Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bayan shekara.
"Wallahi bazan iya zama a gidan nan ba, kawai ka mai dani, gurin Aunty Sarinah!"

       Juyawa yayi tare da janye ni a jikin shi ya zuba min ido, dariya na cin shi. Tab'e baki yayi sannan ya.
"Kiyi hakuri ina sauri gob..."
Tabo Hajiya babbar shi nayi, tare da zuba mishi ido, ina murmushi.

          Rike y'ay'an gwaibar nayi ina kuma tab'o yaya babba, jin hannun shi kawai akan k'uguna, murmushi na kuma saukewa, sannan na riko hannun shi muka koma daki,
 
Ban daki na shiga na hada mishi ruwan wanka, sannan nazo gabanshi na soma taya shi cire kayan shi, sannan yana gamawa muka nufi ban daki, yana shiga ruwan na bishi. Kasa magana yayi har na taimaka mishi ya fasa jikin shi sabida sanyin da ake.

  Na rigashi fitowa, fita nayi zuwa daya dakin, har zan saka hannu a jikin kofar naji ance.
"Yumnahhhhhhhhhhhhhhh!"
Kan Bala'i, ban san lokacin da nayi wani irin juyawa ba, na koma d'akina, dai-dai ya fito daga ban dakin, jikin shi na koma, na juya. Jikina sai wani irin rawa yaƙe.

       Tsabar na razana, kallona yake, tambaya na yayi na gaya mishi, riko hannuna yayi sannan yace.
"Babu abinda zai same ki, Insha Allah! Muje wancan gidan, ki zauna a cikin mu hankalina zai fi kwanciya."

     Da sauri na gyada mishi kai muka shirya, tsaf sannan ya dauki jakata, muka fito.

                 Muna fitowa kamar ance na juya na kalli gidan kawai naga wata mace a tsaye, sanye da bakaken kaya wani irin karar na saka tare da zuɓewa a sume.

        Tashin hankali da dimauta ya shige shi, a take ya kira Taxi ya dauke mu, zuwa gidan shi can.

                   Muna isa gidan ya biya kudin taxi din sannan, ya dauke ni zuwa cikin gidan, a falon su ya kwantar dani, shafa fuskana yayi bayan ya dauko ruwa ya shafa min.

     Kirana yake amma bana jin shi sai zan farka wata mata da take ta, tafiya nake bi. Har muka kure wani unguwa da babu kowa, tsayawa tayi cak. Nima na ja baya.

                    "Wacece ke? Meye had'iki dani!"

            A fusace ta juyo, a cikin abinda bai kai dakika goma ba, kawai ta rike wuyana!

"Halwani! Shine ya haɗa mu! Ki rabu dashi zan rabu da rayuwar Yumnah! Zan baki soyayya da kika jima kina nima, zan kaunace ki sama da kome!"
Tana fadar hakan ta wurgani can gefe.

        Rike wuyana nayi ina tari,
"Akan me zan bar miki shi? Wacce soyayya zaki min Mommy! Mutum da kika tsana! Mutumin da baki kauna? Mijina! Abokin Abbana! Abokin mijinki shi kike cewa na bar miki zaki so Ni, zaki kauna ceni?

....ai kawai ki kashe ni,.idan akan Halwani ne? Toh wallahi.bazan bar miki shi ba, ni dashi mutu karaba!"

         A fusace tayo kaina, da mugun karfi na fara Innalillahi, ganinta nayi kamar an jata da wani abu an likata da kasa, tana kuma mikewa aka kuma buga ta da kasa.

         Na karshen ne, tana mik'ewa ta wurgo min wani abu, yana zuwa ya fadi a gabana, kamar kwai cikin wani irin sauri ya fashe tare da shigewa jikina ta kafana da kofar hancina.

.dariya ta saka tare da cewa gaki ga halwanin, tana gama fad'ar haka ta mike kamar guguwa ta barni a tsaye.

          Lokaci guda naga wani irin abu yana fitowa a jikina, karkade shi nake, naji..an rike hannuna tare da yin baya da kaina, ina son bude idanuna na kasa.
"Hassanah ba zata tab'a nasara akanki ba, koda Jarabawa amma dole aniyarta ya koma kanta!"

Muryan Mama Ladi nake ji, kamar da wasa suka zuba min abu a bakina, rike ni akayi gam. Akayi ana zuba min abu.
sai da na shanye tas, yunkurin amai nake.

Uncle ya rike ni, dai-dai na farka kenan, amai na dinga shekawa, rike ni yayi sabida jin wani abu a wuyana, amai nake idanuna a rufe.

    Cikin wani irin tashin hankalin, da damuwa yake kallona ga Kafaya Bata Gidan ta tafi yawon ta zubar.

    Dakyar abinda Mommy ta wurga min ya fado, sumewa nayi a kirjin shi bayan na gama aman.

        "Alhamdulillah!." Dakin shi ya kai ni ko Kafaya bata taba, shi ga ba, amma ni ya kaini cikin dakin.

        Kwantar dani yayi yazo ya gyara falon, sannan ya kira.

Kanin Hajiya na gombe ya gaya mishi, halin da muke ciki.

         Sun jima suna tare ya gaya mishi kar yayi nisa dani, ya kasance akwai wani kusa dani, sannan ya duba cikin addu'o'in da ya amsa yayi ta tofa min Addu'a, a ruwan zam-zam ina sha, ya bashi abubuwa da yawa.

. ...tun da ya shiga yayi wanka sannan ya gabatar da Sallah da take kanshi, sannan ya fita ya amso abincin da yayi odar kafin yayi Sallah.

Yana amsowa ya zauna yaci na shi, sannan ya dawo kusa da ni ya zauna, yana jiran na farka. Wasa wasa har dare ban farka ba, kwanciya yayi a bayana, tare da rungume ni,

               ----
Fasa madubin da yake kawo mata duk abinda muke aikatawa tayi cikin zafin rai, tana kallon hoton Yumnah da Abbanta.

     Dariya tayi sannan tace.
"Dole na hadaki da wanda zai min kome cikin sauki."

Duk yadda taso tayi aikin kasawa tayi dole ta hakura ranta bai so ba.
     ......
Soyayyar dake sha tsakanin Papa da Safiyya ba iyaka Ooo! Domin su kad'ai ne, sai Mah Naz da take zuwa duba Papa da safe, tayi mugun sanyi tun rasuwar yar Uwarta.

           Girmamawa da Mutuntawa Duk Safiyyah na bawa Hajiya, sosai take ji da ita, sabida nuna mata da tayi ita Uwa ce na gari.

    Ita kuma Safiyyah ta nunawa Hajiya itama Y'a ce, da tasan darajar iyayenta, sosai zaman su ya bada citta.

         ---
Farkawa nayi ina kallon kyakyawan fuskar shi, komawa nayi na lafe a jikin shi, ina wasa da gargasar jikin shi, tare da kallon pink lips din shi, a hankali ba kai hannuna ina shafawa.

          "Na hadu ko?!"

     Murmushi ne ya kwace min, na make kirjinshi, ina dariya. A hankali na rike wuyana nace.
"Sosai! Ai tako ina ma!"

Shafa fuskana ya kuma, sannan yace.
"Kashe wutar da kika kunna, da sauran lokaci!"
  Kashewa nayi,na koma jikin shi ina sauke numfashi a hankali, shafa bayana yake. Har barci yayi gaba da Ni.

           Washi gari bayan sallah asuba, na koma barci, jin ana magana a cikin gidan.

  Fada-fada, a hankali na duba dakin da mamaki, ashe ya sauya min dakine!  Fitowa nayi sanye da doguwar riga, ina kallon yadda ta saka shi a gaba da fada,
Bai mata magana ba, dan aiki yake.

           Ƙamar ba dashi take ba, da sauri ta juya zata nufo ni, yace.
"Waye ya gaya miki ina sonta? Yarinyar da ta gama zagaye mugayen abubuwa! Kai me zanyi da ita, na kawo ta nan ne, sabida na gyara mata zama, dan idan kinji irin zagin da tayi miki, shi yasa na dawo da ita gaban ki, taga yadda zanyi kaca-kaca da ita

Idan ta kuma zaginki ke! Ko kallon ki tayi ki gaya min na mata mugun duka, domin na ita zata cigaba da mana girki a gidan nan, idan ba shi ba, bata da Amfani, amadadin duk karshen sati azo ana gyara mana kayan gidan, ga yar aiki nan.

Toh tunda zan ci amanarki kike gani bari na kaita gurin Sarinah."
Kamar da gaske ya shiga hada kayan gaban shi.

"No! Barta kayi tunani me kyau, bari na fita zamu tafi Calfonia, Insha Allah jibi zamu dawo." Ta fita da sauri, tare da jan bag dinta.

Har bakin kofar yace.
" A dawo lafiya zanyi kewarki!"

Kallon shi nayi yadda ya tsare gida, tare da d'aga min gira, ware hannun shi yayi. Da sauri na shige jikinshi ina dariya a hankali nace.
"Me yasa kake ha'intarta?! Bayan ta yarda da kai.?"
D'ago kai yayi sannan ya hade fusakar mu, kauda nawa nayi sannan yace min.
"Tsarin da suka zo min, dashi dole na koyi cin amanar su, taya zasu haramta min ke? Bayan kina halal dina. Muje Gimbiya kiyi wanka kizo kici abincin dan ina son naci abincin ruhina"

Tare muka yi wanka ya dauko ni, kamar baby. Muka fito, gurin saka kaya ne aka fara, shagali.

Dakyar ya kyale ni, muka ci abinci. Daga nan muka dawo falon.
Hannunshi na cikin rigana, wasa yake da beautiful bra Dina, zame rigar jikina yayi cikin nutsuwa, sannan ya d'ago ni.
Tare da sakani a jikin shi muna kallon juna, wani sumbatar juna muna fara, a hankali muka yi nisa, murdawa mara na yayi, cikin sauri na sauka a jikin shi tare da nufar ban daki, naje na gwada yin fitsari, sai ga Jini.

Wayyo Allah na! Na furta a zuciyata, a lokaci guda ya bani tausayi, saka sanatery pad nayi, tare da gyara jikina, yana tsaye a bakin kofar shiga ban dakin,

Tunda na dawo falon na zauna, cikin damuwa. Tambaya ta yayi na gaya mishi tare da fashewa da kuka, murmushi yayi sannan yace min.
"Toh ai kina min iya naki kokarin, zo ki gwada min yadda zan rage kafin Linah ta dawo, sannan kwana nawa kike!"

Gaya masa kwanakin da nake, sannan na shiga taimaka mishi.

---
Wato idan na duba rayuwar da muke, ina farin ciki. Sosai dan bana jin akwai abinda zai d'aga min hankali, mijina ya tsaya min, kuma yana kan tsaya min, kullum Mamie na tambayar Linah ko akwai wani abu a tsakanina da d'anta, nan zata gaya mata ai idan tana jin sha'awar a wulakantani, sawa take ya min duka.(shawaragi 🤔🙆🏻‍♀️😹🤣? Wallahi kifa ki suke)

... Tun watan da nayi period, ban kuma yi ba, kuma wata uku kenan da dawowar mu nan, idan na cire kwanankin hudu a cikin watanni da muka yi toh akwai katon matsala, amma dake shirme da shiririta ya aure ni, da niman tsokana ce ko niman hanyar rikici na sani, kuma zanyi shi, ganin nima ban yi ba, sai na zata ko haka kawai yaƙi zuwa.

Wani abin mamaki, shine cikar da na kuma, kome nawa kamar an hura balloon, d'aga nonuwa na, har hips ɗina. Sun cika.

Kawai abu daya yaƙe damuna, shine yawan barci, shima har ya fara min mita wai na cika barci, na gaya mishi meke damuna.

Dariya kawai nake.mishi dan ni kaina ina faffutikar yaki da barcin nan.

Amma ina, saima kara samun mafaka yake, nayi wani mugun kiba, har Aunty Sarinah tana tsokana ta.
"Yar uncle! Wannan kibar na lafiya kuwa, ko kinci wake ne?"

Dariya nayi bance mata kome ba, ganin naki magana kawai ta share batun.


Da dare yau ma Kafaya bata gari, ina kan cinyar shi, yana aikin Zungure ni. Na fara jin kamar zuciyata na tashi, daurewa nayi yanzun sai yace min dama na kankaro wulakancin.

Koda ya gama nayi wani irin mugun laushi, yana d'aga ni na yanki jiki tare da suma a jikinshi, duk yadda ya zata zan farka abun yaci tura.

Ban daki ya kai ni tare da min wanka, ya shirya sannan ya dauke ni, zuwa asibiti.

Sun jima a kaina, kafin suka gaya mishi ina da cikin wata biyu da kwana ashirin da shida, dan haka ya kiyayye min sabida lafiyar cikina.

Kasa Magana yayi wasu tashin hankali biyu suka zo mishi daya farin ciki, d'aya fargaban Mamie, Idan ta san da cikin, ji yayi kamar ya fasa ihu, yana shiga dakin da nake ya zuba min ido, haba shi yasa na kara cika da haiba. Ga uban kibar da nayi.

Ya rasa yadda zai yi dani, toh me zai yiwa cikin dan kar ya zama tashin hankalin Mamie.

Zaka yayi har wani lokaci, daga bisani ya fita sakamakon kirar da aka mishi a gurin aikin shi.

......
Tun bayan da ya fita. Da awa biyu na farka, ana kula dani.. sai dai nayi kwana biyu ban ganshi ba, a na Uku sai ga Sarinah, take gaya min yana gurin aikinsu....
Paid before read....
8/30/20, 9:38 PM - Ummi Tandama: 5️⃣4️⃣ tashin hankalin da yake cika mishi zuciya yafi gaban wasa, gani yake kamar bazai iya rayuwa babu ni ba.

Ga kuma Mahaifiyarshi, dan haka yaa shiga damuwa sosai, ina zaune a gidan Sarinah har zuwa sati biyu, a nan ne hankalina ya fara tashi ga cikin ya haifar min da laulayi.

Muna cikin wannan yanayin, Mamie ta diro kasar.

Bamu sani ba, ina kwancen a dakin da aka sauke ni,

Sauke min duka aka yi a cinyata, na tashi a birkice, kallona take kamar taga kashi,
"Mamie don Allah ki bari, karki cutar musu da yar su"

Juyawa tayi ta sakewa Sarinah mari, tare da juyowa kaina, tana min mugun kallo.

Jan nayi da baya, tare da kare jikina dan babu kaya da gani sai zani da vest.
"Zaki gaya min cikin waye a jikinki? Ko sai na baki kamar yadda muka yiwa Khuwailah."
.a tsorace na kalleta cikin tashin hankali Sarinah tace.
"Wallahi kiji tsoron Allah, Mamie "
Sake dauketa da Mari Tayi sannan ta dawo kaina zata dake ni, cikin tashin hankali nace.
"Wallahi na shine!"

Na nuna mata bayan ta, juyawa tayi ta kalle shi, ya koma wani iri, gashi ya fito mishi ta ko ina musamman face din shi, a hankali ya tako zuwa dakin, na sauka a gadon tare da komawa bayan shi na fashe da kuka, ina me rungume shi ta baya.

"Dawo min da ita gaba na, ta gaya min cikin waye?!"

"Mamie! Don Allah karki tab'a min ita."
Buge mishi baki tayi tare da gaya mishi magana, kuka ne ya kwace min, nayi maza zan fito daga bayan shi ya mai dani.

"Cikin waye a jikinki?!"
Ta daka min tsawa, jikina na rawa.
"Wallahi kayi magana sai na tsine maka albarka, dan haka ka bani ita ko kuma na tsine maka,"

Fita nayi daga bayan shi, na isa gabanta tare da zuba gwiwata a kasa, ina kuka sosai.

Kifa min mari tayi, tare da niman dukar cikina, nayi maza na rike hannunta cikin kuka nace.
"Duk da na kusanci zina! Wannan abin cikin nawa ba shege bane! Idan ya kasa magana, zan yi magana. Shi ya kamata ki daka bani ba.

Lokacin da muka dawo da ni da Hajiya Saudiyya da akanki kika kaini asibiti aka min test sabida, sabida kina gudun kar na shafawa danki cuta.

Duk ba laifi bane, nisanta shi da ni, shine Kuskuren da zakiyi. Kasan an duba ni ko na tab'a sanin wani namijin aka ce miki lafiyata lau, sannan kika kuma hada baki a cutar dani, amma na tsallake.
Mamie, nasan bawai banda gata yasa kika tsane ni, ba kawai bako kaunata ne, kuma na yarda da hakan amma shi zai gaya miki kome! Tunda ya kasa magana.

...kin kashe aurenki, yau zaki kashe min nawa. Na ma rasa me zan kiraki keda Mommy na, sabida dukkanku son zuciyar ku, kuke bi!

Idan ban zauna da Ahmad ba kece zaki zauna dashi? Babu abinda zaki tab'a iya mishi wannan dole sai nice zan mishi amma kin kasa gane haka.

.Mamie ana barin halas dan kunya bawai dan son zuciyar mu, jin hana shi Magana zaki Cigaba da rufe min baƙi ne? Shi d'anki ne. Kuma nice sirrin shi, ita wancan da take gantalin da kin san wacece ita da a nera biyar ba zaki barshi ya zauna da ita ba.

Amma kin tsangwami rayuwar mu, kin hanamu sake ke burinki kawai su zauna da matan da kike so, bayan rayuwar duniya ba haka take ba, amma ke yadda kika tsara taki rayuwar kamar ba zaki mutu ba!

Ayya ita duniya! Da ban mamaki take, muna nan wata rana zaki tsinkewa don zuciyarki. Wallahi da kin sake wani abu ya sami cikin jikina.

Allah ko Ahmad bai isa, tunda kin hana shi Magana sai ki sanya shi ya miki abinda kike burin ganin ya faru."

Ina fadar haka na tashi tare da barin d'akin, nazo zan wuce ta dawo dani baya, ya d'aga hannu zata mare ni.
"Wallahi kika tab'a ni! Sai kin ga yadda ake.".

"Halwani ka gani zagina take!"

Shiru yayi kamar baya gurin, ya shiga hada min kayana. Sai Bala'i take mishi.

Abin tausayi yana tattarawar yana share kwalla.

Yana gamawa ya fito tare da mika min abaya na saka, sannan ya rike hannuna zuwa gidan shi na can, tun da muka isa nake kuka.
"Me yasa wanke ni da kayi, ya zama zargi? Me yasa Mamie bata daukar tashin hankali a bakin komai? Waye ya gaya mata ina da ciki?!"

Rike hannuna yayi, cikin tashin hankali yace.
"zaki bar garin nan, ina cikin wata irin masifa da tashin hankali, ban san Yadda zan gaya miki ba, amma cikin biyu za ayi d'aya bana son abinda na dauko da hannuna ya shafe ki.

Ina sane da kome, kije zan zo gare ki, duk da ran daddewa. Don Allah ki kula min da kanki, ina tare dake."

"Wai meke faruwa ne? Ka tsaya kayi min magana ko Mamie zata fahimce ka, me ta, ga wannan laptop din ki tafi dashi, karki tab'a rabuwa dashi, ki bar Mamie bazata tab'a fahimtar mu ba.

Nasan nan da wani lokaci, zaki iya tunanin wani abu a ranki, ban sani ba ko zaki iya min adalci idan halin haka ya taso, amma nasan ke din mai adalci ne, zaki duba kome a tsanake. Sannan insha Allah zan kira ki, kafin nan password ɗin laptop din HalYum ne, karki yarda koda Mamie ce, kai ko Rahbeel ban yarda ka bashi ba.

Kiyi hakuri! Zanyiwa Mamie bayani, akan matsalar mu. Sannan zan kira Hajiya muje, na kaiki, inda zaki samu jirgin korea na gayawa Zein, Zaki zo don Allah ki kula min da amanar kanki. Don Allah karki sake wani yasan abinda muka tattauna, kamar yadda muka yi a farko a yanzu ma muyi tsayayyar magana."

Na kasa fahimtar abinda yake nufin kawai ya dauki, jakata tare da riko hannuna muka fita, har gurin wata mota, ina shiga ya juya min baya, na zata da shi zamu tafi amma sai naga ya bar gurin, kafin nayi wani yunkuri an rufe kofar, haka na juya ina kallon shi, bai juyo ba.

.....
Mamie daga gidan Sarinah, gidan Kafaya ta wuce, bata same ta a gidan ba, dan haka ta shige d'akin Kafaya, tana bincike. Kamar ance ta jango wani drowe, kawai ta sauko wasu, joystick na roba, da ta zata na gaskiyar Ne, sai da ta buga wani tsalle, sannan taga dakyau ba na roba ne.

"Yawwa Baby! Dama na jima ina kwadayinki"

..... Allah ya kyauta, Mamie ta faɗa hannun Linah Kafaya.

---
Yau kwana biyar kenan! Ina kasar Qatar, asalin gidan Zein.
Hidima sosai yake min, tare da Dilshad.
Kana ganin su, zaka san cewa ana girmama juna, hada kayana nake sabida isowar Rahbeel, da Khuwailah, basu gaya min kome ba, amma da alamu akwai abinda ake boye min.
Daren ranar muka koma Riyadh, Inda na sami Mamie itama tayi laushi, amma tsanar da ta min yana nan bata goggu ba.


Ban san ta inda zan same shi ba, amma Mamie da Kafaya, sun sako Ni, a gaba kuma zan gansu suna waya da shi. Nice dai.

Ban san takamaiman abinda ya faru ba, amma naga kowa ya shiga hankalin shi, ga rigimar da Mamie ta kuno min na cikin jikina ya gaya mata ba nashi bane, na nemi uban cikin.

Ta kuma kara da cewa shi ya ce ta gaya min haka, sannan idan na haifi cikin toh shi ya salame ni,
Kunsan halin mutanen, dan haka ta kuma kara min da cewa idan ina ganin karya ne, na kira shi, kuma na gwada haka, daga Ni har Hajiya bai dauki kiran mu ba, nayi juyin duniyar nan, bai dauka ba.

Karshe sai turo min yayi kar na dame shi, kuma kar na kuma kiran shi, sannan na nimawa cikina Ubanshi dan bashi bane.

Iya razana na razana, a firgice nake kallon su, sabida sakon da aka turo a fili Mamie ta sa Rahbeel karantawa.

Yadda na fashe da wani irin kuka, tare da rike kafar Hajiya nace.
"Wallahi ba haka muka yi dashi ba, mun yi magana mai muhimmanci, dashi har yake ce min zai gaya miki, yadda kome ya faru.

Don Allah karki saka min shakku dan dama ya faɗa min haka na iya faru, wallahi babu batun wannan maganar a tsakanina dashi."

Wato Mamie ta gama rudani, tare da jifana da tambayoyinta, wasu na amsa, wasu kuma haka nake binta da ido, kafin wani lokaci ta jefa min tashin hankali a rayuwata.

Ta sanya min kaulani akanshi, karshe tashi nayi na bar falon.
.wasa wasa, na sanya damuwa a raina, na manta da addu'a,

Kai ta kai ko sallah nake, zan ta zancen zuci, karshe sai na manta da raka'a nawa nayi. A cikin wannan yanayin Hajiya ta sani muka dawo gombe, dan Papa Shima zai ajiye aikinsa.

Hmm! Wani irin kitimurmura ake haɗawa na fitar hankali, ba dawo daga. Jimamin ajiye aikin Papa ba, sai ga Rahbeel shima ya ajiye aiki, satin

Please Login or Register in order to submit comment