Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

maryamun sa dagaske tana kaunar sa. Domin ta nuna masa zallar kauna daren ranar.. ya samu gamsuwa fiye da yadda yake tunani. Sai shi mata albarka ya dinga yi. Domin daren ranar sun gurji soyayya tsmkar cin Kwan makauniya. Lamarin sai fatan Allah ya basu zaman lafiya da kaunar juna da yalwar arziki.



::::::


Ko da safe ma hakan ce ta kasance. Al-mustapha mamaki ya cinye shi gaba daya. Domin yadda maryaam ta saki jikin ta da ranta tamkar ba ita ba. Ya sharara son ransa..


Tare sukai aikin gidan gaba daya suka gyara ko'ina gwanin ban sha'awa tamkar da can din masoya ne.


Tanada lectures din rana... Direbobi kuma kowanne an aike shi. Gashi yanada meeting na gaggawa a lokacin. Sai Hamid ne ya temaka ya kaita makarantar har bakin department dinsu......


_ADVERT👇_


_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_


_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._


_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._


_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_


_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_


_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_


*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥




*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*


_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*




FURAR DANKO
Billyn Abdul


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at👇


1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k




_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥


_*BAKON MUNAFIKI!!!*_
_(BA NA MUTUM DAYA BANE)_
_👺🏡👩‍👩‍👦‍👦_




_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_




_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
_®️NANA HAFSATU (MSS XOXO)_


_AREWABOOKS:MSSXOXO_
_WATTPAD:MISSXOXO00_




_PG:50.. (FINALE/KARSHE)_




_________


***Har bakin department dinsu Hamid ya kai hancin motar sa ya sauke Amaal.


"Nagode sosai Yaya Hamid... "


"Allah ya bada sa'ar karatu kanwata. "


"Aameen Yaya... Sai na dawo"


"Toh sai kin dawo"


Fita tayi daga cikin motar bayan ta gyara zaman laffayar dake naade a ajikin tah.


Ta shige cikin department din nasu tana daga masa hannu yana daga mata.. Bai bar wajen ba sai da ya tabbatar ta shige ciki, sannan ya juya kan motar ya koma kan titin da zai sadakaa da wajen makarantar...


Dai dai wani garden bayan ka wuce department din su Amaal ya hango bayan wani namiji da wata mace. Namijin yana daaga wa macen hannu cike da faada yadda yake nuni da ita zaka san masifa yake yi sai watsa hannu baya yake yi..


Rage gudun yayi ya shiga tafiya a hankali da motar yana muskutawa gaba sosai... Kamar Hindu? tabbas ita din ce dai da wannan malamin na su Amaal don ya zo shi daurin auren ma.


Kafin Hamid ya karasa dai dai saitin su Habibi Talba yabar wajen bayan ya sake gaggaasawa hindun bakaken maganganu.


Ta tsugunna ta kife kanta da cinya tana kuka sosai harda shessheka.. Hamid ya samu zuciyar sa da karaaya don baki daya baya son sauraron kukan mace. Bayason yaga mace na zubar da hawaye musanman akan 'da namiji...


Ya fita daga cikin motar sa ya nufi inda Hindun ke tsugunne tana kuka..


"Hindu...." Ya samu kansa da kiran sunan ta karo na farkon a rayuwar sa. Domin basu taba magana ba.


Da sauri ta daaga kai... Duk azaton ta ko Habibi ne ya dawo ya bata hakuri. Kallon su ya sarke dana juna... Ta samu kanta da kasa dauke idanun ta daga kansa... Sanye yake cikin kananun kaya ya dora blazer akai. Ba karamin kyau yayi ba.. ita kuma tana cikin doguwar riga ta atamfa ta yafa dan karamun mayafi


Handkerchief ya zaro daga gaban rigar sa, ya saka yatsu biyu saitin fuskar ta ya murza su suka bada sauti ganin tayi kamar mutum mutumi,


"Snap outta it.... Ungo rike ki goge hawayen ki kinji...?"


Tabi hannun nasa da hankicin da kallo...


"Malam Ina ruwan ka da ni?"


"Wooo. I mean no harm Hindu... Daga temako? Haka kike dama?"


"Ni banason munafurci saura kaje ka gayawa su Abbiey kace ka ganni a haka.. Daman kun saba ai halin gado kuka dakko. Yi sauri kafi ruwa gudu kaje ka fada... Mtssss! Aikin kawai"


Hamid yayi murmushi yana girgiza kai yace,


"Na gano ma ba lefin gayen daya barki bane kece me lefi"


"Dalla Malam ware ka bani waje.. Ina ruwan ka? Kawai saboda shisshigi . Wait biyo ni kayi kenan tun daga gidah dama dan ka dau rahoto ka kai musu?"


Hamid ya sake yin dariya har yana rike cikin sa, Hadi da saka dayan hannun sa ya dafe bishiya.


Hindu ta kalle shi ta dalla masa harara tana yamutsa fuska ta cigaba da cewa,


"Naci dubu sai ceto. Kurwata kur wallahi nan gani nan bari... Wanda yayi gaba yayi gaba na baya sai labari. Shi zakaran da Allah ya nufa da chara ko ana muzu ana shaho sai yayi s....


Hamid ya sake fashewa da draiya. Ya tsugunna a saitin da take yana dubanta sosai yace,


"Akan me zan ke bibiyar ki Hindu...? Ina tunanin wannan shine karo na farko a rayuwata da magana ta fatar baki ta taba hadamu.... Amaal na kawo tanada lectures, An rasa direbobi kowanne yanada aiki... Menene hujjar biyo ki fisabilillahi kema inde ba zuciya da kika biyewa ba, Mai sake sake akan wani dalili gotai gotai da ni zan dinga bibiyar ki, Meye hadani da ke Hindu? Kamar wanda suka saba da har haka zata shiga tsakanin su?look! Abu na biyu wucewa nazo yi zan koma gidah sa sauketa da nayi kenan na taho kan titin nan na hangi bayan mace da namiji kamar suna fada dubada yadda ta baya naga yana watsa hannu yana nuni da yatsa... Macece tanada rauni kuma zubar da mutunci ne ace mace budurwa baliga suna sa'insa da namiji a bainar jama'a akan titi...."


"Toh Ina ruwan ka? Ba sai ka wuce ka tafi ba? Da kai akeyi? Wannan ai shisshigi ne da kankanba... Sai kayi wucewar ka kama hanyar ka na meye zaka tsaya har ka tako kafafu kazo saboda tsabar gulma....?"


Hamid ya sauke katuwar ajiyar zuciya ya sake gyara tsgunnen da yayi yace da ita,


"Koma meye hada ku kiyi hakuri... A matsayin ki na mace be dace kizo nan ki tsugunna kina zubar da hawaye akan wani da namiji ba, Shawarar da zan baki a matsayina na namiji shine ki dena zubar da hawayen ki akan namiji. Duk namijin dayaga kin damu dashi fiye da yadda ya damu dake Allah wulakanci zaki ta gani kala kala...."


"Toh Ina ruwan ka?"


"Shawara ta rage ga mai shiga rijiya hindatullah... Na bar ki lafiya"


"Dan shisshigi kawai"


"Allah ya baki hakuri... Kiyi hakuri ki yafemun shisshigi na ne yaja mun kam.. Amma fa ni haka nake bana gani nayi shiru"


Mtscew... Hindu taja tsaki tana tabe baki.. Hamid ya mike daga gurfanen da yayi ya nufi motar ya shiga ya tafi. Hindu tabi bayan motar da kallo tana hararar ta, Tamkar itace ta mata lefin...


"Dan Allah ki fita daga rayuwata wai ana dole ne? Wallahi bana son ki, Ba zan taba son ki ba. Karki kara kuskura ki zo waje na kina mace sam baki da class ba kida kamun Kai. Ki sani ke din bakya cikin jerin irin matan da ni Habibi Talba nake so... Wallahi da nayi soyayya dake ko auren ki gwara na mutu ba aure akai na kinji Allah ... Kuma wannan rana ta zama itace ta karshe da zaki sake zuwa ki neme ni Allah idan kika sake ko kika kirani a waya sai na zo wajen mahaifan ki na gaya musu su ja miki kunne ki fita a harkata.. Dumbass " ta shiga tunano kalaman da Habibi Talba ya gaya mata tana runtse idanu hawaye masu dumi suka shiga zuba daga idanun nata.


Jikinta duk ya mutu... Ji take inama a dauki ranta ta mutu kawai a lokacin saboda tsananin duniyar data mata zafi shikenan itada Habibi Talba ba haske ? Ba zatayi soyayya dashi ba kenan har ta kai ga sunyi aure?


"Wayyo Allah na" ta fada tana hawaye sosai..


Kiran direba ne ya shigo wayar ta ta dauka ya sheda mata da yana bakin department yana jiran ta...


Sai data sake bude sabon wani shafin kukan tayi mai isar ta, kafin ta katse hawayen ta ta nufi motar ta shiga yaja su suka koma gidah


Hamid yana tafiya a mota yana dariya. Shi gaba daya ma Hindun dariya take ba shi. Gefe daya Kuma maduakakin tausayin ta ne ya kama shi... Tabbas Habibi Talba bai kamata ya dinga wulakanta ta ba tunda tana kaunar sa... Akace ka so me son ka.. sannu a hankali sai ya bita da sigar lallashi ya rabu da ita cikin ruwan sanyi...Amma hayaniya da hargagiya sam babu dadi... Ita kuma yakamata ace ta san itadin macece akwai limit dinta. Babu namijin dake son mace marar kamun kai da bibiyar diddigi.. Son ma so wani sam bashi da dadi. Ka so a so ka shine magana.... Na turawa sukance one sided love/ unrequited love....


_______


*MARYAAM-AMAAL*


Central mosque suka je suka yi sallah, Sannan suka koma theatre don halartar dayar lectures din data rage musu..


Lectures din was boring... Gaba daya ba dadi. Wasu daga cikin daliban hira kawai suke, Wasu na ciye ciye, wasun su kuma mafi yawa bacci suke yi... Yayin da wasu ke ta latse latsen wayar su. Amaal na daga zaune tana jujjuya wayar hannun ta. kawayen ta kuma sun kifa kan su akan benci suna bacci...


Tunanin ta ya lula duniyar Al-mustapha... Idanuwan ta Al-mustapha kawai suke so su gani, Kunnuwanta daddaad'ar maganar sa kawai suke so su ji, Gangar jikin ta na son kasancewa da shi... Zuciyar ta na bugun rashin sa akusa da ita... Ran ta na kewar sa..


Message ta shiga ta rubuta masa sako da,


"Habiby...♥️Fatan kana lafiya? Ka ci abinci kuwa? Ina class lectures din very boring...Ina son ka. Ka kula min da kanka. kasantuwar mu a raye cikin ruhi guda d’aya ya sanya zuciyoyin mu bugawa cikin lokuta makamanta juna.. Honey bunny na♥️ Ina nan zaune cikin class amma zuciya ta tana tare da kai. Kai ne kawai nake gani na ji sanyi a cikinta. Ina nan ina jiran dawowar ka nayi kewar ka sosai..."


Tana gama tura masa ta shiga gallery. Hotunan su kawai ta shiga kalla tana zooming fuskar Al-mustapha... Murmushin fuskar ta sai fadaaada yake yi.


"Banza uwar son miji...." Cewar Zaarah kawarta da ta tashi daga kwanciyar da take ta leka tana kallon Amaal na zooming fuskar Al-mustapha.


Amaal tayi dariya kasa kasa kar malamin su ya jiyo su tace,


"Ai ba haram bane... Halaliyata nake kallo.. Nayi missing dinsa ne ba zaki gane ba"


"Kwata kwata fa 2 to 4... 4 to 6 ne damu amma wannan awoyin kadan har kinyi missing dinsa? Sannu Juliet matar Romeo"


"Ke... Ba zaki gane ba ne... Amma duk second daya sai na tuno Habibi na... Ina kaunar sa fiye da yadda kalamai da baki zasu bayyana miki..."


"Matsalar ku ce"


"Ahhh! No vex mana.. Zaki shiga daga ciki keda Uthman zaki bamu labarin zallar kauna"


Zaarah ta tabe baki tana yamutsa fuska... Suka fashe da dariya baki daya..


Al-mustapha na zaune a ofishin sa yana danna na'urar me kwakwalwa ta computer da ke gaban sa. Karar shigowar sako ya shigo wayar sa.. Janyo ta yayi ganin Amaal ce wadda ta turo hakan yasa shi yin murmushi tun kafin ma ya karanta.. Ya kwantar da kansa ajikin kujerar ya bude sakon yana karantawa yana lumshe idanu hadi da sakin tattausan murmushi, Yaja kasan leben sa yana hango hotan fuskar ta a zuciyar sa...


Sai da ya maimaita sakon data turo sau shida, yana yi yana komawa farko yana tisawa kamar wata hadda... Tukun sannan ya mayar mata da reply,


"Habibty.... My whole world ♥️♥️ Alhamdulillah, Na ci baby na, wani snacks bar aka bude kusa da office... My poor baby.. Allah yabada sa'ar karatu kinji? I love and miss you soo much...Tausayi da tausasawa su ake kira “so” kowa yana da wacce yake so, Ni ke nake so.... Na ke kuma kauna fiye da kalmomi... Da akwai miliyoyin furanni a cikin lambun masoya a wannan duniya. Da a ce zan tsunko kowanne fure na baki shi a hannunki, hakan bai isa ya bayyanar da adadin yadda nake son ki ba...Ke ce murmushi na, kuma ke ce farin-ciki na. Ina kaunar ki sosai...Zan zo na dauke ki da kai na mun karasa meeting din Ina compiling details dinne kawai.."


Tana daga wayar ta taga reply din sa.. Nan da nan ta karanta tana murmushi...Ta manna wayar a kirjin ta tana lumshe idanu hadi da sauke zuciya... Farin ciki ya bayyana a fuskar ta ji take inama yana kusa da ita kawai...


Lecturer din yana gama lectures dinsa ya fita... Daliban kowa ya dinga hamdala saboda baki daya babu dadi lakcar ranar...


Suna zaune da su Zaarah su ma kafin direbobin su suzo daukar su. Chan sai ga tunkarowar motar Al-mustapha department din na su..


A hankali ya karasa parking motar ya bude ya fita... Tana ganin sa ta mike ya nufeta da sauri yana murmushi, daliban nata kallon su suna admiring din su.


"Ina wuni?" Su Zaarah suka hada baki wajen gayshe shi


"Alhamdulillah... Sannun ku...muje ko love?"


"Yeah... Bye!! Ladies" Amaal ta daga musu hannu tana musu gwalo suna dariya.


Bude mata gaban motar yayi ta shiga, daliban kowa nata,


"Awwwwwnnnn"


Sannan ya koma mazaunin sa ya zauna ya tashi motar bakin sa dauke da addua,


"Sannu Baby love..."


"Sannun mu Boothang"


"Me kike so ki ci yanzu?"


"A koshe na ke"


"Banason musu... Abincin school me ze miki? Bari mu karasa la comida corner sai muyi takeaway"


"Tohm..Allah ya saka maka da alkhairi ya kara maka budi me albarka"


"Aameen zumaa taa"


Yar dariyar data rike ta saki sosai tana kallon sa,


"Bana ce ka dena fadar sunan nan ba? Haba baby"


"Akan me zan dai na fada? Ai banyi karya ba, Ke kin ma fi zumar... Allah dai ya karawa daadi daadi"


Amaal ta rufe fuskar ta da tafukan hannuwan ta.. duk sanda ya fadi haka kunya ce take mata dabaibayi..


Haka dai suka cigaba da tafiya a motar suna hirarrakin su na soyayya kamar wasu saurayi da budurwa.. Daga nan suka biya wajen sayar da abincin sukayi ordering favorites din su suka kaama hanyar gidah..


Amaal ta dube shi tana rau rau da idanu, duk sanda dama take son wani abun da haka take farawa,


Ya dubeta yana gimtse dariyar data taho mai, Yasan abunda zata fada... Yace,


"Ya akai? Uhm? Waya taba mun rabin rai na?"


"Kai ne mana..."


"Ni kuma? Da nayi me lover?" Ya tambayeta cike da kulawa.


Ya gangara bakin titi yayi parking motar, Ya juya baaki daya yana fuskantar ta ya sake cewa,


"I'm all ears.... Banason fushin ki Boo, Meya faru? Uhm? Menayi? Uhmmm?"


Tana lankwasa hannuwanta cike da turo bakin ta gaba cikin shagwaba tace,


"Ka 'ki ka kai ni gidan Yaya Yusra, Ta zazzo ita har tace tayi fushi mun ki zuwa... Kace zaka kai ni, ko yaushe idan na maka magana, sai kace abari sai gobe, sai jibi ranakun nata wucewa"


Ya saka hannun sa ya lakuce mata kumatu yana murmushi yace,


"Tuba nake gimbiyar mata... Kiyi mun afuwa dan Allah... Inshaa Allah gobe da yardar Allah zamu je kinji? Bar fushi kinji? Kin hakura? Kin yafe mun?"


Ta kada kai da sauri, tana goge dan guntun hawayen da ke zurara daga idanun ta,


"That's my baby girl.... Kin hakura?"


"Uhm"


"Toh Alhamdulillah..."


Ya tashi motar suka cigaba da tafiya suna hira suna dariya, haka suka karasa gidah gwanin ban sha'awa..


Tare suka ci abincin, suka yi wanka tare hadi da tsarki... Al-mustapha ya fita masallaci yayi sallah. Daya dawo kuma ya tayata assignment din da aka basu kamar ko da yaushe.. kasancewar fannin karatun su daya, na architecture. duk abunda ya sha mata, kai shi take tuntuba....


--------------------


*Haka* rayuwar ta cigaba da garawa... Safiya ta zama rana, Rana ta zama yammaci, Yammaci ya zama dare.... Lalle Allah mabuwayi ne gagara misali..


Kowanne bangare na cikin labarin nan an samu karuwa ta fannin farin ciki da kuma akasin hakan, domin daman gaba daya haka rayuwar ta gaada. Yau da daadi gobe babu...


Su Ikram dasu Najla duk an kawo kudaden auren su an kuma yi tambayar aure tuni... Lefe ake jira akawo. Don an sassaka musu rana gaba daya.. Sarki Junaid da kansa ya taara su baki dayan iyalan nasa yace kowacce ta futo da mijin aure tunda suna da masoyan a kasa ga karamar kanwar su nan Amaal tayi biyayya an aurar da ita tana zaune agidan mijin ta. Don haka suma kowacce ta futo da wanda take so a aurar da ita. Haka suma mazan yace duk su fadi inda suke neman auren aje a tattambayo a hada a aurar da su baki daya. Ya babba su jari mai tsoka kowannen su ciki harda Amaal dake gidan auren ta..


Hindu ce kawai ke gallafiri ba mijin auren, Ba tada wani wanda yake sonta a kasa. Kullum sai ta zubar da hawayen bakin ciki....


Ta shirya zata futa zuwa computer school din da take zuwa ta nufi inda motocin gidan suke don anan direbobin suke gaba daya a zazzaune..


Ta sha mamaki kwarai matuka data ga ba mota ko daya kowanne ya futa kenan..? Taja ta tsaya tana taune kasan murfin biron data saka a baki...


Chan sai ga motar Aayan ta tunkari wajen... Tana hango shi ta dashare baki tana tsayar da shi.. alokacin Hamid ya nufi motar sa shima zai shiga,


"Yaya Aaayan"


"Na'am sis Hindu... "


"Ina kwana?"


"Lafiya lau... Wani abun kike jira ne?"


"Eh! Banga drivers ko daya bane zanje school ne"


Aayaan ya duba agogon hannun sa yana kallonta yafe,


"Ayya gsshi sauri nake dana kai ki"


"Bakomai .... Nasan yanzu wani zai dawo"


"To shikenan sai kin dawo"


"Yauwa"


Motar sa yaja yayi gaba, tabi bayan sa da kallo tana tabe baki


Hamid dake dubanta yayi murmushi. Ya shiga motar sa ya tashe ta ya karasa har gaban Hindun yana zuge gilashi yace,


"Zo na sauke ki"


"Banaso"" Tayi gaba tana hade rai


Ya sake binta da motar yana cewa,


"Haba hindatullah.... Dan Allah kizo na sauke ki.... Kinji?"


"Wai dan Allah meye darangami na da kai? Haba kacika shiga lamarin da banaka ba"


Hamid yayi murmushi yace,


"Lefi ne kenan daga temako?"


"Banason temakon na ka nace"


"Ki temaka kizo na kai ki"


Hindu tayi kwafa ta dube shi a shake tace,


"Idan na shiga ba zaka sake shiga lammurana ba ka amince?"


"Shigo... Naji"


Ya zare lock din daya saka. Ta shiga tana eani yauki... Ya bita da kallo yana mrunushi yace,


"Baki gayshe ni ba"


"Toh sannu"


"Toh sannu ai ba gaisuwa ba ce.. well akace durkusawa waada ba gajiyawa bane.. barka da safiya hindatullah... Fatan kin tashi lafiya?"


"Da ban tashi lafiya ba zaka ganni haka ne?"


"Tuba nake.... Ina ne inda zaa sauke ki?"


Ya ja motar da sauri suka futa daga cikin kandem estate din..


"Second corner by your left... Sai ka shiga you turn na farko by your right adjacent to kinkin mart, nan zan suaka"


"Okay computer school dinnan?"


"Uhm.."


Hamid yayi murmushi, shi dariya Hindu take sa shi sam bakaken maganganun da da hargagiyar ta basa sha masa kai... Ya sauketa har kofar makarantar ta hude zata futa taji lock


"Bude mun na fita mana meye haka?"


"Calm down! Dan ALLAH kinsan dai bazan sace ki ba ko?"


"Yo waya sani wannan abu a dubu?"


"Toh Allah ya kiyaye .... Dan ALLAH wani temako nakeso kiyi mun kinji?"


Ta kalle shi shakeke tace,


"Temako?"


Ya daga kansa cikin tabbatarwa... Domin gaba daya tun ranar da ya ganta a jami'ar su Amaal dinnan tun daga rannan zuciyar sa ke azalzalar sa da son kasancewar Hindu a matsayin wadda zaiyi rayuwa da ita. Yana tausayin ta sosai, Kuma yaji yana son ta lokaci daya..


"Kiban number ki"


Hindu ta fashe da dariya tana nuna kanta,


"Ni Hindu ni zan baka number ta? Akan me?"


"To haramun ne? Number ki nake so mana... Kuma yau dinnan a yanzu nake so ki bani, don ba zaki fita daga motar nan bama sai kin karanto mun"


"Lalle baka da lafiya"


"Uhm na yadda ko me zaki fada"


"Bude mun na fita"


"Anki din"


"Ka bude nache"


"Lalle zamu kwanta a haka... " Yayi baya da kujerar sa yana saukar da kansa zai kwanta tace,


"Wane kalar rashin mutunci ne wannan eh?"


"Ssssssh Hindu ki dinga tausasa harshen ki kefa macece.... Kinji?"


"Ba zan tausasa ba"


"Rokon ki nake ni dai... Ina kallon ki ne tamkar Amaal kanwata.."


"Ba abunda ya hadani da kai da ita"


Hamid yayi murmushi yace,


"Ni bana wani jan magana... straight to the point na ke...Number ki nake so saboda I like you...." Ya fada yana daga nata kafada


Hindu tayi shiru... Gaba daya ko da wasa bata taba kawo haka ba. Duk sai ta dubibice,


"Budemun na fita.."


"Naki din"


"Dan Allah ka bude mun"


"Zan bude idan kika karanto mun number ta ki"


Ta dan saci kallon sa. Kyakkyawar ne na ajin karshe don har yafi Habibi Talba kyau. Sai dai kwafsin dan uwan Hajiya jamila ne kishiyar mahaifiyar ta. Ta yamutsa fuska tace


"Taya zaka so ni kasan dai matsalar da take tsakanin mu ko?"


"Ta ke tsananin su dai.... Hindu alakar mu bata shafi nan ba... Mu rufe kunnuwan mu muyi abinda ya dace ai Allah be hana ba. Zan samu Hayateey na gaya mata abunda nake ji akan ki. Ni wallahi tsakani da Allah nake kaunar ki tun ranar da na ganku dinnan a AUN... Zaki bani ko ba zaki bani ba?"


Hindu tayi shiru ... Idan ta hanashin tana da wanda yake sonta ne? Ko kare baya zuwa wajenta . Bata da kowa ba me zuwa zance,


"Ina wayar?"


ya dakko da sauri ya mika mata ta karba ta saka masa number


Sai daya kira ya tabbatar number tace tayi ringing, kuma tayi saving alokacin tukun sannan yace,


"Karfe nawa zaki tashi nazo na dauke ki?"


"Uku"


"Toh shikenan Allah yabada sa'ar karatu.. kinji?"


Hindu tayi masa murmushi ta daga masa hannu ta shige ciki shi kuma yaja motar ya tafi...



Kamar wasa abu sai ya zama gaske.. zazzafar kauna ta shiga tsakanin Hindu da Hamid. Ya samu Hajiya jamila da sarki Junaid da maganar dukan su suka amince sun kuma bashi goyon baya. Ya sake samun Amaal da maganar itama tayi na'am taji dadi sosai...


Ko da Hindu ta samu Hajiya hadiza da zancen da farko kin yarda tayi, sai da Hindun ta sake wayar mata da kai tukun sannan ta amince sukayi ta murna..Har sukaje suka samu Hajiya Jamila aka yayyafi juna gaba daya...


Aka saka ranar auren su suma a tare da sauran gaba daya harda na Aaayan shima


Aka shirya meeting na dangin gaba daya gwanin ban sha'awa. Akayita tunatarwa akan zumunci ana kuma Allah wadai da Kawu Adamu daya kasance BAKON MUNAFIKin da BANA MUTUM DAYA BANE... Don tuni ma kotun shari'ar musulunci ta yanke musu hukunci da shi da mukarraban sa dai dai dai da laifukan da sukayi...


Hajia maryam ta sake gyara zaman gilashin idanun ta tace


"MENENE TUSHEN MUNAFURCI? : 1. Da farko dai Munafurci wata irin cuta ce acikin zuciya, wacce idan ta kama zuciyar, tana cinye imani ne har sai ya zama babu saura. Daga nan sai Mutum ya zama cikakken MUNAFIKI wato WANDA YAKE BAYYANA IMANI AKQN HARSHENSA, AMMA ZUCIYARSA TANA CIKE DA KAFURCI. Munafukan Farko wadanda suka zauna zamani guda tare da Manzon Allah (saww) sun kasance SUNA SALLAH, SUNA AZUMI, KUMA SUNA RAKA MANZON ALLAH (SAWW) WAJEN YAQI AWASU LOKUTAN. Amma duk da haka Allah (swt) yace “SU FASIQAI NE” Awani wajen ma Allah yayi wahayi ga Annabinsa (saww) cewa : “HAR ABADA KAR KA QARA YIN SALLAH ABISA ‘DAYANSU IDAN YA MUTU. KUMA KAR KA QARA TSAYAWA KAN QABARINSA. SABODA YADDA LAMARIN YAKE, SU SUN KAFIRCE MA ALLAH DA MANZONSA KUMA SUN MUTU SUNA FASIQANCI”. (Suratul Taubah ayah ta 84). SUBHANALLAH!!! Awani wajen kuma Allah ya gaya ma Annabinsa cewa: “DAIDAI NE AGARESU. KO KA

Please Login or Register in order to submit comment