Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

makulashe aciki.


Cikin gidah ma anyi walima da saukar karatun alqurani mai girma. Bayan an nadashin ne kuma aka yi masa rakiya wajen Hajiyan su yaje ya gayshe ta tayi ta saka masa albarka.


Shi da sauran yan uwan sa da suke tare idan aka tsame Alhaji jalaludden da ya bar estate din tun ana sauran kwanaki ayi nadin sarautar...


Hadaddiyar liyafa ce mai dauke da samfurin abinci na gidah da ketare. Bayaga haka ga masu hoto kala kala da masu bada tsaro na farin kaya suma sun zagaye ciki da wajen gidan.


Atamfa ce wata maroon mai kwalliyar ratsin silver color.. itace wadda Gwaggon court ta kawo bandir bandir tasa aka rarraba yara da manya yan uwa mata kowa ya saka ta zama ankon bikin nadin sarauta.a matsayin tata gudunmuwar...


Amaal na zaune akan dressing mirror din dakin su ita kadai... Ta yi kyau tamkar babyn roba. Sanye cikin atamfa ta wajen Gwaggon court data fitar.


Ba wata kwalliya tayi ba amman kwarai matuka tayi kyau.. Atamfar ta amshi yanayin tsarin jikin ta... Samfurin A shape da ya sha stones.


Ta daura dankwali design din channel O ta yane kanta da mayafin daya amshi atamfar.


Hoda kadai ta shafa fara sai kwalli da man leben marar kala. Amman da ke labban nata pink ne sai man leben ya sa kalar su ta dada turuwa sai sheki suke.


Gefe daya mild turaren data shafa sai tashi yake dukkuwa da kasancewar sa marar karfi.


Lokaci zusa lokaci takan daga wayar dake hannun ta ta kalli screen har yanzu basu kira ta ba.


Wayar tace tayi kara da sauri ta dauka ganin mahaifiyar tache,


"Kina Ina ne Amaal?"


"Ina daki Hayateey.."


"Anata hotuna da abbieyn ku yana tanbayar Ina kike? Yan uwan ki sunce basu sani ba. Da kina nan kika tashi kika tafi tun dazu."


"Haka suka ce? Yaa Hindu ce tache mu zo sashen mu mu huta, Muna zuwa kuma mun zazzauna daya bayan daya sai suka tafi suka barni da ita tanata danna waya can ta mike wai tana zuwa zasu kirawo ni. Kar na kuskura wai na dawo wajen ku basanan ayi musu fada. Su fa nake ta jiran kiran su dama mugunta kenan suka shirya mun?"


Hajiya jamila ta sauke nannauyar ajiyar zuciya kawai....Dan tashi tayi dama ta koma gefe take kiran wayar tata a waya...


Sanye take cikin atamfar da gwaggon court ta bayar a matsayin tata gudunmuwar. Amman sai ta dora dankarereriyar laffaya silver color akai ba kadan ba tayi kyau.


"Kina dakin naku yanzu?"


"Eh su nake ta jira fa ko calls dinsu kamar yadda Yaa Hindu tache."


Hajiya jamila ta yi murmushin dayafi kuka ciwo. Ganin dukkanin yaran gasunan sunata daukar hotuna kala kala da abbiey din na su mugunta suka hada mata ashe..


"Na zo ko Hayateey.?"


"Kizo.."


Tana katse kiran ta mike ta sauka... Ta nufi sashen da ake hidimar. Gashi da yar tazara a tsakanin su.


Sai sauri takeyi tanata dube dube ko zata hango wani ya taho a mota. Cikin ikon Allah kuwa sai ga Yayan ta Hamid cikin motar Hayateey .


Tana hanun sa ta tsaya tana murmushi. Yana tsayawa da motar ta bude ta shiga,


"Ina wuni Yaya?"


"Lafiya kalau sissy.... Yana ganki anan?"


"Hmm mugunta su Ya Hindu suka shirya mun. Sukace na zauna zasu kira ni ..Ashe karya suke trap ne. Sai yanzu Hayateey ta kirani tace Ina inane ? Nace mata Ina daki su ya Hindu nake jira su kira mu taho tare. Tache waye su hindun gasu can suna ta hoto da Abbiey. Yama tambayi Ina nake since basu sani ba. Sun dai ga na na tashi na fita tun dazu... Ya dace su mun wannan abun Yaya? Mena musu? " Magana take muryar ta na rawa saboda baki daya sun dagula mata lissafi.


"Kiyi hakuri.... Kinji lovely sis"


"Tohm Yayaa." Ta amsa shi hawayen data makale suka shiga zuba daga idanun ta


"Ki dena kuka please.... Precious hawayen sissy gida? Noo ki dena zubar mana dasu pls... Ungo tissue maza maza goge."


Karbar tissue din tayi ta shiga goge hawayen nata. Maganr sa ta bata dariya tayi murmushi mai sauri.


Daman haka yake son ya ga tayi daria. Don haka ya dan sake fadar wasu abubuwan da zasu sakata dariyar. Tayi dariya kamar yadda ya bukata,


"Yauwa ko kefa..."


"Nagode Yaya...."


Ya karasa da ita har cikin wajen taron.


"Kazo muje mana..."


"Munyi hotuna tun dazu a faada... Amma bara na miki rakiya."


"Yauwa."


Fitowa sukayi daga cikin motar zaka rantse Yaya da kanwa ne uwa daya uba daya saboda yadda suke tsananin kama..


Gashi yaci ado cikin wani arnen yadi silver color.. (Kalar toka) sai suka sake sajewa da atamfar jikin ta.


A haka suka jera suka shiga wajen bakunan su dauke da sallama. Haj jameelah na gano su ta saki murmushi.


Ta nufe su da sauri tana cewa,


"Yauwa... Ku zo a dauki hotunan ko?"


"Ai mun dauka a faada da shi"


"Banason musu Hamid... Na faaada daban wannan daban."


"Tuba nake ranki ya dade"


Dariya sukai baki daya su ukun. Kan maganar Hamid. Sika karasa inda sarki Junaid yake a tsaye masu hotuna nata faman aikin su....


Su Hindu tamkar su hadiye zuciya saboda bakin cikin ganin ta …


Sarki Junaidu na hango su ya fada’da murmushin sa… Ya saka hannu yana musu alamun su karaso fuskar sa kumshe da murmushi.


Amaal ta karasa kusa da shi , Ya janyo hamid gefen sa yayin da hajiya jamila ke gefen Amaal din. Sai suka bada wani style na daban.


Masu hoto suka fara baza musu hotuna ta ko'ina. Amaal ma ta daga wayar ta tayi musu harda vedio. Hamid ma ya karbi wayar Amaal din ya musu su uku. Sarki junaid da Amaal da hajiya jamila.


“Ranka ya dade ka tsaya haka. Yauwa hajiya ke dan dora kanki a kafadarsa. Yauwa kema kanwata koma tacan ki dora kan ki akan kafadar tasa. “ mai hoto ya basu style


Ai kuwa hakan sukayi ba karamin kyau hotunan sukai ba. Hajiya hadiza sai tsaki take jerawa


Data kasa rike hassadar ta sai ta mike ta mangaje me hotan ta wuce. Ya juya yana kallon ta. Saboda ga hanyoyi da zatabi Amman taki sedata mangaje shi tukun.


Haka dai aka cigaba da liyafa aka kare. Mutane suka fara watsewa … jirgi ya shiga jigilar mayar da nesa garuruwan su.


Wanda suke a gidah birnin nukaa kuma suka tattafi gidajen su. Yayinda wadanda suke a wasu kasashen suka tattafi airport.


KANDEM estate ta zama sai yan uwa da abokan arziki tsirari kawai.


Tunda suka fara hotuna har suka gama idanuwan sa akanta suke. Haka ta sake girma? Ya tanbayi zuciyar sa.


Kasa hak’uri yayi saboda BAKON yanayin da ya samu kansa aciki na so yayi mata magana.


Ai kuwa tana futa yabi bayanta da sauri yana kiran sunan ta,


“Amaal…”


Da sauri ta juya don ganin me kiran sunan nata. Hasken wutar kantarki ya haskaka ko'ina da gauraye…


Duk suka tsaya suna fuskantar juna. Gashi ya kafeta da idanu . Dakyar ta iya cewa,


.”Ina wuni? Yaya hisham.?”


“Lafiya kalau….. Kwana da yawa.”


Dan murmushi tayi kawai. Tana lankwasa hannuwan ta.


“Sai anjima” ta fada batare da ta sake cewa komai ba ta juya zata tafi,


Ya bu bayanta da sauri,


“Korata kike?”


“zanje na kwanta ne,. Akwai sch gobe.”


"Kina da waya?”


“Uhm… what about it?”


“Number ki zaki ban”


Tayi saurin girgiza kanta


,”Meyasa?”


"Saboda wayar karatu ce kawai bata amsa waya ba…An hana mu magana da maza"


“Ni ba yayan bane ba… ko kin manta?”


Ta kada kanta. Yayi murmushi ganin ya mata wayo ya sosa keyar sa yace,


“Ban number din to… zan zama online coach dinki, Duk abunda baki sani ba akan studies dinki don’t hesitate to ask me…”


“In shaa Allah”


“Fadi Ina jin ki…. Ga wayan dai”


Ya mika mata wayar tasa. Wallpaper din hotan sa ne agaban rigar tasa an saka hisham07


Ta shiga ta rubuta masa number ta mika masa. Yana karba tayi gaba da sauri har tana hadawa da gudu.


Shi dariya ma abun ya bashi… Ya kuma sake yabawa da nutsuwar ta sosai.


Ya girgiza kai kawai ya juya ya nufi sashen da aka sauke su…


::::::::::::::::::::::




Haka dai rayuwa ta cigaba da garawa.. Abubuwa na dad'i da akasin haka sun faffaru...


BAKON MUNAFIKI na cigaba da bibiyar zuriyar kandemi.


Gefe daya kuma su Amaal sun kammala makarantar secondary har sunyi jamb ma. Sun samu gurbin karatu a jami'ar.


ARDO K UNIVERSITY NUKAA (AUN)..




_ADVERT👇_


_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_


_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._


_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._


_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_


_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_


_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_


*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥




*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*


_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*




FURAR DANKO
Billyn Abdul


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at👇


1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k




_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥
[8/30, 2:21 PM] Hafsaat💞: _BM_


_NA:_


_NANA HAFSATU_


_PAGE: 21_


_BM vip arewabook: https://arewabooks.com/book?id=64a96774d6e097b6d856cfb9._


___




*ARDO K UNIVERSITY NUKAA*
(A U N)


Tana zaune a kofar twin theater lecture hall dinsu da ke department din da take na architecture. Direba take jira yazo ya dauke ta don ta gama lectures dinta na ranar...


Shiru shiru lokaci yanata ja dai taga ya kamata ache yazo ya dauke ta. Don haka ta mike daga zaunen da take ta karkade rigar jikin ta samfarin doguwar riga kirar Egypt. Navy blue color data sha kawaatuwa da wasu duwatsu masu kyalkyali.


Ta yane kanta da mayafin rigar ba kadan ba tayi kyau .. gefen kafadar ta kuma jaka ce blue colo,r zip din ma a zuge yake sakamakon littafai da suka cika jakar da laptop. Ga handsout ta rike a hannun ta.


Ba kadan ba ta kara wani irin musulmin kyawu me tafiya da duk wanda ya daga idanun sa ya dora akan ta..


Ta sake zama cikakkiyar budurwa, kyawun ta ya dada karuwa. Jikin ta ya kara murmurewa da cika sosai.


Hakika dik wanda ya dora idanun sa akan ta ya janye sai ya kara dauka ya dora akanta a a karo na ba adadi saboda zatin halittar da Allah ya azurta ta da shi...


Takawa ta farayi zata fita daga cikin department din zuwa waje.... Malamin su ya futo daga cikin ofishin sa yanata sauri da alama fita zai yi shima


Ta dan ja baya ta bashi dama ya shige. Har ya wuce sai kuma ya juya ya kalleta...


"Ina wuno?" Ta gayshe shi kanta a gefe.


Tsayawa yayi.. Ya dan saci kallon ta... Yadda take lankwasa yatsun hannun ta da suka sha jan lalle da zanen baki ya masa kyau kwarai matuka.


Shima matashin saurayin malami ne da yake ji da kyau da kuma kambun ilimi.. sanye yake cikin riga da wando yan kanti da suka sake bayyana kyawun sa na fulanin usul.


"Lafiya kalau..... A department din ecology kike?" Ya tanbayeta kai kache dagaske yake..sarai yasan a department dinsu take student dinsa ce amma ya samu kansa da zolayar ta,


"A'a..." Ta amsa shi kanta a kasa dai bata dago ba.


"Wane department?"


"Anan department din"


"Architecture ko linguistic da yake baya?"


"Architecture.."


"Oh really...level nawa?"


"Level one na ke.."


"Ahh fresher.... Jambito... Jolly just come jjc"


Ita dai Amaal murmushi kawai tayi. Wanda ya sake sanya shi sake ce mata,


"Amma ai kun gama lectures ko?"


"Eh."


"Karatu kike baki tafi gidah ba?"


"Ina jiran azo dauka na ne..."


"Okay Allah sarki.... Kingane ni ?"


Ta gane shi sarai. Amman ta grigiza kai alamun a'ah.. Yayi mamaki sosai yace,


"Ni din?"


"Eh.."


"Lalle bakya shiga lectures.."


"Ina shiga"


"Amma baki sanni ba a Malaman ku? Ni me daukar 1301.... "


"Oh okay"


Ya sake satar kallon ta. Wannan karon ta daga kanta tana kallon daya bangaren. Wai shi da students mata ke tururuwar son ganin sa da magana da shi har yan level 4 amman yau yar level one karamar yarinya yanata jan ta da hira amman tana sha masa kamshi


Ya samu kansa da jin haushin kansa. Duk da haka dai bai hakura ba ya sake ce mata,


"Care for a free ride?"


Tayi hanzarin girgiza masa kanta.. cikin sanyin murya tace,


"Nagode..... Za'a zo a dauke ni"


"Ya sunan ki?"


"Amaal...."


"Amaal..." Ya maimaita sunan yana jan sa.


Kada masa kai kawai tayi. Ta dan ketare ta gefen sa saboda yadda wayar ta tafara ringing ,


"An zo dauka na." Ta fada tayi gaba abunta


Juyawa yayi yana bin bayan ta da kallo. Wai yau abunda yake wa wadan su shi ake yiwa,


Don haka ya girgiza kai kawai yana murmushi yayi wajen shima. Yanata sauri zai je airport ya dakko babban aminin sa.


Mota ta bude ta shiga da sauri tana ajiyar zuciya. Gaba daya a tsorace take tunda malamin nasu ya tsaya yana mata magana har kawowar tafiyar sa.
Ta dan juya ta kalle shi ta mudubin baya alokacin dayayi reverse ya haye kan tigi.


"Ranki ya dade wanj abun kike so? " Direban ya tambayeta alokacin daya ga ta bawa mudubin baya nutsuwar ta baki daya tana kallo,


"Bakomai..."


"Muje?"


"Eh.... Muje"


Kai tsaye direban ya dauki hanya daga department dinsu na architecture zuwa kandemi..


Yana kai wa gidah ta nufi sashen su ta ajiye kayan ta. Ta shiga bandaki tayi wanka jadi da dauro alwala.


Kayan ta ta sauya zuwa doguwar riga ta atamfa.. Bata daura dankwali ba sai ta yafe kanta da mayafin karami irin na abaya.


"Ke Dr. Habibi Talba ya fara muku lectures kuwa?" Hindu ta tanbayi Amaal datayai hanyar kofa zata fita,


"Habibi Talba?" Ta maimaita sunan tanason tunowa,


Kanta a sama dai tanata son ta tunano inda taji sunan ta kasa ,


"Eh... Wani gaye me tsawo"


"Gaskia ban gane shi ba"


"Ke banason wasa.


"ko wani ne daya mun magana yau..."


Hindu ta tuntsire da dariya daga karshe taja dogon tsaki


"Habibi ne ze miki magana? Whole habjbj Talba ..gurl stop lying. Ba shi bane gaskia. Shi mata ma basa gaban sa. Baya ma tsayawa yayi magana da mace ko malama ce balle ke level one student. Da yake daukar ku ku wajen dari... Har zai tsame ki ya miki magana ke kadai .."


"Inaga wani ne malaman da yawa.."


Da hannu Hindu ta alamae dataje. Ta koma ta mayar da kanta ta kan pillow tana waka.


Amaal ta fita daga bangaren nasu tayi na mahaifiyar ta.


Suna zaune ita da Hamid dake aiki a computer dake gaban sa...


Ta gayshe da su duka. Suka amsa suna sakar mata murmushi.


"Hirar me ake Hayateey?"


"Hirar farin ciki"


"Akan meye"


"Abbiey dinku ne yace yana son ya dora yayan ki akan wani aiki"


"Ma shaa Allah aikin me?"


"Bai fadw ba tukun "


"Allah sa muji alkhairi"


"Aamin"


"Bari naje na gayshe da Hajiya"


"To sai kin dawo"


Mikewa tayi yar wayat ta a hannun ta ta fita. Har tayi bangaren hajjya sai kuma ta fasa..


Sashen da aka kwantar da kakan nasu ta ta shiga


Shiru ba kowa sai karar sautin al- Quran ni ke tashi ahankali.


Tanata sallama.ba amsa ba. Duk azaton ta ma ko suna can cikin dakin marar lafiyar.


Wata irin karar wahalaliya taji ana saukewa ahankali ga marayan kuka da akeyin ahankali ba sauti sosai. Shima sai ka kasa kai


Da sauri ta kutsa cikin. Ba kowa a babban parlorn sai karar tv da keyi tana nuna faifon bidiyon Aljazeera


Sautin muryoyi take ji suna tashi a dakin da marar lafiyar yake. Har zata murda ta shiga. Sai kuma taji sautin takalman kamar zasu fito daga dakin tayi sauei ta zagaya ta baya dayan window ta tsaya jikinta sai rawa yake..


Ana hango cikin dakin da muryar tasu ta 'yar net data yage ta jikin windon


Hannuwan ta dika biyu ta saka ta toshe bakinta alokacin data hango kakan nasu ya daga hannun sa dakyar yana rokon mutanen biyu da bata ganin fuskar su zai bayan su.


"Dama ashe yana magana.... Ko meyake faruwa? " Ta samu kanta da tanbayar zuciyar ta dake cikin waswasi..


"Dan Allah.... Ku kyale ni haka.. ku kashe ni kawai..."


Hawaye ne suka shiga reto a kyakkywar fuskar ta. Alokacin data hango daya daga cikin mutanen biyu ya dakko wata zundumemiyar allura taf da sirinji ya zurmuka masa


Ya saki kuka me tsuma zuciyar duk wanda ya saurara yace,


"Allah ba zai barku ba.... "


Allurar na gama shiga jikin sa. Ya shiga kakkafe jikin sa yana wani irin tari da sauke numfashi.


Can kuma luuu. Tamkar jikin sa ya shanye. Sai kache kayan wanki haka suka matsae da shi suka kwantar dashi akan gadon. Kaman kayan wanki


Ido kawai yake binsuu da shi. Duk wasu sassa na jikin sa suka sake dena aiki. Sai hawaye dake tsiyaya


Ya koma tamkar mutum mutumi kamar ko da yaushe baya magana sai jdanuwan sa da suke abude kawai. Baya iya motsa komai na jikin sa sai dai ataimaka masa ayi masa dukkanin abubuwa..


Amaal ta sake kafa idanun ta alokacin dataga daya daga cikin mutanen dake sanye da facemask baa ganin sa ya taka stool ya mayar da allurar da sirinjin cikin locker dake can saman gadon wajen ac baa ganin ta...


Neman waje sukayi suka zazzauna akan kujerun dake dakin..


Ba jimawa sai ga bappah jalaludden ya shiga dakin bakinnsa dauke da sallama.


Suna ganin sa suka mimmike sika bashi hannu suka gaysa,


"Kun gama komai?"


"Komai yallabai..."


Suka bashi amsa dukkanin su....


Wayar sa ya dakko... Ya shiga contact list ya danno wata number ya kira.


"Mungode sosai fa.... Sun aiwatar da komai cikin kwarewar su .. Yauwa."


Ya katse kiran ya mayar da wayar sa aljihun yayin da ya shiga taka musu zuwa bakin kofa,


"Ga wannan ku kara da kudin mota"


"Mungode yallabai."


"Muje da godia doctor. Sai wani checkup din kenan ko?"


"Eh."Cewar Dr Faisal..


Raka su yayi har bakin kofar fita suka shiga mota suka tafi. Ya yinda shi Kuma ya dawo ciki ya shiga dakin mahaifin na su ya zauna


Amaal da ke sandare a tsaye ta fita daga cikin sashen baki daya da sauri har tana tuntube jikin ta sai rawa yake.


Sauran kadan ta buge kan Bappah Nuraddeen dake tafiya zai shiga ciki


"Ke meye haka?"


"Ba... Bann... B"


Ta kasa magana gaba daya. Ya lura da ita sosai bata hayyacin ta.


"Me kikeson cewa?"


'ba komai Bappah"


"Kin tabbata?" Ya sake tanbayar ta cike da kulawa


"Eh Bappa"


"To shikenan... Je ki"


Ta wuce da sauri shi kuma ya shige ciki yana mamakin abunda ya sauya mata yanayi baki daya...




Zata shjga sashen Hajiya Maryam kakar su wayar ta tafara kara. Hisham ne ke kiranta. Kamar ba zata dauka ba sai kuma ta dauka ta gayshe shi.


Domin shakuwa sosai ta shiga tsakanin su.... Kullum ne sai ya kira sau nawa... Tun bata saki jikin ta da shi ba har sabo ya wanzu a zukatan su.


Tana karasa amsa kiran nasa ta shiga parlorn hajia bakinta dauke da sallama... Babbar tabarma ce irinta cin abinci dinnan akai aka shimfida a parlorn. Yayin da ma'aikatan ke ta jera abinci. Kana ganin hakan kasan tanadin wasu manyan bakin ake...


Hajiyan ta futo daga cikin daki tana dogaraawa da yar sandar ta. Dai dai lokacin da Aayaan ya shigo ciki shima.


Amaal ta gayshe su duka. Ta zauna a gefen Hajiya daga kasa tana matsa mata kafafun ta,


"Hajiya baki za'ai ne?"


"Eh takwara.... Yayan ku ne zai dawo daga kasar waje. zai dawo gidah gaba daya da zama."


"Yayan mu?" Amaal ta tambaya tana kallon Aayaan. Don bata san wane yayan bane..


"cousin dinki ne zai dawo mana.... Mighty, Al-mustapha jalaludden... Musty fresh




_ADVERT👇_


_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_


_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._


_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._


_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_


_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_


_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_


*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥




*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*


_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*




FURAR DANKO
Billyn Abdul


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at👇


1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k




_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥
[8/31, 6:56 PM] Hafsaat💞: _BM_


_NA:_


_NANA HAFSATU_


_PAGE: 22_


_BM vip arewabook: https://arewabooks.com/book?id=64a96774d6e097b6d856cfb9._


___




"Dan gidan Bappan ku... Kin manta Al-mustaphan? Ko da yake gaskia ba lalle ki iya tunawa ba.." Hajiya kakar su ta fada..


"Favorite baza ki iya tuna Musty Fresh ba?"


Ita dai Amaal shiru tayi baki daya... Don gaskia bata gane shi ba. Ta san dai akwai cousin dinta Al-mustaphan bappah jalaludden amma ta manta kamannin sa.


"Na san sunan sa Hajiya.."


"Amman baki sheda shi a fuska ba ko?"


"Eh"


"Gaskia ba lalle ta iya tuna shi ba... Kece karama a wajen Bappah ko?"


"Eh.."


"Tabbas. Ba zata gane shi ba Hajiya. "


Haka dai sukai ta yar hirar su su uku .. Duk kuwa da Amaal dauriya kawai take tana magana jefi jefi. Gaba daya abubuwan data ji ta kuma gano kawai take tunanowa...


Wayar Aayaan ce ta fara kara ya dauka ya kara a kunnen sa,


"Amma kai banza ne wallahi .. Gani nan to"


Hajiya ta dashare baki... Fuskar ta ta mamaye da farin ciki,


"Shi ne?"


"Eh..... Favorite ga wanda ya doke faadar ki nan awajen Hajiya."


Amaal tayi dariya kawai. Hajiya Maryam ta ce,


"Kowa a bayan takwara yake."


"Ai Hajiya kaf kandemi ciki da wajen ta kowa yasan Al-mustapha ne na gaban goshin ki."


Hajiya tayi murmushi kawai batace komai ba.. Aayaan ya futa ba jimawa sai gashi sun shigo tare


Aayaan ne agaba.. Al-mustapha na biye da shi a baya..


Kamshin turaren jikin sa ne ya fara nuna alamun isowar sa gun... Wani irin kamshi mai sanya nutsuwa da kwanciyar hankali ga duk wanda ya shaaka.


Yana sallama Hajiya na amsawa ta fara tafi,


"Dan yaye dan yaye..." Ta shiha fadar sunan da ta kan kira shi da shi. Dake ita ta yaye shi don haka akwai shakuwa sosai a tsakanin su..


Wajen ta ya nufa da sauri . Suka rungume juna.. sanye yake cikin kananun kaya yan kanti.


Rigar ja me ratsin baki sai wando naki.. kananannden gashin kansa ya kwanta luf.


"Hajiya barka da yammaci.... Na same ku lafiya? Ya jiki jikin naki? Allah yakara miki lafiya da nisan kwana mai amfani"


"Da imanin Allah dan yaye "


"In shaa Allahu Hajiya ",


"Ina wuni?" Amaal ta gayshe shi kanta akan wayar ta da take dannawa.


Bai amsa ba ya cigaba da cewa da Hajiya,


"Saura kadan hazl ya hanamu sauka a jirgi yau"


"Subhanallahi Allah ya tsare gaba.. Tana gayshe ka"


"Na amsa.."


"Baka amsa ba Malam.. zaka fada abun naka ko?" Aaayan ya fada yana girgiza kai.


"Baka amsa ba dan yaye."


Ya dan daga Kai ya dube ta..... Don baki daya bai san aina take azaune ba ma.. Ya dai jiyo muryar ta tana gaishe shi.


Gefen fuskar ta kawai yake hangowa saboda ta juya masa baya.. Kuma ta karkace zaman nata sosai..


"Lafiya lau"


Tabe baki tayi ta mike daga zaunen da take,


"Hajiya zan tafi ... Sai da safe."


"Ina zaki je? Zauna ki ci abinci kar ma kice kin koshi maza zauna."


Ba yadda zata yi don ba zatai musu da Hajiya ba. Sai kawai ta koma ta zauna


"Sannu da dawowa dan yaye..."


"Yauwa Hajiya ta.... "


"Takwara zuzzuba muku abincin."


Amaal ji

Please Login or Register in order to submit comment