanyin murya nace "na fada maka lafiyata lau, don Allah ka tafi kawai".
Ya daga kafada, "shikenan, tunda kin dage. Amma ki tabbatar yau babu wani aiki da zaki kara yi, ina jiran ki a falona".
Sai daya manna min peck a goshi, sannan ya fita daga kicin din. Na sauke ajiyar zuciya a hankali, na juya naci gaba da ayyuka na.

A takaice sai bayan la'asar sannan muka ci abincin rana yau. A falon shi na shimfida mana ledar cin abinci, muka zauna. Yaya yafi son cin abinci a kasa, sannan cin abincinshi yafi son su ci tare da wani ko kuma matar shi, saboda haka yanzu abincin safe kadai muke ci a kan dinning. Na dare tun kafin ya dawo daga wajen aiki nake kaiwa falonshi in shirya mishi, muci kayanmu. Ita kuma sai in shirya mata nata akan dinning din.

Bayan mun gama cin abincin, hana ni motsawa ko nan da can yayi. Muna nan har aka kira sallar magriba, sannan ya tafi masallaci. Sai lokacin na dauke kayan abincin na kai kicin. Akwai yar aiki da take zuwa kullum ta mana sharar falo, wanke-wanke da kuma goge-goge, tana dai yin sharar ranar girkina, amma sauran ni nake yin komi da kaina. Musamman ma gyaran dakin Yaya Bilal da falonshi. Ranar girkin Raheemah ma Yaya da kanshi ya umarceni akan in dinga gyara mishi, tunda ita ta gwammace ta mike kafa dai-daya akan kujera tana murza channels, ko kuma ta shura takalmi ta bar gidan yawon gidan makota, akan ta zauna ta gyara dakin mijinta. Ni kuwa ban nuna kyashi ko jin haushina ba, na cigaba da gyara mishi daki.

Dakinshi na koma nayi sallah, ina karatun Al-Kur'ani har aka kira isha'i nayi.
Yau Yaya bai shigo da wuri ba, sai wajen karfe tara ya dawo. Muna babban falo daga ni har Raheemah muna kallo, ko in ce tana kallo, ni a zaune kawai nake.
Ya dawo da ledoji a hannunshi, na tashi na tarbo shi. Dama yace kada in damu da yin girki yau. Na bude ledar naga tsire ne da balangu, yoghurt da roll cakes.

Na ajiye su anan, na shiga kicin na dauko plates nazo na zuba mana. Da ya cewa Raheemah ta sauko, sai ta turo baki gaba, cikin alamun mita tace "uhmmmm! Da yake ita yar gaban goshi ce, dama mana. Yanzu ni har na isa in ce ba zan yi girki ba, ka siyo abinda zamu ci ba tare da ka bata min rai ba?".

Na girgiza kai a hankali cike da takaicin matar. Aikin kenan fa kullum, sam bata da godiyar Allah. Baka taba yin wani abin arziki ba tare data gwasale ka ba, musamman Yaya. Yana iyaka bakin kokarinshi wajen ganin yayi adalci a tsakaninmu, amma bata taba gani ba. Yadda duk karshen wata yake bani dubu ashirin saboda hidimar zuwa da dawowa, musamman cin abinci a asibiti duk da na ce mishi bana bukatar su, amma ya ki, haka yake daukar ashirin dinnan ya bata, maimakon godiya sai ce mishi tayi, "wai ita yanzu shikenan sai ta albarkaci na zata dinga cin kudin hannunshi?", abin ya bani haushi ya kuma bani mamaki kwarai.

Yaya ya daga baki zai amsa ta, nayi saurin tarar numfashinshi, nace "anan zaka ci ne ko kuma zaka koma karamin falo?".
Yaya ya kalleni sosai, nima na kara kallonshi, da alama ya fahimci dalilina na tarar numfashinshi, yace "mu koma falona".
Nayi murmushi tare da kanne mishi ido daya, wanda yasa ya saki murmushin shima tare da mikewa tsaye. Na dauki plate din dana zuba mana namu a ciki,na wuce na kai falonshi, na dawo da niyar daukar yoghurt da cake din.

Tana tsaye a gaban Yayan kamar wadda take tsare shi daga shiga falon nashi, ihu take tun karfinta, wai ya maidata mahaukaciya, tana magana ya dinga shareta.
Yace "wai ke me yasa ba kya son zaman lafiya ne ko kadan Raheemah? Me ma aka yi daya janyo fada da daga murya anan?".
Tace "dama yaushe zaka gani tunda an rufe maka ido? Ni da ake wa rashin adalci ni nake gani, kuma wallahi ba zan yarda ba!".
Yace "sai ki dauki mataki...", ya zagayeta ya wuce. Nima na kwashe sauran kayan na bi bayanshi.

Falon shi kamar nan ne wajen shakatawarmu da hutawa, Raheemah bata cika shiga ba musamman ma ranar da ba girkinta bane, ni kuma ina kokarin kaucewa wajen ranar girkinta saboda shiga hakkinta. Ranar girkina kam acan nake yini musamman idan Yaya yana gida, mu yi ta hirarmu, ko wasanninmu, watarana kuma sai dai mu kwanta kawai, watarana kuma idan yana aiki in barshi yayi aikinshi ni kuma inyi busying kaina da wasu abubuwan.

Yanzu tashar CNN ya kunna yana kallo, ina gefenshi muna cin naman a hankali, lokaci zuwa lokaci zamu dan tattauna akan wani case da zamu ji an fada a tashar ko kuma wani abu. Har muka gama ci, na dauke kayan. Na dawo falon, nayi matashin kai da cinyarshi har dare yayi, ya kashe kayan kallon muka wuce dakinshi.


~~~


Da kyar ya bari muka yi sallama dashi wahsegari na tafi Kaduna. Da kasa ya kekashe akan cewa sai dai in bari mu tafi dashi ranar juma'ah, kamar zan mishi kuka haka na dinga rokonshi ina magiya, nace "idan ma na zauna me zan maka ne Yaya? Ba fa ni zanyi girki ba yau".
Da kyar dai, muka yi sallama ya tafi wajen aiki. Wajen karfe goma sha daya, muka bar garin Abuja.

Tuni gidan biki ya fara cika da yan biki. Gida ya cika ya tumbatsa Masha Allah. Bayan mun gaggaisa da mutane, wasu yan uwan nasu ba da basa cikin kasar ko kusa da gari, sai yanzu muka samu muka gaisa dasu.
Muka lume can kuryar dakin Yaya ni da amarya Janan muna hirar yaushe gamo. Tayi ta min shakiyanci, wai nayi fresh, meye sirrin, ko har an bani ajiya ne?.

Na kuwa danna mata harara, "wai don Allah meye matsalar ki ne? Kullum kiyi ta lakaba min abinda bani da?".

Ta kuwa kwashe da dariya, "to Malama, alamu ne suka nuna haka ba wani abu ba. Ki duba fa yadda kika wani ciko tubarkallah, kin kuma yi haske da abubuwa, idan ba ciki bane to menene?".

Na kada mata idanu, "kiwon Yayanki ne kawai!".
Ta saki ihun dariya, abinda ya janyo su Harira dake falo kenan suma suka fado, suka cigaba da shakiyancinsu. Dana gaji sai na janyo wayata, na dannawa Yaya kira na koma can gefe muka kwashi hirarmu ta masoya.

Washegari aka yi kamu anan cikin gidan. An dauko masu decoration da masu raba abinci, abokanmu da yawa sun zo, haka dangin ta dana Almu sunyi kara ba kadan ba. Gida ya dauki jama'a sosai. Har karfe goma na dare ranar muna kan kafafunmu a tsaye muna kokarin gyara gidan.

A dakin su muka yi parking, baki duk an kaisu dakunan dake cikin gidan, wasu kuma suna dakin Yaya da Ummah.
Ummah ta kawo mana damammiyar fura da kanta, da tasha nono ga sanyi sosai. Tun bayan aurenmu da Yaya, kamar an kara mata kaunata haka nake gani, tunda nazo take ta nan-nan dani, abincin da zan ci ma daga dakinta ake kawo min. Sai naji nima kimarta da mutuncinta sun karu a cikin idanuna.

Bayan munyi wanka don mu dan warware gajiya, muka sha furar data kawo mana, sannan fa kowa ya nemi makwanci. Lokacin karfe sha daya ta wuce. Naso in kira Yaya kafin in kwanta, tun da safe da muka yi waya dashi bamu kara yi ba, amma sanin suna tare da Raheemah yanzu yasa na daure zuciyata. Sai na rubuta sako mai cike da kalamun nuna kewa da kauna, na tura mishi. Cikin sakanni talatin da shigar sakon wayarshi, ya dawo min da amsa.

Nan muka kwashe kusan mintuna arba'in muna musayar kalaman soyayya, kafin muka yi sallama dashi.

Washegari aka yi mothers eve, sai ranar Anty Ameerah tazo. Anty Sarah ita tun jiya tazo, sai dai bata kwana a gidan ba, gidan Yayarta dake aure anan cikin Kaduna taje ta kwana.
Ana gama taro Anty Ameerah ta koma Zaria.

Sai ranar juma'ah Yaya yazo shi da Raheemah. Tunda suka zo bata ma zauna a gidan ba, ranar walima muka yi. Yau ma kamar jiya, ana tashi wajen karfe shida Anty Ameerah ta wuce, ita kuwa Raheemah da tunda suka zo kayanta ma a dakin Yaya ta ajiyesu, ta wuce can. Bata shiga cikinmu ba mu kawayen amarya, muma kuma bamu nemeta ba.

Washegari aka daura aure, muka kai amarya gidan aurenta dake can unguwar rimi. Gini ne na kin karawa, idan ka shiga kamar kada ka fita saboda haduwarshi.
Yanmatan sun ce babu inda zasu tafi sai anguna sun zo sun sayi baki, duk da da yamma ne aka kaita. Na gama shan dariyata nace bari inyi tagging dai nima.

Wajen karfe shida na yamma sai ga kiran wayar Yaya, na fito daga cikin hayaniyar hirar da suke yi, na amsa kiran.
"ki sameni a kofar gida", kawai yace ya kashe wayar.

Na bi wayar da kallo cikin mamaki, kafin na sake kiranshi, nace "muna fa gidan Janan yanzu haka".
Yace "ehh, nan din fa".

Cikin sanyin jiki na koma gidan. Su Anty Sarah da basu jima da zuwa ba, su ganin gida suka zo yi kafin su koma Zaria, ciki har da Anty Ameerah, suna cikin bedroom inda amarya take suna tasu kalar hirar suma.
Na matsa na radawa Janan zan tafi, tace "ina zan tafi yanzu bayan ba'a zo sayen bakin ba?" Nace mata "Yaya yake nema na, yace yana waje".

Ta zaro ido, nayi gaggawar kai mata dukan wasa a hannu kafin tayi tunanin fadin wani abu silly, nace "kada ki wani kawo min wata maganar banza anan, sallama ce kawai zamu yi saboda yau zasu koma Abuja shi da Raheemah".

Amma bata fasa ba, sai data yi commenting din dai. Na dauki jakata kawai na musu sallama akan cewa zan koma can gida, na fita.

Kamar yadda yace kuwa, yana kofar gidan. Na bude murfin motar na shiga, yayi murmushi tare da janyo ni jikinshi, mun dan jima a haka kafin ya dago ni yana kallona, yace "kai baby na, da alama ke ko kewata ma baki yi ba, ji yadda kika yi wani irin kyau kamar ba ke ba?".

Nace "a haka din?".
Yace "sosai ma!". Ya fara kokarin tada motar.
Ban tambayeshi inda zamu je ba, ya fita daga unguwar. Sai gamu a kofar wani gida a can cikin GRA. Na kalleshi cikin mamaki lokacin da naga yayi horn mai gadi ya bude mishi kofar ya shiga.

Muka fito daga cikin motar, kai tsaye ya shige falo dani. Gidan a gyare da komi a ciki, sai dai babu alamun mutane a ciki.
Nace "nan fa?".

Yana ajiye wayoyinshi akan center table yace "gidan da muke kawo baki ne idan aka yi, musamman ma lokutan biki irin haka".

Bandaki ya nuna min yace in shiga inyi alwala, shi kuma ya tafi masallaci. Sai bayan isha'i ya dawo da ledar shake da kayan marmari da take away na abinci a hannunshi.
Ganin take-takenshi, nace "wai ba yau zaku koma ba? Kuma kada ka manta fa tare da matarka kuka zo".

Yace "to sai me? Ina lissafe da yau zaki fita daga girki fa!".
Na zaro ido ina kokarin ja da baya daga rarumar daya kawo min, amma duk da haka sai daya cafko ni yana dariya, yace "come on, anjima kadan fa zan maida ki".
Nace "da gaske?".
Yana murmushi cheekily, yace "da gaske".


A takaice ban kara tunawa da wannan maganar ba sai da naga mun yi ido hudu kuru-kuru da hasken rana, washegari kenan.

Karfe tara Yaya ya shigar da motarshi gidan su Ummah, kunya kamar zan nutse a kasa, duk da dai babu wanda yasan abinda kenan.

Yana kashe motar, na fita da sauri na fada gidan. Allah ya taimakeni babu kowa a falon, da alamu baki sun wuce, na fada dakin su Harira daban. Nan ma FirdauFirdausi kadai na tarar tana gyara gado, ta kalleni cike da mamaki, "daga ina haka?", nayi banza na kyaleta.

Karfe biyu na rana, muka wuce Katsina ni da Is'hak da Yaya ya umarce shi daya kaini. Munyi sallama dasu suna ta min sannu da Ala huta gajiya. Shi Yaya sai da yamma naji yace zasu koma.

Yaran gida sun sha ihu da murnar ganina, aka min masauki a dakin Anty Alawiyya. Da yake ranar Lahdi ce, Baba yana gida.
Aka kaiwa Is'hak abinci yaci, a ranar ya koma Zaria, ranar talata zai dawo ya maida ni.
Ranar haka muka raba dare ni da kannena muna ta shan hira. Sai washegari na shiga gari gaishe-gaishe.

Kulsum ta fara zuwa makaranta abinta, wai wani lecturer ya kyalla idanu a kanta yana ta bibiyarta. Nace mata "kema ki saurare shi mana, sai kiga kun daidaita".
Ta girgiza kai, "ba yanzu ba Na'ilah, ba zan kara yin sake irin wanda nayi ba gaskiya. Ke dai kawia ki taya ni da addu'a".
Nace "to shikenan".

Wannan zuwan nawa naji dadinshi sosai, sai da naji kamar kada lokacin komawata yayi.
Ramata kanta wannan lokacin naga ta sassauto sosai, ko kuma zata iya yiwuwa rashin lafiyar da take yi ce ta sanya hakan.

Ranar talata sai da yamma sannan muka yi sallama dasu cike da kewa, muka wuce. Dole sai a Zaria muka tsaya muka kwana, washegari Laraba muka wuce Abuja. Amma sai da na tsaya a Kaduna sannan.

Na koma gida muka cigaba da gudanar da rayuwarmu. Babu abinda ya canza har yanzu, sai ma wata tsirfa. A gidan na tarar dasu Salame ranar dana koma, wai suna ta shirye-shiryen bikin Haleemo. Sai ranar assabar suka bar gidan, habaici dai har sai dana gaji da ji, amma babu wanda na taba tankawa a cikinsu.


*


Ranar Lahdi da yamma, muna babban falo a zaune, Raheemah ce take yin girki, Yaya ya fita zuwa cikin gari da wannan yammar. Don haka daga ni sai ita, duk da ita tana ta zarya ne ma tsakanin kicin da falon saboda girki da take yi.

Kawai sai karar turo kofa muka ji, mu daga kai haka, sai ganin Anty Ameerah muka yi ta fado falon, wasu matasan yanmata biyu na take mata baya, yayin da maigadi da mai ban ruwan fulawowi suke turo akwatunanta.

Raheemah data mike tsaye zata shiga kicin, tayi tsaye kyam tana kallonsu, nima na bi su da kallon.
Yaya har ya fita bai yi magana akan dawowarta ba, ko kuwa bai san da zuwan nasu bane? Oho!.
Ita kuma ko da wacce tazo?.

Suka mana sannu da gida, Raheemah ta zungura baki gaba ta shige kicin, na amsa musu a sanyaye. Muka gaisa kadaran-kadahan dasu, suka ce sunyi waya da Yaya yace su tambayeni makullin dakinta, na tashi na shiga dakinshi na dauko musu, na nuna musu dakin, suka yi godiya suka tura kai suka shiga ciki, ni kuma na koma falo cikin wani irin yanayi.

Sai da dare Yaya ya dawo. Da yake ranar Raheemah zata fita daga girki, aka yanke shawarar Ameerah zata amsa. Da haka muka aka tashi kowa ta wuce dakinta.

Har ta fita daga girkin, wani ya sake zagayowa, babu wata matsala. Zama muke kadaran-kadahan da ita, idan muka hadu a falo, ko a dakin Yaya, za'a gaisa da ita a mutunce, haka babu ruwanta da shiga harkar da babu ruwanta. Ban taba jin bakinta yayi wata mita ba, ko ya tado magana. Kai ita kwata-kwata ma baka ganinta sai ranar girkinta, sauran ranakun a daki take yini cur, idan ta fito sai dai kicin, ta kwashi kayan makulashe ta koma daki.

Sai nake ganin kamar hakan yafi akan ka wuni kana zage-zage da yada habaici. Har nake cewa kila zata fi Raheemah saukin kai.

Little did I know....




*☆⋆41⋆☆*




Ranar Juma'ah na karbi girki a hannun Ameerah. Kamar yadda na saba, idan ina aikin rana na kan yi iyaka bakin kokarina in ga na dawo da wuri domin in dora abincin dare.
Yau ma aikin dare nayi, na samu wata nurse da muka fara gaisuwar mutunci da ita, Hanifa, na roketa akan ta shigo da wuri ta rike min nawa aikin tunda ita aikin dare take yi, ta amince. Bazawara ce in her 30th. Kirkinta yasa muka fara gaisawa sama-sama da ita, har dai aka fara gaisawa ta sosai. Yanzu yawanci ita take taya ni rike aikina idan zan fita da wuri. A gurguje na mata godiya na wuce. Na riga na kira direban da yake kaini, yana waje yana jirana. Don haka ina fita muka wuce.

Sai karfe bakwai da wasu mintuna muka karasa gida.
Cikin sauri na shige daki, ina shiga na hau cire kayan jikina ina jifa dasu a tsakiyar dakin ba tare dana damu akan in linke su ba. Da yake bana yin sallah, a sukwane na fita daga dakin na fada kicin. Babu kowa a cikin falon.
Allah yasa da zan fita da rana nayi miya na ajiye. Ruwan zafi na dora akan wuta, na nufi dakin Yaya da sauri.

Wani lokacin idan ya fita sallar asuba ya kan dawo kafin ayi isha'i ya ci abinci, idan yana jin yunwa kenan. Idan kuma ya ci abinda ya rike mishi ciki a wajen aikinshi ya kan jira sai bayan isha'i.

Yanzu so nake in ga idan yana falonshi, in ga ko yana bukatar ko da snacks ne yaci kafin in sauke abincin kamar yadda nake mishi sau tari, a ranaku irin wadannan idan ban gama abinci da wuri ba.

Tun kafin in karasa falonshi nake jin sautin karar talabijin, sai kuma sautin magana kamar ana yin hira da yake tashi kadan-kadan.
Nayi sallama a kofar falon tare da turawa, kamar yadda nayi zato, Yaya yana falon a zaune akan

Please Login or Register in order to submit comment