Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

rabi, kaina da yake bugawa kamar ana kwankwasa guduma tallabe cikin hannuwana guda biyu. Dakin babu kowa, Esther ta tafi church, Maimuna kuwa dama rabona da ita tun ranar juma'ah da safe da zan bar daki, ban kara ganinta ba.

Na samu na lallaba da dafa bango na tashi na fita. Ruwan wanka na jona a jikin heater, kasancewar ruwan da aka yi yau da asuba, yasa har yanzu garin sanyi garai. Yana dan yin zafi na je nayi wanka, nayi brush hadi da dauro alwala. Sai dana fara yin sallar walaha sannan na sake dafa wani ruwan a cikin kofi karami, na hada hot chocolate shi kadai na sha. Bayan na sha na balli paracetamol guda biyu na afa a baki na kora da ruwa.

Bayan na gama kin komawa in kwanta nayi, na kuma ki zama in saka tunanin Yaya Bilal da al'amuranshi a cikin raina. Sai kawai na dauki wayata na jona ta a jikin caji ba tare dana kunnata ba, na hada kan kayan wanke-wanke na kulle dakin na sauka kasa nayi.

Bayan na gama na koma dakin, ciwon kan ya dan sauka kadan, amma jifa-jifa na kan ji ya sara min har yanzu. Na bude dakin na shiga tare da maida kofar dakin na rufe. Kasancewar yau students suna ta hutawa kuma safiya ce, wasu kuma sun tafi gida, yasa hostel din yayi shiru babu hayaniya, yadda kasan ma babu kowa.
Na fara da kunna wayata. nasan dai ba zan dawwama a haka ba, komi daren dadewa nasan dole in fuskanci wannan chakwakiya. Ban shirya ba, amma nasan dole ne. Don haka naga gara in fara tun yanzu, the earlier, the better.

Ko minti goma cikakke banyi da kunna wayar ba, ta hau kara. Na saurara da goge-gogen da nake yi tare da tsayar da kira'ar Sheik Minshawi da dan yaro a cikin suratul-Mulk dake tashi daga cikin laptop dina, na dauki wayar. Ganin sunan Yaya Mudatthir na daga da sauri, cike da tunanin ko Anty Sailu ce ta sauka. Sai dai ina dagawa, tun ma kafin inyi magana ya riga ni, yace "wai ni Illo don Allah menene amfanin wayarki ne? Ke kullum aka kira wayarki a kashe? Me yasa ba zaki ajiye wayar kawai ki cire komi nata ba kowa yasan baki amfani da waya?".

Nayi dan murmushi, "Yaya, nasan amfanin wayata ni fa, wasu lokutan rashin caji ne yake sawa idan kun kira kuke ji a kashe".
Yace "kwarai kuwa, ai da yake duk Nigeria baby garin da ake wa kwauron wutar lantarki kamar nan ko?".
Nayi yar dariya, "ni ban ce haka ba. Anty Sailu ta sauka ne?".

Yace "tukuna dai, yanzu haka muna asibiti ma".
Nan da nan naji gabana ya fadi, nace "lafiya? Jikin ne ya motsa?".
Yace "a'ah, amma likitocin sun ce tana bukatar zama a asibitin zuwa lokacin da zata haihu domin su dinga monitoring dinsu ita da babyn. Amma so far dai komi lafiya lau".

Na dan sauke ajiyar zuciya, "Masha Allah, Allah ya sauketa lafiya. Amma nayi fatan ace ina nan yanzu tare daku wallahi".
Yaya yace "to ya zaki yi? Haka karatun ya gada ai. Ina fata dai idan ta haihu zaki zo ko?".
Nace "sosai ma! Ai ko muna exams sai na kansileta nazo!".

Yaya ya saki yar dariya, "ba wani nan. Ke dai kawai kiyi fatan kina free lokacin".
Nace "to shikenan. Ya su Inna? Kwana biyu ma bamu gaisa dasu ba".
Yace "a asibiti na baro ta, ni na dan fito yanzu. Amma idan na koma zan kira ki sai ku gaisa dasu".
Nace "to shikenan, sai ka dawo din".
Yace "babu dai wata matsala ko?".
Nayi dan murmushi a hankali, nace "babu Yaya. Sai anjima". Muka yi bankwana na ajiye wayar.

Aikin da nake yi na komawa, ina yi ina bin kira'ar har na gama. Ina gamawa na fara gyaran wajen da nake. A takaice sai wajen karfe daya na gama komi.
Bayan nayi sallah na fita waje can wajen yar kasuwar su na siyo kayan miya na dawo daki na hada miya na dafa farar shinkafa na ci.

Na dauki system dina na fara aiki akan project din da nake to har zuwa lokacin da Janan ta kira ni, sannan na dakatar da aikin na dauki wayar. Bayan mun gaisa ta watso min tambayar lafiya ta lau dai ko? Na kada idanu kamar ina ganinta, "ehh, ga wanda ya kwana ya wuni cikin tashin hankali da damuwa da rashin barci har da karin ciwon kai, lafiyata lau Jan. Ina fata kinyi kin tashi kin kuwa wuni cikin koshin lafiyata?".

Janan tayi yar dariya, "ai daga ji ma babu tambaya lafiyarki lau, ba sai kin janyo min wani dogon bayani ba. Ya karatu, ina fata dai kinyi ko?".
Na dan saci kallon tulin jotters da textbooks dana fiddo dazu wadanda suke jiran in daga su, tare da sauke ajiyar zuciya lokacin dana tuna akwai fa sauran gingimemen aiki a gabana. Nace "ban fara ba wallahi, amma anjima da yardar Allah zan fara tunda dama revising ne kawai zan yi".
Tace "hummm, nima hakan take. Allah dai ya bamu sa'a". Nace "ameen".

Tayi shiru, hesitating, banyi kokarin katseta ba ko tambayar lafiya, nasan tunda naji haka akwai magana da take son muyi, wadda kuma bata wuce ta mutum daya. Sai da tayi radin kanta tace "me zai hana ba zaki saurari Yaya ba don Allah? Ko sau daya ne Janan, ya cancanci wannan damar daga gareki".

Nayi shiru ina sauraronta, sai data dire aya sannan nace a hankali, "dalilin kenan da yasa kika kira ni dama? Saboda Yaya?".

Itama ta danyi shiru kafin tace "wai me yasa kike cewa haka ne Na'ilah? Ke kinsan cewa tsakanina dake ai babu wannan abin, wallahi jin ki nake kamar yar uwata ta jini, sai dai shima Yayan ina jin shi a cikin jinin jikina. I just want what's best for you Na'ilah, shine kawai!".

Na san duk abinda ta fada hakan take, idan kuma da kunya da kara, bai kamata in watsawa dan uwanta kasa a ido ba, sai dai bana tunanin zan taba iya wannan abu da Janan take kokarin sanyowa, ba zan iya yin wannan karar ba.
Nayi kasa da murya, cikin tsananin son yi bayanin da zata fahimta, wanda kuma ba zata kullace ni ba, nace "Janan... Ke kinsan abinda yake damuna, kin kuma fi kowa sanin yadda nake kin wannan akidar, don haka don Allah don Annabi Jan, ki taimake mu ki daina sako wannan maganar. Kince you just want what is best for me, barin wannan maganar shine mafi a'ala a gareni, don haka don Allah mu daina yin ta kawai. Don Allah kice min kin fahimce ni?".

Tace "na fahimce ki, sai dai Na'ilah, wannan fa ba karamar magana bace ko kuma maganar wasa da zaki ce a barta kamar bata taba faruwa ba. Yaya ma ba zai taba kyaleki ba in gaya miki gaskiya, shirun da kika ga yayi kawai ya baki iska ne ki hada tunaninki waje daya. Ina ga da kin hakura kun yi magana, kiji abinda zai ce mikin".

Na fara gajiya da maganar wannan, tun jiya muke nanatata kamar cin kwan makauniya, cikin nuna alamun gajiya da maganar nace "kamar yadda nace miki, kawai mu bar maganar nan. Babu wani abu da zamu tattauna tsakanina da Yaya Bilal, ke kin sani. Ba zan taba mika wuyana a sare shi ba alhalin ina cikin hankalin kaina, haba Janan, idan har kin tabbatar kina so na kuma kina kaunata, bai ma kamata ace kina nema kiyi convincing dina ba koda wasa".

Itama cikin nuna alamun gajiyawa tace "whatever Na'ilah, ni dai iyaka shawarar da naga zan iya baki kenan. A gani na idan kuka yi maganar, kika yi mishi bayani, zai iya ba zuciyarshi hakuri ya nemi daidai dashi wadda zata iya zama dashi da matan shi tunda ke kin ce baki iyawa. A ganina kenan. Sauran kuma, Yana gareki. Dabara ta rage ga mai shiga rijiya, sai mun hadu a asibiti gobe!". Ta katse wayar.
Na bi wayar da kallo. Daga jin yadda muryarta ta dan daga, ranta ne ya fara baci. Ban yi kokarin sake kiranta ba, na maida wayar na ajiye. Bana tunanin wani abu zai iya canza min kudirina, ciki kuwa har da fushin Janan.
Na fahimci kaunar da take yiwa dan uwanta ce ta haddasa hakan, sai dai me yasa ni ba zasu fahimceni ba? Me yasa ba zata yi kokarin fahimtar dalilina ba??!.
Nayi kokari na kauda tunanina daga kan wannan magana na ci gaba da abinda nake yi.

Sai bayan la'asar sannan na fita karatu. Har aka kira magriba ina can, sai masallaci naje nayi salla. Akan hanya na tsaya na sayi doughnut da yoghurt, na koma class. Sai wajen karfe goma na koma daki. Ina komawa ko kayan jikina ban iya cirewa ba na zube akan katifa saboda barcin daya cika min ido.



*


Washegari kuwa garas na tashi, bayan nayi sallah na fara duk wasu al'adu dana saba kafin in fita zuwa asibiti. Jikina a dan sanyaye yake saboda nerves din jarabawa, kodayake nasan kusan kowa ma haka yake ji, an riga an saba. Na shirya a nutse, ban dora abin karyawa ba saboda azumin sitta shawwal da nake yi, zuwa gobe zan gama gabadaya in Allah ya yarda.

Akan hanyata ta zuwa venue din da zamu yi jarabawar, wayata ta fara pinging alamun shigowar message. Ina dubawa naji gabana yana dukan uku-uku, Yaya ne. Kin dagawa nayi, ina tsoron in daga in karanta abinda zai hana ni sukuni bayan ina da muhimmmiyar jarabawa a gabana.
A kalla kafin in karasa venue din, ya kara turo wasu sakonnin kamar guda uku haka. Na tsaya na bada ajiyar wayar wajen securities bayan na kasheta, sannan na shiga ciki.

Seat dina yana kusa dana Janan ne, yadda muka rabu da ita jiya nayi tunanin ko kallon arziki ba zan samu daga gareta ba, sai ta bani mamaki data haskeni da murmushin man nata, ta dan matsa kadan yadda zata bani waje sosai tana cewa "sai yanzu? Wato kema kin koyi makara ko?".
Na dan saki murmushi a tausashe, duk da yanayin da nake ciki, sai naji raina ya dan yi sanyi, na zauna kusa da ita, "ai kin san zama da madaukin kanwa...".

Tayi yar dariya, "idan ma dani kike, bani na goga miki ba, can zaki je ki nemo wanda ya goga miki yarinya!". Muka yi musayar murmushi.
Ba abin mamaki bane ga halayyar Janan, sanyin zuciya irin nata da kawar da kai har kullum shine abinda ya tsananta tsayin abotarmu da ita. Ina girmamata saboda hakan.

Muka fara revising ya junanmu gami da tambayoyi game da abubuwan da muka karanta, har zuwa lokacin da masu tsaron jarabawar suka shigo. Da misalin karfe tara kenan.
Jarabawar ta daukemu awanni biyu da rabi cur, kusan tare muka gama ni da Janan amma ta riga ni fita. Na mika takardar bakina dauke da addu'o'i iri-iri, idan nayi rashin sa'a jarabawar nan ta dawo min ban san ya zamu karge da Baba ba.

A bakin kofar wajen na sameta tana jirana, na amshi wayar hannuna, muka jera ni da ita hannu da hannu har zuwa cikin hostel. Allah ya taimaka yau sun daga mana shiga cikin asibiti har sai zuwa gobe. Muna ta tattaunawa game da jarabawar har muka shiga hostel din.
Muna shiga ta cire uniform din jikinta, nima na cire nawa. Na ciro mata rigar shan iska, doguwa mai wadataccen fadi, nima na saka shigenta, muka kwanta akan katifata, sai a lokacin na bata labarin Anty Sailu fa tana asibiti, ta jinjina lamarin tare da cewa zata kira ta mata sannu.

Ba karamin dadi naji ba da bata kara tado min zancen Yaya Bilal ba. Again, nan ma ta bani mamaki. Janan ba irin mutanen nan bane masu saurin sakin abu ba, idan ta sako abu a gaba ko kuma wata magana, bata saki don wasa har sai ta cimma nasara. Shi yasa yanzun nake ta kaffa-kaffa da ita, ban san ko me take tunani ba a cikin ranta.

Sai da muka yi sallar azuhur bayan mun koma mun kwanta, sannan na bi bayan sakonnin da Yaya ya turo min dazu, hannuna har rawa yake yi.
Na farkon cewa yayi; _'Hey, you okay?'_

Na biyun kuma: _'Nasan cewa ba ta haka ya kamata in tunkare ki ba, nayi kuskure. Should've thought about it more kafin in tunkare ki ta wannan hanyar, saboda haka ne nake baki hakuri!'._

Sai kuma, _'Baby, na san cewa kina ji a cikin ranki kamar ban kyauta miki ba, ko kuma wasa nake miki da hankali. Ina tabbatar miki da cewa ba haka bane, please let me explain myself!.'_

Akwai kuma wanda na kula ya sake turowa nan da mintuna sha biyar da suka wuce: _'Please baby, da gaske ba zan iya cigaba da zama a haka ba. Nayi kokarin ganin cewa na baki cikakken lokaci domin ki samu kiyi tunani akanmu, I know it's sudden. But that's it! I can't do this anymore.. Let me see you again, please? I promise zan miki bayanin duk abinda kike son ji, kinji baby na?!'_

Ina gama karanta wannan naji wani abu mai zafi ya daki zuciyata, idanuna suka fara min zafi alamun kwalla ta fara taruwa. Na lumshe idanuna tare da kwantar da kaina akan pillow. Yaya Bilal ya riga ya bata rawar shi da tsalle, koda yake tun daga farko dama bashi da wani chance a wajena, amma me yasa raina yake kuna idan na tuna cewa zamu rabu dashi har abada?! Me yasa nake jin kamar ina gab da rasa wani muhimmin bigire na jikina ba? Ko dai zan bi shawarar Janan ne, inyi rethinking wannan bakon al'amari?.
Nayi gaggawar girgiza kaina, inaa! Ba zai yiwu ba!.

A hankali na sake bude idanuna, har yanzu hasken kan wayata bai mutu ba. Na dinga scrolling sama ina kara karanta sakonnin da muka dinga canzawa a tsakaninmu, kafin in san ko shi din wanene. A da, da ban san ko shi din wanene ba, kawai ina jinshi acan kasan raina ne, yeah, ina son shi, kuma ina kaunar shi, amma yanzu dana san ko shi din wanene finally, sai nake ganin komi daban, at least yanzu idan ina tunaninshi zan ga fuska kuma zan ji murya sosai. Sai dai nasan koma menene nake ji game dashi, dole ne in manta dashi. Ko za'a yi me, nasan cewa ba zan taba amincewa da Yaya Bilal ba.

Saboda haka na kashe hasken wayar, na ajiyeta a kusa dani na rufe idanuna cike da fatan barci ya dauke ni a lokacin.


***


"... Na'ilah?!".

Da sauri na bude idanuna, Janan na zaune kusa dani tana kallona cike da yar damuwa a fuskarta. Na sauke idanuna akan agogo, naga har karfe hudu da rabi tayi. Na tashi zaune ina salati. Tace "har an kira sallah, ki tashi muyi mu leka waje mu ga abinda zamu lalubo na shan ruwa, yau anan zan sha ruwa".

Na mike tsaye, ko don barcin da nayi ne? Jikina naji yayi min wani nauyi. Na tashi na dauki hulata na fita, idanun Janan a kaina. Nasan dalili, mafarkin da nayi ne wanda ta tashe ni a daidai lokacin da bana son tashi, daidai lokacin da nake kwadayi, kuma nake marmarin ganin wannan mutumi da duk duniya babu wani mahaluki da yake kada min sassan jiki kamar shi ba. Amma kullum anan nake tsayawa, ban taba ganin fuskarshi, muryarshi ma haka nan nake jinta sama-sama kamar ba a kusa dani yake ba. Wani lokacin ni nake tashi a karan kaina, watarana kuma sai ayi arashi wani ne a kusa dani zai tashe ni. Koma dai menene, na zubawa sarautar Allah ido ne kawai domin ni kam na kasa gane wannan abu.

Bayan munyi sallah, muka fita zuwa kasuwa muka sayo abubuwan da zamu bukata, muka dawo muka yi yam balls da kunun aya. Har muka gama shan ruwa da ita bata yi alamun sake tado maganar jiya ba, don haka naji na fara relaxing. Cikin annashuwa kamar yadda muka saba muka sha ruwanmu, na tashi na rakata ta hau mota na dawo, na tattare kayan da muka bata na ajiye a inda nake tara kayan wanke-wanke, nayi sallar isha'i.

Daga nan common naje nayi kallo. Karfe goma na dawo daki. Na samu Maimuna da Esther a daki, na musu sannu suka amsa nayi shirin kwanciya barci na kwanta.
Wani irin sad feeling da naji ya rufe ni a lokacin, da ace da ne, da yanzu muna nan muna zuba soyayyarmu ni da Muhammadu na. Me yasa Yaya Bilal ne zai zama Muhammad? Mai yasa ba wani mutum ne daban ba, wanda bashi da mata daya balle mata har biyu? Me yasa? Wai me yasa abubuwa suke zo min ne a hagunce?
Daren ranar yau dai da kuka shabe-shabe nayi barci.















*☆⋆24⋆☆*






Ni a karan kaina nasan cewa idan nace bana yin kewar Yaya Bilal to karya nake yi, ina kewar shi fiye da tunanina. Sai dai wani sashe na zuciyata yasan cewa yaudarar kaina kawai nake yi. Ko zan mutu, ko zuciyata zata tsattsage saboda damuwa, zama da Yaya Bilal ba zai taba zama maganin hakan ba. Don haka nake iyaka bakin kokarina wajen ganin na danne duk ma wata kewa, so da bege da nake ji game dashi. Nasan cewa na dan lokaci ne, nan da lokaci kadan zan daina.

Sai dai duk wanda ya ganni, yasan cewa ina cikin damuwa. Idanuna kadai sun isa shaida, saboda bana samun barci mai yawa. Ko nayi, saboda tsananin sanya maganar Yaya Bilal da matanshi a cikin raina, haka zanyi ta mafarkinshi. Watarana ma har da matanshi, wani lokacin kuma barcin ne ma gabadaya baya zuwa.

Yanzu ma muna zaune a cikin ward ni da Janan da wata Aisha, a ranar alhamis kenan. Janan da Aisha ne suke ta hirar su, ni kuwa hankalina yana kan wata calender dake rataye a wajen. A zahiri idan ka kalleni, zaka yi tunanin jerin magungunan dake cikin takardar nake karantawa ko kirgawa, amma a hakikanin gaskiya hankalina ma kwata-kwata baya tare dasu. Tunani nake, tun wannan text din da Yaya Bilal yayi min ranar litinin, har yau bai sake kirana ba, kuma bai sake turo min wani sakon ba. Ta wani bangaren naji dadin hakan, so nake ya barni, ya kyaleni, idan ma da hali ya manta dani. Duk da cewa nasan har abada zan dinga kallonshi da wannan maganar, ba zan taba mantawa ba, sai dai in binne abin acan karshen bangon zuciyata.
Ta wani bangaren kuma tunani nake, dama kirarin da yake akan cewa yana sona duk kuri ne da cika baki? Har ya manta dani kenan? A yadda yake nunawa dinnan, nayi zaton zai zage damtsensa ne har sai inda karfinsa ya kare. Amma dana fara irin wannan tunanin, sai inyi gaggawar katse kaina, idan ma ya ci gaba da bibiyata babu abinda hakan zai sa sai ma kara min ciwon kai da damuwa da hakan zai yi. Don haka gara ma yaje can ya karata da matanshi ya fiye min alkhairi. Shima wannan kuri ne kawai da zuciyata take yi, can can kasanta, tana fatan ace ba haka bane.
Kai wasu lokutan sai inji da ace ana cire zuciyata a sake sabuwa, da na garzaya zuwa ko'ina ne na canza tawa. Komi nisan wajen kuwa.

Nayi nisa cikin tunani, ban ankara ba sai ganin Dr. Na Abba nayi a kaina yana snapping hannuwanshi a fuskata. Nayi firgigit! Kamar wadda ta tashi daga barci na kalleshi.
Yayi dan murmushi, "haba Nas, wannan dogon tunani haka har ina? Idan dai don nine kada ki damu, gani a gabanki. Ba zan matsa ko nan da can ba har sai kinyi min iznin hakan!".

Ban san sanda na saki dan murmushi ba, Allah ya zubawa mutumin baiwar iya ba mutane dariya koda mutum bai shirya ba kuwa, ko kuwa ni ce kadai?.
Yace "haba! Ko ke fa? Ba gashi har kyakkyawan murmushin nan naki ya fito ba? Wallahi ba karamin kyau kike yi ba idan kika yi murmushi!".
Nan ma ban iya daurewa ba sai dana kara yin wani murmushin.

Yace "so what's up? Kwana biyu na daina ganinki anan, nayi zaton ko kin bar ward dinne. Jiya sister Mairo take ce min ba canza ku aka yi. Kin san yanzu evening duty nake yi, ina ga shi yasa bamu cika haduwa ba".
Na dan gyada kai tare da cewa "haka ne kam, ya aiki?".
Yace "Alhamdulillah. Ko kina da yan mintunan da zaki taka min zuwa nan waje Na'ilah? Ba don kowa na shigo da wuri ba sai don ke".

Sai lokacin na kula da cewa yau ba sanye yake da labcoat dinshi ba. Na juya na kalli su Janan da suke yan rubuce-rubuce da danne-dannen waya, amma ni nasan hankalinsu gabadaya a kanmu yake. Na gyada mishi kai a hankali tare da sauka daga kan kujerar da nake, ni dashi muka jera muka fita.
Bai furta min komi ba, nima kuma banyi yunkurin cewa komi ba har muka fita waje. Kaina a kasa yake, ina dai bin sawun kafarshi ne dake sanye cikin takalmi sau ciki, don haka ban san sanda muka isa wajen ajiye motocin likitocin asibitin dake ta wannan bangaren ba, sai dana ji ya ja birki sannan. Ya jingina da jar motar shi 406, ni kuma na tsaya ina fuskantar shi.

Yace "Wato Na'ilah dalilin da yasa na so mu kebance muyi magana dake shine, ina so ne inji inda maganar mu ta kwana ne. Shin, har yanzu kina ganin bani da chance ne a wajenki?".
Na dan yi wuri-wuri da ido, kafin in tsaida su waje daya, murya a shake nace "to ni me zance maka kuma, ina tunanin tun ranar nan na fada maka anyi min miji a gida?".

Yayi dan murmushi, yace "Hmm, Na'ilah kenan! Aka yi miki miji ko kuma kika yiwa kanki miji, kika fada min?".
Nace "kamar yaya? ban gane ba!".
Yace "come on mana, daga jin yadda kike cewa 'ai anyi min miji a gida!', ko dan jariri yaji yasan cewa kin fadi ne kawai don kiji dadin bakinki!".

Ban san lokacin dana kyalkyale da dariya ba, musamman lokacin daya make murya wai shi ala dole kwaikwayo na yake yi. Shima yayi murmushin ya kara jingina da motarshi yana dan murmushi, nayi shiru ina girgiza kai, amma murmushin fuskata bai bace ba.
Yace "da gaske ba. So I'll like it idan kika manta da zancen mijin da ba'a riga an san ko wanene ba, let's talk about us for now. Kamar yadda na fada miki ranar nan, gaskiya kina burgeni. Kuma ina fatan ace zaki bani dama, mu samu fahimtar juna a tsakaninmu. Me kike tunani?".

Nace "magana ta gaskiya ni a halin da ake ciki yanzu likita, babu wannan maganar a cikin raina yanzu. Ina fata hakan bai bata maka rai ba?".
Ya girgiza kai, "ko kadan. Kin san ku mata da jan aji, hakan ba matsala bace a wurina. Zan baki iyaka lokacin da kike bukata, amma ina neman alfarmar dinga yin waya dake zuwa lokacin da zaki sauko?".

Nasan wannan rana ba zata taba zuwa ba, don dai mu rabu lafiya dashi sai kawai na gyada mishi kai. Yayi dan murmushi, "yauwa, nagode. Muje in dan taka miki ko?".
Nayi yar dariya, nace "nayi zaton ni na rako ka?".
Yayi yar dariya, "a'ah, ni na isa? Kawai dai ina so ne mu dan tattauna dake ne a waje dama dai kawai".

Muka sake kwasa muka sake komawa dai, anan ne yake dan fada min tarihin rayuwarshi. Gidansu yana palladan, har kwatance yayi min amma da yake ba sanin unguwar sosai nayi ba ban gane ba. Ya fara min bayani akan irin rayuwar da yayi, da kalar makarantun da yayi, muka koma wajensu Janan.
Muka yi sallama dashi ya juya ya tafi, ni kuma na zauna akan kujerar da nake. Ina zama naci karo da idanun Janan tana hararata. Nace "malama lafiyarki kuwa?".

Tace "ban sani ba. Ni zo ki raka ni waje inje in sayo wani abu in ci".
Ba musu na tashi na bi bayanta, da yake karfe sha biyu da rabi ta kusa, lokacin tafiya sallah yayi. Muka yiwa Aisha sallama muka fita, nace mata "ai nayi zaton kina azumi ne yau".
Tace "a'ah".

Please Login or Register in order to submit comment