Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

_👺🏡👩‍👩‍👦‍👦_




_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_




_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
_®️NANA HAFSATU (MSS XOXO)_


__AREWABOOKS:MSSXOXO_
_WATTPAD:MISSXOXO00_






_FREE PAGE: 004_


_ADVERT👇_


_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_


_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._


_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._


_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_


_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_


_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_


____
ASOKORO




Sannu a hankali motocin suka dauke su zuwa hamshakiyar unguwar ta asokoro da ke birnin Abuja. Tsayawa bayyana tsaruwar unguwar da ke lullube da bishiyu ma bata lokaci ne.


Abu daya zuwa biyu zan iya fayyace muku kamar dankareren gidan Alhaji Abubakhar daya sha kudi ya koshi.


Dauke gidan yake da fenti kalar sararin samaniya. Sai shekin kalar toka ne ke walwali ajikin sa. Ga wasu bishiyu da wani jijjigaggen gate.


Motocin su suka kutsa cikin gidan dake dauke da babbar harabar farfajiya da zaa iya faka motoci da yawa.


Sai kukan tsintsaye ne ke tashi daga garden din da ke gefen wata kofa acikin gidan ta baya.


Ma'aikatan gidan suka tashi da sauri don temakawa bakin da suka ga suna ta fitowa daga cikin motocin.


Amaal na fitowa daga mota ta sauke nannauyar ajiyar zuciya. Sakamakon gajiya dake dawainiya da ita ga wani bacci dankararre dake kokarin rufe mata idanu.


Dakyar ta iya jan kafafun ta tabi bayan ayarin na su da suka shiga cikin gidan bakunan su dauke da sallama.


Alhaji Abubakhar ne agaba sai Hisham dake biye masa abaya. Sai tawagar su amaal dake bayan su.




Daga sama ta sakko. Kana kallon ta sau daya kasan matar gidan ce. Duba da tsananin kama da suke yi da Hisham din. Sai dai Hisham din ya debo tsawon mahaifin na sa Alhaji Abubakhar. Amma komai na mahaifiyar sa ya dauka harta murmushin da take yi.


Sanye take cikin wadatacciyar doguwar riga ta atamfa. Samfarjn style din T-bubu. Ta yane kanta da babban mayafi.


"Bismillan ku lale marhaba... Ku zazzauna dan Allah..Hisham basu nan su zauna mana ka koma can."


Amsawa suka shiga yi baki dayan su . Nan suka sake sabuwar gaisuwa daya bayan daya bayan sun zazzauna akan kujerun parlorn. Dake parlorn babban ne dake shake da setin kujeru uku kowanne kuma Turkish Royal. Da suka tsaru karshen haduwa.


Tashi tayi ta nufi wata kofa wadda itace zata sadaaka da kitchen. Tana kiran,


"Hadiza kuzo ke da su Laure."


"Toh Hajiya."


Cikin mintuna kalilan sai ga maaikatan sun fara ajiye tirarrukan abinci da abin sha.


"Ga bandaku na uku anan akwai biyu a sama. Ga wajen sallah can da hijabai."


Suka shiga yi mata godiya. Amb junaid na daga zaune bayan ya sha ruwan robar da ke hannun sa ya ajiye yace,


"Sannu da kokari... Mun tashe ku a tsaye. Allah ya saka da alkhairi."


"Bakomai...Mune da godiya. Allah yabar zumunci."


"Allahumma Aaameen." Yan parlorn baki daya suka hada baki wajen amsa ta


Mai gidan ta. Alhaji Abubakhar ya ce da ita,


"Yau buri na ya cika, babban bakon mu da nake burin kasancewar ziyarar sa agidah na yazo . Takanas da kansa da iyalan sa. Gaskia nayi matukar farin ciki. Shine Ambassador Junaid da nake gaya miki yana Madina shi da iyalan sa baki daya... Tun lokacin da aka bashi mukamin har ya zuwa ajiyewar aikin sa bayan shekaru hudu ne yanzu nake ji ko yallabai?"


"Eh shekaru hudu ne ranka ya dade" Amb. Junajd ya amsa shi.


"To kiga fa.... Sai yanzu Allah yayi ya waiwayo gidah Baki daya da iyalan sa. Bai fara sauka a koina ba sai gidah nan ya amshi tarin gayyatar da nake ta masa. Ina rokon ya zoyarci gidan ya zama bako na."


Amb junaid yayi murmushi kawai yana girgiza kai,


"Baka da dama ranka ya dade"


"Allah yallabai dagaske na ke. Ai kowa ya sani. Naciri babbar tuta. Har garin nukaa zani takanas nayiwa Hajiya godiya."


"Saboda transit din da mukayi anan?"


Suka tafa suna kyalkyalewa da dariya. Ragowar yan parlorn na tayasu. Idan ka cire Amaal da Hisham a gefe da ke wa juna kallon kasan idanu...


"Toh Allah yasa dai su iya cin cimar tamu ta nan ko daddyn Hisham?"


"Chi kai... Ai bamu baro gidah ba. Dukkanin abincin da ake ci a Nigeria munaci acan. " Cewar Hajiya hadiza tana karkada kafa daya kan daya.


Haka dai suna yar hirarrakun su jefi jefi, Suka kammala cin abinci tas. Don wanu abun ma ko tabashi basuyi ba. Dubada girke girken da akayi musu suna da yawa . Don haka sai sadaukar da wasu akayi ga mabukata awaje.


Bayan nan bandakin suka shisshhga suka yi tsarki. Masuyin sallah suka yiyyi. Mazan suka fita sukayi jam'i awaje. Kafin daga baya suka dawo ciki aka cigaba da hira.


"Ni fa nayi mamakin girman Hisham."cewar amb junaid.


Hisham dake gefe ya saka hannun sa a bayan kansa ya shafo keyar sa yana kakaro murmushi..


"Allah Alhaji? Dan dai ka dade baka ganshi bane. Gashi nan ya zama cikakken pilot."


"Kwarai kuwa tunda shine ya dakko mu ai daga can zuwa nan.. Don badan Allah ya temaka ma yayi dan tsaiko ba ai da tuni jirgi ya daga yabar mu. Amaal ta tafi siyan abu a shago lokacin ya kure."


"Ai gwara ku tsautsayi ne. Shi fa saboda tsabar wauta jakar wayoyin sa data kayan sa ya manta a shagon wani baban abokin aikin sa balarabe. Wai wani abu ya zube a rigar tasa yaje ya canza waye waye duk shirme dai. Nace wannan ai wauta ce. Sai ache saboda jirgin mu ne."


Hisham ya tsrae Amaal da idanu. Kallon su ya sarke tayi saurin janye nata. Shi kuma yaki dauke nasa sai ma sake kafeta da yayi da idanun har ta kasa nutsuwa sosai tanata mutsul mutsul awajen zaman ta.


"Menene hakane Amaal?" Cewar Hajiya J. mahaifiyar ta.


"Bakomai Hayateey zama na na gyara." Tana daga idanun ta suka hada kallo yayi mata murmushi. Domin sarai ya jiyo abunda ta fada da ma tanbayar da mahaifiyar tata ta mata.


"To ai tsautsayi ne wannan yana iya jawa kan kowa. Banga lefin sa ba ga mai lefi, wannan yarinyar fa ita da gangan fa tana sani tatafi siyayyar shago itama. "


Alhaji Abubakhar yayi murmushi jin abunda amb junaid ya fada. Ya dan juya ya kalli amaal din,


"Itama yar wajen ka ce?


"Ta karshe ce ma..."


"Auta ce kenan?"


Amb. Junaid ya daga masa kafin yace,


"Eh auta ce..... Sunan Hajiya taci ai."


"Haba?"


"Allah kuwa."


"Ma shaa ALLAHU mai babban suna... Uwata ta kai na. Me ake kiran ki da shi?"


Cikin sanyayyar muryar ta mai sanyin da dadi ga duk wanda ya saurara. Ahankali a kuma nutse cike da tarbiya ga biyayya ga wanda kanta a kasa tace,


"Maryam... Amma Amaal ake kira na da shi ...."


*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥




*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*


_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*




FURAR DANKO
Billyn Abdul


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at👇


1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k




_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥
[7/20, 9:32 PM] Hafsaat💞: _*BAKON MUNAFIKI!!!*_
_(BA NA MUTUM DAYA BANE)_
_👺🏡👩‍👩‍👦‍👦_




_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_




_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
_®️NANA HAFSATU (MSS XOXO)_


__AREWABOOKS:MSSXOXO_
_WATTPAD:MISSXOXO00_


_005_


_SHAFIN KARSHE NA KYAUTA/LAST FREE PAGE_
__


°°°Hisham ya daga kai da sauri ya kalleta, Itama wannan karon shi din take kalla. Ba wanda ya janye idanun sa. Mamaki take ashe ba balarabe bane. Yayin da shi dinma hakan take a tasa zuciyar. Yana mamakin dama ba balarabiya bace?


"Gata nan kaman Hisham itama ita kadai ce awajen mahaifiyar ta."


"Allah sarki .. Allah ya raya mana su baki daya ya musu albarka."


"Allahumma Aameen." Cewar amb. Junajd ya sake muskutawa ya gyara zaman sa. Kafin ya cigaba da cewa,


"Ga Hadiza fa ... Ko ka sheda ta?"


"Kwarai kuwa nasan hadiza ba kanwar su labbo ba?"


"Tabbas itace.... Lalle baka da mantuwa, To ga yaranta nan Abubakhar daya ci sunan marigayi yaya?"


'kwarai Yaya. Allah ya gafarta masa."


"Amin Amin, Muna ce da shi sadeeq, Daga shi sai mai bjye masa wancen safwan, Sai Na'eelah da najwa ga sunan a jere."


"Sai kuma Hindu da baka fada ba. Saboda ita agola ce? Wallahi Alhaji ka sauya halin ka. A wajen bare ma sai an raba hali. Hindu dai ko ban aure ka ba ai idan da kara kai ma yar kace. Tunda ni da kai a duk tsatso daya muka fito. Wannan 'ya tace itama Hindu amman ba shine uban ta ba kamar yadda bai lissafo da ita ba. Mahaifin ta dan uwa ne agare mu ni da shi. Mahaifin ta shine babban cousin a family din kandemi" Cewar hadiza matar sa ta fari.


Tamkar kasa ta tsage ya fada haka yake ji... Kunya duk ta dabaibaye shi. Gashi ita datai maganar ko a jikin ta tacigaba da danna wayar hannun ta.


Parlorn yayi tsit kamar ruwa ya cinye su. Chan dai Alhaji Abubakhar yayi breaking silence din yace,


"Su kuma wadannan yan biyun fa ga sunan kamar su daya baa gane su.?"


Amb junaid ya juya ya jalle su yana murmushi. Kafin ya saka yatsa yayi nuni da haj jameelah yace,


"Ga kuma jameela. Itace mai daki na ta biyu bayan hadiza. Kamar yadda na gaya maka dazu. Amaal ce kawai Allah ya albarkance ta da ita... Itama sai bayan shekaru.."


"Haka... Allah ya raya su duka Amin."


"Amin amin... Sai mai dakina ta karshe... Ruwaida.. Gata nan. Itace mahaifiyar yan biyun da kake magana yanzu. Su kadai ne yaranta."


"Ma shaa ALLAHU... Allah yayi musu albarka ya raya su duka Amin.."


"Allahumma Ameen."


Ya sake daga robar ruwa ya kafa a baki ya sha bayan ya sauke dankarereriyar ajiyar zuciya yace,


"Hadiza, Jamila, Ruwaida...." Ya kira sunayen matan nasa daya bayan daya..


Dukkanin sh suka juya suna kallon sa. Suka kuma kasa kunne don jin abunda zai ce,


Ya saka yatsa yayi nuni da Alhaji Abubakhar yace,


"Wannan shine babban aboki na da nake gaya muku. Kai ya wuce aboki ma ya zama amini. Ya kere wasu da suke ganin su yan uwan na ne na jini. Ya mun abunda a duniya bazan taba mantawa da da tarin allhairinnsa agare ni ba."


"Kabar maganar nan Junaid... Haba mana kamar wasu yara sakarkaru."


"Kyale ni sai na fada... Amini na ne... Alhaji Abubakhar mai murmushin kudi'. Ko a wani hali kuka tsinci kanku a duniya da rai na ko bayan rai na, Ku kuma godewa Allah daya azurta ku da shi. Ku kira shi a ko'ina ne zai zo yayi bakin kokarin sa. Mutumi ne da yake adali, Mai dattako, cikar kamala, alheri, Mutunci, gaskiya, Amana da rikon ta, tausayi, kawaici, kauda kai, hakuri, da Imani ga biyayya, ga ladabi ga kamewa, ga temako... Alhaji Abubakhar mutumi ne da baya gajiyawa wanda yasan halacci ba kuma ya mantawa da alkhairi komai tarin sharrin da ka bishi da shi, Yayi da jikin sa yayi da aljihun sa ...zuwan mu zuwa Nigeria ko ince dawowar mu da dik wani zuwa hutu da duk wata tafiya Dr abubakhr ya dauke mun ita ni da iyali na da ahali na gaba daya free of charge muke shiga kasashe...Allah ya saka masa da alkhairi ya biya masa dukkanin wasu bukatn sa Amin... Ga matar sa nan kuna gani sunan ta Aisha.. Ga kuma dan su da Allah ya azurta su da shi Hisham shine matukin jirgin daya kawo mu man... Bugu da kari ma jirgin mahaifin sa ne gashi a zaune na Dr abubakhr ne..


"Duk wani Hisham da kuka gani na gidan mai hotel da sauran su duk na de abubakhar ne yayi masa laqabi da sunan dan sa Hisham, kamar su: Hisham airlines,Hisham travel and tours, Hisham palace, Hisham showroom, Hisham plaza, Hisham oil and gas ltd, Al'Hisham international university., Hisham mart, Hisham luxury. Wadannan kadan kenan daga mallakin tarin kadarorin abubakhr. Babban oil mogul ne na kasar nan. Duk samda zamuzo Nigeria idan kukaga nasa an fita da motoci an musu full tanks to shine yasa lalle na'aika a dibamun mai kyauta... Kadan kenan daga cikin temammakin da yake yi ko ince ya saba yi ya ke kuma kan yi...Na roke ku da duk wanda yayi sallah ko yake addua ya dinga kamo sunan bawan Allah nan yana masa addua. Yana kuma rokon Allah daya kara kareshi ya azurta shi ya biya masa dukkanin bukatunnsa ya kuma yaye masa damuwar sa da lefukan sa. Allah ya saka masa da alkhairi ya jikan mabaifa."


Baki daya parlorn suka shiga amsa addu'oin amb junaid.


Haka dai suka karasa yar hirar dasike yi. Kafin akai su babban masaukin baki da aka tanadar acikin gidan dake dauke da komai na more rayuwar yau da kullum. Komai yaji babuce kawai babu agidan nan.


Amaal waje daya suke da mahaifiyar ta, daki ne yana kallon daki. Bayan tayi wanka a bandakin dake cikin dakinn ta zura babban hijabin dake ajiye akan sallaya ta zura kayan bacci aciki.


"Hayateey bara naje wajen Abbiey."


"Toh."


Fita tayi daga dakin ta nufi dakin da taga an shigar da akwatin mahaifin nata aciki.


Kwankwasa kofar tayi tana daga tsaye a bakin kofar ta waje,


"Shigo..." Ya amsa ta daga cikin dakin


Ta murda kofar dakin ta shiga bakinta dauke da sallama.


Yana daga zaune akan wata kujera. Gaban sa kuma laptop ce yana aiki acikin ta. Daga kai yayi ya kalleta yana murmushi


"Hajiyata"


"Naam Abbiey... Barkan ka da dare"


"Barkan mu dai uwata ta kai na
"


Karasa shiga tayi. Ta zube daga dan nesa da shi tana mai aika gaisuwar ta agare shi chike da biyayya,


" Abbiey barka da dare,"


"Me sunan yan gayu... Uwata tafi ta kowa."


Nan ma murmushin tayi. Tana mai hada yatsunta wajen lankwasa su cike da maduakakiyar kunya.


"Menene uwata ?"


Nan ma.shirun tayi tana murmushi.


Ya ajiye wayar sa da ke hannun sa yana nazartar ta sosai,


"Ina jin ki..."


"Abbiey dama... Dama ... "


"Ina jin ki Hajiya ta"


,"Dama zuwa nayi wajen ka na nemi gafara abisa lefin da nayi maka ,"


Ya danyi tattausan murmushi kawai yana girgiza kai,


"Uwata ai bata lefi...... Tashi kije na yafe miki duniya da lahira duk kuwa da ban rike ki da komai ba. Da lefin da kikai da lefukan baya da ki kai dama wadanda zaki agaba. Duka na yafe miki. Allah ya miki albarka..."


Murda kofar dakin akayi aka shigo. Hajiya hadiza ce. Tana tafe da kayanta samfarin riga da skirt da daurin ture kaga tsiya


Ta dubi Amaal shekeke tana yamutsa fuska,


"Hmm an turo ki ki kasa ki tsare kenan , Kai gaskia baki saar gyatuma ba. To kije ki gaya mata idan ta isa tazo nan ba wai ta turo ki ba. ... Tashi ki fita kema chan daya munafuka,"


"Meye haka hadiza?" Cewar amb. J. yana binta da kallon bata kyauta da abunda tayi ba.


"To ai gaskia ne. Naga ba kwanan ta bane. Na wane dalili ne zata turo yar ta kawai don ta zo ta h..."


"Ya isa haka Hadiza. Ba girman ki bane."


"To tashi ta fita. Ko na fadi abunda zai fi karfin sauraron ta wallahi."


Girgiza kai kawai yayi cike da takaicin ta dama kalaman ta marasa kan gado. Ya dubi Amaal dake tsakure duk ta dubibice tanata harde yan yatsunta na hannu yace da ita,


"Je ki ki kwanta uwata... Allah ya tashe mu lafiya. Ya kuma yafe mana baki daya Amin. Ki kwanta ki huta kinji ko?"


"Tohm abbiey."


"Ki saki ranki ki sawa zuciyar ki nutsuwa kinji? "


"Tohm abbiey." Ta bashi amsa tana kokarin murda kofar zata fita


Ya sake cewa da ita,


"Sai da safe. Baki mun komai ba kinji? Allah ya mana afuwa gaba daya Amin. Kar a manta da adduoin bacci kinji ko?"


"Tohm abbiey in shaa Allah. Sai da safe." Tayi saurin fita ta rufe kofar. Sakamakon wasu zafafan harara da hadiza ke aika mata .


Amaal na fita daga cikin dakin ta sauke ajiyar zuciya. Hadi da saka hannu ta dafe kirjin ta dake bugawa tamkar zai fado a kasa saboda tsananin tashin hankalin data shiga...


Samun kanta tayi da fita ta kofar da zata sadaaka da waje.. saboda gumin tsoron da ke zurara daga idanun ta . Wani kayataccen garden mai dauke da fitilu masu matukar kyau da kayatarwa da ke kallon kofar ta shiga


Tamkar tsakar rana saboda yadda hasken fitilu daban daban suka dallare wajen. Ta sanya hannun ta tana shafa fulawawwakin da ke shuke cikin wani gini me basu ruwa.


Ta sake sauke zuciya a karo na ba adadi alokacin da ta tuno mugayen kallon da hadiza ta rika jefa mata. Ta samu kanta da girgiza kai kawai can kasan maqoshi don ita ta dauka a zuci ma tayi tace


"Allah ya kyauta...."


"Amin... Ya kyauta abunda yafu haka ma.."


Da sauri sauran kadan ta saki fitsarin tsoro dubada tasan ita kadai ce awajen gashi dare ne. Uwa uba a zuciya take tunanin tayi maganar kawai taji murya da ta amsata daga bayan ta.


"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun... Ta fada da dan karfin ta." Hadi da sake bude baki zata saki zundumemiyar kara yayi saurin zuwa gaban ta, Hadi da saka tattausan hannun sa ya toshe mata baki...


Ya rankwafa har saitin fuskar ta yana bin zara zaren gashin idanun ta da kallo,


"Calm down...Matsoraciya ce ke dama? Meya kwan kiyi addua sai kara da zaki saki? A daren nan kusan kowa yayi bacci meya fito da ke ma?"


Tanata girgiza masa kai. Sam ya manta ya toshe mata baki da tafun hannun sa. Ya nata mata magana shiru


Data gaji ta saka hakora ta gartsana masa cizo ya saki hannun dakyar yana yarfe shi hade da runtse idanun sa.


"Akan wane dalili zaki cijeni?"


"Bakinta ka rufe mana..."


Ya juya ya dankara mata harara yana mulmula wajen da ta cije shi.


"Lefuka biyu kika mun...." Ya fada yana hura iska awajen data gartsana masa cizo


"Ba abunda na maka.." tafada tana tafiya hanyar fita zata gudu ya sha gaban ta da sauri


"A Madina kika zuba mun milkshake a jiki na... Yanzu kuma kin cije ni. "


"Duka ba da gangan nayi ba. Allah ya baka hakuri" magana take tana turo baki gaba saboda tsabar shagwaba ta autanci


"Zo ki dressing mun cizon nan da kika mun. Da hakoran ki kaman na vampire "


"Ka samu babba yamaka...ni ba muharramar ka bace." Ta fada tana tuna kashedin da Hayateey ke mata shekarun baya na karta bari namii ya taba ko da hannun ta ne zata haihu.


Dariya abun ya bashi gege daya kuma ya yaba da hankalin ta,


"Shekarun ki nawa?"


"I'm clocking sixteen...."


"Sha shida?" Ya sake tanbayar ta cike da madaukakin mamaki.


"Eh"


"Ashe ke girman finkaso ce da su buredi?"


'tubarkAllah..."


Ta tabe baki Hadi da ketarewa ta bayan sa ta fuce da sauri har tana tuntube tayi cikin masaukin su..


Ta shedawa Hayateey dinta dukkanin abinda ya faru da take wajen Abbiey dinsu dama lekawarta garden inda Hisham ya sameta


Mahaifiyar tata ta sake jan kunnenta sosai game da ilimin rayuwa. Sun dan jima suna yan hirarrakun su, Kafin daga bisani kuma subi lafiyar gadajen dakunan nasu bayan sunyi tsarki...




×××


Kwanakin su biyu a burnin Abuja dakyar amb ya amince suka kwan biyun ma saboda yadda aminin na sa ya dinga rokon sa dan Allah su sake kwana


Ai kwa suna cike kwanaki biyun suka biyi jirgin safe daga babban birnin Nigeria wato Abuja zuwa ga garin NUKAA.. wato NUKAA STATE dake nahiyar kasar Nigeria...


Motoci da masu tsaro ne suka je suka dakko su daga filin jirgi zuwa babbar unguwar datafi kowace unguwa tsadar rayuwa da manyan masu kudi .


A cikin unguwar katafaren babban gidan. Ko ince girman gidan kusan yankin wani kauyen.. Anan hamshakin gidan yake.


Gidah ne na yan uwa masu zumunci dai dai misali.. Wanda suka ta-da kai suka koma koshi da kudi... Ana damawa da su a nahiyoyi da ketare.


Babban gidah ne na yan uwan da suka hada manyan maaikatan gwamnati, manyan yan siyasa, alkalai na kotu, frofesoshi na jami'u, manyan malami na sunna da dai sauran su.


Estate daya ce me kama da gari guda ko karamin kauye saboda tsananin girman ta. Kudi yayi kuka agidan nan domun ya hada komai idan aka cire babu da dangin ta.


×× A tare motocin da sukayi convoy suka shiga cikin babban jijjigaggen gate din dake dauke da gidaje masu matukar kyau da tsada. Ciki harda islamiya, computer school , gym, garden, swimming pool da dai sauran abubuwan more rayuwa na yau da kullum...kaf birnin NUKAA ko na cikin kauyuka sunsan attajirar zuriyar KANDEM...




*KANDEM ESTATE......*




Babban gidah ne na zuri'ar yan uwa da suka kunshi rassa......












--------


_ANAN NA KAWO SHAFUKAN KYAUTA NA WANNAN LITTAFI MAI SUNA A SAMA.._


_KU ZO A DAMA DAKU CIKIN TAFIYAR ZAFAFA BIYAR AKAN KUDI MAI RAHUSA.. AKWAI DARUSSA SOSAI NA QARUWA ACIKI..._


_LITTAFIN BAKON MUNAFIKI YAZO DA WANI SALO NA DABAN..._


_YA ZATA KAYA NE A KANDEM ESTATE? SHIN WACECE KO WANENE BAKON MUNAFIKIN ACIKI?_


_YA RAYUWAR AMAAL ZATA KASANCE???WACCE CAKWAKIYA CHE ZATA CHUDE TA?_


_AMB JUNAID MAGIDANCI NE MAI MATA UKU DA TARIN YARA CIKI HARDA AGOLA DA YAKE RIKO..._


_TUKUNNA MA ME KANDEM ESTATE DIN TA KE CIKI NE? GA TARIN ZURI'AH DA SUKA HADU WAJE DAYA? ZUMUNCHIN ZAI TARWATSE NE KO KUWA MATSALOLIN CIKIN SA NE ZASU WARWARE ZUMUNTAR TA SAKE QULLUWA?_


_KADA KU MANTA AMAAL A SHAFUKAN KYAUTA TANA YARINYA YAR SHEKARU SHA SHIDA..YA ZATA KAYA IDAN TA SAKE GIRMA? MENENE ZAI KUNNO KAI KUMA....?_


_GEFE DAYA KUMA GA HISHAAM KYAKKYAWAN MATASHIN MATUKIN JIRGI MAI JINI A JIKA, WANDA YA TASO CIKIN DUKIYA YA BAWA KADARORI BAYA..._




_AAYAN, AL-MUSDHAFA, HAMID/HABIBI TALBA ..RIGIJI GABJIN FA KENAN TO SU KUMA WADANNAN DIN SU WAYE🙊???_


_DANKARI MAKARI...AKWAI KASURGUMAR CHAKWAKIYA MAI LULLUBE DA TARKO NA ZUMUNTA....._


_DUKA DUKA AMSOSHIN TAMBAYOYIN DAMA WADANDA BAN LISSAFO BA ZASU ZO MUKU NE CIKIN LITTAFIN NA:_


_BAKON MUNAFIKI_
_(BA NA MUTUM DAYA BANE)_




..
*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥




*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*


_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*




FURAR DANKO
Billyn Abdul


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at👇


1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k




_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥
[8/7, 7:06 PM] Hafsaat💞: _*BAKON MUNAFIKI!!!*_
_(BA NA MUTUM DAYA BANE)_
_👺🏡👩‍👩‍👦‍👦_




_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_




_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
_®️NANA HAFSATU (MSS XOXO)_


__AREWABOOKS:MSSXOXO_
_WATTPAD:MISSXOXO00_






_PAID PAGE:06_



*KANDEM ESTATE*


Babban gidah ne da ke dauke da jimillar yan uwa wanda suka hadu waje daya suka zama tsintsiya madaurin ki daya.


Dukkanin wanda ke a birnin Nukaa ya san da ahalin zuri'ar kandem. Fulani ne na usul. Tarihi ya bayyana cewa tsatson ahalin zuri'ar kandem sune suka kafa garin Nukaa..


Domin a shekaru masu tarin shudewa ance ahalin nasu ne suka taho suka yanki jeji suka baza dabbobin su. Suke kuma sassake bishiyu suna yin itache dasu suna hada wuta suna zama abakin ta. Shanuwa suke tatsa suna sha shine abincin su....


Ance kakan kakan kakan su wato Ardo

Please Login or Register in order to submit comment