Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

To itama bata matsa ba, tace to, muka yi sallama ta tafi.

Itama na kula tun maganar nan da muka yi da ita ranar da Yaya Bilal zai zo, bata kara tado min zancen ba. Amma kuma gabadaya sai nake ganinta kamar ba Janan dita ba, kamar ta canza. Duk da bata fito kai tsaye ta nuna min wata canjin fuska ba ko wani abu, amma she just seems very distant.

Shi yasa nake jin kamar an dauko duk wani nauyi da damuwa ta duniya an dora min. Duk duniya, Janan ita kadai ce abokiyar shawarata. Kafin in nemi Kulsum ko Yaya Mudatthir ko Fatsu da suke manyan abokan shawarata, da wata shawara, Janan nake fara nema. Mu zamu kashe mu binne a tsakaninmu babu wanda ya sani balle yaji labari, sai idan tayi wari ne a mafiya lokuta suke ji.
Yanzu kuwa da babu ita, sai naji kamar komi ya hargitse min.

Nasan babu ta yadda za ayi in nemeta da shawara game da dan uwanta, bayan duk wasu abubuwa da maganganun da nayi game dashi. Nasan ranar na bata haushi ba karami ba, amma kuma ai gaskiyata na fada mata ba wani abu ba. A tunanina zata fahimceni, nayi zaton zata fahimci inda na saka gaba. Sai dai abinda na manta shine, dan uwa, dan uwa ne. Yaya Bilal dan uwan Janan ne, hakan yana nufin cewa ko a halin runtsi da wuya, zata iya zabar Yaya Bilal da gudu ta barni. Balle wa zai juri yaji kalmar rashin so zuwa ga Yayanshi da yake matukar so da girmamawa na fita daga bakin abokinshi? Babu.
Shi yasa na fahimceta, ban kuma ji haushinta ba. Shi yasa nima ban kara tada mata maganar ba, kunya ma ba zata barni ba. To wai ma ince mata me? 'Ni fa tunanin Yayanki ya ki barin zuciyata, kuma lokaci na karshe da muka yi waya dashi na zabga mishi rashin mutuncin da bai cancanta ba, shi yasa bai sake bibiyar rayuwata ba har yanzu, me kike tunanin yakamata inyi yanzu!', yeah, da alamu na fara rasa alkiblata ma ni yanzu.

Tun wannan kwanciyar da nayi, ban motsa ba. Sai da Janan ta kira ni, lokacin har duhun dare ya fara shigowa sannan na motsa. Wuyana ya amsa da ciwo saboda kwanciyar da nayi a gefe daya na tsawon lokaci ba tare da na motsa ba, haka nan ina yamutsa fuska na dauki wayar muka gaisa. Ta sanar dani isarta gida kenan, na mata sannu da zuwa tare da sakon ta gaida su Ummah.

Muna cikin maganar na jiyo sautin muryar Yaya a can background din wayar, kamar ma dariya yake yi lokacin. Naji kamar anyi freezing din komi da kowa a lokacin banda ni dashi, muryar Janan ta dauke kamar bata wajen, babu abinda nake ji a cikin kunnena a lokacin sai sautin tattausar dariyar Yaya Bilal da take tashi a lokacin ina jinta kamar busar sarewa saboda yadda take tashi very deep, very soothing.

Ban san dalilin da yasa naji kwalla mai zafi ta ciko min idanu ba, amma zata iya yiwuwa saboda tsananin dadi da salamar da naji sun sauka a cikin zuciayata ne a lokacin, ban taba tunanin zan ji dadin jin muryar wata halitta a doron kasa bayan dogon lokaci da muka dauka ba tare da mun hadu ko mun ji muryar juna kamar yadda naji dadin jin muryar Yaya Bilal yanzu ba, ban taba ba.

Allah ne ya bani ikon dawowa cikin hayyacina kafin Janan ta fahimci wani abu, ko kuwa ta fahimtar kyaleni kawai tayi? Koma dai menene ban damu ba a lokacin, damuwata daya a lokacin inyi gaggawar katse kiran wannan kafin jin muryar Yaya ta sanya ni yin abinda ban shirya yi ba, ni da nake gudunshi tun karfina, in kare da making fool out of myself.
Don haka nayi gaggawar yin sallama da Janan, tana tambayar lafiya? Ina lalubo dalilin da nasan ko dan jariri haihuwar yau ba zai yi convincing ba na jefa mata, na kuma kashe wayar ba tare dana jira abinda zata ce ba.

Lokacin dana koma kan katifa na kwanta, idanu a lumshe, hannu daya dafe da gefen kaina da yake bugawa, zuciyata da wani irin nauyi kamar an dauki wani gungumemen dutse an aza mata, babu abinda yake cikin raina sai tunanin azabar bata isa ba haka ba? Anya, ba zan nemawa zuciyata sanyi ba??!.







~Am really, very, very sorry. Please ku yi maneji da wannan, in shaa Allah gobe zaku samu dogon feji.













*☆⋆27⋆☆*





Ranar Lahdi a cikin makaranta na yini. Tun wajen karfe goma sha daya na safe na tafi wajen Aylah, tsohuwar room mate dina wadda muka zauna da ita last year. A wajenta na yini, muka sha hirar yaushe gamo da ita. Da yammaci kuma na tafi wanke kaina saloon din cikin makaranta.
Tashin hankalin dana shiga cikin yan kwanakin nan, ba muhimman al'amura kadai na banzatar ba, har ma da kananan irin wanke kai da yanke farce na manta. Ban ankara ba sai da naji kaina yana masifar tashi, sannan.

Da yake akwai wata mata dana saba zuwa wajenta tun ma muna cikin makaranta, nasan duk da cewa yau Lahdi ce tana nan saboda musulma ce ita. Don haka kai tsaye na wuce shagonta. Abinda naci karo dashi ne a gabana daga shiga cikin shagon, ban shiryawa ba.

Adi, Raheemah da Salamah a zaune akan kujerun jira da aka tanada a shagon, yayin da ake wa Adi karin gashin kanti a kanta. Muka tsaya muka danyi kallon-kallo dasu, kafin muka kauda kanmu mu duka, babu wanda ya nuna alamun yasan wani. Na dai musu sannu, nima kuma na samu waje can gefensu na zauna.
Rabon da in gansu su dukansu, tun azumin farko da naje gidansu, gashi yanzu har muna tunkarar watan Zhul-Hijja nan da yan kwanaki.

Ina nan zaune ina wasa da wayata kawai, ina sauraren hirar da suke tayi da yake mu kadai ne a cikin shagon. Tsantsar gulma ce suke yi, wadda nafi kyautata zaton akan Haleemo ce, babu kunya balle tsoron Allah. Wani karin abin haushin shine, Raheemah tana fita domin ta dauki kiran da aka yi mata a waya, suka ajiye hirar Haleemo gefe suka dasa tata. Na girgiza kaina cike da takaicin halayya irin tasu, ku a tsakaninku kuna a matsayin yan uwa babu aminci da amana, ina ga wadanda ba yan uwansu ba kuma?.
Kafin kace me, naji na kosa da zama wajen, da ba don na riga na shigo wajen ba da wallahi baya zanyi.

Allah ya taimaka ba'a jima ba wata daga cikin yan aikin wajen tazo ta kama kaina. Ta tambayeni retouching zanyi ko kuma wankewa kawai? Nace mata wankewa, don ni koda wasa ban taba sanyawa kaina relaxer ba. Yanayin natural santsi da laushin shi yafi yi min.
Na cire gyalena na ajiye a gefe, muka koma can gefe inda ta wanke min shi tas, muka koma tayi drying. Tana gama gyarawa, na sallameta na kara gaba na barsu acan.

Ina fita na sake cin karo da Haleemo, wani mutum daga ganinshi babba ne ya sauketa a mota, itama dai kallon-kallon muka yi, na tabe mata baki na wucewa ta.
Sai da nayi sallar magriba anan sannan na koma cikin asibiti.


*


Washegari da safe bayan duk mum gama ayyukan da suka kamata muyi a cikin ward, su dressing, bada magungunan yara majinyata da sauransu dai, duk muna zaune a nurses station. A yanzu wani yaro da ake yiwa blood transfusion muke monitoring dinshi duk bayan mintuna sha biyar, don haka muke zaune kusa da wajen.

Wasu matrons ne su biyu daga can gefenmu, suna ta zuba hirarsu. Da alama daya daga cikinsu ce aka yiwa aure, yanzu haka tana kan yin hutun amarcinta ne.

Sister Mairo ce take cewa "... Ai ina gaya miki, daga zuwanta sai ga mata a kicin washegari tana girka abinci, ba fa nata ita kadai ba, wai har uwargidan da 'ya'yanta saboda uwargidan ta tashi da ciwon ciki. Nace to a haka za'a ci amarcin ne? Me zata ji, me zata karas? Allah na tuba duk wanda bai ji dadin kwanakin nan bakwai na aure ba, ai bai ji dadin amarci ba!".

Daya sister din da ban san sunanta ba ta kwashe da dariya, tace "maganinta kenan ai. Nan muka zo, wace irin nasiha ce ba'a mata ba akan Alhaji Mati? Amma ita ta nace ta kekashe kasa, wai mutum mai mata ko wanda ya taba yin aure is more responsible, waye da waye, gashi nan ai tun ba'a je ko'ina ba, zata zama yar bauta. Ai ni wallahi inaa, Allah ya tsare ni wallahi. Ko a lokacin da Abban su Humairah yake ihun mata biyu zai aura ban ko daga ido na kalleshi ba balle in wani daga jijiyar wuyana, abu daya na sani koma mata nawa dai zai aura, anan zasu zo su sameni dai. Sai na gama tsintar abinda zan tsinta, na gama morewa mijina yadda naso sannan in bar mata sauran. No biggie!". Suka sake sakin dariya.

Ina kallon yadda Janan take watso min wani irin kallo daga can kasan idanuna. Ban san abinda take sakawa ba a cikin ranta, bana kuma fatan in sani. Don haka nayi shiru, kunnuwana duka biyun akan hirarrakin da su sister Mairo suke yi, wanda yawancin hirar akan ire-iren abubuwan da suke yawo ne a cikin raina.
Har dai lokacin da zamu sake duba yaron nan yayi, muka dauki abubuwan da zamu bukata ni da Janan muka je muka duba shi tare da rubuta cigaban da aka samu game dashi, muka fito.

Muna fitowa, muka ci karo da Dr. Na Abba, ya ja ya dakata yana kallonmu cikin murmushi, "hey, 'yanmata!".

Ni da Janan muka maida mishi martanin murmushin tare da gaida shi ya amsa. Janan ta dan yi gaba kadan, ni kuma na dan dakata haka nan muka gaisa. Bamu ja hirar da tsayi ba, saboda yace yana da patients amma yayi min alkawarin sake zagayowa zuwa anjima, nace mishi babu damuwa. Ya wuce, ni kuma na daga kafa na karasa wajen Janan muka cigaba da tafiya zuwa wajen da muke zaune.
Zuwa lokacin da muka koma, su Sister Mairo sun canza hirar da suke yi zuwa ta sana'o'in hannu.

Muna sake komawa wajen yaron a karo na hudu, muka tarar an gama mishi transfusion din. Saboda haka bayan munyi handling din bayanan yaron wajen likitan daya duba shi, ni da Janan muka wuce masallaci domin raka Janan tayi sallar azuhur.

Bayan tayi sallar, muna kan hanyar dawowa, Janan ta kalleni, tace "na yi zaton zaki sayi wani abu ki ci tunda ba azumi kike yi ba yau?".
Tunda muka fito waje sai lokacin tayi min magana. Na girgiza mata kai a sanyaye, nace "bana jin yunwa!".

Daidai lokacin mun je wani dogon corridor, Janan taja ta tsaya tana fuskanta ta. Tace "kada ki ce min rashin son auren Yaya da kike yi, yana da nasaba da maganganun da su sister Mairo suka dinga yi dazu?". Na zuba mata idanu kawai ina kallonta.

Tace "Na'ilah, haba don Allah! Wa yace miki rayuwa zata tafi a haka ne? Da dai nayi shiru in ga iyaka gudun ruwanki ne, amma da alamun baki da niyar tsayawa a matsaya daya, don haka na gaji da kallonki haka nan. Duk kin bi kin kwarzabi kanki Na'ilah, kin hana kan ki sukuni, kin hana kanki kwanciyar hankali, haka ake yi dama? Wai a kanki ne mai mata ya fara neman auren budurwa ne? Shi Yaya Bilal din ba mutum bane? Mutum ne shi, guda dayan shi sukutum. Amma ke kin hana kanki kwanciyar hankali, kin hana na kusa dake samun nasu kwanciyar hankalin saboda wani dalili naki mara fa'ida!". Tayi shiru tana ajiye numfashi. Har yanzu ban ce mata komi ba, ban ma yi yunkurin tanka mata ba.

Tayi kwafa, "to naji. Ina ce kin ce baki son Yayan? Kin ce ya kyale ki? Ba ya kyale ki din ba? To kuma menene na sanya kanki cikin damuwa? So kike yi ya dinga bin ki duk inda zaki je, kina wulakanta shi Na'ilah? Meye haka kike yi wai?".

Nan ma na sake yin shiru, haka kawai naji kwalla ta ciko min idanu, na sadda kaina kasa ina sauraronta tana zuba bayanai. Ni kaina a halin da ake ciki yanzu, ban san me nake tunani ba, ban kuma san me nake so ba. Ina son Yaya Bilal ya cigaba da kirana, ya cigaba da kulawa da ni, ina son in kasance dashi. Sai dai a duk lokacin da tunanin zama da kishiyoyi musamman irin su Ameerah da Raheemah ya fado min cikin raina, sai inji duk wani abu da nake ji game dashi ya bi iska.

Darare da dama da na sha zama, ina kokarin lallashin kaina, sai dai I just can't bring myself to do that! Na kasa! A duk lokacin dana tuna da irin ukuba, tashin hankali, damuwa da rikicin da muka shiga ciki, ko kuma wanda muke ciki har yanzu a gidanmu, wanda kishiyoyi ne suka yi sanadin haka sai inji zuciyata ta dugunzuma, inji hankalina ya tashi.

Jin shirun da nayi, yasa ta dafa kafadata, tare da tallabo kaina da hannunta daya. Bani da zabi sai na daga idanuna da suka cika da kwalla na sauke a kanta.

Ta girgiza kanta, tace "wallahi mamaki kike bani Na'ilah. You are just beating yourself akan abu mai sauki. Sai me don Yaya Bilal yana da mata? Ke yanzu ba abin alfahari bane a gareki, mutum kamar Yaya Bilal ya so ki, ya sadaukar da muhimman bigire nashi a kanki? Ba yabon kai ba, Yaya Bilal kyakkyawan mutum ne, mafarkin kowace diya mace. Amma ke ga damar samunshi a ruwan sanyi kin samu, kin zauna kina jan aji da kawo wasu dalilai naki da basu da makama ko kadan. Gaya min, matan shi ne, rashin haihuwar da baya yi ne, ko kuma shi a karan kanshi ne?? Idan mata ne, yace miki ba a waje daya zai hada ki dasu ba. Idan kuma haihuwa ce, ina mai tabbatar miki da cewa Yaya Bilal lafiyarsa lau, Allah ne bai kawo mishi haihuwa ba har yanzu. Idan kuma shi dinne, menene aibun Yaya Bilal saboda Allah? Ni dai nasan Yayana mutum ne mai nagarta, sai dai idan anki Allah ne za'a ce bai yi ba!".

Tunda ta fara maganar nake girgiza mata kai, amma banyi yunkurin katseta ba sai data dire aya. Nace "ban taba tunanin kin Yaya saboda rashin haihuwa ba, ita haihuwa nasan ta Allah ce, duk kuma kokarin mutum, idan Allah bai mishi baiwar haihuwar ba, babu abinda zai iya yi game da hakan sai dai hakuri kawai. Don haka ban taba yin wannan tunanin ba. Sai dai kamar yadda kika ce, yes matan Yaya, sannan shi a karan kanshi ba tsaran aurena bane. Meye hadin biri da gada idan ba rigima ba? Daidai ruwa daidai tsaki, sai kiga an zauna lafiya. In gaya miki gaskiya Yaya Bilal ya fi karfina.

Ba son kai ba, aure nake so inyi mai cike da kwanciyar hankali Janan, ba zan baro masifar kishiya ba, sannan kuma in fada cikin wata wadda ma tafi waccan, kuma ina sane. Idan nayi haka ban yiwa kaina adalci ba. Na fa san komi Janan, ba yau aka auren soyayya ba a gaban idanunmu ba, amma tun kafin aje ko'ina kiga labari ya sha banban. Wannan wadanda ba zaune suke da kishiya bama fa kenan, ina ga wadanda zasu zauna da kishiya? Allah ya gani, so nake in shimfida rayuwar aure mai ma'ana, daga ni sai mijina sai 'ya'yan da zamu haifa. Wannan itace rayuwar dana dinga hangowa kaina Janan, bana kuma tunanin zan iya kauda kai, ina ji ina gani, in kai kaina cikin kabari na!".

Ina dire maganar ta tare ni, "to wa yace miki ba zaki iya irin rayuwar da kike hangowa ba da Yaya Bilal? Kin gwada ne kin gani?".

Nayi dan murmushi cike da kunar zuciya, nace "Janan kenan! Ke baki san kaidi irin na kishiya ba, baki san komi game da sharri da kissa da kisisina irin ta kishiya ba, bana kuma tunanin zaki taba sani. Don haka ki kama bakinki kawai ki ja, ni naga abinda na gani da idanun nan nawa, abinda na gani kuma ba abu bane mai kyau, don haka tarihi fa ba zai maimaita kansa a kaina ba Janan! To dame ma zan ji ne? Da miji zan ji, ko kuwa tashin hankalin kishiya? Barni dai inji da abu daya, hankalina zai fi kwanciya!".

Janan kallona take yi kamar wata sabuwar halitta, nasan yadda na hakikance ne abin yake bata mamaki. Bazan damu ba though, ance wai riga-kafi yafi magani, kuma hanyar lafiya a bita da shekara. Gwanda dai in tsaya kyam akan ra'ayina, idan zuciyata ta fara rawa akan wannan maganar, me zai faru kenan? Na san it's only a matter of time, da zan manta da wani Yaya Bilal. Balle duka mai ya rage mana a Zaria? Yan watanni ne kawai. Idan na samu na lallabi zuciyata, na lallaba na bar Zaria, nasan ikon Allah ne kawai zai sake dawo da ni cikinta. Kenan idan na tafi, ta ina zan ga Yaya balle har wani tunanin zama dashi da masifaffun matanshi ya darsu a cikin raina? Abinda nake bukatar inyi kawai shine in daure, in kuma yi kokarin mantawa dashi.
Sai dai fadar, tafi aikatawar dadin fada.

Janan ta girgiza kanta cikin rashin sanin abin cewa, tace "gaskiya kinyi nisa da yawa, Allah ya ganar dake".
Nima na girgiza mata kaina, nace "ba zaki taba ganewa ba Janan, ba zaki gane ba!".

Bata ce komi ba, ta cigaba da tafiya. Nima na bi bayanta.
Tun daga wannan yar sa'insa da muka yi, babu wanda ya sake tado maganar har lokacin tashinmu yayi. Kai babu ma wata doguwar magana data sake hada mu da ita, naga kamar ma wani haushi na take ji. Ni ma da yake raina a dagule yake, ban wani damu ba. Lokacin tashi yana yi, na bar ward din. Ranar ko sallama bamu yi ba.


Ina komawa daki na dora indomie, ba wata yunwa nake ji ba, amma tunda ranar garin yau ta waye babu komi a cikin cikina sai biskit din pure bliss da hot chocolate. Ina gama dafawa na dora ruwan shayi, na dauki lemun tsami na matse a cikin shayin na juye a cikin mug. Dana gama na daukesu zuwa gefen katifata na ajiye, ni kuma na zauna. Laptop dina na dauka na kunna kallon wani American film, 'Another Cinderella Story' na fara kallo ina kuma cin indomin. Kallo kawai nake yi, amma bana wani fahimtar kallon. Har na gama na kauda kayan, na dawo na cigaba da kallon. Ina nan zaune Esther ta dawo, na mata sannu da zuwa, na maida hankalina kacokam ga film din da nake kallo don bani da kuzarin zama yin hira da ita. To da yake ma ba zama ya kawo ta ba, kayan jikinta kawai ta canza ta sake fita.
Ina cikin yin kallon barci ya kwashe ni.

















*☆⋆28⋆☆*






Ban jima da fara barcin ba amma, kiran daya shigo cikin wayata ya katse min shi.
Na zabura na tashi zaune tare da lalubar wayata, duk da kalar ringtone din, hakan bai hana ni kara duba sunan mai kiran ba domin in tabbatar da cewa da gaske ne ba mafarki ba.
Ban san dalilin da yasa na kasa goge lambar Yaya Bilal daga cikin wayata ba, kai ko suna har yanzu ban iya canza mishi ba. Har yau 'Muhammadu na' ne a jiki, shine kuma yake tsalle yana karawa akan screen din wayata.

Duk da tsananin rawar da hannuna yake yi, da yadda zuciyata take bugawa, da yadda nasan bani da abinda zan ce mishi, hakan bai hana ni dagawa ba.
Hatta da muryata rawa take yi lokacin da naji muryarshi tana ratsawa ta cikin dodon kunnena, na amsa cikin sanyin jiki da murya. Yaushe rabon da inji wannan muryar? Ji nake kamar na shekara da shekaru.

Yaya Bilal yace "hmmm, Na'ilah kenan, manyan kasa. Kin gama fushin ne?".
Nace "fushi kuma, fushin me zan yi?".
Yace "nima ban sani ba Na'ilah, kawai dai nasan kina yin fushi. Amma duk ba wannan ba, kina ganin zamu iya magana yanzu? Are you ready for that?". Nayi shiru ina sauraronshi, ina tunanin ya dauki shirun da nayi a matsayin go ahead, don haka ya fara magana.

Yace "ba kya ganin it's high time, mu ajiye duk wasu abubuwan da suka faru a baya a bayanmu mu fuskanci gaba? Bai kamata ace muna ta tsalle-tsalle a waje daya ba kamar kananan yara, please let's do this like the matured people we are!".

Tabdijam! Naji wani kululu ya makale min a makoshi, cikin nuna alamun bacin rai nace "kana nufin kace min ni yarinya ce ko kuma ina dabi'a irin ta yara?".

Yace "ban ce ko daya daga ciki ba, illa iyaka ina so in nuna miki cewa wannan kauce-kauce da kike yi babu abinda zai haddasa mana sai bata lokacinmu da yake yi kawai. Na'ilah, mu fa ba kananan yara bane, bai kamata ace mun dauki magana daya muna ta nanata ba, bayan muna da yadda zamu fuskanci matsalar mu kuma magance ta. Saboda haka yanzu ki fada min, meye matsalar ki game dani? Kin san ina son ki ko?".

Amsar dana bashi ta fito daga cikin bakina tun ma kafin in tauna ta, kai ban ma san na fade ta ba sai dana ji tana ringing a cikin kunnuwana, da kuma shirun daya biyo bayan na furta ta, da alamun shi kanshi bai yi tsammaninta ba; "nima ina sonka!".

Kusan sakanni biyar da fadin hakan, kafin naji yayi gyaran murya, ni kam sai aka barni da kyafta idanu, yace "good. To menene matsalar? Na riga na fada miki idan ta matana ne baki da matsala da su, gidan ki daban zan ware miki, ba lallai sai kun hadu dasu ba. Wannan ganin damar ki ne, idan kin so haduwa dasu sai ki hadu dasu, idan baki so ba, sai kiyi yadda kike so. Bayan wannan kuma sai me? Ban takura ki ba Na'ilah, zan jira ki gama karatunki kafin a tado maganar auren, bayan nan zan bar ki kiyi aikinki, ba zan hana ki ba. Sai me kike bukata kuma?".

Shi a tunaninshi rashin hada mu gida daya kamar wani solution ne, sai dai a nawa tunanin, wannan ba komi bane. Ya hada mu gida daya ko bai hana ba, duk dai yana da mata ne dai, kuma zamu yi sharing dinshi dasu. Na daga baki nace "bani da wata matsala Yaya, kayi hakuri. Nima ba wai ina jindadin wasa da hankalinka da nake yi bane, amma the fact that zan zauna da kishiya daya ma bana so balle kuma har biyu, kayi hakuri don Allah".

Yace "shi kuma son da muke yiwa juna fa? Kin kasa daukar matsaya daya Na'ilah ki zauna a kanta, daga yau kice wannan, sai gobe ki ce wannan. Kina ganin ina da lokacin zama bin kanki ne? I can't leave my work da duk wasu harkokina, ina chasing dinki Na'ilah! I just can't. Don haka idan zaki zauna ki yanke shawarar da zata fisshemu, gwanda ma tun wuri ki yanke. Haba! Na gaji! Na gaji wallahi!! Wai baki da zuciyar tausayi ne? Ko ke baki san kaddara ba ne? Kada ki manta da cewa Annabinmu ma da muke yin koyi da koyarwa shi bai zauna da mata daya ba. Ke a ganinki rashin zama da kishiya zai hana ki rayuwar farinciki a gidan aurenki bane ko me? Kina ina mata da dama suke baro gidan auren nasu babu kishiya ba kome, gasu nan birjik suna yawo akan titi muna ganinsu, amma kuma masu kishiyar suna zaune a nasu gidan salin-alin suna zaman lafiya? Kin kishiya da kike yi kamar izgilanci ne kike yiwa Allah, tunda kin karanta, kin kuma san cewa ba haramun bane a musulunci. Ita kishiyar hauka ce?!".

Yadda ya hakikance yana fada yasa naji nima raina ya dauko baci, a tunanina idan ba'a lallasheni ba, bai kamata ace za ayi min ihu ba. Nace "da kake maganar kaddara da kuma izgilanci, shi Allah ai baya dorawa rai abinda ba zai iya

Please Login or Register in order to submit comment