Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kafin mu kwanta da dare.
Da asuba tun ma kafin alarm dina ya buga, Muhammad zai kira ni ta waya, nan kira kawai zai yi in tashi, to idan na gama ne zamu yi wayar minti biyar zuwa goma, sai muyi sallama. In shiga wanka in shirya, in karya, in fita. Kafin in karasa ward ya turo min text mai cike da kalamai dadada da zasu sa in yini ina kallon wayata cikin murmushi, ina kara karanta shi over and over, sai in tura mishi amsa. Kafin yamma ta fadi at least zamu yi musayar messages sau uku ko fi, sannan da dare dole ne sai ya kira ni kafin in kwanta barci, watarana ma muna cikin hirar barci zai daukeni sai dai ya kashe wayar in yaji shiru.

Ni kaina nasan cewa na canza, kamar wani abu yayi snapping a jikina ne. Duk wasu makamai da katangu dana sa a jikina, daya bayan daya Muhammad ya bisu ya sassare, kamar basu taba wanzuwa ba.
Wani abu ne da bai taba faruwa dani a tarihin rayuwata, da shekaruna dai-daya har ashirin da hudu a duniya ba. Ban kuma taba zaton zai farun ba. Amma yanzu daya faru, sai nake jin ina zargi da tuhumar kaina, me yasa tun farko ban bar kaina nima naji dadin wannan abu ba? Na dinga takura kaina, ina matsawa kaina? Kodayake, komi yana da lokaci, kuma kamar yadda Janan take yawan cewa, _'idan lokacin ki kamu da so yayi, baki da yadda zaki yi, kina so ko ba kya so, zaki fada tarkon ko, kin sani ko baki sani ba!'._
To yanzun ma ina tunanin abinda ya faru kenan, lokaci na ne yayi. Na kamu da soyayya, soyayyar Muhammad mai zurfi. Zurfin da ya kai naji ina so inyi kugi da karaji, wanda duk duniya da mutanen cikinta zasu ji cewa ina cikin zazzafar kaunar mutumin da ban taba sakawa a cikin idanuna ba!.


* * *



"Kyawunta ace wannan azumi da zai zo, wani mutumin kirkin zai zo ya dauki dubu ko hamsin ce ya baka, ya hada ka da buhun masara, gero, sukari ko rabin buhu ne! Kai ai da kakar ka ta yanke sa'a!! Sai ka nemi inuwa mai ni'ima kawai ka fuske, ka yini tun safe har dare a kwance Malam, babu ruwanka!!".
Wani kwandastan mota da muka hayo daga asibitin Shika zuwa kasuwar Samaru yake cewa. Duk cikin motar aka saka dariya.

Wani mutum daga baya yace "wannan duk mafarki ne kake yi, wanda baya zama gaskiya. Abu mai yawa da zaka samu daga hannun manyan nan shine kwanon masara ko gero, ba'a hada maka guda biyu ma. Sai ka samu wani mai tsoron Allah shine zai kawo wata lalatacciyar dari biyu ya dora maka yace kayi nika. Ai yanzu wannan alherin a tsakanin masu kudi kawai ake yi, ka dauka ka kai gidan mai kudi, shima idan ya tashi yin nashi sai ya maido maka. Su kuma talakawa sai suje su nemo da karfinsu".

Wani ya cafe zancen, "ai sai dai kawai Allah ya kara rufa mana asiri. Wata irin rayuwa ake yi ta danniya da rashin tsoron Allah, mai shi ya dannewa mara shi, masu kudin namu kuma basa taimakon talakawanmu. Kowa kanshi ya sani ba wani abu ba, Allah dai yasa mu dace!". Duk muka amsa da ameen.
Har motar ta tsaya a bakin kasuwar, da yawanmu muka fita daga ciki, wasu suna ta tururuwar shiga, da alamu ranar da ake zabgawa yau ta gama dakar su.

Ni da Janan muka tsallaka titi muka shiga kasuwar. Kasancewar Azumi yana ta gabatowa, ana tunanin nan da kwanaki biyar masu zuwa ma za'a tashi dashi. Shi yasa nace bari in shiga kasuwa in dan yi sayayya da sauran kudin da nake dasu kafin in cinye su.
Mun shiga mun danyi saye-sayen mu, muka fito hannu riki-riki da kaya. A bakin titi muka tsaya, Jan zata tsallaka ta hau bus zuwa PZ ni kuma in matsa gaba in hau wadda zata maida ni asibiti. Kallon motoci, masu mashina, kekuna da ma masu tafiya akan kafafu da keken guragu nake yi suna ta karakaina, kowa harkar dake gabanshi ce ta dame shi.

Janan ta fara daddabata da sauri, nayi saurin juyawa na kalleta, wata mota da take wucewa ta gabanmu wadda dan banzan go-slow din da ake yi ya saketa, nace "lafiya?".
Tace "waccan motar bata miki kama data Umar ba?".
Na kara bin motar da kallo wadda zuwa yanzu ta bace min, yanzu da tayi maganar sai naga irin tashi ce, amma kuma garin Zaria mai fadi, ba lallai ace shi kadai yake da irin wannan motar ba. Ko yanzu da zamu baro asibiti naga wata nurse ta fita a cikin irin motar tashi, wadda har kala bata banbanta su ba. Balle kuma wannan motar dana hango kamar mata da miji ne a ciki? Sannan bugu da kari, Umar yana Kaduna ba Zaria ba.

Dana juyewa Janan wannan bayanai, sai ta gyada kai, tace "haka ne, mantawa nayi". Muka samu ababen hawan suka ragu a lokacin, ta tsallaka da sauri tana min bye-bye, sannan ne nima na juya na shiga bus.





Ranar Juma'ah da wuri na fita zuwa cikin asibiti, kasancewar da wuri na tashi. Ranar tun daga cikin hostel muka fara waya da Muhammad har na shiga cikin ward, sannan muka yi sallama dashi akan cewa zai kira ni kafin ya tafi masallaci.

Har karfe goma na safe babu Janan babu alamunta, hankalina yana bakin kofa, da naji alamun za'a shigo sai inyi sauri in kalli kofar cikin tsammanin itace, sai in ga wani daban. Ganin karfe goma tana shirin wucewa yasa na lalubo wayata daga cikin aljihun wandon uniform dina na kirata cikin faduwar gaba. Hakan bai taba faruwa da Janan ba. Duk son makararta, Janan bata yin fashi, don haka ne naji na damu.

Wayarta tayi ta kara tana katsewa, a karo na kusan uku ne ta daga. Da sauri na fara jero mata tambayoyi, "wai ya ne har yanzu baki zo bane? Baki tashi da wuri bane ko kuma yau kinyi shawarar kin zuwa ne?!"..
Daga farko shiru aka yi, kafin daga baya inji muryar da ba ta Janan ba tace "uhmm, Janan din bata ji dadi bane".

Naji gabana ya fadi, nayi salati na sanar da Ubangiji, nace "lafiya, me ya sameta? Waye kuma?".
Mai maganar yace "Asthma dinta ne ta tashi, sannan Bilal ne". Na kalli wayar cike da mamaki, kwata-kwata muryar bata yi kama da tashi ba, a takaice ma dai muryar bata yi kama data mace ba balle namiji. Amma sai nafi kyautata hakan a matsayin sharrin network kawai.

Nace "Subhanallah! Kuna gida ne?".
Yace "a'ah, muna asibitin Delicate dake bayan gidanmu, kin san shi?".
Nace "ehh, gani nan zuwa". Na kashe wayar da sauri na maida ta aljihu.

Kayana na dauka a gaggauce, na tunkari office din matron din ward din. Na kwankwasa ta min izinin shiga. A gaggauce na mata bayanin abinda ake ciki, nan tace in tafi kawai babu komi, har ma ta kara da 'ki dubata. Sai ranar Monday idan jikin nata ya warware', na mata godiya na fita a sukwane kamar wadda zata tashi sama.
Wata irin wahalalliyar asthma gareta, bata cika tashi ba, amma duk ranar data tashi sai ta jikatar da ita. Shi yasa naji hankalina ya kasa kwanciya, ko tunanin komawa hostel in canza kayan jikina banyi ba. Allah ya taimaka na samu abin hawa da sauri kasancewar ranar Juma'ah ce, kowa yana kokarin ya je inda zai je kafin lokacin masallaci yayi.




~Phewwwwww!!!!!






#F.W.A







*☆⋆14⋆☆*





Halin dana sameta a ciki ya sanyayar min da jiki, gabadayanta ta fita daga hayyacinta don ma sun ce wai a hakan ma tayi dama. Yayan da Anty Sarah kadai na tarar a asibitin, a cewarsu wai Raheemah bata jima da barin asibitin ba. Na zauna a gefen gadon tare da shafa gefen fuskarta cike da tausayi, har ta dan fada, gashi yanayin numfashinta bai gama daidaituwa ba har yanzu.
Muna zaune a hakan har rana tayi, Yaya yake ta shiga da fita daga ofishin likita zuwa inda aka kwantar da ita din. An samu tayi barci, bayan anyi mata allura har aka samu numfashinta ya daidaita.

Da lokacin tafiya masallaci yayi, Yaya ya tafi akan cewa zai turo Raheemah tazo ta zauna damu, sai dai har aka fito daga masallacin, har muma muka yi tamu sallar bamu ga alamunta.
Lokacin daya dawo ina kan sallaya a zaune, Anty Sarah kuma tana zaune akan farar kujera tana jan carbi, ya ajiye ledar take away a gefen gadon, yace "ga abinci kuci, likitan yace zamu iya tafiya gida da ita idan ta tashi".
Anty Sarah tace ta koshi, nima nace na koshi da yake cikina a cike yake.

Karan text daya shigo wayata ne yasa na maida hankalina ga wayar, na duba naga daga Muhammad ne. "Hey baby!", abinda ya turo kenan. Na kara maimaita text din cikin mamakin kalmomin, motsin da Jan ta fara yi ne yasa na wancakalar da wayar gefe na nufeta da sauri. Yaya ya taimaka mata ta zauna akan gadon, gabadayanmu sannu muke jera mata tana amsawa a hankali.

Yaya ya dauko madarar ruwa ya fasa tare da mika mata, ta amsa ta sha kamar rabi ta maida mishi sauran, yace "har kin koshi?", ta gyada mishi kai.
Anty Sarah tace "dama ba lallai ta iya cin abinci yanzu ba".
Yaya ya umarcemu da mu hada kan kayanmu, ya miko gyalen Janan na yafa mata. Da taimakona ta sauko daga kan gadon, ina tallabe da ita a jikina muka fita daga asibitin zuwa wajen da Yaya yayi parking din motarshi. Ya bude mana gidan baya duk muka shige ciki. Bayan ya gama clearing din komi a asibitin, yazo ya shiga motar ya tayar muka tafi.

Yaya Bilal ya kashe motar a ainihin inda suke ajiye motocinsu, farko-farkon shiga gidan, daga nan tafiya ce zaka yi kadan daga bangaren damar ka da zata sadaka da wani zagayayyen karamin garden, grass carpet ne shimfide a wajen, wajen yana da fadi sai kuma bishiyoyin mangwaro, gwaiba, gwanda, ayaba, da sauran kayan marmari dai. Daga gefen garden dinne aka shimfida doguwar hanya da interlocks, kanana masu kyau, itace zata sadaka zuwa bangaren Yaya Bilal. Wadda kuma tayi barin hagu itace zata sada ka da bangaren su Anty Sarah.

Kan Janan yana kan kafadata, wani barcin ne yake kokarin daukarta. A hankali na tasheta, muka fito daga motar. Anty Sarah ta mana fatan Allah sauwake, ta wuce sashenta muna mata godiya. Rabin jikin Janan yana jikina, na tallabota muka wuce saboda har yanzu jikinta babu karfi sosai. Yaya Bilal yana binmu a baya hannu rike da makullin motarshi da kuma ledar take away din da yayi.

Gabadaya mutanen gidan suna falo, wannan karon a zaune suke kawai suna hira sabanin kallo da suka saba yi a yawancin lokuta. Raheemah ce ta fara ankara da shigarmu falon, ta mike tana zuba sannu da zuwa cikin alamun borin kunya, kannenta suma suka mike, "ah.., har kun dawo ashe? Yanzu muke cewa mu tashi mu koma fa! Sannunku, ya jikin?".
Muka amsa musu ciki-ciki, Yaya ya umarce ni da in taimaka mata Janan zuwa dakinta, don haka na gewaye su muka wuce zuwa dakinta. Bansan Yayan yana bayanmu ba sai dana ji karan sake bude kofa bayan na maida na rufe.
Na kwantar da ita akan katifarta, na ja abin rufa na rufa mata daga kafafunta zuwa rabin jikinta, tuni barci yayi awon gaba da ita. Yaya ya miko min ledar hannunshi, yace "ki samu ki zauna kici abinci haka nan, ki zauna ki huta kema".

Na karbi ledar, kaina a kasa, wata irin kunyarshi naji ta lullube ni wanda na rasa dalilin hakan. Nace "to, nagode, Allah ya amfana".
Ya girgiza kai a hankali, wani irin kallo a cikin kwayar idanuwanshi da suka sanya naji jikina ya dauki wata irin kyarma, ikon Allah! Ko dai bani da lafiya ne nima?! Yace "ni ne da godiya Na'ilah! You've no idea how grateful I am right now!".

Subhanallah!! Me ke shirin faruwa da ni ne? Jin fitar sunana daga bakinshi ya haifar min da jin wani irin abu a cikin raina, shin ko mai yasa hakan? Hakan bai taba faruwa dani ba! Sannan muryar Yaya Bilal, yau naji tana min kama da wata murya hallau, matsalar na kasa tunawa ko a ina ne na ji muryar.
Ban san lokacin daya juya ya bar dakin ba, sai karar rufe kofa naji.
Na bude ledar na fito da take away din ciki, guda biyu ne da lemukan fanta suma guda biyu, don haka na dauki daya na ajiye, dayan kuma na barsu a cikin ledar na fita domin in mikawa Anty Sarah nata.

A falo Yaya Bilal ne a tsaye kikam, kamar wani tsohon soja. Su kuma suna lafe akan kujeru kamar wadanda aka kama sun nannagawa sarki garinsu karya. Daga yanayin fuskar shi da take a cune da yadda bakinshi yake kumfa, zaka san cewa fada yake musu, fada kuma bana wasa ba. Tunda nake dashi ban taba ganin fadan shi ba sai yau. Janan tana yawan cewa Yaya Bilal yana da fada, duk da cewa baka sanin fadanshi sai ka mugun tabo shi sannan, to da alamun yau dai an tabo shi.

Ni dai na kada kai na fita. Yau kofar gidan na Anty Sarah a bude take, abin mamaki, na tura kofar na shiga. Tana kicin. Yanayin gidanta da ka shiga kicin zaka fara tararwa, sai falo da kuma bedrooms. Ta dago ta kalleni lokacin dana shiga, nace "kofar a bude take, shi yasa na shigo kai tsaye".
Tace "babu komi, ina tsammanin Mimah ne yanzu shi yasa, ya aka yi?".
Na mika mata ledar hannuna, "dama abincin da Yaya ya kai ne na kawo miki".
Murmushi naga tayi wanda ya bani mamaki, tace "da kin barshi wallahi kun ci, kin ga abinci ma nake shirin dorawa yanzu".
Nace "a'ah wallahi, ai guda biyu ne ya kawo".
Tace "to shikenan, na gode. Ya Janan din?". Nace "ta koma barci", daga haka na juya na fita daga gidan.

Har na koma can, Yaya fada yake yi, "... In fada muku gaskiya ba zan dauki wannan cin mutuncin ba! An fada muku ita yar aiki ce? Ko kuma bata san ciwon kanta ba? Waye bai san tana da asthma ba, da zaku barta tayi aikin da zai tado mata shi?!". Ya dire maganar yana sauke numfashi cikin bacin rai.

Raheemah ce ta samu ta iya magana duk cikinsu, "kayi hakuri, hakan ba zata kara faruwa ba. Ita ce tace zata yi ai...".

Tun ma kafin ta karasa ya katseta, "ke kuma saboda rashin hankali sai kuka barta ko? Na fa san abinnan ba tun yau yake faruwa ba, ina sane, iyaka gudun ruwanku ne kawai nake so in gani. Wallahi Tallahi, kunji rantsuwar da nayi, ba zan yi kaffara ba! Idan makamancin haka ya sake faruwa, gabadayanku sai kun bar min gidana. Kuma daga yau, duk wadda take son yin girki, ta shiga ta girka abinda zata ci ban yi mata iyaka da komi na gidannan ba, amma kun gama cin abincin Janan. Ba zata kara muku girki ba, haka ko tsinke ta tsince a gidannan da sunan shara ko gyara Allah zamanku a gidan nan ya kare! Kun dai ji na fada muku!!". Ya wuce dakinshi fuuuu! Kamar kububuwa tare da maida kofar dakin ya gamtso kamar tashin duniya. Mu kuwa duk muka bi bayanshi da kallo baki a dage.

Maimakon hakan ya dan zame musu darasi, su dan saduda koda na dan lokaci ne, inaa. Tunzura su ma yayi.
Adi ce ta fara jan tsaki, "mtswww, aikin banza! Yo mun taba matseta muka ce dole sai ta mana girki ko aiki? Kashi zamu bata idan bata mana aikin bane? Har da za'a zauna ana zagin mutane akan wata banzar bazara, gidan banza dana wofi! An fada musu mu bamu da gidan iyaye ne da za'a zo ana zaginmu ana mana gori?".

Salama ta cafe maganar, "ke ma dai kya fada. Aikin banza dana wofi, da dai ace bamu da gidan uba ne da sai muji haushi, to mun gode Allah muna da gidan uba, kuma ba a inda ba'a son zamanmu muke zaune ba! An fada mishi mu mabaratan abinci ne??".

Raheemah kuma tana ta kokarin sanya su suyi shiru a dan tsorace, "don Allah kuyi shiru mana!", ko kuma tace "don Allah kuyi a hankali kada ya jiyo ku ya sake fitowa!". Na girgiza kai kawai, wato shi dai mai rai ba'a taba iya mishi. Allah ya kyauta.
Na barsu anan na koma daki. Har yanzu Janan barci take yi. Na duba cikin kayanta na ciro doguwar rigar leshi mara nauyi, na dauki kayan na shiga bandaki na sanya na fito, na sake zama a gabanta.

Har bayan sallar la'asar bata tashi ba, bayan nayi sallah na zauna naci abincin da Yaya ya kawo mana, na maida sauran na rufe dana koshi. Ina nan a zaune naji karan buga kofa, na tashi na bude. Ga mamakina Anty Sarah ce a tsaye da kwando a hannunta, na mata sannu tare da bata hanya ta shiga cikin dakin. Tace "har yanzu bata tashi ba?".
Nace "wallahi har yanzu, kila an hada mata da allurar barci ne". Ta gyada kai idanunta akan Janan din, "Allah ya bata lafiya". Nace "ameen".

Ta min nuni da kwandon data ajiye, tace "ga wannan idan ta tashi sai taci, ba yawa".
Nace "Allah ya saka da alkhairi". Ta amsa tare da tashi ta fita, na bi bayanta na maida kofar dakin zan rufe. Su Raheemah suna falon a zaune har yanzu, ta wuce ta gabansu. Ina tunanin basu cika shiri dasu ba, kila ma hakan ce ta goge mu, ko kuwa wani abu daban? Naga kwana biyu kamar ta dan sassauto.

Sai wajen karfe biyar sannan ta farka, jikinta ya dan yi karfi ba kamar dazu ba. Na taimaka mata zuwa bandaki tayi wanka da ruwa mai dumi. Bayan ta fito na zuba mata abinda Anty Sarah ta kawo, wani irin abu ne tayi da kifi ban ma san sunanshi ba, kamar ta soya kifin, kamar kuma dahuwar ruwa ce, ga veggies da abin yasha sai tashin kamshi yake yi kuwa. Na zuba mata ta samu ta dan ci, tayi sallar azuhur da la'asar da aka yi tana barci. Na ballo magungunanta da aka rubuto mata ta sha, ta zauna a gefen katifa ta dauki wayarta da tun dazu sai gajiya nayi na sakata a silent saboda yadda ake kira.

Ummah ta fara kira, taje umara kamar shekaranjiya naji Janan tace ta tafi. Bayan sun gaisa ta tabbatar mata da lafiyarta lau yanzu, ta miko min wayar muka gaisa da ita. Bayan munyi sallama ne ta amshi wayar ta kira Ya Almu. Ni kuma na dauki wayata ina game.

Bayan sallar magriba Yaya Bilal ya sake shigo mana da abinci, chips ne da sauce da gasasshiyar kaza, nan ma sake zama yayi ya zuba mata dogon sharhi akan aikin gida, ya fada ya kara maimaitawa, daga wannan rana kada ta kuskura ta sake cewa zata yi kowani irin aiki ne in dai na gidan ne.

Ashe wai gyaran gida ne suke yi saboda matsowar azumi, wanda ake tsammanin ranar litinin ko talata za'a tashi dashi. Ita ta fara dauko maganar ayi aikin tun daga farko ranar Alhamis bayan ta koma gida, shine sun shiga can cikin gidan, wani daki da suka maida dakin tarkace kawai, zasu gyara shi da niyar da azumi za'a dinga taruwa acan ana sallar tarawihi, suna fara aikin suka fara zamewa daya bayan daya har suka barta, wannan kura data shaka ita ce fa ta tado mata asthma. Allah ne ya taimaka da asubahin washegarin yau, Yaya Bilal daya dawo jiya da dare, ya leka dakin kasancewar bai samu ya ganta ba daya dawo, shine fa ya sameta a cikin mawuyacin hali. Da Allah kadai yasan abinda zai faru.

Bayan mun ci kaza da chips munyi nak, kwanciya muka yi tun wajen karfe taran dare don ba karamar gajiya muka yi ba daga ni har ita.
Ta kalleni lokacin da nake ta faman buga keyboard din wayata ina turawa Muhammad sako, tun wayar da muka yi da safe bamu yi wata ba har yanzu, haka tun text din daya tura min lokacin da muna asibiti bai sake tura wani ba, nima ban sake tura mishi ba saboda ban samu kaina ba sai yanzu. Bayan na tura mishi ne, idanuna suka sauka akan conversation dina da muka sha yi da Umar, rabon da in ga text dinshi a wayata kusan sati biyu kenan, haka ma kira. Tun ni ina yi da tura text, har na gaji na hakura kawai na koma gefe ina jiran ya sake waiwayata.

Janan ta dafa goshina, tace "ke ma fa kamar baki da lafiya, jikinki zafi sosai".
Na kai bayan hannu na ina dafa wuyana, "lafiya ta lau Jan, ina tunanin yanayin nan ne, ko kuma mura. Kin san yadda murata take".
Muna hira kadan-kadan da ita dai har barci ya kwashe mu.


*


Washegari ma haka Anty Sarah ta kawo wa Janan abin kari, bayan fitarta muka koma gefe ni da Janan muna gulmar kirkin da tayi kwanannan.
"Allah da gaske dama can tana da kirkinta, kafin zuwan Anty Raheemah kenan. Tana zuwa kwata-kwata sai ta hau kulle kanta a gidanta, ina tunanin jinin su ne bai zo daya ba". Cewar Janan tana shan romon naman kan sa data kai mana.

Ni kam na kasa cin komi, sai sandwich daya na samu naci wanda tayi filling da sauce din kwai da sardines na gwangwani, ga cucumber a ciki, shima rabi, sai shayin dana hado mana da nake ta kurba. Tashi nayi bakina salam babu dadi, ga wani shafal da nake jina kamar babu laka a jikina ko kuma idan aka hure ni zan fadi, gefen kaina bugawa yake yi tun karfinshi idan nayi dan motsi, jiya da zazzabi na kwana a jikina, ga wani jiri da nake ji idan na tashi, daurewa kawai nake yi muna hira da Janan, amma Allah kadai yasan yadda kaina yake sarawa. Ita kam jikinta da kwari tubarkallah, kamar ba ita bace tasha jinyar nan jiya ba. Da safe su Raheemah sun leko sun mata sannu da jiki suka kara gaba. Kamar ma unguwa muka fita, don mu kadai muka yini a gidan, sai bayan isha'i suka dawo.

Janan ce ta takura akan sai mun fita bakin titi mun sayo tangerine da mango.
Nace "wai ke ma ga Ahmad nan, ki tura shi mana?".
Tace "ke zaki fita kiyi gadin gidan ko? Yadda Yaya zai dawo ya tadda baya nan ya tsige ni da raina ko?".
Nace "to yanzu kina tunanin idan ya dawo yaga bamu nan, ba zai tsige ki da ran naki ba dai?".
Tayi dariya, "sis, ki taso kawai mu fita, babu abinda zai faru. Ni fa bana jin dadin jikina wallahi, ai nayi kokari, kusan awanni na arba'in da takwas fa ba tare dana taka waje ba!".

Na jefa mata harara, "da can kuma da kike fin sati ma ba tare da kin fita ba fa?".
Tace "wannan ai ya banbanta, don Allah taso mu tafi kada mu bata lokaci har Yaya ya dawo".

Duk da ban so ba, haka nan na tashi na bi bayanta muka fita. Har yanzu ina jin jikina ba daidai ba, duk da dai tunda nasha paracetamol da yammar nan, zazzabin ya sauka, amma har yanzu ina jin jirin kadan-kadan da kuma ciwon kai.

Can bakin titi muka fita, muka yi siyo duk abubuwan da idanunmu suka dora ido a kansu. Niki-niki haka muka juya gida hannuwa cike da ledoji. A hankali muke tafe akan titin, yanayin unguwarsu kamar G.R.A haka take, da rana ma baka cika ganin mutane suna shawagi ba balle da dare. Yanzu ma sai jifa-jifa muke ganin mutane, sai kuwa ababen hawa da suke ta wucewa. Wasu na fita wasu na shiga.

Gab da zamu shiga gidan naji nayi turus, sakamakon wata mota dana hango can gaba kadan da gidan. Idan da ba don wata sticker dake bayan motar ba, an rubuta 'born to fight', da

Please Login or Register in order to submit comment