Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dauka ba sai dai bawa ya dorawa kanshi. Saboda haka ina ji ina gani ba zan kai kaina wajen wahala ba. Tunda nace ka kyaleni, bana so, ba sai ka kyale ni din ba? Ana dole ne?!!".

Yace "haka kika ce ko? To ba laifi. Dama ina bin kanki ne kawai saboda kada kice anyi miki rashin adalci ko wani abu, amma tunda ke kunnenki na kashi ne, kuma idanuwanki a rufe suke, ba kya fahimtar komi, to zan biyo miki ta hanyar da baki so. Idan ke kin iya yiwa zuciyarki rashin adalci ne, ni ba zan cuci kaina ba akan wani dalili can naki! Ina ce ba mahaifinki ne da bakinshi yace ba zaki aureni saboda ina da mata ba ko? Kuma ba Allahn daya halicce ki bane? To ki kashe kunnenki da kyau, ki saurareni kiji, maganar neman aurenki yanzu na fara ta, ba kuma zan tsaya ba sai inda karfina ya kare. Zan kuma yi duk abinda zan yi in ga cewa kin shiga gidan da kike matukar ki, don Allah ki kashe kanki ranar da aka kaiki gidana a matsayin matar aure, sai in ga karshen tsana!".

Nace "Wallahi ba zai yiwu ba, ba kuma zan yarda ba. Ni dama nasan ba sona kake yi ba kamar yadda kake ikirari, in Allah ya yarda sai Allah ya shiga tsakanin nagari da mugu. Mugun kudirinka ba zai cika a kaina ba!".
Yace "zamu gani Na'ilah!". Daga haka ya kashe wayar.

Naji kamar in fasa ihu, jikina har rawa yake yi tsabar bacin rai. Lallai Yaya Bilal has got some nerves! Har yana da bakin da zai daga yace wai zai aureni ba da izinina ba? Har yana da wannan ikon a kaina?! To ai idan yasan wata bai san wata ba. Zan ga da abinda yake takama dashi kuwa!.

Na share hawayen da suka zubo min, na kara daukar wayata da nayi jifa da ita, na shiga cikin contacts dina. Ina ganin sunan wanda nake bukatar gani, na danna kiran ba tare da bata lokaci ba. Tayi kara daya, biyu, ana uku aka dauka.
.Cike da cheeriness da alamun tsokana da baka taba raba muryarshi da ita, yace "hello, Nas. Ya kike?".

Na dauki ajiyar numfashi na sauke a hankali, na dan kakaro murmushi duk da nasan cewa ba ganina yake yi ba, nace "hello Doctor, maganar ganin iyayena da kayi ranar nan, ka shirya yi yanzu?".

Yace "of course Na'ilah! Dama ni ai jiranki kawai nake yi. Yaushe ake bukatar gani na ne?".
Nace "idan ma a gobe ka shirya, zaka iya zuwa ka gansu".
Yace "Masha Allah, that's good. How about in zo anjima sai mu sake tattaunawa akan yadda za ayi?".
Na dan jinjina kai sama, "yeah, hakan ma yayi. Sai ka zo kenan?". Yace "in shaa Allah. Gani nan zuwa".
Nace "sai kazo!". Na ajiye kan wayar.


*




Kwana uku bayan haka, Janan ta shigo asibiti tun da safe ranar alhamis. Abin ya bani mamaki. A bakin hostel muka ci karo da ita, ni zan fita ita kuma zata shiga. Na kalleta cike da mamaki, nace "lafiya kuwa? Mai ya shigo dake nan da wuri ne?".

Bata tsaya amsawa ko yi min bayani ba, taja hannuna muka koma daga ciki, can gefe, tace "abinda kika yi kina ganin shine daidai a wajenki?".
Nace "me nayi?".
Tace "Yaya Mudatthir ya kira ni dazu tun da sassafe".

Sai lokacin na fahimci dalilin shigowarta din da kuma tambayoyinta. Nima bamu jima da yin wayar dashi ba.
A yadda muka yi da Dr. Na Abba lokacin da yazo ranar litinin, mun tsaya akan cewa zai je Gashua ya samu su Malam su akan maganar mu. A washegari talata na kira su Fatsu na sanar dasu bakin da zasu yi, zai je ne kawai suyi magana, a san dashi, sannan a tsaida ranar da yakamata magabatanshi su je. Su Malam suka yi farinciki matuka, har Fatsu tana cewa har ta cire rai da zaton zata ga wannan rana, ni dai kawai uhmm nace mata.

A daren ranar jiya bayan Dr. ya kira ni ya sanar dani cewa sun dauki hanyar Kano daga Gashua, Yaya ya kira ni. Tambayata kawai ya hau yi akan wai na tabbatar da cewa wanda na turo mishi na amince dashi? Nace ta yaya zan tura wanda naji ban aminta dashi ba wajen iyayena?. Yaya yayi shiru kamar ba zai yi magana ba, kafin yace "amma kuma Baba yace wani yaje wajenshi a jiya din, shima duk akan maganar ki ne!".
Naji an fara min wani luguden daka a kirji, ashe dai Yaya Bilal da gaske yake ba da wasa ba. Amma a zahiri sai na dake, nace "ni fa bansan ko wanene ba, don ni babu wani wanda muka yi magana dashi akan zai zo bayan Dr. Na Abba".
Yaya yace "to ai shikenan".
Daga nan muka dan yi hira, na tambayeshi jikin Sailu da har yanzu tana asibiti. Yace dukansu lafiya lau. Sannan muka yi sallama.

To yau kuma da safe sai ya sake kirana, yana tambayar wai dama wanda yaje wajen Baba Yayan Janan ne? Nace "ni fa Yaya na fada maka ban san kowanene ba".
Yace "kada ki raina min wayo mana Na'ilah. Ni nasan yadda kika sako karatun nan naki a gaba, maganar aure yanzu bata cikin kanki. Tunda naji dama wai kin turo wani gida kai tsaye, nasan da wata a kasa. Don haka ki fada min abinda yake faruwa".
Nace "to ni Yaya sai dai kuma in karya kake so in maka, amma babu abinda yake faruwa. Kawai na samu wanda hankalina ya kwanta dashi ne, dama can don dai ban samu wanda ya shiryawa auren bane".
Yace "ina wannan yaron da kuke tare dashi kuma fa, sojan nan?". Nace "ni tun yaushe da muka rabu dashi?".

Yaya Mudatthir yace "shikenan Na'ilah, ni dai ina shawartarki da ki bi koma menene a hankali!". Bai jira abinda zan ce mishi ba ya kashe wayar.
Na bi wayar da kallo cikin yamutsa fuska, me yasa ne yake wani magana yana bani a linke? Sai ban saka maganar a kaina ba, naci gaba da shiryawa ta.

To kuma gashi ina fita naci karo da Janan, itama tana bani tata linkakkiyar maganar.

Nace mata "eh, ina ganin shine mafi a'ala a wajena Janan. Ina ganin kuma hankalina zai fi kwanciya a hakan".
Tace "ki dai bi a hankali, kada kije ganin neman gira ki rasa idanu. Ki gujewa garwashi ki fada cikin wuta!".

Na dan jefa mata harara, "ni fa saboda wutar da Yayanki ya hada min yan kwanakin nan, kwalwata bata gane maganganu masu baki biyu. Don haka ki daina bani a dunkule kawai ki fito ki min magana kai tsaye don bana fahimtarki".

Itama ta harareni, tace "shi wanda kike likewa din, kina da tabbacin zai rike ki kamar yadda kike hange ne? Kin kuwa san waye Dr. Na Abba? Shekarunshi talatin da biyar, aurenshi bakwai Na'ilah! Aure bakwai! Amma yanzu bashi tare da mata ko guda daya sai 'ya'ya kashi-kashi dake gaban mahaifiyarshi wadanda matanshi suke ajiyewa idan suka rabu. Kin san me yake hada shi da matan har su rabu? Kika sani ko yana da wasu halaye da basu dace bane shi yasa? Kina da tabbacin ke idan kika aure shi a hakan, zaki zauna a gidanshi ne? Wallahi ina jiye miki yin dana sani Na'ilah".

Nace "na farko ba ni na like mishi ba, idan da wanda ya likewa wani a cikinmu to shine. Sannan nasan da labarin hakan ai, kawai mutane ne da basu rabuwa da tashin zaune-tsaye. Kika sani ko matan nashi ne masu halaye marasa kyau? Idan ma ba hakan bane, wai meye ruwan mutane ne da rayuwarshi iye?".

Janan ta daga baki cike da mamakina, tace "wai lafiyarki lau kuwa? Kin ma san abinda kike fada ne? Auren mutumin wannan da zaki yi sunan shi gudun gara, kin guji auren mai mata kin fada gidan mai 'ya'ya. Yo ba gwara auren mai matar da kika sani ba sau dubu akan wanda baki sani ba? Kodayake, rayuwarki ce ai. Kiyi duk yadda kike so da ita. Daga yau na daina yi miki magana game da Yaya Bilal in Allah ya yarda. Kiyi duk abinda kike ganin shine daidai a wajenki, jiki magayi!".

Ta juya ta wuce abinta, ni kuma na bita da kallo na wasu lokuta, kafin na bi bayanta da sauri ina kwala mata kira.

Da yamma Yaya Mudatthir ya kirani, Anty Sailu ta haifo yaranta maza biyu.







🙏🙏🙏🙏










*☆⋆29⋆☆*





"Yanzu yaushe kike tunanin zamu tafi wajen sunan ne? Ina ganin kamar mu tafi Talata ko? Ya kike gani?".
Janan take tambayata a washegarin ranar da aka yi haka, bayan mun dawo daga masallaci.

Nace "zaki je ne?".
Ta dan yamutsa fuska cikin nuna alamun rashin jin dadi, "ban gane ba? Kina tunanin ba zan je bane ko me?".
Nace "kinga, ni fa ba cewa nayi ki hayayyako min bane. Nasan Yayanki da protectiveness dinshi, ban sani ko zai barki kije bane, shi yasa".

"Wannan kuma matsalar mu ce ni dashi, don't you think? Kawai ki fada min lokacin da kike ganin yakamata mu tafi!". Ta fada a dan zafafe, har sai dana kara kallonta cikin mamaki.

Naja tunga na juya ina kallonta tare da kama kugu, nace "ni fa na kasa gane miki ne, tun da kika zo yau kike hade min girar sama data kasa. Na miki wani abu ne?". Duk yadda naso inyi masking damuwar data lullubeni, na kasa. Janan ita ce mutum daya kacal da duk duniya nake ganinta kamar jinina, kai wasu lokutan ma fiye da jinina. Ita ce kuma kadai nake ganin duk duniya, babu abinda ba zan iya sadaukar mata ba. Sai dai banyi tunanin sadaukarwa zata zo da consequences kamar wannan ba, wannan shine abu dayan da ba zan taba iya sadaukarwa ba. Don haka nake iyaka bakin kokarina wajen ganin cewa ban biye mata mun raba kai a tsakiyar titi ba, nasan cewa zuciyarta cike take da haushina dankar. Amma na fara kaiwa bango.

Tayi ajiyar zuciya, kanta yayi kasa cike da nuna nadama, "am sorry... Kawai na kasa wrapping kaina akan abubuwan da kike yi ne. Kin san cewa na damu dake, bana so ki aikata abinda zai zo ya zame miki dana sani daga baya wallahi. Why not Yaya Bilal kam? Kinga bayan mun bar nan, babu ruwanmu da tunanin rabuwa, zamu sake zama tif da taya, mu zama yan uwa na hakika".

Na dan sosa saman hancina cikin nuna alamun gajiya da zancen wannan, kamar ba ita bace take ihun maganar wannan ba zata sake hada mu ba jiya-jiyan nan.
Nace "Janan kenan! Wai ke a tunaninki zan iya jera kafada ne da matan Yaya Bilal muyi kishi dasu? Ki dube su fa ki dube ni, me zan nuna musu bayan bakar fata da tsaurin ido? Yadda yake da mata fararen nan tubarkallah, kamar ka taba jini ya fito, ban san me yake nema a wajena ba".

Janan ta kwashe da dariya, tace "babe! Wani lokacin shirmen ki dariya yake bani wallahi. You are very shallow, God! To an fada miki farin fata shine auren? Shi kanshi Yayan idan zan iya tunawa, ai ba fari bane. Allah wallahi ina shawartarki ni dai, ki sake zama kiyi tunani. Har ga Allah ba wai don Yaya yana Yayana bane, amma da ace shi wanda kika kafewa din kina son shi, kuma zai iya rike ki cikin mutunci, wallahi da baki kara jin bakina cikin maganar nan ba. Saboda ba karamin bata min rai kika yi jiyan nan ba".

Nace "kiyi hakuri", cikin sanyin murya. Jiyan yini nayi cike da damuwar bacin ran dana haddasa mata. Sai dai hakan fa bai yi kusa daya sanyayar min da gwiwa ba. "Amma wa yace miki bana son Dr. ne? Kina tunanin zan iya amincewa da auren wani bayan bana son shi? Kawai zama da kishiya ne baya cikin abubuwan da zan iya yarda Jan".



"Ke dai kawai ki ce, tsoron matan Yaya kike yi. Kina tsoron kiyi hadaka dasu, ki dinga challenging dinsu, suna challenging dinki, kina tsoron may be, you'll lose...". Ta fada cike da confidence, kamar tana da tabbacin abinda yasa nake gudun auren Yaya Bilal din kenan.

Nayi dariya da daga jin ta kasan bata kai zuci ba, nace "Jan kenan. Kin sanni sarai da tarar aradu da ka, sai dai wannan aradun tafi karfina, idan na dauketa tarwatsa ni zata yi. Maganin kada ayi, kada a fara. Gwanda in zauna a inda Allah Ya ajiye ni, kada in kai kaina inda zan hallaka!".

Da alamun ta fara gajiya da kokarin sanya ni fahimta da take ta kokarin yi tunda zancen wannan ya taso, tayi kwafa, "shi yasa zaki gwammace ki cuci kanki kenan akan ki bi zuciyarki? 'Cause let's face it, kina son Yaya Hilal, ni nasan wannan. Yanzu kin gwammace akan wani dalili naki na daban, wanda ba na Allah da Annabi ba, ki tauye zuciyarki da rayuwarki?".

Na daga kai na kalleta sosai, cikin girgiza kai, "baki san abinda na gani ba Jan, baki kuma dandana abinda na dandana ba, ba zaki taba fahimta ba... Ina kallo kiri-kiri ba zan jefa kaina inda nasan takaicin miji ko kuma na matansa ne zai kashe ni ba, ko kuma duka. Ba zan iya ba!!". Na kara maimaita mata, don tasan cewa da gaske nake, kuma ba zan canza maganata ba.

"To amma idan fa shi wanda kika kafe zaki aura din, shima yazo zai kara aure daga baya?".

Nayi shiru cikin tunani, lokaci zuwa lokaci ina irin wannan tunanin, sai dai har yau akan mafita daya nake sauka, "sai ya zaba ko ni, ko ita!".
Maganar ta fito tun daga kasan zuciyata har cikin bakina, babu wata tantama ko fargaba.

Ta zare ido cikin mamaki, ta daga baki zata yi magana, nayi gaggawar katseta, "na san abinda kike kokarin yi Jan, maganar gaskiya zan fada miki, itace ki daina bata yawun bakinki. So kike yi kiyi provoking dina, ko kiyi convincing dina, koma dai wannene daga ciki ba zai yi aiki a kaina ba. Kin san hali na sarai. Zama da kishiya daya ma bai cikin tsarina, Allah ya gani, balle kuma mai mata har biyu? Not a chance! Ba wai ba zan yi bane, ba zan iya ba! Don haka gwanda ma kiyi hakuri kawai, mu canza magana, kafin rayukanmu su zo su baci a banza!".

Maganar da nayi ta sosa mata rai, sai dai tasan kamar yadda nace, idan ta kafe akan wannan maganar, lallai rayukanmu zasu baci. Don haka ta girgiza kai kawai, "Allah ya ganar dake" kadai ta iya furtawa.
Nayi murmushi ina kai gorar yoghurt din dake hannuna baki, "Ameen".
Ban nuna mata na kula da kallon da take min ba na takaici da ban haushi, abu daya na sani, ba zan taba canza magana, ra'ayi, ko tsari na ba. Ba zan taba zama da kishiya ba!!.

Janan ta juya taci gaba da tunkarar pediatric ward bayan wannan, na bi bayanta da sauri tare da sankala hannuna bayan wuyanta, ina kallonta cikin kokarin ganin na dan yi lifting din mood dinta.
"Come now Jan, kada ki bari wannan maganar ta shiga tsakaninmu mana, shi yasa seriously maganar nan does not appeal to me that much. Haka kike so inje in auri yayan naki, idan muka yi fada ki dinga goyon bayanshi?".
Na fada cike da tsokana.

Janan tayi dan murmushi kawai, "Na'ilah kenan. Ni nasan ko hakan ta faru babu ta yadda za ayi in juya miki baya, ko mai zai faru kuwa... Yanzu mu bar wannan maganar, yaushe kike ganin yakamata mu tafi?".

Na dan sauke ajiyar zuciya cike da jindadin ta bar maganar, nace "kin san fa da kyar ne su bari mu tafi har na kwana hudu Janan".

Tayi yar dariya, daidai lokacin da muka shiga cikin ward dinmu muka wuce nursing station kai tsaye, tace "mu masu uwa a gindin murhu? Ango guda fa garemu a cikin wajennan, Allah na tuba ko wata ne ai ba zamu samu wata matsala ba".

Na jefa mata harara cikin wasa, nace "amma kinsan bana using mutane to my advantage ko?".

Tana shirin bani amsa, muka ji gyaran murya a gefenmu, muka daga kai. Dan halas dinne a tsaye a gefenmu, ni da Janan muka gaida shi ya amsa da murmushi akan fuskarshi from ear to ear, idanunshi a kaina yace "amaryata!".

Yadda kasan saukar aradu haka naji kalmar, wani irin vile feeling dana ji ya taso min daga can cikin cikina ya makale min a makoshi, yadda kasan zanyi amai. Na daure na hadiye shi, na kakaro murmushi duk da ni a karan kaina ban ji alamun murmushin ba. Nace "Dakta!".

Ya dan girgiza kai, "gaskiya zamu zauna muyi magana akan wannan sunan Na'ilah dear. Amma wannan zama zamu yi na musamman, ya kike?".

Na amsa a tausashe, duk da cewa can kasan zuciyata ji nake kamar ana tafasa min ita. Lallai idan aka cigaba da tafiya a haka, akwai matsala.

Ya jima anan muna yar hira dashi, Janan tashi tayi ta bamu waje. Rabin hirar sama-sama muka yi ta saboda hankalina baya tare da ni. Har sai daya kai ga tambayata lafiya? Na mishi karyar kaina ne yake ciwo. Nan da nan ya rikice, ya fara watso min tambayar ina bukatar ganin likita ne? Nace mishi a'ah, nagode.
Ranar da wuri muka tashi saboda ciwon kan da nace mishi ina yi, hasalima a motar shi ya kaini har gaban hostel dinmu, ya hado ni da tulin magunguna da yoghurts. Sai dai duk abinnan da rawar jikin nan da yake yi, ban ji wannan so da kaunar da nake ji ba a duk lokacin da Yaya ya nuna min kulawarshi ba.


Da kyar muka samu suka barmu zamu tafi ranar Laraba, shima sai da Dr. Na Abba ya sanya baki sannan.

Ranar larabar, da kanshi ya kaini har tasha inda zamu hau mota, muna zuwa muka hadu da Janan itama zuwanta kenan.
Muka yi sallama da Dakta, ya hada ni da dubu ashirin, goma muyi kudin mota, goma kuma in ba maijego ta sai wa yara kwalli. Da kyar ma dai na amshi kudin sai daya fara nuna alamun bacin ranshi sannan na amsa na mishi godiya. Muka hau mota muka tafi.

Motarmu ta samu matsala can wajejen Hadejia, gyaran da aka tsaya akan yi yasa bamu isa cikin garin Gashua ba sai karfe tara na dare. Yaya Mudatthir ne da kanshi yaje ya dauko mu daga tasha kamar yadda ya saba a yawancin lokuta. A gidan Malam muka sauka.

A gurguje muka yi wanka muka dan ci abinda aka ajiye mana, daga haka muka bi lafiyar katifa.

Washegari muka yiwa gidan suna tsinke. Yara sun ci sunan Malam da sunan Mahaifin Sailuba din.
Yinin nan cur haka muka yi shi cikin kujiba-kujiba, da kai da kawowa. Mutane ne mu na dangi, wadanda suke da son zumunci da karah. Taron da sunan Sailuba yayi, da irin alkhairan da suka samu ita da 'ya'yanta kadai ya isa ya tabbatar maka da hakan. A gidanta muka kwana ranar, saboda bayan watsewar yan taron suna, mun zauna gyara mata gidan har zuwa tsakiyar dare. Sai hakura ma muka yi muka bar wasu ayyukan zuwa washegari.












*☆⋆30⋆☆*




Dogon salatin da Fatsu ta ja ne ya tashe ni daga dan barcin daya fara daukata. Sai da daren nan muka dawo daga gidan sunan, bayan mun ci abinci mun dan kimtsa, muka yi sallah. Muna gamawa Janan ta fita waje inda Fatsu take zaune tana sak'arta, ni kuwa na kwanta akan abin sallar muna waya da ango na to be, wanda bamu jima akan wayar ba muka yi sallama saboda ciwon kai, gajiya, da barci da suka lullube ni (don dai kawai ya kyale ni). Ban san ma barci ya daukeni ba sai da naji wannan salati.

Na zabura nayi waje a sukwane, dankwali a hannu. A tsakar gida na samesu zaune akan tabarma, hasken wuta da aka kawo da yammacin nan ya haskake wajen. Na kallesu a rikice, nace "lafiya, me yake faruwa ne?!".

Fatsu da take tafa hannuwa, cikin salati har yanzu ta kalleni kamar na bullo wasu kawuna daga jikina. Na bisu da kallo ita da Janan cike da mamaki.

Sai data gama salatinta da sallallami sannan ta dakata, ta kama haba tana girgiza kai, tace "oh ni jikar su! Na'ilah wace irin shiririta ce nake ji haka? Kanki daya kuwa?".

Na fara raba kallo tsakaninta da Janan, fuska na bayyana tsananin mamaki da nake ciki. Nace "wai me yake faruwa ne? Kin sanya ni a duhu!".

Ta min dakuwa da hannuwanta biyu, "amshi nan ja'irar kawai! Ke dai wallahi baki ji dadin halinki ba. Dama wannan dan banzan ra'ayin rikau din naki yana nan? Nayi zaton duk yarinta ce ta janyo haka. To wallahi bari kiji, ba dani za ayi wannan haukan ba. Ina Yayan naki yake ne? Bari yanzu a kira min shi yazo!".

Ta fara neman wayarta tana cigaba da mitar dana kasa fahimtar abinda take cewa.
Na daura dankwalina tare da zama a gefen Janan da tayi tsumu-tsumu.
Nace "wai ni akan menene kike ta wannan fada ne kam, Fatsu na?".

Ta hararoni da duka idanuwanta, dama gasu tubarkallah, manya ne. Tace "gidanku nace! Wato ma baki san akan menene nake miki magana bane? To akan wannan yaro Yayan wannan yarinya da yake nemanki ne, kika badawa idanunki toka wai ke baki auren mai mata. Ba'a auren aka auri uwaki? Ko a gidanku don iyayenki mata nawa ne a ciki? To bari kiji in gaya miki, tun ma kafin tafiya tayi nisa, ki sallami wannan dan dukurkushin yaron da yazo nan. Ni dama tunda na ganshi naji raina bai kwanta dashi ba".

Duk da haushin Janan da naji ya ciko ni, hakan bai hana ni kwashewa da dariya ba, itama Janan ina ji ta saki dariyar. Nace "ji Fatsu don Allah, wai dan dukurkushi. Idan baki son mutum bai kamata ki bata mishi suna ba wallahi".

Ta dauki zaren da take saka dashi ta jefe ni dashi, "gidanku! Wato ke abin dariya ma ya baki kenan? Bari dai ki ga...", ta komawa neman wayarta, tana ganinta ta mikawa Janan ita, "yauwa yar nan lalubo min Mudan ki kira shi, ce mishi yazo yanzu-yanzu".

Dan halas din, kafin Janan ta ma lalubo lambar shi, sai gashi ya kwaro sallama ya shigo. Fatsu ta ware hannuwa kamar wadda zata rungume shi, na hau danne dariyar data taso min despite haushi da tsoron abinda zai je ya dawo daya cika min ciki. Fatsu ta harareni, ni kuma na harari Janan. A raina ina saka kalar rashin kirkin da zan mata idan muka samu muka kebe. Wato da biyu tazo Gashua kenan? Zata yi bayani ne.

Yaya ya samu waje ya zauna, shima dai cike da murmushi da kuma mamakin dabiar Fatsu a daidai wannan lokacin.
Yace "me yake faruwa ne anan?".

Fatsu ta gyara zama, "dama kiran ka nake kokarin yi yanzu. Kaji-kaji abinda yake faruwa".

Ta zauna ta zayyane mishi magana da halin da muke ciki da Yaya Bilal yanzu, babu ragi babu kari. Yaya bai ce komi ba tunda ta fara maganar, har ta direta.

Sannan yace, "ni dama nasan da walakin wai goro a miya, nasan tunda ta turo wani akan yazo ya ganmu kamar daga sama, nasan da wata a kasa. Ke yanzu a tunaninki hakan shine daidai a gareki? Ba zaki yi tunani wanda zai fissheki ba Na'ilah?".

Na turo baki gaba, "to ni Yaya wai nace muku ina son shi ne? Abun ai sai yayi min yawa, wai shege da hauka. Da wanne zan ji ne? Da rashin so ko kuma zama da kishiyoyi?".

Yaya ya kama baki, "ni kike fadawa haka Na'ilah? Lallai wuyanki yayi kauri da yawa. To bari kiji in gaya miki, idan ke idanunki a rufe suke, mu namu a bude suke tar, kuma babu ta yadda za ayi muna kallonki ki bi hanyar da bata dace ba kin ji na fada miki...".
Ya hau fada ta inda yake shiga bata nan yake fita ba, daga karshe dai ya kare da, ".. don haka tun ma kafin magana tayi nisa, ki sallami mutumin nan. Mu dukanmu hankulanmu basu kwanta dashi ba, balle me ma zaki yi da mutum mai auri saki? Kina da tabbacin zai

Please Login or Register in order to submit comment