Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

batayi ba shi yafi kona mata rai. Shysa ta kasa kokawa dashi. Atuwa ta ajiye gallon din hannunta tamike.

"Ka chikata ta wanke bahayar mana. Fisabilillahi mata tana kasayarwa kaje ka cafkota. KO kyankyami bakkai Ardo? Allah ya kyauta."

Rumalle data gaji cikin zafin nama ta tattaro kafafun Ardo ta nanashi da kasa.

"Allah me alheri " Atuwa ta fada tana sarawa Rumalle.

"Kai Usmanu ku rikemun shi kafin na fito." Rumalle ta fada hade da komawa cikin bandaki tashiga karasawa tana jan tsaki.

Su Usmanu suka hau Ardo da kokawa. Ga gam suka rike Ardo. Baya da damar kwacewa saboda tsananin yadda suka tamke shi. Idrisu kuwa ya haye saman kafafun Ardo ya zaune

"Charanchas Ardodo. Allah me alheri."

Duk kuwa da a daddaure yake. Ardo bai fasa daga kai ya dankarawa Atuwa harara ba..

"Allah ya kwashe miki albarka Atuwa. "

Atuwa ta ja yar yarkaccacciyar kujerar ta ta zauna. Sam taki tarewa Ardo saboda tsananin yadda zuciyar ta ke 'kullace da shi. Ya cire su ya ajiye a matsayin matan sa. Bayan kowacce da igiyoyi biyu akanta. Ya shika su sau 'dad daya. Yadda ya yakice al'amuran yaran sa da yaran nasa baki daya tamkar ba shine ubansu ba. Cin su. Shan su. Tufatar da su, Makaranta kai dama dik wani hakkin su da ke kansa ya tattara ya ajiye a gefe. Tun wasu na jinjirai wasu kuma tun kan a haife su ya dora tsanar su a kambun zuciyar sa.

Rumalle tafuto daga bandaki tashige daki ko takan Ardo dake mutsimutsi da hannuwa bata bi ba. Kaya ta sauya ta zura hijabi ta fice. Kai tsaye ta wuce gidan mai unguwa. Bata jima ba ta fito ta dawo. Tabarmarta ta dakko ta shimfida a tsakiyar gidan. Atuwa na ganin haka ta sake gyara zaman da tayi akan yar kujerar ta. jimmamman daii na daga kuryar dakinta a rakube.

"Ku cika shi. Ga me unguwa Nan zuwa." Rumalle tabawa su Usmanu umanrni.

Ardo cikin takaici ya fashe da kuka yana kwashewa Yan gidan baki daya albarka .. Ba jimawa sai ga zagin mai unguwa na doka sallama

"Mai unguwa Yana neman iso. Assalamu Alaikum. Mai unguwa na neman iso. "

"Shigo zagi. Ku shigo. "

Mai unguwa da zagi suka shigaa. Nan Ardo ya fesa musu komai. Rumalle ma tafadi yadda akayi. Mai unguwa ya nisa kafin yace,

"Abu na farko dai shine an kafa.maka dokar hana shikan da kake wa matan ka. Da Kuma kara karen auren da kake yi. Bayan gida bata koshi ba. Iyali ba suturar kirki da sauran su. Dole ire iren matsalolin nan su yi maka yawa. Kuma zahirin gaskia inada masaniyar kyautar gida daka yiwa matar ka Rumalle . Domin a satin auren KU. Ta kawo mun takardar shedar mallaka ta gidan nan. Ta Kuma gayan yadda akayi.

"Zahirin gaskia banidaa ta cewa anan. Domin sheda de ta jima a hannu na. Kuma bazan iya cewa kyauta ta badu ko bata badu ba. Wannan sai dai sharia tashigo ciki. Amma kafin sannan inason ka san kai ne silar faruwar komai Ardo. Yawa yawan auren ka. Shi yake sa kake shiga cikin matsaloli. Sam yaran ka mata basa gaban ka. 'Da daya tal da Allah ya baka ka dorawa kulaficin so Allah ya dauke abinsa ya bar ka da halin ka. Yanzu kai wannan kadai bai isheka ishara ba? Matar ka kuna zaune da dadi ba dadi da yaran ku a tsakani. Haka kawai akan wata figalalliyar tinkiya ka shika ta. Sai gashi ta auri wanda yafi ka komai. Itada yaranta shar da su sun bar halin rashi sun koma na samu.

"Dan mijin Kuma shike auren diyar ka . Ko wannan bai isheka ishara ba? Ko kuwa su Hajara yaran Atuwa ba auren sukayi ba? Kowacce kuma tana zaune gidanta cikin koshin lapia. Dadin aure ya sa ka bawa matar da kayi sabuwa gidan ka kacokam shi kadai daka mallaka a duniya. Nan bangaren babu abunda ya shafeni. Na tura zagi da takardar ya kai kotin gangare. Muje can ayi shari'ah

"Amma kafin sannan inason jan hankalin ka Ardo kana saurara ko?"

Ardo ya fyace hancin ssa da kasan rigar sa kafin yace,

"Ni ban bata gidah ba Mai unguwa. Mahaukacin ina ne ni ?"

"Mahaukacin rimin kebe mana. Shashasha, sakarai, Sauna. Wanda kaf rimin kebe ba Wanda aka dauka wawa gara irin ka. Kayi haihuwa tayi 10 amma gaba daya bakada hankali. Hankalin ka daya ne wajen neman aure kawai. Gaba daya bakasan falalar haihuwar 'ya'ya mata ba. Toh ka saurara kaji:

"Bincike ta bangaren tarihi da zamantakewa duk sun tabbatar
da cewar 'ya'ya mata sunfi 'ya'ya maza tausayin iyaye da yin
biyayya garesu.
Zaka iya tarar da mutum ya haifi 'ya'ya maza guda biyar ko
sama da haka duk sun girma amma abin da zai ci ma ya
gagareshi saboda duk cikinsu babu mai tsayawa ya kula da
rayuwarsa bayan tsufansa. Amma duk wanda ya haifi 'ya'ya
mata koda kwaya biyu ne sai kaga sun taimakeshi, sun tallafi
rayuwarsa komai tsananin talaucin da suke ciki.
Haihuwar 'ya'ya mata babbar falala ce daga Allah wacce ke
samar da farin ciki anan duniya, sannan ga babban sakamako
a lahira kamar yadda hadisai da yawa suka tabbatar.
Misali yazo acikin hadisi cewa Manzon Allah (sallal Lahu
alaihi wa aalihi wa sallam) yace "Duk wanda aka bashi 'ya'ya
mata guda biyu ya kula dasu kuma ya tarbiyyantar dasu, to
sune suturarsa (wato zasu kareshi) daga shiga wuta"
Koda Manzon Allah (saww) zamu ga cewa acikin jumlar
"ya'yan da Allah ya bashi, matan sunfi yawa. Kuma zuriyarsa
ma ta hanyar yarsa mace suka wanzu.
"Ya mace rahama ce, jin qai ce, baiwa ce, daukaka ce,
mutunci ce, hutu ce, farin ciki ce, albarka ce, falala ce, kuma
alfarma ce.
Kuma hadisi ya tabbatar mana da cewa:
•Amatsayinta na 'ya ('diya) tana samar wa mahaifanta dalilin
shiga aljannah.
- Amatsayinta na uwa, tana samar wa 'ya'yanta Qofar shiga
Aljannah.
? Amatsayinta na 'yar uwa tana samar wa 'dan uwanta hanyar
shiga Aljannah.
- Mace ce ta fara gaskata Annabi Muhammad (sallal Lahu
alaihi wa aalihi wa sallam) alokacin da Allah ya aikoshi.
Nana Khadijah.
- Mace ce ta fara samun darajar yin shahada (rasa rai ta
dalikin kare addini). - Sayyidah Sumayyah.
- Ta dalilin mace ne al'ummar Musulmai muka samu falalar
yin taimama idan larura ta kamamu. - Nana A'ishah.

? Mace ce ta samu darajar samun sakon gaisuwa daga Allah
(SWT) - Nana Khadijah.
- Mace ce tayi jinyar Annabi (saww) a karshen rayuwarsa ta
nan duniya, kuma a hannunta ya koma ga Allah.
- Nana
A'ishah.
- Mace ce ta haifi Shugabannin samarin Aljannah, kuma ita ta
tarbiyyantar das - Nana Fatimah.
Wani Alkali yace "Acikin shekaru ashirin da biyar (25) da nayi
ina alkalanci, ba'a ta'ba kawo min shari'ar 'ya mace wacce ta
bijire wa mahaifinta ba. Amma nasha gain 'ya'ya matan dake
barowa gidan aurensu domin suyi jinyar mahaifansu"
Nagode wa Allah, yanzu haka ina da: A'ishah, Aminah, Fatima
Mukarramah, Fatimah Munawwarah, da Ramlat.
Fatana Allah ya rayasu, ya kula min da sha'aninsu ya tsaresu
daga dukkan abun Qi, tare da dukkan 'ya'yan musulmai baki
daya. Ameen.
DAGA ZAUREN FIQHU 07064213990 (10/06/1441)

"ka ji manazarta suka ce. Saboda haka ka zauna Kayi tunani. Domin arzikin da kake matukar son samu a 'yayaa mazan ta iya yiwuwa ajikin 'yaya matan zaka samu ninkin fiye da yadda kake muradin so. Toh Allah ya zabi abunda yafi alheri. Yasa abunda hukuma ko ince shari'ah zata zartar ya zama shine mafificin alkhairi. Gobe da yardar Allah sai muje muji yadda zasu yanke komi. Ni bari na tashi zanje ta'aziyya can kasan mil tara."

Ardo ya mike yabi bayan Mai unguwa. Ya rakashi har kofar gidah. Mai unguwar ya sake bashi shawara hade da neman fatan alkhairi abisa abinda zai wakana a kotu. Ardo ya gangara can karshen layi ya takure. Gaba daya ya rasa meke masa dadi a duniya. SOn ZUCIYA ta kai shi ta baro shi.


×××××××××.

Bayan sallar ishai. Haj Mari . Da hajia Amina sune suka yiwa Zaraah rakiyar kai amarya. Zuwa sashen su itada Maheer. Dake can karshen gidan an sake kawata shi. Bayan sun kaita ta gaggaysa dasu Haj Jidda da Iklima da suke a matsayin mahaifan sa Mata. Dukkan su suka kasa boye hassadar su.

Kuka kam Zaraah ta shashi kamar Wadda zaa dauke daga garin.. Sun kaita dakinta tare da sake bata shawarwari akan sabuwar rayuwar data shigaa na makarantar aure.

Sun jima suna ja mata kunne. Kafin su mata sallama su tafi. Maheer dake cikin mota tun dazu. Sai a sannan ya futo ya rufe motar. Hannunsa dauke da ledoji. Ya Sha ado cikin manyan kaya kalar sararin samaniya. Ya mjrza hula zanna bukar.. yanata tashin kamshin baccarat rouge. Ya jefa mint flavored gum a bakin sa. Yana taunawa ahankali .

Ya bude kofar ya sshiga ciki. Bakinsa dauke da sallama. Tafiya yake cikin takun kasaita. Ado da kamshi sun dabaibaye ilahirin gidan dake turare da turaren wutar yerwa incense and more.. Ya bude hanci ya shaki kamshin yana lumshe idanu .

A haka ya karasa dakin Zaraah . Tana lullube cikin laffaya. Sai kamshi ke tashi hade da shesshekar kuka. Ya karasa ciki yana sallama a hankali cikin wata iriyar murya mai tattare da nutsuwa da cikar Kamala .

Ajiye ledojin yayi a bedside drawer ya karasa kusa da ita. Taja can gefe tana kara sautin kukanta sosai.

Maheer ya samu kansa da janyota jikin sa. Wata nutsuwa ta rufe su a take. Duk shure shuren da take Maheer yaki cikata. Ahankali cikin muryar lallashi ya shjga rad'a mata a kunnenta,

"Haba Zaraah . Sarauniyar mata. Kukan ya isa dan Allah. Saurare ni da kyau kiji,.Ni fa yayan ki ne. Kuma nanda lokaci kalilan zan roki su Bappah su warware auren mu tunda ba ma son....juna KO ?" Ya karashe ahankali yana danne dariyar dake son fashewa.

Zaraah tasamu kanta da daga kai. Yasaka hannun sa daya yana shafa bayanta alamar rarrashi.

"Yauwa Zaraah.. Ko kefa? Yanzu dai bari na gaya miki abunda nakeso da wanda banaso ko?"

Ta daga kai. Tayi luf tana shakar kamshin sa. Munafuka🙄

Ahankali cikin wani salo da kwarewa. Maheer ya tsinci kansa da fadawa Zaraah abubuwan da yakeso da Wanda bayaso ..ya karkare da,

"Inada wani cuta...Ana ce dashi sleepwalking a turance. Yauwa saboda kakkiga wataa rana nazo dakin ki na kwanta cikin dare. KO na Miki na wani abun daban .Ba a hayyaci na nake ba. " Ya karasa fada cikin muryar umarni Kai kace gaske ne.

"Zaraah! Kinji ko?"

"Na ji. "

"Yauwa. Kuma ta yadda su Bappah zasu yarda a raba aurenmu shine idan sukaga muna kyautawa junan mu. Bama nuna kiyayya da sauran su..zakiga lokaci daya da mun same su da maganar zasu amince. Kin gane ko?"

Ta sake daga kai tamkar gaula.. Maheer ya saki murmushi kafin ya sake cewa,

"Zamu cigaba da karasa karatun ki na islamiyya a gidah. Kafin ki koma makarantar bayan wani dan lokaci . Kinji ko?"

"Eh"

"Yauwa yar kanwata Zaraah. Allahumma Bareek!!" Ya karasa fada hade da samun kansa da sakarwa Zaraah zazzafar sumba a goshinta. Ya tabbatar wa kansa a yan kwanakin nan yafara jin wani abu game da Zaraah .

Ta janye jikinta da sauri. Murmushi ya yi ..kafin ya janyo ledojin ya bubbude su,

"Gashi kamar yadda al'ada ta tanadar. Kici ki koshi Yar kanwata . Bari Yayan naki ya tafi dakin sa. Sai da safe ko?"

Ta samu kanta da girgiza kai da sauri. Maheer ya fuce yana murmushi. Ita kuwa dama kamshin kazar ya mata dadi. Nan danan ta wanko hannu a bandaki tayi bisimilla tana ci tana korawa da yogoberry.

Ta nannade sauran ta ajiye .Ta yo wanka ta zura kayan bacci ta haye gado bayan tayi alwala. Ta tottofe jikinta da addu'oi tayi kwanciyarta.

Cikin bacci tafara jiyo kyakkyawar rungumar da akayi mata. Tamkar wani zai kwace ta. Da sauri ta yunkura ta janyo wayarta ta kunna fitila .wa zata gani in ba Maheer ba👩‍?

Har zata tashe shi sai ta tuna maganar da yace mata akan cutar sleepwalking da yakeda ita. Dake batada man Kai saita koma ta kwanta. Dama abunda Maheer keso kenan. Ya sake kankame ta. Bayan kallo daya zakayiwa fuskar sa kasan shirya zancen sa yayi da sani.


Asubah ta gari. SO DA ZUCIYA dake Shirin Zama abu daya💯🤣


Unedited 😭
2/12/22, 11:37 - Buhainat: *Zafafa biyar na kudi ne, idan kina so ki karanta ki tuntubi 08184017082 or 09134848107* 

I'm on Instagram as @zafafabiyar5. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*SO DA ZUCIYA*

*NANA HAFSATU*


*35*

Maheer na ganin ta kwanta bayan ta kashe fitilar. Ya samu zuciyar sa da jin dadi da kuma nutsuwa. Ya sake rungumota sosai. Tamkar za'a kwace masa ita.

Zaraah gaba daya ba yadda zata yi ne. Don bil haqqi gani take ciwon sleepwalking din nasa ne ya tashi. Don haka ta daure kawai ta koma ta kwanta tana runtse idanu.

Ya sake rungumota yana shakar kamshin gashin kanta.

"Alhamdulillah Ala Ni'imatul Islaam" ya furta kasan makoshi yana jan numfashi.

Zaraah daketa tunanin yadda zata zame daga jikin sa. Tashiga tutture hannuwan sa. Maheer ya hanata ta hanyar janyo bargo ya rufe su baki daya.

Ganin karatun na neman canza salo yasa Zaraah zare hannunsa da karfi. Hakan yasa Maheer ya yaye bargon ya mike kamar wani roba roba ya fuce daga dakin.

Zaraah ta koma tabi lapiar gado ta kwanta. Tana sake tabbatarwa cikin zuciyarta lalle yanada ciwon sleepwalking din daya ce.

Shi kuwa Maheer koda ya koma dakin sa. Samun kansa yayi da sakin lallausan murmishi. Bai koma bacci ba. Bandaki ya shige ya dauro alwala ya tada sallar nafila. Ya jima a sujjada Yana kwararawa Allah godia a bisa auren da yayi. Da Kuma samun albarka acikin auren nasu hade da adduar neman zaman lapia da samun yara masu albarka.


×××××

WASHE-GARI


Zaraah ta jima tana bacci bayan sallar asubah da tayi ta koma. Koda ta farka ta Yi matukar mamakin ganin yadda rana ta dallare dakin. Alamun gari ya waye.

Da sauri ta mike tashige bandaki. Wanka tayo ta tsaya cikin bandakin tana yin turaren jiki dana lalle na dukkan na yerwa incense and more . Sai data kammala tsaf tukun sannan ta koma cikin daki. Ta shirya cikin wata riga da zani na atamfar Ghana mai launin ja da baki. Batayi wata kwalliya ba . Tadai shafa man baki da kwalli. Ta dakko katon hijabi ta saka

Parlorn ta bude kofa ta leka. Caraf ta hango Maheer. Ya zauna akan kujera yana daddanna laptop din gaban sa. Ahankali tashiga tura kofar zata koma. Maheer dake kallonta ta wutsiyar idanu ya kira ta da sauri

"Zo nan yar kanwata....!"
Ya karasa babu alamun daria a fuskar sa. Don karta gano wayo ya mata daren jia.

Ita kuwa dik a 'darare take. Jiya kawai take tunanowa. Gefe daya kuma tausayin sa ya shigeta. Na ciwon sleepwalking da yake da shi.

"Ina kwana?"

"Yana kwano! Ina zakije da hijabi ko sallah zakiyi?"

Ta girgiza masa kai alamun a'ah.

"To meya na saka hijabi...uhm? Ga abinci can a dinning je ki ci. Addayo ce ta Aiko aka lawo mana. Idan kin gama kizo mu Fara karatu."

Batayi musu ba. Ta mike ta nufi dinning din ta juya baya tanacin abincin ta ahankali . Kunya gaba daya ta lullube ta. Tana karasa ci. Takoma daga can gefe ta tsakure.

"Zo nan mu Fara. Dawo nan"

Zaraah ta matsa daga can, Tashi yayi ya koma kusa da ita .

"Yar kanwata. Zamu Fara da hadith"

ARBA'UNA HADITH (21) HADISI NA ASHIRIN DA DAYA


An karɓo daga Abu Amrin ko Abi Amrata, Sufyanu ɗan Abdullahi (R.A) ya ce, "Na ce, "Ya Manzon Allah (?)! Faɗa min wata magana a cikin addinin musulunci, wadda ba zan sake tambayar waninka ba game da ita." Sai ya ce, "Ka ce, "Na yi imani da Allah." sannan kuma ka daidaitu." Muslim (#38) ya rawaito.

Ya karasa fada, Hadi da saka kasan hannun sa ya goge labban Zaraah da karamun ketchup ya makale mata.

"Sorry datti na goge miki. Afuwan! Kin hakura? Uhm?"

Ta samu kanta da daga kai alamun eh. Maheer yayi murmushi kafin yace,


"Zamu dora da SHARHI na hadisin da muka katanta' Kina sauraro. ?"

Ta sake daga kai. Don gani take tamkar an sauya shi lokaci daya . Shi Mai zafin rai da Bata rai yau shiketa tarairayarta?

"Zaraah! Kina sauraro na?"

"Eh"

"Wannan hadisi ingantacce ne, Imamu Muslim ne ya rawaito shi. Dangane da bayanin imani da Allah, wannan ya riga ya gabata a baya. A duk lokacin da aka faɗi imani, mun san
yana da rukunai guda shida, waɗanda muka yi bayaninsu a cikin hadisi na biyu, a jerin hadisan wannan littafi mai albarka. Sannan kuma da sauran abubuwan da imani ba ya cika sai da su, duk yana cikin, "Na yi imani da Allah...." Daidaituwa kuwa, a nan tana nufin daidaituwa a kan tafarki madaidaici: Kada ka ƙara, kada ka rage kan abin da shari'a ta dora ma, ka nisanci dangogin abubuwan da aka haramta maka, ka yi ƙoƙarin neman halal a cikin dukkanin al'amuran da za ka yi. Wannan shi ne daidaito. Duk mutumin da ya dace da waɗannan abubuwa guda biyu, ga imani ga daidaito, to shi kenan sai aljanna. Shi ya sa Annabi (?) da kansa, aka umarce shi da daidaito, aka ce masa (Ka daidaita kamar yadda aka umarce ka). [Hud 112]."

Ya karasa a hankali a Kuma nutse.

"Biya muji"

Karanto masa ta shiga yi. Inda tayi kuskure ya na gyara mata. A haka suka karasa. Zaman kurame yabiyo ba. Ba jimawa Yan biyu suka shigo Mata. Hakan yasa Maheer fita ya Basu waje.

Bai dawo ba sai dare. Lokacin Zaraah harta kwanta. Ya shige bandakin sa yayi wanka ya sauya kayan bacci. Kai tsaye ya sake koma dakin Zaraah. Ya zare bargon ahankali ya shige ciki.

Zaraah najinsa tayi shiru. Ahankali ya saka hannun ya fuskanto da fyskar ta zuwa tasa. A hankali ya saka tattausan labbansa cikin na Zaraah. Ya shjga Bata rantsattsiyar sumba. Wanda ya samu kansa cikin zirarar da hawaye daya rasa na meye. Da sauri ya mike ya fuce dakin sa. Don idan ya cigaba yasan Wasa zai canza.

Murmushi yayi byan ya kwanta akan gadonsa. Ya janyo paper da bjro ya shigaa rubutu Yana murmushi bayan ya saka kwanan wata da lokaci.

"At the first kiss I felt something melt inside me that hurt in an exquisite way. All my longings, all my dreams and sweet anguish, all the secrets that slept deep within me came awake, everything was transformed and enchanted, everything made sense. Zaraah. Ki temaka ki mallakamin ZUCIYAR Ki. Zan shayar da ke SO tacacce marar gauraye

Na gaskata cewa tasirin dake boye a cikin muryarki sinadari ne dake gusar da damuwa ga duk wanda ya saurareta Aduk lokacin da naji muryarki inajin tamkar a wannan lokacin aka Halicci farin ciki.

kallon farko da nayi miki na fahimci cewa kina da baiwar da Duk wani da namiji zaiji yana soki. baya ga haka ke kyakkyawace , na dade ina neman hanyar da xan furta maki soyayyata sai dai xuciyata tana jiye min wani abu, daxaki amince da syyyt da nayi farin ciki domin na dade ina fatan naga cewa mun xamo masoyan juna ni da ke, hakik babu wata makusa a gareki domin kinada kyawun da kowa zaiso yayi rayuwa dake.

RIMIN KEBE
KOTI MAI SHARIAH GALI BASHARI


" Yauwa. Ina malam Ardo da matar sa Rumalle? Ku shigo alkali zai saurari shari'ar ku." Masinja ya karasa fada ya koma cikin kotu

Yayinda Atuwa tayi gaba Kai kace itace Wadda zaai shari'ar akanta.

"Allah me alheri. Yau za a kafta. Jar ubancan kayya kai. " Sahun gaba ta samu ta zauna. Yayinda Ardo dasu Rumalle kowa Yana muzurai suka samu waje suka zazzauna..


*_WAIWAYE......ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_*

*ZAFAFANKU BIYAR 🔥🔥🔥🔥sune suka sake dawo muku da wasu nau'in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA*

*_SANIN HALI.....yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_*

*GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi*

*JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE*

*_DEEN MARSHALL👉🏾 Mamuhghee_*

*_HALIN GIRMA👉🏾hafsat rano_*

*_TAKUN SAƘA👉🏾billyn abdul_*

*_SO DA ZUCIYA👉🏾miss xoxo_*

*_ƊABI'AR ZUCIYA👉🏾huguma_*

*DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR...ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL*

2👉🏾400
3👉🏾500
4👉🏾700
5👉🏾1000

*Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

08184017082

*IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU*

09134848107

*_HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽
#team zafafa biyar
2/17/22, 09:48 - Buhainat: ××SO DA ZUCIYA××

××NH××


××ZAFAFA2022 PAID BOOKS××


×××

   Mai shari'ah Gali bashari ya dawo daga ciki daya shigaa. Duk aka mike tsaye. Suka hada baki wajen fad'ar:

"Kottttt (court)"

Zama yayi . Bayan ya dan tsaya. Masinjan sa dake rike da wasu takaddu ya ajiye masa gabansa.

Mai shari'ah ya daga gilashi yana dan kallon mutanen dake wajen. Kafin ya mayar kan takardun. Masinja ya mike tsaye.

"Shari'ah ta gaba itace ta. Malam Ardo borkindo da mai dakin sa Rumalle.. Abisa kyautar da malam Ardo yayiwa mai dakin nasa acewarta ya bata gidan da suke ciki kyau...."

Bai karasa ba Ardo ya mike.

"Wabillahil lazi karya take ban bata gidah ba."

"Da girman Allah ya bani. Haka suke danginsu na borkindo . Wallahi karya yake ya bani."

"Zahiri 'kanzon kurege ne. Bai bata ba." Cewar jimmamman

"A hayye landantsan. Na rantse da gemun Ar" Cewar Atuwa dake daga hannuwa sama zata fara kwararo rantsuwa.

Bata karasaba. Mai Shari's ya mike saboda yadda suka gigita shi baki daya.

"Waya baku damar magana?" Cewar masinja. Da shi kansa sun hautsina shi.

Mai unguwa ya shigaa daga musu hannu alamar su dakata.

"Kai ne mai gidan? Malam Ardo ko?"

"Zahiri ni ne ya mai shari'ah"

"Wacece Rumallen acikin ku?" Mai shari'ah ya tambaya had'e da zama daga mikewar da yayi.

"Ni ce nan. Rumalle uwar su Usmanu ba. Mamallakiyar gidan Ardo baki daya."

Mai shari'ah ya danyi kasa da kansa saboda yadda dariya taso kufce masa. Ganin gaba tarin sakarmaru ne agaban sa.

"Ke kuma fa?"

"Ni ce nan jimmamman. Mai dakin sace ni ma."

"Sai ni Atuwa. Uwargidah kuma kujerar tsakar gidan malam Ardodo . Uwar su sailuba. Ranka ya dade suriki na ma anan yake aikin yamma idan ya taso. Yana auren 'yar waje na Hajara" Atuwa ta karasa fada bayan ko tambayar ta bai ba. Ta Kuma juya ta dallawa masinjan dake cewa tayi shiru harara.

"Masha Allah malam Ardo. Allah ya raya zuri'ah . Ya kuma hade kanku baki daya Aamin. "Mai shari'ah ya karasa fada hadi da kallon takardar gaban sa kafin ya sake cewa.

"Kafin sannan bari na danyi sharhi akan kyauta a musulunce. Kowa na wajen nan ya saurara ya kuma tsinci abin tsinta. Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jinkai. Dukkan yabo da godiya na Allah ne, Ubagijin halittu, Wanda da ni’imarSa kyawawan abubuwa suke cika, kuma Ya sanya yin kyauta da kyauta-yi cikin kyawawan dabi’un Musulmi. Tsira da Amincin Allah su kara tabbata ga mafificin halittu, Annabi Muhammadu dan Abdullahi (Sallallahu Alaihi Wasallam), wanda Allah Ya aiko shi, ya kasance jinkai ga talikai, kuma ya koyar da cewa kyauta da kyauta-yi ba ta rage dukiya; Amincin Allah ya tabbata ga halayensa da sahabbansa, sannan da duk wadanda suka bi gurabunsu cikin kyautatawa har zuwa Ranar karshe.

"Lallai, mafi kyawun cikar zance shi ne Littafin Allah (Alkur’ani), kuma mafi alherin shiriya ita ce ta Annabi Muhammadu (Sallallahu Alaihi Wasallam). Mafi sharrin al’amari shi ne wanda aka kirkire shi cikin addini; duk abin da aka kirkira cikin addini bata ne, wanda kuma karshensa wuta. Allah Ya kare mu daga gare ta. Amin.

"Shin kafin mu tsunduma ga sauraron shari’ah, Na duba na kuma karanta shari’ar dake gaba dama abunda ta kunsa. Naga kuma ya kamata mu san shin za mu ga shi ma talaka ko yana da irin gudunmawar da yake iya bayarwa a karkashin tsarin na kyauta da kyauta-yi? Domin kowa yana da abin da zai iya bayarwa:

"Shi Musulmi na gaskiya yana da dabi’a da hali na kyauta da kyauta-yi komai talaucinsa, kuma komai kankantar abin da ya bayar, ana lissafe shi a wannan matsayi. Kai, ya ma dai ishe shi a ce yana da shauki a cikin zuciyarsa da tausayin wadanda suka fi shi talauci, saboda yakan yi tunanin irin halin da suke ciki na rashi da babu. Duk yadda mutum ya kai ga talauci, to yau da gobe, sai ya samu wanda ya fi shi, shi ya sa hadisai da dama suke kwadaitar da mara shi ya bayar da komai kankantar abin da ya samu don Allah, gwargwadon karfi da iyawarsa, lamarin da zai sa ya ji

Please Login or Register in order to submit comment