Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

cewa zanyi ba ita bace. Sai dai wannan babu tantama motar Umar ce, amma me zai kawo shi nan yanzu? Janan tana tambayata lafiya? Amma hankalina baya wajenta, wayata nake kokarin cirowa. A tunanina kila ya kira ni ban ji kiran ba, yanzu haka ma kila ni yake jira ko wani abu. Amma babu kiran Umar a wayata babu alamunshi.

Na kalli Janan ina nuna mata motar, da yake akwai hasken da kwayayen dake kofar gidajen unguwar suke badawa, take ta gane motar, tace "kai! Kamar motar Umar dinki fa!".
Babu ko tantama nace "motar shi ce, amma me yake yi anan? Ko kirana fa bai yi ba!".
Tace "ko dai bashi bane?". Da sauri na hau girgiza mata kai, gabadaya na rasa akan abinda ya kamata inyi tunani a lokacin. Haka kawai naji jikina ya dauki wata irin rawa, ba kuma zazzabin da nake ji bane ya haddasa ta ba.

Ba tare da tunanin komi ba, naji na fara daga kafa ta zuwa wajen motar. Duk taku daya, rawar jikina karuwa take yi, haka bugun zuciyata yake ninkuwa.

Ban san tunanin me nake yi ba dana tunkari motar gadan gadan ba, amma ban shiryawa ganin abinda idanu na suka gane min ba. Ban shirya ba!.

Umar ne kamar yadda nayi zato, zaune a gaban motar, sai dai ba shi kadai bane kamar yadda nayi zato. Tare suke da ba wata ba illa Haleemo. A zaunen ma zama na rashin da'a, saboda kusancinsu kamar a kan cinyarshi take zaune saboda irin zaman da suka yi. Ba wannan kadai ba, daidai lokacin da wata mota ta danno cikin layin a sukwane, haskenta ya dallare gaban motar, daidai lokacin da bakinsu ya hade da kiss. Hannuwanshi na yawo a wuyanta da bayanta.

Naji kamar an katse duk wata magudanar jini a jikina, ban san lokacin da kayan hannuna suka zube ba. Innalillahi, me idanuna suke gani ne haka??! Da sauri na kauda kaina don bazan iya kallon irin wannan badala dake afkuwa a gabana ba.

Tunanin farko daya dirar min, shine in kwashe kayana da suka zube a kasa in wuce gida, tunda dai sam basu san da kalar wainar da muke soyawa ba, sai kuma naga inaa! Don haka kafin ma in sake tunanin yin wani abu, naji kafafuna sun daukeni zuwa wajen motar. Na tsaya a daidai wajen da direba yake zama na bubbuga.

Sai da aka dauki lokaci kafin aka yi kasa da tinted glass din da aka saka aka rufe motar, Umar ya zuro kanshi waje. Yadda idanunshi suka waro cikin gigita yasa naji wata irin tsanar shi ta cika min rai, me yasa zai yi min haka??

Da sauri ya fito daga cikin motar yana wani kame-kame, "hh-hheyyy... Sweetie. M-me kike yi... anan?!", ya tambaya cikin rawar murya.

Na daure, na cije, na tattaro duk wani kwarin gwiwa daya rage min, nace "oh, wai zamu wuce ne sai naga kamar motarka, nace bari in tabbatar. Ashe kai dinne. Mai kake yi anan? Nayi tunanin kana Kaduna??".

Ya fara shafa bayan wuyanshi yana wuri-wuri da ido, "wannan? Ai dazu na dawo, tunda na tafi ban dawo ba sai yau! Ai ayyuka ne suka yi yawa! Kusan satina daya ban daga wayata ba saboda aiki!! Yanzu.... Yanzu ma wani abokina ne anan unguwar nazo gani, ai ban ma gane layin gidan su kawarki bane saboda duhu. Me ma kike yi anan unguwar? Nayi zaton kina Shika??!".

Ji nayi na gama sauraren kame-kamen da yake yi, rainin wayon yayi yawa. Banyi wata-wata ba na daga hannu na watsa mishi tafi...










#F.W.A
















*☆⋆15⋆☆*





Ba shi kadai ba, ni kaina nayi mamakin marin dana mishi, amma banyi nadamar hakan ba.
Ya dafe kuncinshi yana kallona cikin zare ido, "sweetie....!".

Cikin tsananin tsiwa da balbalin masifa nace "idan ka sake kirana da wannan sunan, Allah ya isa ban yafe maka ba Umar!!".
Yayi sararo a tsaye da baki a bude, ya rasa abin cewa. Nace "dama abinda kake yi kenan? Nayi tunanin cewa abubuwan da kake nuna min kawai kana yi ne saboda desperation, ashe halinka ne?". Munafikin sai yayi shiru kai a kasa yana muzurai. Daidai lokacin Haleemo ta fito daga cikin motar, kai a kasa babu kunya babu tsoron Allah tana nukutu.

Na kalleta, wani tsabar takaici yana cina, ji nike kamar in kamata in hadata da bango ko motar, amma na cije don nasan shaidan ne yake so ya zuga ni. Na nunata da yatsa, "akan wannan abin ne ka yaudare ni? Akan wannan abin ka share ni tsawon watanni, ina bibiyarka kana yazga ni kamar wata mara aikin yi? Ba ni kuka cuta ba wallahi, kan ku kuka zalunta. Kuma ni babu abinda zan ce muku, babu kuma mummunar addu'ar da zanyi muku. Sai dai ku sani, za ku gani da idanunku, Allah ya kara muku dankon kauna!". Daga haka na juya da sauri na wuce, babu wanda ya iya cewa uffan a cikinsu. Janan data tsaya ta tsince kayan da suka zube, ta biyo bayana da sauri, jerawa muka yi muna tafiya ba tare da dayanmu ya cewa daya ci kanki ba.

Muna shiga daki naji jikina ya dauki wata irin rawa, ba shiri na lalubi kujera na zauna. Na kai hannuwana duka biyu na dafe kaina ina girgizawa, dama abinda yake faruwa kenan, ni ina gefe guda na hangame baki ban san abinda ke wakana ba? Lallai, idan kana raye zaka sha kallo. Kallo ba na wasa ba kuwa.

Janan ta zauna a kasa tana fuskantata, babu wanda ya iya magana a cikinmu, har muka dauki lokaci mai tsayi a hakan. Can na daga baki, a hankali nace "me yasa? Saboda bana son shi ne ko me?".
Janan ta dafa kafafuna da nake ta jijjigawa, cikin tausasshiyar murya tace "ko kadan, kawai son zuciya ne da rashin godiyar Allah. Kiyi hakuri, ban san hakan zata faru ba".

Na kura mata rikitattun idanuna da nasan sun rine da jan bacin rai, nace "me kike nufi?".
Tace "kamar sati biyu da suka wuce, na taba ganin hoton Umar din a wayar Haleemo, sai nake tambayarta a ina ta san shi, sai tace min abokin saurayinta ne. Ni kuma sai na share maganar. Ranar nan da nace miki kamar Umar, ni na tabbata na gan su su biyun, nasan banyi kuskure ba. Dana nuna miki kika musa sai naga babu amfanin fitowa gar da gar in fada miki, tunda ban tabbatar da alakar dake tsakaninsu ba... Don Allah kiyi hakuri!".

Na girgiza mata kai, "ki daina bada hakuri akan laifin da ba ke kika aikata shi ba Jan. Haushina daya, daya bari son zuciya ya rinjaye shi har ya iya juya min baya, amma kanshi ya yiwa ba wani ba. Na kuma gode Allah da yasa na ga hakan da idanuna, basu dinke ni a baibai ba. Da muka zo muka yi aure a haka, inyi yaya?".

Janan snorted, na bita da kallo cikin mamaki, tace "wai ke don Allah kina tunanin Umar yana da sha'awar kuyi aure?".
Na bita da kallo mai dauke da alamar tambaya, amma dai duk da haka na amsa mata, nace "ehh mana, me kike tunani ne, daukar lokacin da muka yi a tare a banza zata tashi ba tare da munyi aure ba?".
Tace "abinda nafi zargi kenan!", zanyi magana tayi gaggawar katseni, "ki duba fa, ba fa yau kuke tare dashi ba, amma bai taba tado miki maganar aure ba. Idan ma kin tado sai ya hau miki kame-kame, baki taba zargin ko baya son auren bane?".

Nayi shiru cikin tunani, ban taba yin wannan tunanin ba. Nafi kyautata zaton ko rashin maganar aure da baya min, baya so ne in hada karatuna da aure, yafi so sai na gama sannan ya fara maganar, don haka ban taba kawo zargin wani abu ba. Don haka na girgiza kaina kawai.

Tace "ko ma menene, ki godewa Allah daya nuna miki hakan tun kafin zance yayi nisa. Samari irin su Umar su kan yi iyaka bakin kokarinsu wajen ganin sun cimma burinsu akan macen data burge su. Ina tunanin dalilin daya tsayar dashi kenan, ko kuma sun yi tsubbace-tsubbacen da suka saba sun shawo kanshi".

Na girgiza kai, "babu boka babu malam a cikin wannan lamari, ina tabbatar miki Umar a cikin hankalinshi yake".
A nutse na warware mata dalilin daya haddasa fadan da muka yi dashi last time, har ma wasu fadan da muka yi akan matsala irin wannan, wanda bata taba jin hakan ba sai yanzu.

Ta kama baki cike da tu'ajjibi, tace "kin gani ko? wato da yaga cewa ta bangarenki babu sa'a, shine ita kuma data kai kanta yace bari ya biye mata. Kila a dabararshi idan ya gama da ita sai ya dawo kanki? Ko kuma wani shiri gare shi na daban?".

Nayi shiru kawai ina kara juya lamarin a cikin raina. Har yanzu kaina bai gama yayewa ba, mamakin abin bai sakeni ba. Dama ana haka a duniyarmu? Kina sane, kana sane, ku take sanin, ku yaudari kanku ku yaudari wasu? Ina jin labarin snatching da dama, mafi yawa a labarai ko a gidajen radio ko a fina-finai, ban taba zaton yana faruwa da gaske ba, sai gashi yau ya faru a gaban idona, a kaina kuma.

Duk yadda naso in jurewa abin, kasawa nayi. Ji na nayi kawai hawaye na bin fuskata. Janan take ta bubbuga bayana tana bani kalamai masu kwantar da hankali, har naji zuciyata ta dan yi sanyi, amma nasan cewa na dan lokaci ne.

A hankali na mike, jiri yana kwasata, na shiga bayi. Tsaye nayi a gaban babbar mirror dake manne a bangon bandakin ina karewa kaina kallo. Idanuwa sunyi luhu-luhu, sun kuma yi jawur, daga ganina babu tambaya kasan kuka na gama shaka. Ko yanzun ma wasu hawayen ne suka ciko min idanu. Me na yiwa Umar a duniya dana cancanki wannan yaudarar daga gareshi? Ko kuwa Haleemo zan ce? Shin wai, ta yaya ma har suka hadu suka kulla wannan cin amana? Tun yaushe kuma??

Wato dai kaji tsoron dan Adam. Kuma kaji tsoron mutane masu halin shiru-shiru, sai yanzu nake gane gaskiyar Jan da tace halinta yafi na sauran muni. Lallai na ga misali akan kaina.
Na ciza lebena na kasa ina danne kwallar data ciko min ido. Ba zan kara zubda hawaye akan su ba, they are not worth it!. Na wanke fuskata kawai na daura alwala na fita. Katifa kawai na hau na kwanta, na ji wayata tana kara da vibrating, ina dagawa naga Umar ne yake kiran. Na jinjina kai kawai cikin rashin abin cewa, lallai rashin ta ido irin ta dan mutum tayi yawa. Wayar na dauka kawai na kashe nayi jifa da ita can bayan katifar, na sake komawa na kwanta.
Janan duk yadda taso ta ja ni da hira, kasawa nayi. Haka nan ta hakura tayi shiru. Har barci ya dauketa idanuna biyu, ina ta saka da warwara har barcin ya daukeni nima.


Washegari haka na tashi da matsanancin zazzabi da ciwon kai a jikina. Da kyar na iya yin sallar asuba, na koma na kara kwanciya na kawo bargo mai nauyi na rufawa jikina, amma hakan bai hana ni rawar sanyi ba. Har wajen karfe takwas na safe ina cikin wannan hali.
Janan tana zaune a gefena tana kallona cike da alamun damuwa rubuce a fuskarta, tun da asubahin take bin kaina akan in shirya mu tafi asibiti, amma na ki tashi. Yanzun ma abinda take ta fama dani kenan, "don Allah ki tashi Na'ilah, jikin ki kara rikicewa yake yi". Ta fada cikin alamun lallashi da kuma roko, kai kawai na girgiza mata alamun a'ah, na kara jan bargo na rufa.

Ta kura min idanu, akwai alamun takaici da kurar da ita da nake yi rubuce baro-baro akan fuskarta. Tace "shikenan, kiyi duk abinda kika ga dama, an fada miki na damu ne?".

Ta ga dai bani da alamun motsawa, sai ta kara matsowa kusa dani, cikin sanyin murya, cike kuma da nuna tausayi tace "haba Na'ilah! Ke da nake ganinki da hankalinki da komi, amma ki kasa yarda da abinda Allah ya tsaro miki? Akan namiji! Haba Na'ilah!! Akan namiji zaki zauna ki kashe kanki? In fada miki gaskiya? A banza zaki kashe kanki idan ma haka ne, mantawa zai yi dake, dama can bai daukeki a bakin komi ba. Yanzu haka ma kila ya riga da ya manta dake, kila yanzu haka suna can suna kwasar soyayyarsu babu abinda ya dame su yayin da ke kina nan kin saka bakin cikinsu a cikin ranki, kina nema ki kashe kanki a banza!".

Na samu na girgiza kaina da kyar, murya na fita da kyar, ina ganinta dishi-dishi, nace "ba akan Umar bane!".
Ta fusata, "to akan waye idan ba shi ba? Ke karamar yarinya ce da za a dinga bin kanki akan rashin lafiyarki wai? Idan kina so in yarda ki taso mu tafi asibiti yanzun nan!".
Nace "mura ce kawai ba wani abu ba, zuwa anjima zai sauka, ki daina damuwa".
Ta hau girgiza kai, "wannan kafar kai taki ban san irinta ba wallahi, Allah ya kyauta miki!".
Na lumshe idanuna kawai saboda yadda nake jin sunyi min nauyi. Janan kuma ta saka ni a gaba tana kallo. Wani wahalallen barci ya daukeni kenan, naji alamun taba kofa alamun an fita. Ba'a jima ba aka sake bude kofar aka dawo.

Jin tashin murya ba daya a dakin ba yasa na bude idanuna da kyar.
Yaya Bilal ya kalleni fuska babu yabo ba fallasa, sai dai can cikin kwayar idanunshi, akwai wata kwantacciyar damuwa dana tabbatar ba rashin lafiya ta bace ta haifar da ita ba. Wannan, ko kuma dai idanuna ne suke min gizo kawai.

Ya dauke kallonshi daga kaina ya maida kan Janan dake tsaye a gefenshi, "me ya sameta?".
Tace "zazzabi ne da ciwon kai, tun jiya da dare, amma bata son mu je asibiti. Kuma zazzabin karuwa ma yake yi maimakon ya ragu".
Ya sake maida kallonshi kaina, duk da halin da nake ciki kasa daukar kallon shi nayi. Wasu irin sakonni ne suke fita daga cikin idanun nashi, bana tunanin shi kanshi ya san suna fita. Ga... Dan saurara! Wasu irin sakonni nake nufi? Anya kaina bai fara motsi ba kuwa? Ni wacece din shi da zan ce yana turo min sakonni ta idanunshi? Wow! Dama naji ance zafin zazzabi yana sa mutum ya dinga sambatu kila ma har da ganin hallucinations. Babu mamaki abinda nake gani kenan nima yanzu.

Maganar da Yaya yake yi ce ta dawo dani daga rants din da nake zabgawa a cikin kaina, yace "bari in kira Dr. Zubair in gani, Allah yasa yana kusa". Ya juya ya fita daga dakin wayarshi a hannu yana dannawa. Janan kuma ta dawo gefena ta zauna, hannu ta kai tana daga goshina zuwa wuyana, ni kaina nasan ba karamin zafi jikina ya dauka ba, har wani tiririn zafi nake ji a jikina.

Ba ayi cikakkun mintuna goma da fitar Yaya ba sai gashi ya dawo. Yace "bismillah dakta, shigo".

Janan ta tashi da sauri ta dauki gyale ta dora akan kayan barcinta. Ni kuwa dama kayan barcin dana saka doguwar rigar cotton ce mai dan gajeren hannu wanda ya tsaya min a damtsen hannu.

Yaya ya fara shigowa dakin, wanda nake zaton shine likitan daya kira ya biyo bayanshi. Ya ajiye dan karamin akwatin daya shigo dashi, ya bude ya fara ciro abubuwan gwaji da sauransu. Yana fiddo komi ya fara aikinshi.
Cikin awa daya sai gani manne da drip a hannu, da tulin magungunan malaria, har ma da typhoid.










#F.W.A







*☆⋆16⋆☆*





Ana sa min ruwan barci mai nauyi ya daukeni. Lokacin dana motsa har an cire ruwan, da alamun rana tayi sosai ko kuma ma lokacin azzuhur yayi saboda Janan dana hango akan abin sallah.
Jikina yayi karfi sosai fiye da lokacin dana tashi dazu da safe, na lallaba na tashi zaune. Cikin ikon Allah babu jirin da nake ji da kuma ciwon kan. Janan da taji motsina ta juyo, murmushi ta saki a hankali, "har kin tashi?". Na gyada mata kai.

Ta tashi ta matso inda nake, "sannu, zaki iya tashi tsaye ko sai na kama ki?".
Nace "zan iya, jikina yayi karfi yanzu".
Tayi dan murmushi, "well, ai dole. Ruwa da kika sha!". Na murmusa kawai ina girgiza kai. A hankali na mike tsaye, karfin jikin nawa ba sosai bane, haka nan na lallaba na shiga bandaki. Sai da nayi wankan ne ma naji jikina ya danyi karfi ma, nayi brush tare da dauro alwala na fito. Janan bata dakin, na zauna na shafa mai tare da bude wardrobe dinta na ciro wata buba ta wani jan yadi mai taushi na saka. Da yake haka na taho shekaranjiya zikal dina, kayanta nake amfani dasu. Don ma yanayin jikinta da nawa kusan daya ne, abinda zan nuna mata kawai cikar kirji, amma bayan haka babu wani bambanci mai yawa a tsakaninmu.

Na shimfida abin sallah na tayar da sallah, bayan nayi na jero nafilfili, na zauna ina jan casbaha. Janan ta shigo dakin, na bita da kallo tana ajiye wani babban flask, fita ta sake yi ta dawo da gorar ruwa da faranti da cokali. Sai data ajiye sannan ta kalleni, "taso ki ci abinci, ki sha magani".

Sai da tayi maganar abinci sannan naji cikina yana juyawa, ba musu na tashi na cire hijabin jikina na ninke ta da abin sallar. Tun kafin in zauna kamshin kifi ya cika min hanci, naji yawun bakina ya guda. A kasa na zauna muna fuskantar juna, ta turo min plate cike da faten doya. Anyi garnishing dinshi da green beans, peas, alayyahu, hanta da aka yanka kanana, ga kifi da dafaffen kwai a gefe. Ina yin loma daya na lumshe idanuna, kai na hau girgizawa, "ramgwadi! Gaskiya yau ba karamin baje basira kika yi wajen girkin nan ba, meye sirrin?".

Ta kalleni, "ke yanzu nace miki ni na dafa wannan abincin yarda zaki yi? Yanzu na amsa shi wajen Anty Sarah".
Na bude baki cikin mamaki, watakila lokacin da yan kirki suke kan Anty Sarah bamu taba sa'ar cin karo dasu ba sai a wannan lokacin. Iyaka sanina da ita, wannan baya daga cikin halayen dana santa dashi. Amma zata iya yiwuwa dama can hakan take, kila sanin hakan ne bamu taba yi ba.
Nace "ta kyauta sosai, nagode".
Ta kai cokali daya bakinta, "ta shigo ne taga yanayin jikina fa sai ta ganki da drip a hannu. Dazu kuma sai ta turo Mimah tace in je in amsar mana abinci". Na gyada mata kai. Har muka gama cin abincin babu wanda ya sake yin magana. Bayan mun gama, Janan ta kauda kayan can gefe, ta dauko magungunan ta fara balla tana miko min. Da kyar na iya watsa su a baki na hadiye. Wannan yana daga cikin dalilan da suka sa naki tashi dazu da safe zuwa asibiti yana nufin allura da magunguna, ni kuma bana son allura da magunguna.

Janan ta harareni lokacin dana hadiye kwayar maganin karshe da kyar, na fara kakari. Tace "dazu ai da ana tsira miki allura a jiki ko a jikinki".
Nace "kema kin san saboda bana cikin hankalin kaina ne, amma ina ji ina gani in zauna a tsira min allura? hauka nake?".
Ta kwashe da dariya, na harareta, "muguwa kawai!". Gwalo ta min kamar wata karamar yarinya.

Tashi tayi ta dauki kwanukan ta fita. Na lallaba na lalubo wayata daga bayan katifa inda na jefata jiya. Nasan anyi ta nemana babu kakkautawa, musamman ma Muhammad. Na kunna wayar na tsaya tayi loading kafin na bude ta, nayi gaskiya kuwa. Sakonni daga Muhammad sun fi cikin kwando, tambayarshi daya, lafiya? Na hade fuska lokacin dana kula daga cikin sakonnin akwai na Umar, ko kara kallonsu ban yi ba na goge su gabadaya. Na tafi dungurungum nayi blocking dinshi daga wayata.

Komawa nayi daya bayan daya ina karanta sakonnin shi. Duk karantawar da zan yi, zuciyata kara narkewa take yi cike da begen shi, Allah ya sani, a kullum kaunar bawan Allahn nan kara yado take yi a sassan zuciyata. Ban sani hakan ko abu mai kyau bane ko kuma akasinsa. Kafin in gama karantawa jikina yayi wani irin sanyi, daga cikin kalaman shi kawai, babu tantama zaka karanci tsananin kulawa, tsantsar so, da kauna mara iyaka a cikinsu. Jikina yayi sanyi saboda babu mahalukin daya taba nuna min kwatankwacin irin wannan so, kauna da kulawar da wannan bawan Allahn yake nuna min. A duniya yanzu waye yake damuwa kawai don ya kira wayar wani daga dare zuwa safe ya ji a kashe? Sai Muhammad. Sai daya kai ga tambayar ko dai wani laifi yayi min ne, a cikin sakon. Ina gama karanta shi na lalubo lambar shi na danna kira, ban ma san me zan ce mishi ba. Sai dai cewa aka yi line busy, alamun yana waya. Don haka naci gaba da karanta sauran sakonninshi, nasan idan yaga missed call dina zai kira.

Janan ta dawo dakin da waya a kunnenta, daga yanayin yadda take maganar da Yaya Bilal take wayar. Hankalina yana kan sakonnin M.B da nake ta nanatawa, kamar wani karatu. Don haka sama-sama nake jin muryarta a kaina. Bayan ta gama ta zauna a gefena, tace "Yaya ne ya kira yana tambayar ko kin tashi nace eh. Yana Funtua shi da Anty Ameerah, wai ya kaita wajen sunan kawarta," ta fada tana tabe baki, ni kuma na dan murmusa saboda yadda ta bani dariya, "yace a duba ki da jiki dai kafin ya dawo".
Nace "babu komi wallahi, ai na warware".

Tace "yauwa, na ma tuna! Ummah tace tana so ta duba ki itama". Ta ciro wayarta ta kirata, bayan sun gaisa sun yi yar hira, Janan ta miko min wayar na amsa, na gaisheta cike da girmamawa kamar tana gabana. Tace "Janan dai ta goga miki, daga zuwa jinya sai kema ki buge da jinya?", ni da Janan muka yi dariya sosai. Mun jima muna hira da ita, Ummahn su Janan ta iya bi da mutum cikin sanyin kalami kaji ka saki da ita, akwai lokuta da dama da zamu fara hira da ita cikin dari-dari ko rashin sakin jiki, amma cikin dan kankanin lokaci zan ji na saki da ita sosai, inji na hau hira da ita sosai. Wasu lokutan sai daga baya zan zauna ina mamakin hakan. Munyi sallama da ita tana ta zuba mana addu'o'i kamar yadda ta saba, na kashe wayar na mikawa Janan.

Kwanciya tayi rigingine tana kallon ceiling din dakin, ni kuma na lalubo game din candy crush a wayata ina bugawa. Shiru ya ratsa dakin na dan wani lokaci, can naji tace "Nan da sati biyu Yaya zai tafi umarah shima".
Na kalleta cikin mamakin dalilin da yasa ta fada min, nace "and?".

Ta kalleni tana wani yin kasa-kasa da idanu, "don Allah kizo ki taya ni zama kafin ya dawo!".
Na zaro ido, "wa? Ni?? Ki rufa min asiri in mutu maza su kaini ba mata ba! Ana zaman lafiya, da hankalin kaina, anya kina ma so na kuwa?".
Ta harareni, "yo meye na wani zaro ido? Wuta nace ki zo ki taya ni zama?".
Na koma na kwanta ina dariya, "lallai ma, zama a gidan nan naku ai sai wanda ya shirya, ni kuma ban shirya ba. Jira nake goben nan tayi, idan na cira kafa na bar nan gidan sai kuma baba ya gani. Idan da son rai na ne ma, har in bar Zaria ba zan kara zuwa nan ba!".

Tace "inaa, kema kin san wasa kike yi coz you are stuck with me babe, babu yadda zaki yi dani. Sannan gobe babu inda zamu je sai jikinki ya kara yin kwari sannan, maybe zuwa talata?".
Na kalleta ina dan murmushi cike da jindadi, "babu wani hutu da nake bukata don ni nan garas nake ji na, amma kuma wa zai ki hutu koda na kwana daya ne musamman daga wannan asibitin?". Itama tayi murmushi.

Karan da wayata tayi ne yasa na kalli hannuna duk da kida na musamman ne, na riga nasan mai kiran. Na turo baki cikin shagwaba, ban san dalili ba, duk lokacin da nake tare da Muhammad, na kan ji ni kamar wata yarinya karama, kamar wata sabuwar halitta.
Cikin shagwabar na daga, yana ta magana nayi shiru, yace "haba baby na, come on, talk to me mana. Nayi laifi ko? Am sorry!". Nayi shiru ina jinshi ya cigaba da cewa

Please Login or Register in order to submit comment