Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

din yayi dadi sosai..


Washegari da safe Al-mustapha ya sulale kaman ya tafi office ya bar kasar.... A kuma ranar ne zaa fara hidimar babbar liyafar bikin da duk Nigeria ta dauka har kafafen yada labarai anata haskawa.


Yan uwa da abokan arzuka, Matan sarakuna, gwamnoni dana ministici, daktoci, furofesoshi,jakadu kai da duk wani who is who ya bayyana a babban dakin liyafar da za'a gudanar da biki irin na sarauta na, gimbiya Amaal.. Wato Grand kamu/ Royal mother's eve..


Duke decorations din wajen royal blue color ne da brown.. waje ne daya hadu wanda alkalami yayi kadan wajen zayyano muku haduwa da tsaruwar wajen... Sai dai mu kira shi da monumental event....


Hajia Jamila tayi shiga cikin wata rantsattsiyar lafaya golden color me kyalkyalin blue. Gwal kam ta zuba shi a hannu da yatsu da wuya da kunne... Lamarin sai wanda ya hasaso kawai..


Hakama dukkanin sauran yan'uwa kowanne yaci ado ya koshi cikin asoebi na Royal blue color..


Sai bayan da aka hallara ango da amarya suka shiga...kanta a nannade yake da mayafin daya dache da golden rigar da ke jikin ta tana jan kasa ... Rigar ta hadu hakama takalmin ta da yar clutch bag din dake hannun ta....itama ta zuba ruwan gold ba karya.. sai dai a lullube take cikin alkyabba blue color take kanta a kasa..


Ango Hisham na gefe cikin wani haddaden yadi daya sha aiki me tsada. Takalmin sa da agogon sa da hular sa dik kalar yadin jikin sa ne.. sai azurfar da ke kyalkyali a yatsan sa..


Algaita ce ke tashi.... Da kirarin dogarai da jakadai da ke gefe da gefe... Kawai kuyi picturing komai..


Magana ake ta TheRoyalWedding.... #H&MIslamicDuo💞🥳


_ADVERT👇_


_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_


_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._


_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._


_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_


_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_


_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_


*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥




*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*


_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*




FURAR DANKO
Billyn Abdul


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at👇


1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k




_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥
[9/22, 5:08 PM] Hafsaat💞: _BAKON MUNAFIKI_
_(BA NA MUTUM DAYA BA NE)_


_NA:_


_NANA HAFSATU_


_PAGE: 40_


_BM vip arewabook: https://arewabooks.com/book?id=64a96774d6e097b6d856cfb9._


___



*Bayan* shigar amarya da ango.... A kayi addu'oi.. Daga bisani MC yana kallon ipad din dake hannun sa yace yana umartar ango Hisham ya fita za'ayi kamun amarya ba 'bata lokaci..


Hakan kuwa akayi... Hisham ya mike wani abokin sa yayi masa rakiya suka fita waje suka koma mota suka zauna..


Daga nan kaman yadda al'adar su take aka fara mata kamu da nono a kwarya.. Yan uwa duk suka taru akanta. Bayan an kammala aka cire mata alkyabbar aka dakko sabon lace aka bude aka rufa mata akanta.. Yan uwan ango suka taso aka tsadance da kawayen amarya suka biya kudi mai tarin yawa aka kama Amaal amarya.. Aka yiyyi hotuna... Ango ya shiga shima akayi da shi ..


Daga nan kuma kawayen amarya suka dauki amarya suka fita da ita bayan an danyi photo-sessions da ita...


Mc ya sake bada umarni kan ayi shiru a kuma mike don karrama shigowar amarya da dangin ta tare da kawayen ta..


Ba da jimawa ba kuwa sai ga kawayen amarya a gaba sun fara shiga ciki. Daga baya kuma Amaal ce da yan uwanta baki daya sunyi anko mazan ma sun saka hula blue akan manyan kayan dake jikin su.


Gwanin ban sha'awa haka suka rakata har high table ta zauna. Ta sauya wasu kayan zuwa wasu yan gaske da sukayi matukar mata kyau sika kuma karbi jikin ta..


Hamid shine ya bada tarihin amarya.. don tausayi sai da mutane da yawa suka zubar da hawaye. Kasancewar ya bada takaitaccen tarihin yadda Amaal din ta shaku da mahaifiyar ta sosai. Da wasu daga cikin kyawawan halayen ta na biyayaya da yadda da kaddara. Ya bada tarihin makarantun da tayi tun tana karama har ya zuwa matakin karatun da take na jami'a.


Bayan ya gama kuma ya mikawa abokin ango mic inda shima ya bada tarihin ango Hisham da kyawawan halayen sa.


Atakaice dai dukkan su sunada kyawawan halaye kuma sun dace da juna.


Anci, an sha, an gyagije an raba kyautttuka an dau hotuna.. kawayen amarya da angwaye sunyi games suma sun ci gifts sosai


Daga karshe aka tashi daga hadaddiyar liyafar. Duk wanda ya halarta ya futa daga dakin taron cikin dimbin farin ciki marar misaltuwa.


Mota suka shiga shi da ita da a baya, Sai Yusra agaba. Abokin sa kuma na gaba yana tukawa suka koma kandemi.Yusra da abokin suka fita daga motar suka basu waje..


Amaal nata lankwasa hannuwan ta. Mamaki dankare a kirjinta ji take kaman mafarki wai yau itace ake bikin ta?


"Babe...."


Da sauri ta juya ta kalle shi... Kallon ta yake shima.. ya sakar mata murmushi yace,


"Tunanin me kikeyi?"


"Bakomai.."


"Dagaske..?"


"Uhm..."


"Shikenan... Kinga kyan da kikayi yau kuwa?"


Hannuwanta tasaka da suka sha kunshi ta rufe fuskar ta da su.. Cike da jin kunyar kalaman sa


Ya dan rankwafa yana kallon fuskar data rufe ya girgiza kai yana murmushi yace,


"Dole na biya kudin kwalliyar nan.. da farko dai waye yayi gyaran jiki? Uhm? Ta cancanci kyauta matuka..."


"Kamfanin turaren yerwa incense and more ."


"Ma shaa Allahu... Tana wane gari?"


"Kano."


"Ki aiko da account number dinta zan saka mata wani abun. Allah ya saka mata da alkhairi. "


"Inshaa' Allahu.. Aameen."


"Kwalliyar fa?"


"Beelanah beaute.... Itama a kano take."


"Photographer?"


"Zaarah. Ng itama a kano take"


"Wanda tayi abinci fa? Bana kasar wajen ba"


"La comida corner ce, Da rano scrumptious meals.."


"Ma shaa Allahu... Dika ki aiko mun da bank details dinsu. "


"In shaa Allahu.."


"Maryaam "


"Na'am..."


"Gobe zaa daura mana aure..."


Kanta a kasa tace,


"Eh.."


"Maryaam inaso ki yafe mun dukkanin wani abu danayi miki akan sani ko rashin sa. Dan Allah ki gafarce ni kinji?"


Amaal ta daga kai ta dube shi... Da sauri tace,


"Meya kawo wannan zancen Yaya Hisham? Ba abunda ka mun"


"Maryam! Dana saka zaa aura mun kema ai na cuce ki .. Ba fa so na kike ba Amaal biyayya kikaiwa iyayen ki kawai",


"Ban tsane ka ba Yaya Hisham"


"Amma bakya so na ai maryaam"


"Inayj mana "


"Son yaya da kanwa ba... Ba son zamantakewar aure ba ."


Batace masa komai ba.. kanta dai yana kasa tana lankwasa hannuwan ta,


"Ki yafemun kinji..?"


"Ba abunda ka mun fa... To nima ka yafe mun"


"Yauwa ko ke fa . Toh Allah ya miki albarka Amin"


"Amin..."


Bude kofa yayi ya fito itama ta bude ta fita. Yusra tayi murmushi tace dasu,


"Kun shanya mu kamar wasu kayan wanki.. gobe de za'a daura ku tattara ku tafi"


Hisham yayi murmushi yace,


"Ku gafarce mu ..... Bamu wani gaisa bane duk yau shine muka gaysa "


Abokin sa ya bashi hannu suka tafa yana dariya..


Har kofar sashen Hajiya jamila Hisham ya raka Amaal. Mutane nata tsokanar su,


"Sai da safe .... Allah ya tashemu lafiya ma'abociyar kyau da kyawun hali"


"Mu kwana lafiya Yaya hisham..."


"Yaya Hisham this Yaya Hisham that .. Ana cutata ana cemun wani Yaya bana so."


Murmushi tayi tache,


"To shikenan na daina."


Sai da suka shige cikin gidah sannan ya juya ya koma wajen abokin sa, abokin har yayi wajen mota yace da shi,


"Zo ka raka ni ciki "


"Okay tohm"


Sashen Hajiya Maryam suka nifa... Ba mutane sosai. Suka gaggaysa da su. Duk aka fita aka basu waje su da hajiyan. Ya sake durkusawa ya gayshe ta cike da girmamawa,


"Ango ango"


"Na'am hajjaju...." Ya faada a kunyace,


"Allah ya sa albarka da alkhairi kaji ko"


"Ameen hajia... Dama wajen ki na zo" ya fada yana lankwasa yatsu cike da kunyar data dabaibaye shi


"Toh Allah yasa muji alkhairi...."


"Aameen Hajiya.."


Abokin nasa ya mike ya basu waje ya fita.. hajiyan tace,


"Ina sauraron ka? Ko mu koma daaka yafu sirri?"


"Nanma ya isa hajia"


"Toh Allah yayi albarka"


"Aamin Hajiya... " Ya sauke nannauyar ajiyar zuciya,


"Ina sauraron ka...."


"Hajiya dama zuwa nayi na roke ki abisa abunda nake tafe dashi. Kuma ina fatan zaki duba zance na da tsanaki ki goyi bayana"


"Toh... Allah yasa muji alkhairi. Ina sauraron ka"


Hisham ya sake muskutawa yace,


"Dan Allah Hajiya ku dbi girman biyayyar da Maryam tayi muku"


"Wani lefin tayi?"


"Wallahi ba abunda tayi Hajiya. Zan iya ce miki tunda nake da ita Allah bata tabamun wani lefi wai dazesa naji haushin ta ba. Tana bani girma sosai. Kuma tanada nutsuwa da hankali ga biyayya. Don biyayyar cema ta amince zata aureni"


"Ina sauraron ka"


"Wato Hajiya nayi duba na tsanaki, Kuma na sassaurari wa'azi duk da ba wai nace abu ne mekyau ba kasancewar budurwa ma ca akai a mata zabin miji bazawara kuma a barta ta zaba da kanta"..


"Wannan zance naka haka yake"


"To Hajiya.... Magana ta gaskiya idan na amince aka daura aure na da Maryam wallahi wallahi wallahi na kwareta... Kuma Allah zai mata sakayya"


"SubhanAllahi meyasa kache haka hashimu? Bayan kowa yasan kai da ita kuna kaunar juna?"


"Wallahi hadin zance na ne na samu su baba nace da su soyaya mike ai muna waya da magana ta kafar sadarwa. Tabbas muna waya da magana ta kafar sadarwar amman karatu nake koya mata kuma wallahi amatsayin Yaya da kanwa muke maganar. Ni ne na sawa raina wani kuduri naji Ina son kasancewa da ita a inuwar aure. Na samu iyaye na da maganar sukace sai sun tabbatar idan tana sona.. da akayi maganar anan parlorn naki nema bata nuna ba haka bane tache eh munayi ta kuma amince. Wallahi hajiya na ha'inceta idan har aka daura auren nan gobe. Wallahi wallahi biyayya kawai takeyi amman ...


Bai karasa ba Hajiya ta girgiza kai kawai tace,


"Idan na fuskance ka so kake a fasa daura auren nan gobe idan Allah ya Kai mu?"


"Eh...."


"Me zaku gayawa mahaifan ku ?"


'wallahi Allah maryaam batada masaniyar dukkanin abunda na gaya miki. Ni na yanke shawara ta. Saboda zuciyata ta kasa nutsuwa. Banason Allah ya kamani akan abunda ba haka bane. Na mata kazafi na nuna da yardarta itw kuma tayi biyayya ta amince. Hajiya dan Allah ki saka baki kada a daura auren nan gobe idan Allah ya kai mu"


"Tirkashi..." Hajiya tafada tana mai sauke nannauyar ajiyar zuciya. Baki daya itama kanta ya kulle. Ta cigaba da cewa


"Ai idan kukayi auren zaku daidaita kanku hashimu .. zata so ka sannu ahankali " Ta fada cikin tabbatarwa, Ko kadan bata damu da ba daidai take fadan sunan nasa ba. Hisham ne take kiran sa da hashimu


Ya girgiza kai yana hada hannuwan sa yace,


"Wallahi bazan iya auren maryam ba hajia. Na amince a hadani da koma wacece acikin zuriyar kandemi amman banda Maryam ba zan shiga hakkin ta ba."


"Ni bansan me zan fada ba hashimu. Bari a kira su gaba daya.. Duk hukuncin da suka yanke shine daidai.. Ungo dannomun lambar Nuraddeen." Ta Mika masa yar wayarta


Karba yayi ya kira mata Bappah Nuraddeen. Ta saka a kunne bugu bjyu ya dauka ta sheda masa ya tatttaro kan kowa suzo bangaren ta harda Amaal.


Ta kuma tashi ta shiga dakin mai gidan ta Alhaji Muhammad shima ta kirawo shi. Suka gaysa da Hisham ya zauna akan kujera. Hisham din na gaban su a zaune kansa akasa


Ba jimawa kuwa sai ga tuttulowar su gaaba daya. Ciki harda sarki Junaid da iyayen Hisham din. Gaba daya dai suka hallara


"Maimaita abunda kache hashimu"


"Hisham ne Hajia" Yusra ta fada tana dariya


Duk suka danyi Daria. Hisham din ya dan saci kallon mahafin sa. Muryar sa na dan rawa ya zayyane komai tun daga farko ya sake fada ya karkade da,


"Wallahi wallahi wallahi bazan iya auren maryaam ba. Idan na bari aka aura mata ni hakika na cuceta, Na ha'inceta, na zalunceta na kuma shiga hakkin ta kuma Allah ba zai bar ni ba. Tunda karya na hada na fada muku cikin tabbatarwa. Amma ita ta amince saboda ganin girman ku da tsananin biyayyar ta tace eh hakane muna soyayya. Wallahi Allah amatsayin Yaya da kanwa muke da ita tamkar na jini. Hasalima ni coaching dinta nake Ina koya mata wasu abubuwan na makaranta ta waya ko messages . Bappah, Baba, Kaka, Hajiya... Dan Allah ku gafarce ni.. ku karbi roko na kada ku aurawa Maryam ni gobe idan Allah ya kaimu wallahi kamar yadda na fadawa Hajiya yarinyar na batada masaniyar abunda nake gaya muku dai dai da rana daya batada daba mun complain na zaluntar ta da nayi ba nace muna soyayya har aka sa mana ranar aure ba, Bata taba nuna mun ba ai karya na shirya nace muna soyayya ba.. Dan Allah karku aurawa Maryam ni. Karku bata mata rayuwa ta auri wanda takewa kallon yayan ta na jini .... Ni Hisham na amince a aura mun wata daga cikin wannan zuriyar na kandemi goben idan Allah ya kai mu.. amman Dan ALLAH jar a aurawa maryam ni. A barta ta auri wani daban.. Dan Allah"


Duk sukayi shiru...Tamkar mafarki ko a kallon wasan kwaikwayo na talabijin. Alhaji Abubakhar ya mike cikin zafin nama ya tattare kasan hannun rigar sa jikake,


'Taasss.. Faaas, Chasss' Ya sharara masa maruka guda uku lafiyayyu a gefe da gefen fuskar sa.


"Mutumin banza... Daman sharri kayi mata ka cuce ta? "


Ya sake daga hannu zai sake marin sa Bappah Nuraddeen ya rike masa hannu. Sarki Junaid ma ya tashi ya janye Hisham daga wajen ya mayar da shi gefen da yake,


"Meye abun marin nasa? Haba Abubakhar? Idan ka bibiyama kila amaal dince ta nuna bata so" Cewar sarki junaid.


"Walahi daidai da minti daga maryaam bata taba nuna mun batason aurena ba. Ba kuma taba cewa ai karya nayi mata ba ba soyayya mike ba. Wallahi Allah " Hisham ya fada cikin tabbatarwa


"Yo ai ni gaba daya ma na rasa abunda zance..."Bappah Nuraddeen ya fada yana tallabe habar sa cike da damuwa


Amaal dake gefen Hajiya jamila sai raba idanuwa take. ita da tai tasan kalau fa suka rabu da shi ya rakata har kofar shiga sashen su.


Haka dai akayita maganar ana neman bakin zaren. Dakyar dai aka hakura kan ba zaa daura auren da Amaal din ba ganin yadda Hisham yake zubar da hawaye sosai kan inde aka daura to wallahi ya shiga hakkin ta kuma Allah ba zai barshi ba.


Ana cikin maganganun ne Hajia maryam tace


"Wai har yanzu dan yaye be kira waya ba an san inda yake? Tukunna ma yana Ina jama'a?"


Duk sukaita tofq albarkacin bakunan su. Yusra dake gefe tace,


"Na kira aminin sa. Habibi Talba yace Hamma Al-mustapha ya tafi Manchester England"


Bappah jalaludden ya bude baki yace,


"Ina?"


"Manchester"


Ya dubi hajia Jidda mahaifiyar su yusra yace,


"Ya gaya miki me?"


"A'ah..."


"To me yaron nan yake nufi?"


"Bappah Al-mustapha ba zai iya zama ana auren amaal ba. Shi yasa ya tafi." Aayaan ya fada cikin tabbatarwa.


"Wai yaron nan dama yana kan bakan sa?"


Hajia maryam tace,


"Ni kallon sa kawai nake... Ya bude baki yayi mata magana yaki sai zurfin ciki. Yadda yake nuna mata kamar yafu kowa tsanar ta a duniya. Bayan tun tana zanin goyo yake kaunar ta."


"Wai Al-mustapha dai namu?" Bappah junaid ya tambaya yana zare idanu,


"Shi dai...Muma rufe mana yake. A nasa haukan ba zamu gane ba. Tun muna Buckingham muka sani. Hotunan ta tun tana karama har na wanda ta girma, ko a'ina ya same su oho, yana nan dasu."


"Ammw yaron nan sakarai ne"


Ita dai Amaal jin su take tamkar a mafarki. Duk abubuwan da suke fada yana shifa ya futa ta dayan kunnen na ta. Al-mustapha kuma? Kai gaskia ba dai ita ba. A duniya ba wanda ya tsane ta sama da shi


"Ni ma na lura yana son ta sosai... Wanda ya zauna anan dinnan ko ranar da muke nan duka?" Hisham yake tambayar Aaayan.


"Shi dai. Ai mugun gara ne dab wahala. Wai shi sharukan baban soyayya ya hakura ya bar ma ka."


Sika saka dariya baki daya... Bappah Abdullahi yace,


"Kuma ba shine ba shida lafiya bane bayasan damuwa sosai?"


"Shine . Can daya Wawa. Ku rabu da shi ya karaci zaman sa acan idan yaga dama ma kar ya waiwayo gidah gaba daya" bappah jalaludden ya fada cikin halin ko in kula


"Ba za'ai haka ba Yaya.. da kai da kaya ai duk mallakar wuya me... Abunda yayi Al-mustapha shi yayi Amaal "sarki junaid ya fada


"Ba fa za'ai abundq kake tunani ba. Ni ba sakarai bane. Ba zaa shiga hakkin yarinya ba "


"Ni na amince tunda 'da na ne" sarki Junaid ya fada


"Ni kuma ban amince ba tunda 'ya ta ce" Cewar Bappah Jalaludden


Yan parlorn suka saka dariya baki daya. Bappah Nuraddeen yace


"Mutane sunzo dai ko'ina gari ya cika idan baa daura aure gobe ba da matsala. Idan Kuma akwai wata hanyar da za abi to tun yanzu a sanar musu a daren nan kan an fasa daurin aure gobe "


"Zaa daura aure inshaa Allahu .. hjsham da ne awaje na. Kuma ya roki alfarma dole zan cika masa .. wa kake so acikin zuriyar kandemi ka fada gobe da yardar Allah sai a daura muku aure kaji?"


Hisham yayi shiru can ya daga kai yana kakaro murmushi yace,


"Duk wadda aka bani Bappa "


"Yusra.... Zaki biyayya ki auri Hisham?"


Yusra da daga Kai da sauri tace,


"Na amince bappah junaid "


Suka saka dariya dika parlorn ciki harda Amaal da ita kanta yusran ta bata dariya.


"Nagode diyar albarka... Hisham yusra ta maka?"


"Bappah .. maganar ma was beyond my expectations. Na karba da hannu dubu bama biyu ba."


Nanma aka sake fashewa da dariya. Aayaan yace


"Dama can kuna crushing juna da alama.. da sauri kowanne na amince Bappah"


Yusra ta jefa mai pillow tana rufe fuskar ta da tafukan hannayen ta..


"Allah ya muku albarka.... Gobe inshaa Allah sai ayi daurin auren. Aayan kikkira masu hoton yau kache kar su wanke su kar su saka please da tv stations dika dai a cure komai"


". In shaa Allah Bappah "


Haka dai suka yita mayar da zancen aka shiga wata hirar ta daban. Kafin daga bisani kowanne ya nufi sashen sa dan kwanciya bacci saboda dare yaja ainun


====




WASHE-GARI


Bayan sallar jumu'ah dubban mutane ne suka sheda daurin auren jikokin Alhaji Muhammad Wanda aka gabatar a masallacin central mosque da ke cikin masarautar kandemi... Wanda Bappah Nuraddeen ne ya zama waly... Akan sadaki mafi daraja,


Amarya, [Fatima-Yusra Jalaludden Muhammad] da angon ta [Captain. Hisham Abubakhar].


Sai amarya [Maryaam-Amaaal Junaid Muhammad] da angon ta [Arc. Al-mustapha jalaludden Muhammad].


Akayi rantsattsiyar liyafa/grand reception bayan an daura auren na maza. Anci an sha an kuma gyatse..Duk kuwa da babu ango daya wato Al-mustapha...


Yan uwa da abokan arzuka suka bi amare da angwayen da adduoin zaman lafiya da zuriya dayyiba...







AL-MUSTAPHA WEDS MARYAAM AMAAL...
#AWEDDINGTOREMEMBER💞💞




_ADVERT👇_


_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_


_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._


_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._


_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_


_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_


_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_


*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥




*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*


_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*




FURAR DANKO
Billyn Abdul


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at👇


1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k




_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥


[9/25, 1:27 PM] Hafsaat💞: _BAKON MUNAFIKI_
_(BA NA MUTUM DAYA BA NE)_


_NA:_


_NANA HAFSATU_


_PAGE: 41_


_BM vip arewabook: https://arewabooks.com/book?id=64a96774d6e097b6d856cfb9._


___


_AMAAL_




*Tana* kwance a dakin Hayateey akan gado... Wani zazzabi taji yana neman rufe ta gaba daya.. jikin ta ya fara daukar zafi yana kakkarwa. Gefe daya kuma kanta ne ke ciwo yana mata barazanar fadowa. Ga gabanta na dukan uku uku...


Sanye take cikin doguwar riga ta lace peach color style din bubu.Dankwalin kanta ya zame, Kwantaccen gashin ta ya bayyana a kanannade yayi bakikkirin da shi irin na larabawa.


Cikin haka mahaifiyar ta ta shiga dakin bakinta dauke da sallama. Amaal ta amsa tana daga kwancen ta dan daga kanta,


"Hayateey..."


"Na'am Habibty"


Zama tayi a kusa da ita akan gadon. Amaal din ta dan mike daga kwancen da take ta zauna ta jingina...


Hajia Jamila sai jujjuya yadda zata fito ta gayawa Amaal zancen an daura mata aure ta ke..


Ganin Amaal din na mutsu mutsu har da rufe idanu tana dan dartse labbanta cikin ciwo...tace da ita,


"Meya same ki?" Ta karasa fada tana dafa kan Amaal din ya dau zafi rau.


"SubhanAllahi baki da lafiya da ma?"


Amaal din ta daga kai dakyar saboda tsananin ciwon da yake mata tace,


"Eh... Gabobi na da kai na kaman ana datsani"


"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun... Tun yaushe kuma baki fada ba fisabilillahi?"


"Ba'a wani dade ba ne Hayateey.. bayan na fito daga wanka"


"Tashi tashi muje asibiti"


"Hayateey zai tsagai ta. Zan tashi na sha Panadol pain and fever"


"Banason musu tashi muje.kin manta abbiey ya hana a shan magani da ka ba tare da prescription din likita ba?"


"Tohm"


Mikewa tayi dakyar. Ta janyo mayafin ta wani madedeci ta yafa shi. Hajia Jamila ta dan dubeta ta ce,


"Canza mayafi saka babba ko hijabi"


Ba tayi musu ba ta janyo hijabin sallar ta ta saka. Don azaton ta Hayateey ta gaya mata hakan ne kila saboda kar ya dinga zame mata tunda batada lafiya.


Wajen motoci suka nufa, Hayateey na rike da hannun Amaal dake jiri ne ke dan daukar ta.


Hamid na ganin su ya taso. Waya ce a hannun sa yana dannawa,


"Hayateey ina zuwa?"


"Wallahi Amaal ce ba lafiya kaganta nan nace muzo muje asibiti"


"SubhanAllahi dearest sissy.. ya jikin?"


"Da sauki Yaya Hamid" ta fada tana runtse idanu saboda yadda kanta ke mata nauyi,


Mota ya shiga ya bude da sauri ya tashe ta ya kawo ta gaban su,


Hajia Jamila ta shigar da Amaal gidan baya ita kuma ta koma gaba ta zauna. Hamid ya jasu suka fita daga cikin sashen zuwa asibitin cikin gidan dake can baya ta dayan gate din


Suna zuwa aka fara mata gwaje gwaje ba baya lokaci. Sakamakon ya fito ta kamu ne da zazzabin ciwon sauro na malaria da kuma zazzabin typhoid.


Nan da nan aka fara mata wasu allurori aka kuma bata magunguna masu kyau. Cikin ikon Allah kuma jikin nata yayi karfi


"Sannu Amaal"


"Yauwa Hayateey"


"Sannu dearest sissy"


"Yauwa Yaya Hamid"


Motar suka koma suka shiga Hamid ya ja sika dauki hanyar gidah... Hayateey ta temaka mata suka shiga cikin sashen su..


Daki ta shige ta kwanta. Ba jimawa kuwa bacci ya dauke ta... Da ke batada nauyin bacci ana budo kofar ta bude idanun ta.


Yusra ce ta shiga bakin ta dauke da sallama... Amaal da ke kwance ta dan daga kanta tana amsa mata,


"Baby sis"


"Yaya yusra.."


Mikewa tayi. Yusran ta karasa tana ce da ita,


"Ashe bakya jin dadi? "


"Eh!!Amma da sauki .. bari nayi brush"
Ta shige bandaki ta wanke bakinta da mouth wash hade da yin brush sannan ta futo,


"Ya jikin na ki to?"


"Da sauki Alhamdulillah Yaya yusra"


Yusran ta nemi gefen gado ta zauna. Sanye take cikin doguwar riga blue

Please Login or Register in order to submit comment