Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._


_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._


_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_


_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_


_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_


*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥




*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*


_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*




FURAR DANKO
Billyn Abdul


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at👇


1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k




_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥
[9/7, 9:32 PM] Hafsaat💞: _BM_


_NA:_


_NANA HAFSATU_


_PAGE: 27_


_BM vip arewabook: https://arewabooks.com/book?id=64a96774d6e097b6d856cfb9._


___


*Yana* kishingide a parlon sa bayan sallar ishai.. wayar sa ce a hannun sa yana dubawa... Yana kuma duba wata takarda da ya ajiye a gaban sa. Fuskar sa sakale da gilashi na kara gani.


Hamid ne agabansa. Da laptop yana karanto wa sarki Junaid bayani. shima sarki Junaid din yana daga kansa idan Hamid yayi masa bayani..alamun gamsuwa....


"Yauwa gashi nan ranka ya dade... Million takwas dinnan ya za'ai da ita... A saka a bankin ko ....?


Zuruf sai ga shigar hajiya hadiza... Ta wurgawa Hamid harara tana duban sarki Junaid


"Sallamamme... Wai aache ka ajiye naka yaran a gefe. Kaje ka dakko wannan da da abunda ka hada da shi, Ka bashi amanar dukiyar kandemi gaba daya.. wai ajiyan sarki junaid. Sannan yaron da shi da jamila Allah tatsekaa zasu yi.. tatsa zasu yita yi maka kamar saniya.. ka dai canza tsari don mutanen kandemi suna yi da kai kan. ",


Sarki junaidu ya yamutsa fuska. Tinda ta shigo tana magana yana dauke da wayar hannun sa ya yana sosa goshin sa. Cike da kosawa yace,


"Kingama?"


"Da bngama ba ai bzanyi shiru ba ko"


"Hadiza saka lasifika ki kirawo sunan yan gidan mu ... Ki gaya musu abubuwan da ke faruwa..."


"Eh ai saboda ba tsoron su kike ji ba ai shiyasa"


"Sallamamme."


"Fita...walk out", ya fada a tsawace.


Ta futa da sauri har tana zubar da kwalla saboda bacin rai,


A hanyar fita sukai kichibus da su bappah Nuraddeen..


"Hadiza..."


"Ah hadiza ce?"


Kasa musu magana tayi. Ta daga kanta kawai ,, kuka ya kufce mata ta ja baya da sauri tana Jan hanci


"Meya faru?"


"Babu komai.. Barkan ku da warhaka. Na bar ku lafiya" Tana karasa fada tayi gaba tana share hawayen ta


Da sauri suka karasa shiga ciki... Alokacin hamida ya mike da computer a hannun sa yayi masa sallama zai tafi


Ya durkusa ya gayshe su da su sannan ya fuche bayan yayiwa sarki Junaid sai da safe


Gayshe da su yayi cike da girmamawa kamar ba sarki bane agare su,


"Meya faru da hadiza...? Naga ta futa tana kuka?"


"Ba wani abu Kawu.... Hadiza haka take kunsani kuma"


"Tabbas.. amman inason sanin menene ya hadu ku."


"Wai dan taga wannan yaron awaje na muna maganar budget da shi... Banker ne dan gidan kanwar Jamila marigayiya Rukayyah. "


"Kudin take so ba ka bata ba ko Ya ya?"


"Wai akan na bashi ajiyar kandemi.... Thou kawai fa account na sa ya bude na masarauta haka dik abun foundation zaa dinga sakawa a account din ya zama in charge... Meye lefi aciki Kawu? Ko kuwa Yaya?"


"Kasan mata sai ahankali....."


"Hakane kam.. Allah ya rufa asiri"


"Wato Kawu abunda yasa na nemi izinin ganawa da ku akan baba ne.... Ni a nawa tunanin nake gani kaman mu sake fita dashi waje a duba lafiyar sa... Ko kuwa? Tunda ya warware kuma Alhamdulillah yana samun lafiya fiye da baya,.. Amma wannan rashin maganar tasa yana damun Hajiya kwarai matuka.... Ya kuke ga ni?"


"Wannan batu naka yayi sarki., Allah yasa a mizani"


"Gaskia ka kawo shawara me kyau .... Musanman da yanzun naga likitocin basa zuwa Kuma... "


"Nima abunda na lura kenan... Inaga sunyi iya yin su "


"Hakane kam.. Toh Allah ya iya mana da iyawar sa Amin"


"Sai a gayawa su Gwaggon court yadda aka yanke...."


"In shaa Allahu "


"Allah ya dafa mana...... Aameen Yaa Rabbi"


"Toy bari muje.. ka huta lafiya"


"Sai da safe Kawu .... Sai da safe Yaya"


"Allah ya tashemu lafiya Amin"


"Alahumma Aameen."


Suna fita ya sauke ajiyar zuciya. Hadi da daga kansa yana tunani. Hajiya jamila ta shiga bakinta dauke da sallama. Ya amsa mata


"Barka da dare ranka ya dade"


"Barkan mu...."


"Ko zaka watsa ruwa?"


Girgiza mata Kai yayi alamun a'ah


"Ko kana bukatar space ne abbiyen su?"


"No kakki damu kiyi zaman ki."


"To ai ba nason damuwar da ke dabaibaye da Kai... Duk wani tsanani yana tare da sauki, Komai nisan dare gari zai waye Allah zai bayyana mai gaskiya... Dan Allah ka dena saka damuwar nan da yawa .. Dan Allah kaji?" Ta karasa fada muryar ta a raunane... Fuskar ta ta tatrare da damuwar data same shi,


Ya daga kansa ya kalleta yana murmushi. Yayi mata alama da hannu data dawo kusa da shi ta zauna,


"Godiya nake takawaa"


Dan murmushi yayi jin abunda ta fada. Ya saka hannu ya lakuce mata gefen kumatu yace,


"Gimbiya sarauniyar mata..... Allah ya miki albarka"


"Aàmin Aaamin ranks ya dade. Allah ya kara maka lafiya da nisan kwana mai amfani ya kara tsare mana Kai da tsarewar sa."


"Aameen Aameen" ya amsa yana mai kamo hannunta cikin nasa yace,


"Wato binciken da akayi na abubuwan da Amaal ta dakko a sashen baba su allurorin Nan?"


"Eh.... "


Wani murmushi yayi me cuwo yaCe,


"Ni mutane na bani mamaki wallahi. Akan neman duniya wai sai ka lalata lahirar ka? Akan wane dalili zaka dinga kokarin kashe mutumin da Allah ya raya kwanansa bai kare ba? "


"Ina sauraron ka abbieyn su..."


"Baki daya tsubbu ne acikin kayan nan Kashi 90.... Kashi goma na ciki kuma ana illata shi ne ta hanyar gurbanta duk wasu sassa na jikin sa ahankali. Wannan tashin da baya iyayi baya komai sai dai a masa... wai ashe wata allura ce da akewa doki kakkarfa turawa keyi ma bama a nan kasar hausa ba. Turawa kewa dokunan su don rage musu karfi. Kuma allurar dokunan ma rabi ake musu bayan kwana biyu ayi musu rabin. Amman babaa kullum daya suke masa. Ki duba kiga karfin doki ana masa rabi ace nutum daya sukutum. Badan yanada sauran kwana ba wallahi da tuni sunci galaba akan sa ya mutu...."


"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun.... Hasbun' Allahu wa ni'imal wakil... Kai duniya Ina zaki damu... Innalillahi wa inna ilaihi rajiun wallahi gaba daya bakaji yadda jiki na yake rawa ba... "


"Wallahi wasu basajin tsoron Allah ko kadan basa fargabar Allah ya karbi rayukan su ahalin da sike muguntar. Me zasuje su cewa Allah? Ko kinsan Karin ruwan da ake masa shima ruwan tsibbu ne na chusa cuta arasa maganin ta?"


"Kai innalillahi wa inna ilaihi rajiun....."


"Wasu abubuwan ma na manta.. Amma yarinyar nan amaal sai dai fatan Allah yasa ta gama da duniya lafiya Allah ya saka mata da mafificin alkhairin sa ya biyata da gidan aljanna. Ya bata miji nagari Wanda zai so ta ya kaunace ta har karshen raguwar su Amin"


"Aaamddn Amin."


"Na nemi iznin ganin su Kawu ai basu dade da futa ba..."


"Allah sarki ka sanar da su kenan?"


"Ban fada ba.... Na dai ce ya kamata a mayar da abbiey din asibiti..Amma a kàsar waje don gano dalilin dayasa baya magana.."


"Eh Hakan ya kamata gaskia... Allah yasa aje a sa'a "


"Aameen... Aaameen"


"Ina Aamaal?"


"Tayi bacci...."


Ya sauke nannauyar ajiyar zuciya kansa a sama


"Meya faru... Wani abun ne?"


"Bakomai..... Taci a mata babbar kyauta ne.... Allah ya mata albarka"


"Allahumma Aameen."


"Allah ya kareta da kariyar Sa....."


"Ameen abbieyn su.. a hado tea din?"


"Eh..... Banda sugar amma"


"Tom."


Mikewa tayi ta nufi dinning area komai a killace a Kuma jere yadda ya dache.


Ta hado masa tea din ta kawo masa cike da girmamawa ta durkusa ya karba yana murmushi hadi da shi mata albarka...




======================


Zuciyar sa che ke ta masa saqe saqe yana mamakin samuwar warakar Alhaji Muhamamd bayan dubban kudin da aka kashe na ganin an salwantar da rayuwar sa...


Mikewa yayi ya zura jallabiyar daya cire. Ya futo daga sashen sa ya nufi bangaren Alhaji Muhammad inda yake da bashi da lafiya..


Bude bangaren yayi ya shiga da spare key din hannun sa.. yana shiga ya rufe kofar da key ya haura sama.


Dakin ya shiga ya murda kofar ya rufe.. ya nufi Wani corrdorr ya ciro memoru card ajikin wata yar waya dake makale da CCTV.


Ya zauna akan kujera ya buda laptop din dake gaban sa ya kunnata.. Nan da nan ya sassaka dukkanin abunda zai bukata take faifen bidiyon ya fara haskawa na kowanne kwanaki har ya zuwa ranar da amaal ta hadu da Bappah Nuraddeen awaje lokacin data jiyo ta Kuma gano likitocin suna yiwa Alhaji Muhamamd allura yana kuka me wahalarwa...


Da sanda taje ta curo ruwan jikin sa da allurorin nan gaba daya ta saka aleda ta futar da su.... Yana karasa kalla ya dartsane harshen sa yana ciza cike da takaici.


Ya saka hannu ya dafe kansa saboda tsananin bacin rai. Computer ya janyo ya saka kafar sa akai ya dinga takata kamar ita tayi masa lefin.ya farfasata awajen yayi 'daya daya da ita.


Ya dauki memory card din ya nannade a tissue ya shiga bandaki yajefa a masai yayi flushing ..


Dama jiokin sa ya bashi itace.... yaja tsaki yafu a kirga..wayar sa ya janyo ya rubuta sakon da zai rubuta ya mike yana cewa,


" Uba da 'ya ke hargitsa mun dik wasu lissafi...... Junaid sai kayi dana sanin waiwayowar ka kandemi...Na hane ka kaki hanuwa ko? Ka dawo har ka karbi karagar mulkin kandemi..... To ka sani ka kana gab da shiga cikin matsananciyar musiba mai wahalar fita... Mu zuba!!!!!"


Ficewa yayi daga sashen gaba daya ransa a matukar bache yana sake harzuka tamkar wani kasurgumin zaki.....




*ARDO' K UNIVERSITY NUKAA*
(A U N)




Isa direba ya zura hancin motar cikin jami'ar dataci sunan marigayi mai martaba sarkin Nukaa, Alhaji Ardo kandemi...


Jamii'a ce da ke sahun farko na jerin jam'iyoyi da ake ji da su a garin Nukaa dama najeriya gaba daya.. dalibai daga kasashe ne ke zuwa karkashin ta suyi karatu...


Su ikhram ya fara kai wa departments dinsu daga karshe ya dauki hanyar kai amaal nata department din inda zasuyi lectures


"Hajiya karama aina zan ajiye ki ne?" Isa direba ya tanbayi Hindu dake owners corner tana tauna chingam.


"Department din da zaka kai ta...." Ta bashi amsa tana nuni da amaal da yatsa..


"Toh ranki ya dade..."


Ya kai su har department din. Amaal ta sauka tana gyara zaman jilbab din dake jikin ta Kalar maroon color. Ba kadan ba tayi kyau.


Yayin da Hindu ke sanye cikin riga da skirt sun matse ta .. halittun jikin ta sun bayyana ta yafa yalolon mayafi Kalar kayan .. tayi dauri rabin gashin ta awaje . Fuskar nan tasha foundation kamar amaryar karya. Ta zuba janbaki ja daya kara haskaka ta. Gefe daya Kuma turare ne ke tashi daga jikin ta...


Amaal ta mike ta fara tafiya. Hindu ta kira ta da,


"Ke..."


Ja tayi ta tsaya... Don ta saba ji da haka take kiran ta. Hindun ta taka ta sameta tana cewa,


"Ina ne office dinsa?"


"Wa?"


"Saurayi na da kikace eh malamin ku ne"


"Wallahi bansani ba"


"Karya kike"


"Allah bansani ba... "


"To tsaya dai...." Ta fada tana janyo wayar ta a jaka


Amaal ta dubu agigon dake daure a wutsiyar hannun ta. Batasan tayi latti a lectures. Amma gudun masifa yasa ta ja ta tsaya


Kiran sa Hindu tayi a waya .. sai data kira sau uku kafin ya dauka,


"Na zo fa...."


"Kina department din?"


"Eh...."


"Okay bani minti uku... Na fita bakin gate ne taho da aboki na... Yanzu zamu dawo.. "


"Alright."


"Na tafi ne?"


"No tsaya yazo seki tafi ..."


Amaal saura kadan ta fashe da kuka har ga Allah batasan lecturer din ya rigata shiga don baya bari ashiga idan ya riga shiga.


Sai da aka debi kusan minti Sha bjyar kafin motocin biyu su danno Kai parking lodge din.


Motar Habibi Talba ce agaba sai tashi a baya... Amaal na ganin motar malamin nasu tache,


"Gashinan yazo.. Na je?"


Hindu ta daga Kai ta haska mata harara.. Ta shiga gyara mayafin ta tana mayar dashi gefe..


"Baby H?" Cewar Habib Talba daya fito daga motar yana takowa wajen su. Idanun sa akan Hindu.


"Na'am Habibi..... "


Amaal na ganin sun hadu ta sulalae zata tafi.... Ashe Habib Talba ya hango ta,


"Zo nan..."


Ta waiwayo tana nuna kanta


"Ni?"


"A'ah.... Ni"


Komawa tayi kanta a kasa tace,


"Ina kwana?"


"Lafiya...wait tare na ganku kunsan juna ne?" Ya nuna amaal yana tanbayar Hindu..


"Step sister din sisters dina ce...."


"Omo...." Habib Talba ya fada yana smirking face


Amaal ita ko ajikin ta fatan ta su kyaleta ta tafi .


"Lecture na sai nan da one hour so kafin nan bari muje can mu zauna ko... "


"Sure... Why not?"


"Okay... Yauwa kinga ga motar aboki na can ki bashi key din nan kice ya jirani a office idan nagama zan zo sai mu wuce.."


"Okay tohm." Amaal ta saka hannu ta karbi mukullin.


Kai tsaye ta nufi motar.. Sai kallon motar take kamar akwai ire iren su a agidah. Wata zuciyar ta bata amsa da


"Ai ba dan ku kadai aka kera ba..."


Motar ta nufa ta kwankwasa ..yana danna waya ... Batare daya daga Kai ya dubi me kwankwasawar ba azaton sa habibi abokin sa ne. Ya sauke mudubin kasa,


Ta zura hannu ta mika mukullin cikin zazzakar muryar ta tache,


" Gashi inji Malam Habibi... Zan nuna maka office dinsa wai ka jira shi idan ya gama zai zo ku tafi..",


Cikin daga kai da sauri domin muryar ta na shige da wadda ke sanya shi nutsuwa ya daga kai kenan ya sauke akan kyakkywar fuskar ta.....


_ADVERT👇_


_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_


_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._


_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._


_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_


_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_


_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_


*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥




*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*


_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*




FURAR DANKO
Billyn Abdul


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at👇


1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k




_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥
[9/9, 12:24 PM] Hafsaat💞: _BAKON MUNAFIKI_
_(BA NA MUTUM DAYA BA NE)_


_NA:_


_NANA HAFSATU_


_PAGE: 28_


_BM vip arewabook: https://arewabooks.com/book?id=64a96774d6e097b6d856cfb9._


___


Kanta a gefe ganin bai karbi mukullin ba wulakanci ne ko bai ji bane ga lokacin lectures dinta na kurewa.. Hakan ya sa ta juyar da kanta tache,


"Ga shi inji Malam Habibi....w...,


Ta nemi labbanta da kasa furta sauran kalmomin da zasu karashe zancen...


Sai kache ba shine ya gama kalleta ba. Yadda ya hade fuskar sa ya fuzge mukullin kamar fadaa ita lamarin nasa ma sai ya fara bata tsoro kuma ganin kamar yaga wata dodo..


Bude murfin motar yayi... Ya koma ya rufe yana wani shan kamshi. Ita dai ganin yayi kamar be santa ba yasa ta juya tayi gaba ..


"Baki iya gaisuwa bane....?"


Ta jiyo muryar sa a bayan ta... Tana cigaba da tafiyar ba tare data jiyo ba tache,


"Ina kwana...?"


"Yana gidan ku ...."


Tabe baki tayi... Dama tasan salon ya gasa mata magana ne.. Har office din ta rakashi tache,


"Gashi...."


"Zo nan...."Ya kira ta ganin ta juya zata tafi,


"Dan Allah... Zan makara a lectures ne " ta fada tanata rau rau d idanu muryar ta a sanyaye a kuma shagwabe kasancewar haka take magana amman wani sai ya dauka yanga ce...


Ya samu kansa da son sake jin muryar tata... Yana wani muzurai yache,


"Wato kula maza kike ma ko?"


"What?"


"Oh yes.... Da kawar ki Habibi yake magana right?"


Takaicin tambayoyin sa tamkar ta daka tsalle ta sharara masa mari. Kasancewar shi din dogo ne sosai ya fita tsawo. Duk kuwa da ita dinma doguwa ce... amman ya kere ta a tsawp


"Tambayar ki nake.... Ko anan ma rashin kunyar zaki mun ne?"


"Kayi hakuri... Ni ba rashin kunya nake maka na... Sauri nake zan shiga lectures dan Allah..."


Har ya zura mukulli zai bude kofar office din sai kuma ya fasa... Yana takawa wajenta tana ja baya... Har ta kai karshen bango. Gabanta na tsananta bugawa tamkar zai fado. Gashi tayi masa kyau tamkar ya rungumeta da halal dinsa ce...


Ya saka hannu daya ya tokare ta.... Ta juyar da fuskar ta gefe... Kamshin turaren jikin sa na Tom-Ford ya gauraye ta baki daya..


Kasa kasa yace,


"Baki bani amsar tanbaya ta ba.... Kula maza kike ko?"


"Dan Allah ka k.....


Bata karasa ba wayar ta tafara ringing. Tayi haka zata dauka yayi sauri ya wafce ya matsa gefe ta bi shi tana rokan sa,


"Dan Allah ka bani wayata..."


"Yaya Hisham..... Waye Yaya Hisham? Kaf zuriyar Ardo kandemi bamu da Hisham... Ohh daya daga cikin samarin ki ne ko?"


"Yaya Hisham dan.... Dan aminin abbiey ne, Dan Allah kayi hakuri kaban wayata."


"Ai dole ki so na naki wayar ki saboda samarin ki kala kala.... Waya sani ma ko habibin ma saurayin ki ne"


"Ni malami na ne... Sannan ba wata kawata da ke kula shi. Wadda kake zaton ko kawata ce suke tare ba kowa bace fache Yaya Hindu.."


"Hindu?"


"Dan Allah kaban wayata..."


"Je ki lectures din ki dawo..."


"Dan Allah kayi hakuri ina amfani da ita a lectures wajen browsing. Dan Allah kaban wayata"


"So kike kawai na baki kiyi waya da beloved dinki Haysam"


"Hisham.."


"Oh harda gyarawa? wato na furta sunan saurayin ki ba dai dai ba ko?"


Langabar da kai tayi... Kanta a kasa tace,


"Ka bani wayata... Please"


"Magana zaki gaya mun?"


"Ni ban isa ba"


"Gashi nan karan kada miya dan abokin bappah ma kina ce masa yaya.ban cancanci ki kirani da yayan ba sai wani ka ban waya ta.... Ko dan kinga kin fara girma? Kina shiga cikin yammata? Ko kin dauka nima Ina cikin admirers dinki kamar Aayan?"


"Kayi hakuri...." Ta shiga bashi hakuri don dik bata ga abunda yayi zafi dazai dinga ga samata maganganu ba..


"Yauwa karki dauka nima ko irin Aayan ne me rawar jiki akan ki... Ko a kafa aka dauran ke sai na kunche..You're not my type, not even close. ...... "
Kasa cewa komai tayi... Tsananin kiyayyar da yake mata yayi yawa.


"Yauwa gwara ki sani don renin na ki yayi yawa... Ko mata sun kare ni Al-mustapha ba zan taba iya soyayya da ke ba.... Baki da abunda nake so a mache ke baki ma cika macen ba. Yanzu kike tasowa. Kina Wani ji da kan ki...


Bai karasa ba still kiran Hisham ya sake shigowa.. cike da takaici ya cilla mata wayar ta dauka da sauri zata tafi ya daka mata tsawa,


"Ke..."


Tsayawa tayi. Amman zucjyar ta sai ta kasa hakuri. Hawayen data ke makalewa na cin nutincin daya ke ta mata ne suka fara zuba a kyakkywar fuskar ta.


"Dan Allah kayi hakuri .... Yaya Al-mustapha!! Zan shiga lectures." Tana karasa fada tayi gaba sam taki waiwayowa tana ji yana sake daka mata tsawa tayi banza da shi...


Yaci mata mutinci akan lefin data basan na meye ba... Ya tozarta ta akan hukuncin da shi kadai yasan kan sa.. Ya gasa mata maganganu akan fadan daya kirkire shi haka kawai ba tare dama sanjya ba...


Haka ta karasa Ardo kandemi auditorium (one thousand sitters) inda zasuyi lectures. tana tafe tana tsiyayyayar da ruwan hawaye...


Agaban auditorium din taci karo da kawayenta su biyu a tsaye da sauran yan ajin... Suna ganin ta suka tako wajen ta


"Ke meye haka....kukan me kike?" Hafsat kawarta ta tanbaye ta


"Ai shine... Babes meya faru? Ko menstrual cramps kike?" Cewar Zaarah dayar kawar ta su..


Bata amsa su ba ta dubi sauran mutanen wajen tace,


"Ya haka? Ina lectures din?"


"Ke mike jira dama... Wai baze samu zuwa ba ya bada handout aje ayi karatu zeyi open test next class din sa...."


"Alhamdulillah....." Ta sauke katuwar zuciya tana goge hawayen


"Wait..... Gurlll. Karki cemun akan lectures kike kuka?"


"Hakane ma.... Zaarah kin gano ta."


Murmushi tayi jin abunda suka fada. Maganar da Al-mustapha ya gaggaasa mata suka sake zuwa mata kai... Ta girgiza musu kai kawai tache,


"Ko daya....thou rasa lectures dinma ya dameni. Na dauka an shiga..."


"Zo nan ki wassafa mana labari... " Suka ja hannun ta suka koma wajen wasu kujeru suka zauna,


"Meya faru....?"


"Plss babes"


"Kun cika damuwa wallahi.... Allah ba komai.. Ba wani abu"


"To fada mana koma menene dai..."


"Ni da ...."


"Yaya Hisham...?"


"Bassam?"


Dariya sika bata yadda suka fara fado sunaye... Ta girgiza kai kawai.


"To waye please?"


"Ni da Yaya na ne...."


"Mts... Shine kika kuka? Ai dama wasu yayyun maza haka suke sai a slow.."


"Chill babes.... Komai mai wucewa ne... Bare fadan yan uwa baya karewa idan ba aure kayi ka bar musu gidan ba."


Dariya tayi kawai tana kada musu kai alamun tohmmm...


"Muje gashassh suya muci abinci kafin next lecture din ko?" Cewar Zaarah kawar su.


"Yauwa daman Ina craving tsiren kodar nan.." Hafsat ta fada tana rataya jakarta


Amaal ta mike tsaye suka nufi gashash suya and cafe dake cikin jami'ar ta su..


__
__


Tana tafiya ya saka hannun sa ya naushi bango cike da jin haushi kansa da kansa...


Ya akai wadannan maganganun sika fita daga bakin sa? Babu dadi abunda ya mata gaskia..


Gashi ba zai iya bin ta yaba ta hakuri ba... Ya nufi inda yaga tayi ta bache masa da gani da alama da sauri tabar wajen..


Jikin sa a sanyaye ya saka mukulli ya bude ofishin ya shiga.. Mema kwan ya zauna sai ya nemi bango ya jingina da shi ya daga kansa yana tunanin bakaken maganganun daya gasa mata...


Abunda zuciyar sa take son fada daban .... Wanda bakinsa da labban sa suka furta daban..


Ya saka hannu ya dafe kansa yana jujjuya shi...


"Goddamn it!!!..... Kayi shirme Al-mustapha... Kayi shirme"


Knocking office din akayi sai kuma ya turo kofar ya shiga.. bakin sa dauke da sallama...


"Ahh... Guy kana Ina ne?" Ya shiga dube dube..


Ya juya zai rufe kofar ya lura da Al-mustapha ya rakube a bangon bayan kofar kansa a sama ya lula duniyar tunani....


"Maza... Meye haka?" Ya tambaye shi yana girgiza kafadar sa..


Sai a sannan Al-mustapha ya dawo daga duniyar tunanin daya tafi...


"Ka dawo?"


"Inata sallama ma na dauka baka man wallahi... Da niyar zan rufe kofar kuma sai na gano ka.. meya ke faruwa ne? "


"Bakomai... Kai na ne yake ciwo amma ya dena..."


Ya samu waje ya zauna... Shima Habibi ya zauna akan kujerar dake fuskantar wadda Al-mustapha yake akai...


"Ya kan yanzu?"


"Ya dena..."


"Yauwa ma shaa Allah... Kaga yarinyar data rakoka office dinnan?"


Al-mustapha ya muskuta ya gyara zaman sa yana kallon habubi Talba sosai,


"Yeah...what about her? Menene please.. eh?"


"Omo... chill! Kaga yadda ka gigice kuwa ..."


"Aboki na get to the point please.."


"Well.... Ni fa nayi mata... I want to wife her... Long story short ba wani kwana kwana maza so na ke na auri yarinyar nan ..."


Wayar sa dake hannun sa ce ta subuce ta fadi a kasa jin abunda Habibi Talba ke fada..


Habibi Talba da sauri ya dakko wayar yana kallon screen dinta,


"Kaci screen wallahi ta fashe... Meye haka?"


Al-mustapha ya karbi wayar ya jefata a aljihu yana duban Habibi Talba


"Kace me?"


"Malam wayar ka taci screen"


"Ba damuwa ai.... Amaal... Kasan Maryam Amaal ne?"


"Sunanta kenan?"


Wani dogon tsaki

Please Login or Register in order to submit comment