Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yi kokari, yanzu haka aikin wata na maida gefe nayi wannan din fa. Nayi alkawarin nan da kwana biyu zan gama muku, kin san bama yin haka dake Esther".

Muna nan tsaye, sai ga Haleemo a gabanmu. Bata ko yi acknowledging dinmu ba, ta hau zazzagawa mai dinki masifa. Apparently, ita ce wadda ya ture dinkinta dake kan layi ya mana namu. Tun yana bata hakuri, har shima ya hau sama ya fara zuba mata tata kalar masifa, mu kam muka koma gefe muna kallonsu.

Ta ja tsaki, "matsalarku kenan dama wallahi, ku kwata-kwata baku san mutumci ba. Su waye suka fito da martabar wannan shagon idan ba mu ba?".

Yace "ke kada fa ki kawo min rainin wayau nan wajen. Kada ki manta ko wancan dinkin dana miki, baki cika min kudina ba. Wannan ma kika wani ciccibo kaya kika kawo min babu ko sisi, an gaya miki ni din bawanki ne wai?".

Sai lokacin ta kallomu, ta fara borin kunya, "to ni nace ba zan baka kudin ka bane? Kada ka wulakanta ni a gaban mutane mana!".
Ni da Janan muka danne dariyar data ke neman subuce mana.

Shi kuwa Mike yayi dan tsaki, "whatever, kin san ni bana irin wadannan tone-tonen. Su ma don dinkin aure ne shi yasa ma na ajiye nakin gefe guda".
Ta kallemu ido a zare, "aure zaku yi?".

Nayi murmushi nace "eh".
Tare da bude jakata na dauko iv na mika mata, ta amsa ta karanta. Tace "to Allah ya sanya alkhairi". Muka ce ameen.

Bayan mun tabbatar da cewa zuwa jibi zamu dawo mu amshi dinkin mu, muka tafi muka bar su suna cigaba da sa'insar su.

A kofar wajen, muka samu Umar tsaye a jikin motar shi, da alama budurwar tashi yake jira. Muka yi kallon-kallo dashi, muka zagaye shi muka wuce abinmu ba tare da wani yayi magana ba. Janan gida ta wuce, ni da Esther kuma muka koma cikin asibiti.


Muna shiga daki sai ga kiran wayar Janan, wai Anty Sarah tayi yar diyarta kamar Mimah. Na mata fatan samun sauki da barka muka yi sallama.

Ranar juma'ah muka yi induction dinmu, bayan an rantsar damu, mun karbi nursing license dinmu, aka shiga shagalin ciye-ciye da shaye-shaye. Allah kadai yasan irin farincikin da muke ciki a wannan ranar. Duk da cewa convocation dinmu nan da satika biyu ne, amma kuma induction ya ma fi muhimmanci ga nurses nesa ba kusa ba. Yinin ranar guda, kira ne kawai yake shiga yana fita daga wayata, sakonni na taya murna daga yan uwa da abokan arziki.

Da yamma bayan mun gama shagalin, ni da Janan muka dauki hanya zuwa barka. Kasancewar gobe asabar zan wuce gida. Gashua zan fara zuwa inyi kwana biyu, sallama da yan uwa da abokan arziki, sai in wuce Katsina daga can.

Napep din da muka hayo daga bakina titi yayi parking a kofar gidan, muka biya shi, sannan muka fita daga ciki.
Na daga kai na kalli gidan da kallo, yan kadan daga cikin memories dana tara a gidan, suka dinga flooding suna shiga cikin kwakwalwata. Na girgiza kai a hankali, ina kokarin shaking din komi daga cikin kaina.

Ni da Janan muka shiga gidan, bayan mun gaisa da maigadin gidan. Kai tsaye dakin Anty Sarah muka wuce. Da yake yamma ce, babu cunkuson mutane sosai. Muka gaisa na mata barka, ta amsa tare da min godiya. Yanayin yadda take fara'a da tambayata bayan rabuwa, sai kayi tunanin irin mun saba sosai dinnan ne.
Aka miko min diya na amsa, kamar yadda Janan tace, kamar su daya da Mimah babu banbanci. Na kura mata idanu ina kallo kamar in sude ta saboda birgewa. Yadda ta nade cikin towel din da aka nadeta a ciki, kamar irin magen nan sabin haihuwa, very adorable.

Mun jima sosai dasu ana yar hira, ba karamin mamakinta ta nuna ba akan maganar aurena da taji ba. Musamman ma da wani, ba... Bata karasa ba, naji Janan tayi saurin ta katse mata maganar. Na bisu da kallon mamaki, ban tsaya tambayarta wa take nufi ba, duk nayi zaton da Umar take, don haka na share maganar don nima bana son tuni akan irin rayuwarmu da Umar, da irin cin amanar da yayi min.

Ina shirin tashi da niyar yi musu sallama in tafi, kawai naji tashin sautin muryar data matukar rikitar dani. Da sauri na koma cikin kujerar dana fara tashi dabas, wata irin rawar jiki ta ziyarce ni. Ba shiri na fara janyo salati da hailala ina ja ina karawa a cikin raina.

Yaya Bilal da Yaya Jameel suka shigo cikin falon. Yaya Jameel sanye da casual jeans and T-shirt, yayin da kamar kodayaushe, Yaya Bilal yake sanye da shadda ruwan sararin samaniya, rataye a kafadarshi ta dama, brief case dinshi ce, da alamu dawowarshi kenan daga wajen aiki.

Suka samu waje suka zauna, kallon nan daya dana musu, ban sake daga kai na kallesu ba. Falon daga mu, maijegon, sai kuwa wata makociyarsu Ikilima data shigo bayan mun shigo muma.

Ina jin tashin muryarsu suna gaisawa da mutanen falon, nasan nima dole ne in gaida su.
Na daga baki da kyar na gaida su, ba tare dana iya daga kai na kallesu ba. Tashin muryar Yaya Jameel kadai naji ya amsa, hakan yasa naji jikina ya kara yin sanyi.

Ko lokacin da Janan ta karbi diyar daga hannuna da niyar mika musu, ban iya daga kaina ba.

Na yan wasu lokuta, dakin ya dauki shiru, babu motsin abinda kake ji, sai tashin muryar Yaya Bilal kawai da kake ji yana tashi, yana yiwa jaririyar addu'o'in tsari da kariya kala-kala.

A lokacin ne na samu na iya daga kaina a hankali, na saci kallon inda Yaya Bilal din yake zaune dauke da yarinyar. Rabon da in saka shi a cikin idanuna ko kuma inji muryarshi, run rana daya tsare ni a hanya a asibiti da kuma lokacin da muka yi waya dashi ta karshe.
A yanzu da nake kallonshi, yadda ya rike yarinyar nan a hannunshi kan-kam, kamar wanda yake tsoron wani abu ya faru da ita. Tsananin soyayya da zaka gani a cikin idanunshi, tsantsar adoration da wani irin hope, hope wanda ya kasa boyuwa a cikin kwayar idanunshi, ya sanya naji wani matsi a cikin zuciyata har sai da naji kwalla ta cika min idanu. Ba zan iya jurar wannan abu ba, na zabura na tashi tsaye da sauri, har wayata da take kan cinyata ta fadi. Nayi sauri na wawureta tare da sungumar jakata na rataya, na kalli Janan da Anty Sarah da suka bini da kallo cike da mamaki.
Nace "zan tafi ne, Anty Allah ya raya baby, Janan, sai mun hadu ko?". Anty ta amsa da ameen, Janan kuma ta matso kusa dani da niyar taka min zuwa waje.

Ina tunanin sai lokacin Yaya Jameel ya kula da nice a cikin falon, yace "a'ah! Wai dama Na'ilah ce?".

Na daga kai a hankali ba tare dana kalli inda yake ba.

Yace "ke kuma sai kawai muji labarin aurenki daga sama babu sanarwa kamar saukar aradu?". Mutanen falom suka saki dariya da jin haka, nima sai dana dan murmusa.
Yace "da gaske fa! Da har munyi fushi ai, daga baya dai na hakura. Allah yasa ranar asabar din zamu je daurin auren wani abokinmu, tunda shi nashi da safe ne ba kamar naku na rana ba, in Allah ya yarda zamu yi kokari mu leka".
Na gyada kai a hankali, nace "Allah ya yarda". Ban tsaya jiran jin wani yace wani abu ba, na daga kafa na fita daga cikin falon da sauri Janan tana bina a baya.

Muna fita, Allah ya taimakeni naga dan adaidaita sahu, na tsayar dashi da sauri na haye. Ko tsayawa muyi sallamar kirki ni da Janan banyi ba, dan adaidaitan yaja muka tafi.

A cikin adaidaitan, na saka fuskata cikin hannuwana, ina kokarin slowing down irin gudun da zuciyata take yi. Nayi tunanin na manta da Yaya Bilal a cikin raina. Nayi zaton na binne shi a cikin raina gabadaya. Ashe I was wrong. Innalillahi, na shiga uku. A haka zanyi auren?.

Cikin wannan tashin hankalin na sauka garin Gashua washegari. Ganin su Fatsu da kuma yan biyun Sailu da suka yi wayo bul-bul abinsu, shi ya sanya gabadaya na manta da ganin Yaya Bilal da abinda hakan ya haddasa min a cikin raina.

Tunda na sauka ban huta ba, Fatsu bata bari ko rintsawa inyi cikin sauki. Ina sauka, masu gyaran jiki suka tare ni da kayansu na tsuguno da turaruka. Washegari kuma aka yi su dilka da halawa. Kwana biyun nan da nayi, ba karamin gyara na sha ba. Ni a karan kaina sai da naji canji a jikina ba na wasa ba.

Ko a ranar da zan tafi, tare muka tafi da wata mai gyaran jikin, zata cigaba da gyaran data fara har zuwa ranar da za'a kaini gidana. Daga Maiduguri tazo, diyar wata aminiyar Fatsu ce wadda suke mutunci da ita sosai.


*

Tun ana saura kwana uku biki gida ta fara cika da yan'uwa na nesa. Mutanen Gashua da yawansu sun zo, sauran kuma sun tsaya a gida da yake suma can kalar nasu bikin zasu yi.

Janan ana saura kwana biyu fara biki tazo, muka hadu dasu Kulsum da sauran abokanmu muka cigaba da planning harkar bikinmu.
Da yake akwai dakuna biyu manya spare a cikin gidan, nan aka gyarawa yan biki. Duk da haka, ranar da aka fara harkokin bikin, sai da wasu bakin suka dangana da dakin Anty Alawiyya da namu dakin. Su Hajiya Ramata kam kane-kane tayi, babu wanda yayi gigin tunkarar dakinta ma saboda yadda ta cune fuska.
Ranar bikin ma haka ta yini tana ta shiga da fita tana zubda habaici, sai dai duk cikinmu babu wanda ya tanka mata. Muka cigaba da gudanar da bikinmu.

Wani abin mamaki shine, har ranar da muka yi walima, babu wanda muka gani ya leko daga cikin dangin anguna. Shi dama ango sai ranar daurin aure muka yi dashi zai zo, kwana uku ne kadai aka dauka ana shagulgulan bikin Koda na mishi korafi, cewa yayi kada in damu, zasu zo ne. Har ranar daurin aure shiru.
Maganar tafiya ma bai sake tada min ita ba, kuma a yadda muke tunani, an daura aure ranar asabar, jirginsu zai tashi ranar Lahdi da yamma. Dana taba tambayarshi yadda za ayi, naga yana neman manna min hauka, wai me yasa na cika wutar ciki ne da gajen hakuri? Na ga an daura auren ne ya dauki kafa ya barni ne? In zuba idanu mana in ga abinda zai faru. Na bashi hakuri a lokacin, na kuma kawo idanun na zuba mishi kawai.

Ranar assabar, ranar da za'a daura aure. Karfe goma sha biyu na safiyar ranar za'a daura auren a babban masallacin juma'ah dake nan cikin unguwarmu. Da safen muna can gidansu Kulsum saboda yadda gidanmu ya cika da jama'a babu masaka tsinke.
Na lume akan katifar Inna a can uwar daka, duk da uwar kwalliyar da nasha, da kuma zufar da ake yi, hakan bai hana ni fita ko nan da falo ba. Tunda garin yau ya waye, ko in ce tun a daren jiya ma, nake jin wata irin faduwar gaba akai-akai. Zuwa yanzu gabadaya jikina yayi sanyi lakwas kamar an watsa min ruwan sanyi a jiki.
Idanuna kur akan agogon bangon dake cikin dakin makale a jikin bango. Duk wucewar dakika daya, da karuwar faduwar gabana take wucewa. Har lokacin da hannuwan agogon suka hau kan sha biyu, suna nuna karfe sha biyu ce daidai a wannan lokacin. Jikina ya hau rawa yana kadawa, shikenan, na zama danyar nama.

Karfe goma sha biyu da rabi, na jiyo muryar Malam a tsakar gida da sauran muryoyi. Ban san abinda yake faruwa ba, ban kuma yi yunkurin tashi inji mai yake faruwa din ba, na cigaba da zamana. Sai da Inna ta shigo dakin ta ganni, tace "kina nan ashe? Ai an daga auren zuwa karfe hudu na yamma".

Daga farko ajiyar zuciya naji ta ziyarce ni, kafin na kalleta a rikice, "me yasa?".
Tace "wallahi nima Malam bai fada min ba, kawai dai yace sun ce an daga".
Ina ji da yawa suna fata da addu'ar Allah yasa hakan shi yafi alkhairi, a zuciyata nace ameen.
Idan haka ne, kenan yana nufin sai gobe sannan za'a tafi Zaria da ni. Tsarin dama shine idan aka daura auren yanzu, zuwa bayan azzuhur kuma sai yan kai amarya su dauki hanya. Nayi kokarin tuntubar angon nawa ta waya inji yadda ake ciki, waya bata shiga. Tun da yau tayi ban samu wayar shi ba, nayi tunanin ko network ne ya hana tunda a jiya da rana da muka yi wayar mu ta karshe dashi, yace yau da sassafe zasu taho da abokan shi.
Na sake kokarin tuntubar babban amininshi, Salisu inji ko me yake faruwa, wayar shi ta karaci kara har sau biyu bai daga ba. Daga karshe na maida wayar cikin jaka.

Haka kawai naji wani kuzari ya shige ni, na mike na fito tsakar gida, muka cigaba da harkar mu ni da 'yanmata na.

Kafin yammar tayi, gabadayanmu mun canza kayan jikinmu. Ni da Janan muka saka yadin da Ummahnsu ta dinka mana, su kuma sauran yanmata suka sanya ankon da muka yi.
Duk kokarin su shirya suke yi, saboda saurin kada anguna su zo damar hoto ta wuce su. Angunan da har yanzu banji wani yace yaji daga garesu ba. Har yanzu muna gidan Inna ne.

Bayan gotawar karfe hudu da mintuna kadan, muka jiyo sautin guda daga cikin gidanmu. Naji kafafuna sun yi wani irin lakwas, na fara kokarin zamewa kasa da sauri na jingina da bango.

Duk da haka, sai da naji wasu irin black spots suna kokarin dabaibaye idanuna lokacin da wata zabiya, irin marokan nan, ta fado gidan tana rangada guda.

"Ina amarya, amarsu ta ango! A zo a bani tukuicin wannan daddadan sako da zan isar, nima kakata ta yanke saka. Wa ya sani ko daga kanki sana'ar roko ta barni? Allah ya yarda, alkawarin Allah ya tabbata, aure ya dauru....!!".





✌✌✌😉😎











*☆⋆33⋆☆*





Marokiya bata kula da halin hargitsi da amarya ta shiga bane da alama. Sai data gama jan kirarinta, ta kara gaba. Duk cikinsu bana tunanin wani ya kula da halin da nake ciki ma gabadaya.

Tana fita, wani marokin ya leko shi har da yar karamar gangar shi a hannu, ya tsaya daga soro yana zuba nashi kirarin.
"Ina amarya, tazo ita kuma ta bani kujerar makkah. Ranar farinciki da murna ga masoya, Allah ya nufa, alkawarin Allah ya cika, aure ya dauru tsakanin Muhammadu Bilal da Malama Na'ilah!! Allah ya bamu ikon dawowa badi war haka mu sake shafa wata fatihar ta 'ya'yanku! Eh, a gayawa amarya, maroki dan na Halimeme na jiran nashi kason, ango Bilalu ya burge shi da sababbin kudi babu ko kari, farare tas bugun Abuja!....".

Ai lokacin amarya Na'ilah babu ita. Tunda ya furta kalmar sunan Bilal, naji duk wata dauriya ta rike kafafuna su tsaya a tsaye ta bar jikina, karshe dai sai dana kai ga silalewa kasa.
Abu na karshe dana gani, shine confused fuskokin mutanen da suka yo kaina a rikice, suna kwala min kira, duhu ya mamaye ni gabadaya...!


*


Ban tuna komi ba lokacin dana tashi. Mutane hudu ne a kaina lokacin dana farfado daga suman da nake kyautata tunanin nayi. Janan da Anty Halima kadai na iya ganewa, sauran biyun tare suka zo da Anty Haliman daga Gashua, ban gane su ba.

Na tashi zaune, Janan tayi saurin tara filo a bayana yadda zan ji dadin jingina duk da protests dina na cewa kada ta damu.
Dakin da muke ciki daga gani babu tantama asibiti ne, ko kuma karamin clinic.
Janan ta bude gorar ruwan faro ta tsiyaya a cikin kofi ta miko min, na amsa na kafa kai na sha tare da mika mata, ta amsa ta ajiye.

Na dafe kaina da yake sarawa tunda na tashi, ina kallonsu.
"Me ya faru ne?". Na tambaya cikin sarkewar murya, wincing lokacin da naji kaina ya kara sarawa kamar ana buga ganga.

Janan tace "Wanda zaki aura ne ya faru!", duk yadda taso ta nuna tsana da venom a cikin muryarta, fuskarta dauke take da murmushi mai tsananin taushi.

Sai lokacin komi ya fara dawo min cikin kai daki-daki.

Na fara girgiza kai a hankali, kafin na fara da karfi ina ja da baya har sai da bayana ya hade da allon gadon. Na dora hannuwa biyu kai, ihu naso kurmawa, amma babu abinda ya iya fita daga bakina. Daga karshe dai na samu sautin, "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Na shiga uku na lalace!!".
Kafin naji na barke da wani irin kuka.

Anty Halima ta matso ta rungumeni jikinta ta fara shafa gadon bayana cikin alamun lallashi. Tace "ke 'yar nan, ki kiyayi kanki ke kuwa, menene na shiga uku? Allah ya dube ki, ya baki miji na nunawa sa'a. Kowa yasan dama hakan da mamaki, ka auri wanda baka shiryawa ba, amma bai kamata kalma ta shiga cikin uku ta fita daga bakinki ba. Ki godewa Allah, Allah kadai yasan irin hikimar da take cikin wannan juyin lamari daya faru".
Amma kuma kukan naci gaba dayi, har ma na yanzu yafi na dazu sauti.

Tun tana lallashi, har ta gaji, ta koma gefe ta zubawa sarautar Allah ido, tana kuma mitar ai sai inje inyi tayi, a kaina farau?, amma ban kulata ba.
Sai da nayi ya ishe ni, kuka share-share har da majina, 'sai kace wadda aka aiko mata da sakon mutuwar uba, ba aure ba!' a cewar Anty Halima bayan taga yadda fuskata ta baci da hawaye.

Janan tana gefe, kallona take daya bayan daya, babu alamun damuwa ko digo daya akan fuskarta sai ma amusement rather. Hakan ya kara tunzura ni.
Ta zari tissue ta miko min, na warta na share hawayen fuskata da majina, nayi jifa da tissue din can gefe guda.

Janan ta kasa danne dariyarta, tace "a'ah, baiwar Allah. Ba fa shi ya kar zomon ba, haka muma da kike wani huhhura mana hanci. Don haka idan ma zaki ware ne yarinya, ki warware".

Na harareta tare da sake wartar wani tissue din na goge idanuna da suka cika da hawaye.
Nace "wane warwarewa kuma? Ai wallahi zuwa zasu yi su warware aurennan yadda suka kulla shi, don wallahi ba za ayi wannan kwamacalar dani ba! Idan kuma ba haka ba sai dai in bar musu garin wallahi!".

Su duka suka yi shagara da baki suna kallona, kafin Anty Halima ta daga baki da niyar fara magana, "wannan wace maganar banza ce kike yi? Ke...".

Maganar ta katse sakamakon kofar dakin da aka turo aka shigo, duk muka kalli kofar. Faduwar gaban data ziyarceni a lokacin da muka hada ido da ba kowa ba illa Yaya Bilal Allah kadai yasan irinta. Nayi saurin kauda kaina na kalli Yaya Mudatthir, daga ganin yanayin fuskarshi kasan cewa sun gama jin abinda na gama fada yanzu. Sai dai ban ji ko dar ba a cikin raina, hasalima can cikin raina cewa nayi gwanda da maganar ta shiga kunnen wanda aka yi dominta.
Fuskar Yaya babu yabo babu fallasa, ya cewa su Yaya Halima "Anty ko zaku dan bamu waje?".

Babu musu suka fita suka bar dakin, suka barmu mu kadai. Yayan ya kalleni fuska cike da warning tsantsa, kafin ya shima ya juya ya fita, har da maida kofar dakin ya rufe. Na harari kofar kamar ita ta min laifin.

A hankali ya tako cikin taku dai-daya, yazo ya tsaya min aka kamar wani tsohon soja, ya zuba min ido. Ni kuwa naci gaba da kallon kofar da Yaya Mudatthir ya bi stubbornly.

Ganin an dauki lokuta masu yawa ba tare dana sake ko jin motsin shi ba, yasa na daga idanu a hankali na kalli inda yake. Yana tsaye a wajen har lokacin, ko yanayin tsayuwarshi bai canza ba, idanunshi manya tubarkallah dasu kamar na Janan, a kaina. Na turo baki tare da sake dauke kaina.

Ina jin sautin murmushin daya saki, ya ja farar kujera dake can karshen dakin, ya ajiyeta a gefena ya zauna.
Murya can kasa, kamar mai rada yace "ya jikin?".

Nan ma ban ce komi ba, na kurawa mayafin da aka lullube gadon da nake kai idanu.

Ya sauke ajiyar zuciya, "ko ki amsa, ko kada ki amsa, hakan babu abinda zai sa, kuma babu abinda zai hana Na'ilah. Abinda ya faru dai ya riga ya faru...".

Nayi saurin katse shi, "bai riga ya faru ba, ni wallahi ban yarda ba, aurennan sai an zo an raba shi, dama tun farko ai sai dana ce ba zan aure ka ba!".

Yayi wani kicin-kicin da rai, "wannan kuma sai ki samu wanda ya daura auren kiyi mishi bayani, sai ya warware. Tunda nima ina zaman zamana sai kiran waya kawai naji ance za'a karbi wakilcin aurena, in kawo sadaki. Kin kuwa ga nima daga sama na tsinci maganar kamar ke dinnan".

Nace "to haka ake aure, babu tambayar wadda zata yi zaman auren?".

Ya daga kafada sama, "kamar yadda nace ne, zuwa zaki yi ki tambayi wadanda suka daura auren. Amma a shawarce, zan baki shawarar ki ma sauke wani girman kai, jiji da kai da jan ajin da kike yi, kamar yadda nace, abinda ya faru dai ya riga ya faru sai dai kuma a tari na gaba. Yakamata ki san irin kalaman da zasu fito daga bakinki, saboda da da yanzu ba daya bane, idan kinyi da na kyaleki, ina mai tabbatar miki da cewa yanzu fa ba zan kyaleki ba saboda a karkashin Ikona kike, saboda haka ki kula".

Kawai sai na sa kuka, yayi zaune a gefe yana kallona bashi da niyar furta ci kanki, nayi na gama na share hawayena, nace "to dama haka ake auren ne, tun kafin aje ko'ina ka fara cin zalina da gindaya min sharadi".

Yace "watch it Na'ilah! Yadda fa baki shiryawa auren nan ba, haka fa nima. To meye ma amfanin auren idan babu doka da sharudda? Abinda nake so ki sani shine, lokacin lallashi da bin kai ya kare tsakanina dake, tunda ke kafiyar kai tasa baki fahimtar komi sai an biyo miki ta bayan gida, let's bring it on then. Ta kowace hanya kika bullo, nasan ta yadda zan taro ki.

Ke yanzu hakan bai isheki ishara ba? Ki hakura ki saddakar, ki mika wuya ga hikima irin ta Allah ba? Ni din dai da kika dinga gudu Na'ilah, kina ihu da sanarwar ba zaki aure ni ba, ni din dai kika buge da aure bayan kin gama kewaye-kewayenki. Dama kin hakura tun farko, kin kauda wannan girman kan da kike ji dashi, da yanzu muna cikin farinciki gabadayanmu. Amma yanzu wa gari ya waya? Saboda tsabar son kai da taurin rai irin naki, kinga abinda kika janyo mana ai. Yaushe rabon da kici abinci ya cika miki ciki? Yaushe rabon da kiyi barci mai dadi? Yaushe rabon da ki samu sanyin zuciya da sukuni a cikin ranki? Yaushe rabon da ki samu wadataccen kwanciyar hankali? Ki duba kiga yadda kika bi kika rame, kika kare kamar kudin guzuri? Ni da kika dinga gudun ma dai sai da nazo na fiki kwanciyar hankali da jindadin rayuwa. Hakan bai isheki ishara ba Na'ilah? Me kuma kike bukatar gani da zai tabbatar miki da cewa ba'a taba tsallake abinda Allah ya riga ya tsara maka? Duk zullewarka, zaka yi ne ka gama. At the end of the day dai, sai ka komawa wannan kaddarar taka!".

Nayi shiru ina sauraron yadda yake maganar a zafafe, daga ji babu tambaya a matukar fusace yake, dani ko kuma wani.
Naci gaba da shesshekata har da jan majina, yace "ni yanzu haka Zaria zan wuce abina, zan je in fara shirin inda za'a sauke ki. Don haka kina da sati daya, daga yanzu zuwa rana irin ta yau, ki gama yanke shawarar yadda zaki yi, aure tsakaninmu dai ya dauru, babu kuma wani mahaluki da zai sanya ni datse shi, don haka you might as well take heart, shawarata a gareki kenan".

Ya mike yana gyara link din hannun rigar shi, "duk abinda kike bukata, zaki iya kiran wayata, ko

Please Login or Register in order to submit comment