Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Jindadina daya, da bata sake biyo ni ba.

Na bude wajen direba a motata Benz, ruwan ash mai haske sosai daya zama kamar white-gold, wadda na saya da kudina da albashina duk da dai sai da Yaya ya min ciko, lol.
Na maida kofar na rufe, na kwantar da Muhaaseen a seat dinta dake bayan motar. Sannan na sauke wani dogon numfashi da ban san na rike ba.
Sai dana nutsu, sannan na tashi motar tare da ja na fita daga cikin unguwar a hankali.


*


Na kwankwasa kofar dakin Yaya sannan na tura kofar na shiga.
Yana zaune a tsakiyar dakin akan carpet, Muhaaseen na kwance akan cinyarshi tana yan wasanninta na yara. Laptop dinshi da tarin takardu da jaridu shimfide a gefenshi suna jiran ya karkata hankalinshi garesu. Hankalinshi baya kan su though, kai gabadaya ma baya cikin dakin. Idanunshi na kan Muhaaseen, kamar wanda yake kula da duk wani motsi da tayi, sai dai daga gani kawai idanunshi ne suke kallonta, amma gabadaya hankalinshi baya ma cikin dakin. Tuni yayi nisa a cikin duniyar tunani.

A nutse na ajiye farantin dana shiga dashi a kusa dashi. Karamar kettle ce dana zuba shayi a ciki, sai fresh grapes da berries a cikin wani bowl.
A hankali na kai hannu na dauke Muhaaseen daga jikinshi. Yayi firgigit! Ya zabura yana kallona a dan rikice.
Na kalleshi cike da alamun tambaya, kusan kwananmu takwas da dawowa daga Zaria, amma na kasa gane kanshi. Duk lokacin da zaka ganshi, a zaune yake ko yayi tagumi, ko kuma yayi zurfi cikin tunani. Haka a yawancin lokuta zan tashi cikin dare in ganshi zaune a tsakiyar gado cikin zuzzurfan tunani, sai dai duk lokacin da zan tambayeshi abinda yake faruwa sai dai ya girgiza kai kawai. Ko yace ya gaji ne, ko aiki ne ya mishi yawa, ko kuma wani abu dai. Wanda daga ni har shi mun san cewa ba haka bane.
Amma gabadaya yan kwanakin nan naga abubuwan nashi sun fara yin yawa, na kula har wasu dark spots sun fara fito mishi a kasan idanunshi alamun akwai abin da yake matukar damunshi.

Ban ce mishi komi ba, na tura mishi plate din dana shigo dashi. Cikin sanyin jiki ya janyo laptop dinshi ya fara aiki, na kula da yadda hannunshi yake dan yin rawa slightly. Nan ma na kauda kaina. Na dauki inabin tare da kaishi saitin bakinshi. Ya dago kai ya kalleni yayi dan murmushi tare da daga bakinshi ya karbi inabin, sai daya hada da yatsata ya dan ciza.
Da sauri na janye yatsar tare da sakin dan kara a hankali, hakan yasa Muhaaseen dake kan cinyata ta zabura. Nayi saurin fara lallashinta ina hararar shi ta kasan ido, yayi kamar bai san abinda yake faruwa ba, sai dan siririn murmushin daya saki na tsokana.

Ina gama lallaba Muhaaseen tayi barci, na kwantar da ita a cikin crib dinta dake gefen gadon da muke kwanciya. Na sake komawa gefen Yaya na zauna, yana aikinshi ni kuma ina cin abubuwan da na ajiye ina kuma bashi, har muka gama su. Sannan na dauke kayan na kai kicin. Sai dana tsaya na kashe duk wasu abubuwan wuta sannan na wuce dakina, nayi shirin da zanyi na kwanciya sannan na koma dakin Yaya.
Har yanzu yana zaune inda yake, sai dai ba aiki yake yi ba, al'adarshi ta tunani yake. Raina gabadaya naji ya dagule.

Na zauna a gefenshi tare da nade kafafuna sosai ina fuskantarshi, cikin sanyin murya nace "Abban Maama, wani abu yana faruwa ne?".

Yayi saurin girgiza kai yana kokarin mazewa kamar yadda ya saba, "me kika gani?".

Nace "meye ma ban gani ba? Wani abu ya faru ne a Zaria? Tun muna can fa na kula da canzawar da kayi, ina kuma ta tambayarka amma sai dai kace min babu komi. A tunanina ni din abokiyar shawararka ce, kamar yadda kake abokin shawarata?".

Da sauri ya hau gyada kai kamar wani karamin yaro, "haka ne baby, na sani. Just... Ban ma san ta inda zan dauko zancen bane".
Jin haka yasa na kara matsawa kusa dashi sosai, "to menene? Ka fada min, kaji? Idan ma wani abu ne da yafi karfinka zamu iya hada karfi da karfe, idan ma yafi karfinmu dai duk babu abinda zai gagara, kaji? Menene?".

Yayi shiru yana kallona cikin tunani. Kai ya girgiza kawai, "I'm sorry baby, maybe next time, amma ba yanzu ba".
Nayi kasa-kasa da ido, "Yaya...!"
Sai dai ban kai ga karasa fadar abinda nayi niyar fada ba, naga ya tashi da sauri kamar wanda aka mintsina yayi hanyar bayi. Na bishi da kallo cike da tsananin mamaki, a hankali wani abu mai kama da takaici ya tsaya min a makoshi. A ganina ina laifin wanda ya damu da damuwarka? Akalla kullum zan tambayi Yaya abinda yake damunshi, yafi sau a kirga. A tunanina, ko bai fada don muyi maganin abin ba, ai zai fada ko don raba damuwarka da wani kamar ka cirewa ranka rabin damuwar ne.
Nayi kwafa a hankali tare da mikewa tsaye ina karkade kayan jikina. Ko kofar bayin daya shiga ban kara kallo ba, na wuce wajen da Muhaaseen take kwance na tofe ta da addu'o'i. Na haye kan gado tare da shafe nawa jikin nima da addu'ar kwanciya barci.

Ban ma san lokacin da Yayan ya fito daga bandakin ba saboda lokacin barci ya fara daukata. Daga can dai naji lokacin daya hayo kan gadon ya kwanta tare da laluboni jikinshi, nayi banza na share shi. Kodayake, shariyar ta dan lokaci ce, babu shiri na manta da dan guntun fushin da nake yi na kara kwantar da kaina akan faffadan kirjin mijina.

Cikin tsakiyar dare na farka, tunda na laluba gefena naji babu kowa nasan cewa Yaya sana'ar yake yi. Na mike zaune da kyar tare da daukar bargo na rufe saman ruwan cikina dashi, saboda sanyin da yake dan bugowa a lokacin.
Kamar yadda nayi zato, zaune yake a gefen gadon, ya zira kafafunshi ta kasa, kanshi a kasa, ban sani ba duk cikin tunanin ne, ko kuwa barci yake yi a haka?.

A hankali na kai hannu na dafa samar kafadarshi, daga yadda jikinshi yayi tensing, nasan cewa idanunshi biyu.
Nace "Abban Maama...".

Kaico! Masana iya magana dama sukan ce wai rashin sani yafi dare duhu, kuma dana sani k'eya ce.
Da ace nasan kalmomin da zasu fito daga bakinshi, da ban farka ba, da ban yi tunanin yi mishi magana ba a tun farkon fari, dana sani da naci gaba da kwanciyata koda kuwa na kasa komawa barci. Ban shiryawa jin abinda ya fito daga bakinshi ba.

"Na'ilah, aure zan yi!".

Kalma mafi muni data taba shiga cikin dodon kunnena a cikin tarihin rayuwata kenan. Naji duk wasu ayyukan dake wakana a cikin kwalwata sun dakata da aiki, kai ni a karan kaina sai naji ni kamar wata sassaken sak'ago, ko wata statue. Na kasa numfashi, na kasa motsa komi a jikina, na kasa tuna komi a cikin raina. Wadannan kalmomi hudu daya furta, su kadai nake fahimta, su kadai kuma suke min yawo a cikin kaina.

Ban san lokacin daya juyo ya fuskanceni ba, sai da naji hannunshi da a da, idan ya taba ni dasu na kanji duk wata gajiya da wahala dake tattare dani ta gudu daga jikina a take, amma yau ya banbanta. Sai naji kamar ya dauko duk wata gajiyar duniya ya dora min ne, babu shiri na fara kokarin zame nawa hannun daya kama, amma bai bari hakan ta faru ba.

"Na'ilah, baby, ki saurareni don Allah, wallahi ba wai don bana sonki bane zanyi wannan auren, I love you more than anything in this world, bani da zabi ne, don Allah ki saurareni, kinji?".

Na daga idanuna da na kasa tsayar dasu waje daya. Daga jin zafin da suke min, nasan cewa cike suke da hawaye, sun kuma canza kala. Cikin muryar da ni kaina sai dana yi mamakin jin ta fita daga bakina, nace "me kace?".

Ya kara damke tafin hannuna cikin nashi, "please baby, ki bari in fara miki bayani kafin...".
"aure kace?", na katseshi ta hanyar jefe mishi wannan tambayar, ba tare da tunanin maganganun da yake fada ba.

A hankali, kamar wanda yake tsoron wani abu, ya daga kai sama.

Ban san lokacin dana kwace hannuna ba, na dira daga kan gadon cikin wani irin sauri da rawar jiki da ban taba zaton akwai irinsu a duniya ba.
Yaya yayi kokarin sake kamo ni, amma ina! Gabadaya duk wani sauran tunani daya rage a jikina yayi kaura. Ture shi na sake yi. Daya matsa da kiran sunana da kokarin kamo ni, sai kawai na kasa da gudu. Na fada dakina na maida kofar da sauri na kulle da makulli na hada da sakata.

Tsaye a tsakiyar daki, hannuwa biyu da suke ta rawa rike da wayata ina lalube cikin jerin contacts dina, amma na kasa ganin komi saboda hawaye da suka cika min idanu har sun fara zuba, balle inyi tunanin wanda zan kira a cikin tsalelen daren wannan.
A gefe guda kuma Yaya yana daga waje yana buga min kofar dakin tare da magiya akan in bude muyi magana.
Daga karshe dai silalewa tsakiyar dakin nayi da hannuwana biyu aka.

An fara kiraye-kirayen sallah a wasu masallatan lokacin da Yaya ya dakata da bugun kofar da yake yi, ina jin karar sawayenshi lokacin da yake barin kofar dakin. Na bi kofar dakin da harara kamar shine tsaye a wajen.
Ba'a jima ba sai gashi ya dawo da Muhaaseen, karan kukanta da naji ne yasa na dan dawo cikin duniyar, daga fari da kamar ba zan tashi ba, naga dai babu laifinta a ciki. Na mike tsaye ina layi da jan kafa na bude kofar dakin, nayi tsaye kyam tare da mika mishi hannu, naki matsawa gefe balle ya samu damar shigowa.
Yana miko min ita na karbeta tare da kokarin maida kofar in rufe, yayi saurin sanya kafarshi daya ya tare ni, "baby please...".
Ban jira ya karasa ba na katse shi da nawa warning din, "don't!".

Babu musu ya janye kafarshi, na maida kofar na rufe garam, da ba don Allah yasa ya matsa da wuri ba da babu abinda zai hana in buga kofar nan a fuskarshi. Too bad, abinda naso ya faru kenan, babu abinda nake tunani a lokacin sai gwara in saba mishi kamanni in gani ko wadda zai aura din zata cigaba da son shi a hakan. Juyawa nayi zuwa cikin dakin na zauna a gefen gado.

Tunani na farko daya fara zuwar min shine asubahi ta farko in kama hanya in bar mishi gidan, in yaso sai ya dauko wadda yake so din ya ajiye a gidan nashi, daga baya dai naga cewa wannan gurguwar shawara ce, idan ma na tashi ina zan tafi? Gida dai nasan ko na sha giyar wake, Baba ba zai barni in zauna ba, in ma ce mishi me? Gashua kuwa... Bana ma sako ta cikin lissafi. Nasan ko numfashi ba zan gama ajiyewa ba zan ganni na dawo Abuja.

Tunda nayi sallar asubahi, na koma na kwanta. Duk da dan banzan barcin daya cika min ido, amma na kasa komawa barci. Ta yaya ma zan iya barci a cikin wannan halin?. Hawaye ne masu dan karen zafi da daci suke min zarya a kumatu. Rabin filon da nayi matashin kai dashi ya jike da lemar hawayena.

Wani sashe na can kasan zuciyata kuwa yana fada min I'm just being a hypocrite.
Bai taba fada ba, amma can wani bangare na tunani na yana fada min cewa ba zan taba zama ni kadai a cikin gidan Yaya ba, na sani. Shi yasa na kasa zama comfortable, na kasa sakin jiki balle har in saba da zama ni daya din, amma me yasa duk da hakan, zafin da nake ji a yanzu ya wuce misali?.

Har gari yayi haske, rana ta fito, ban motsa daga inda nake ba, ganin barcin ba zai yiwu ba yanzu yasa na tashi. Sai dana fara shirya Muhaaseen data tashi sannan nima na shirya cikin uniform dina.
Na nadeta cikin shawul mai taushi, na dauki abubuwan da zan bukata na bude kofar dakin na fita.
A falo na kwantar da ita tare da sauran kayan hannuna na shiga kicin. Duk da bana jin yunwa, amma kuma I can't find it in me to starve my husband, ba ma zan ji dadi ba idan ban mishi girkin ba. Don haka na kunna gas. Ganin cewa lokaci ya riga ya kure, yasa nayi sauce din kwai kawai na dafa shayi, na kai kan dinning da biredi na ajiye. Har yanzu Yaya bai fito ba, watakila barci ne ya kwashe shi. Nayi kwafa da nayi tunanin haka, watau shi har lokacin yin barci ya samu? Ya mishi kyau.
*
Tunda naje asibiti na kasa tabuka komi, tun safe har lokacin tashinmu yayi. Yan kananun ayyuka kamar su dressing da sauransu, sai sauran abokan aikina ne suka dinga yin su. Sunyi tambayar duniya, ce musu ciwon kai nake yi kawai na dinga yin. Haka nan na koma gida dai ranar.
Kasa daurewa nayi, na kira Sailu a waya ina kuka tun karfina da jan majina, mata ta rikice ta hau tambayata abinda yake faruwa. Na zayyane mata abinda kenan, ban boye mata komi ba.
Ina gamawa taja tsaki, na daga baki hangangam cikin mamaki ina saurarenta, tace "to sai me? Ni Wallahi nayi zaton wani mummunan abu ne ya faru, har kin bani tsoro".

Na share hawayen fuskata nace "haba Sailuba, yanzu wannan ba mummunan abu bane?".

Tace "mummuna a ina? Yo wai ita kishiyar karshen rayuwarki ce ko me? Yadda kike yi dinnan sai wani yayi tunanin baki taba zama da kishiyar bane, ke da kika zauna da mata har biyu, kika kuma zauna lafiya balle daya?".

Nace "to ita dayar kinsan halinta ne? Ko kuwa kinsan da abinda zata shigo? Su biyun kin san kalar gwagwarmayar da muka sha dasu? Wata fa har sanadin rayuwata ta kusa yi, dayar kuma taso laka min sharrin kisan kai. Haka kawai ina zaman-zamana azo a sanya ni a uku!".

Sailu ta dan saki dariya, "haba dai, kada ki zama raguwa mana. To wai ma, zaki hana shi yin auren nan ne? In fada miki gaskiya, gwanda tun kuna shaidar juna ki hakura, wallahi ki bashi amincewarki. Allah kadai yasan abinda yake cikin auren nan, kuma duk wasu bore-borenki da tashe-tashen hankulanki, babu fa abinda zai hana. Sai dai idan Allah bai nufa ba, ko kuma idan shi din bai ga damar yi bane kawai. Wannan zamani ma Allah na tuba, wa yake wani tayar da hankalinshi akan wata kishiya? Kin san Allah? Ki daina gani yanzu yana wani bin kanki yana lallashinki, na dan lokaci ne. Tun kafin ya daina biye miki, ki bada kai bori ya hau, don ba zaki ji dadi ba wallahi".

Na daga baki nace, "amma...".
Tace "amma me? Ni fa in nice ke ko? Wallahi babu wani tada hankalina da zanyi, akan me? Miji ne, nasan yana min son da babu wata 'ya mace da zata iya kamo kafata. Idan kuma kika iya rawar ki da takunki, wallahi ko ta shigo babu wani abu da zai sauya. Don haka don Allah ki kwantar da hankalinki Na'ilah, nasan cewa baki son kishiya, amma ina tabbatar miki da cewa ba duka fa aka taru aka zama daya ba. Duk wadda kika ga tayi wani da ba daidai ba, dama can halinta ne. Ke yanzu da ya aureki, kin taba tunanin daidai da rana daya akan kiyi yadda zaki yi ki kori kishiyoyinki?".

Na girgiza kai a hankali, kafin na tuna cewa bata gani na, na daga baki da kyar nace "a'ah", maganganunta sun sanya min rawar jiki, sun kuma jefa ni cikin tunani.

Tace "to kin gani? Halayenki masu kyau ne, haka kuma niyarki tsarkakkiya ce. Zata iya yiwuwa itama wadda zai aura din, maybe, itama niyarta daya da taki. Ba zaki taba sani ba. Kada ki damu, kinji?".

Na kai hannuwa ina share hawayen fuskata with determination, nace "haka ne, nagode Sailu".

Tace "ni ce da godiya Na'ilah, naji dadi da kika fara nema na. Baki nemi wadda zata jefa tunanin da zai jirkitar dake ba. Sai anjima". Muka kashe wayar.

Na koma na kwanta tare da ajiye wayar a gefena, maganganun da muka tattauna da ita suna kara min tariya a cikin kaina.



Karfe kusan bakwai Yaya ya dawo daga wajen aiki. Ina kan abin sallah ina lazumi lokacin daya leko dakina, bai ce komi ba ya wuce inda Muhaaseen take kwance yana mata yan wasanni. Ban ce mishi komi ba har ya gama, ya juyo yana kallona with wariness.
Wani abu yazo ya cake ni a kirji, har yaushe ne mijina ya fara kallona da wannan sigar? Har yaushe ya fara kallona a tsorace, kamar wanda yake tsoron yana daga baki ruwan alkaba'i ne zai fita daga cikin bakina? Ko kuma yana tsoron in yanke mishi kai ne? Oho!. Kodayake, wannan ba shine karonshi na farko ba, waya san abinda tsofin matan shi suka mishi lokacin daya tashi yin aurena?.
Wata dariya ta nemi ta kubce min a lokacin, the irony! Wani lokaci can daya wuce, nima fa shirin shigowa gidan nake yi, ba tare da tunanin abinda matanshi suke dandana ba ta dalilin haka. Sai gashi yanzu nima ina dandanarshi. Allah kenan. Kodayake, auren da aka yi bada son raina ba, ina ma hankalina ya kai ga tunanin halin da matanshi suke ciki?.

Yace "madam, barka da war haka".
Murya a sanyaye nace "sannu da zuwa, ya aiki?".
Yadda ya kalleni cike da mamaki yasa nima na kalleshi cike da mamakin, ko bai yi zaton zan amsa mishi bane? Yace "uhmm, lafiya lau. Ya asibitin?".
Na gyada mishi kai.

Muka yi shiru daga ni har shi, kafin yace "Baby, don Allah ki fara saurarata kiji abinda zan ce". Yayi shiru yana kallona yaga ta yadda zan karbi zancen, ban nuna komi ba, sai idanu dana zuba mishi alamun ina saurarenshi.
Yace "Hajara, diyar Alhaji Musbahu ce, abokin baban nan nawa da naje dubawa a Zaria kwanaki. Cewa yayi kawai ya bani ita, zai aura min ita, ni kuma ban san ta yadda zan yi in ce mishi bana son diyarshi ko kuma ba zan iya aurenta ba. Yayi mana halacci matuka a lokacin da muka bukaci taimako. Don Allah kiyi hakuri, amma idan har ba zaki iya ba, wallahi zan iya cewa na fasa".

A raina nace 'kamar gaske!'.
Na kauda kaina gefe ina jin kwalla na ciko min idanu, nace "ni har na isa in hana ka kara aure? Wacece ni?".

Ban san cewa ya tashi daga inda yake ba, sai da naji ya kamo tafin hannuna, yace "saboda kin isa baby, kin kuma kai matsayin da zaki hana ni din in hanu".
Wata yar siririyar kwalla ta zubo min a kan kumatu ya kai yatsa ya dauketa. Sai na fashe da kuka na fada jikinshi, cikin kukan nake cewa "nasan cewa fada kawai kake yi, amma ba zaka fasa ba!".

Yana shafa bayana a hankali, cike da alamun lallashi yake cewa "try me baby, da gaske nake".
Sai dana lafa da kukan, sannan yaci gaba da cewa, "zata zo ta ganki, idan kika ji bata kwanta miki a rai ba, to sai dai suyi hakuri".
Na dan jefa mishi harara, "ni bana wani son ganinta!".
Yayi murmushi a sanyaye, "I'm sorry baby, I love you!".
Ban ce mishi komi ba, don a lokacin wani sashe na zuciyata rada min yake, 'ya daina sonki yanzu!'.


**


Ranar Lahdi da rana, ina falo ina duba wasu manyan textbooks akan midwifery, duk da karatu dana gama hakan bai hana ni cigaba da neman ilimi ta textbooks ba, idan ma Allah ya bani dama so nake in cigaba da masters dina. Kofa naji ana knocking. Cikin mamakin wanda zai zo a daidai wannan lokaci na tashi na nufi kofar. Yaya ya fita dazu da safe, kan cewa zai je wani waje ya dawo, nasan ma bashi bane tunda da shine da ba zai tsaya yin knocking ba.

Wasu matasan yan mata biyu naci karo dasu, ba laifi dukansu kyawawa ne. Dayar zata yi sa'ata, fara ce ba can ba, doguwa mai dan jiki, yayin da dayar kuma daga ganinta kasan kanwar dayar ce, yanayin kamanninsu da surarsu kusan daya ce, kawai dai karamar tafi babbar kiba da fari.
Nayi yar fara'a duk da cewa ban san su ba, na musu iso zuwa ciki. Sai da suka zauna akan kujera, sannan naje na dauko lemu da ruwa na kawo musu.
Na zauna muka gaisa dasu, nace "ko kuna neman wani gida ne?".

Karamar ce tayi saurin cewa "a'ah, Yaya Bilal ne ya kawo mu nan!".

Na karkata kai ina kallonsu cikin mamaki, me zai hadinsu da Bilal? Na gyada kai a hankali nace "Allah sarki!".

Karamar ta sake cewa "ni sunana Zainab, wannan kuma Hajara". Ta nuna babbar.
Sai lokacin na kula da yadda babbar take ta sunke kai tunda suka shigo. Wow!! Sai lokacin na fahimci komi. Ita ce Hajarar dama? What a nerve she has! Da har ta iya kwaso kafafu tazo min gida.

Kafin in iya daga baki in ce wani abu, Yaya ya shigo cikin falon. Ya zauna a gefena, Allah ne ya iya bani ikon samun dauriya, na cije ban dankara mishi harara ba.
Yace "Madam, ga Hajara na kawo miki".
Na gyada kai ina dan murmushin yake, "aikuwa na ga Hajara"...


Shi ya zama jagorar hirar tamu, ga mamakina cikin dan lokaci kankani muka saki jiki daga ni har su. Ko lokacin da lokacin sallah yayi, tafiya yayi ya barmu. Na kaisu dakina suka yi sallah, muka koma falo. Dana shiga kicin haka suka biyo ni, duk da magiyar dana musu akan su koma falo suyi kallo ko wani abu, fir suka ki. Duk wannan abin da ake yi, Muhaaseen na bayan Hajara a goye.
Kafin Yaya ya dawo mun gama girki. Muka zauna mu duka muka ci ana ta hira.

Anan na fahimci cewa dukansu a Abuja suka tashi, shima Babansu matanshi biyu, in fact, Zainab step sister din Hajarar ce. Ita Zainab tana Abuja uni tana karantar mass com, tana aji daya. Ita kuma Hajara wannan shekarar ta gama degree dinta akan architecture a jami'ar Tafawa 'Balewa, Bauchi.
A abinda na karanta a cikin dan lokacin, shine suna da wani irin sanyin hali da hangen nesa, haka iliminsu ya tabo ta kowane fanni.

Zuwa lokacin da yamma tayi, suka mana sallama akan zasu tafi, sai naji kamar kada su tafi. Allah ya gani, naji dadin zuwansu sosai. Suma daga ganin yadda suka mike din zasu tafi, hakan take. Shima sai da direban da aka turo ya daukesu yazo, sannan suka tashi.

Na shiga daki cikin drawers dina da nake ajiyar abubuwa saboda bakin ba zata, na ciro musu turaruka masu kamshi, chocolates, kayan kwalliya, cike da leda na fito. Muka musu rakiya har gaban motarsu ni da Yaya. Sai da zasu shiga sannan Yaya ya karbi Muhasseen a hannun Hajara, na kula Allah ya hada jininsu sosai.

Na mikawa Zainab ledar hannuna, da taki karba, na harareta cikin wasa, "ko dai kin raina ne?".
Ta zaro ido da sauri, a lokaci guda kuma ta sanya hannu ta karba, "haba dai Anty! Mungode sosai, Allah ya amfana!". Wani halin nasu mai burgewa kenan, akwai godiya. Daidai da abinci wannan dana zuba mana, sai da suka biyo mu da godiya da addu'a.
Nace "babu komi wallahi, ku gaida su Mama Sai mun zo ziyara".
Hajara tace "sai mun ganku!". Daga haka direban yaja mota suka fita daga cikin farfajiyar gidan.

Yaya ya sakalo hannunshi daya akan kafadata, dayan kuma yana rike da Muhaaseen. Yace "ya?".

Na daga kai na kalleshi ina dan murmushi, "uhmm, ba laifi. She doesn't look that bad!".
Yaya yayi murmushi a hankali, ya shafo hancinshi da nawa, "haka ne?".
Na gyada kai ina murmushi. Da gaske ne kuma, haka kawai naji hankalina ya kwanta da ita sosai. Kai duk da cewa tun kafin zuwansu dama na saddakar, amma hankalina bai kwanta ba.
Yanzu kuwa dana ganta, sai naji hankalina ya kwanta da ita sosai, shima auren hankalina ya kwanta dashi.

Watakila maybe, just

Please Login or Register in order to submit comment