Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fiffito su ma."


"Tohm."


Takalmi ta zura, kafafunta sanye cikin safa baka. Tana gaba mahaifiyar ta ta na biye da ita a baya sanye take ita cikin doguwar rigar leshi dinkin bubu ta rufa babban mayafi.


Suna fita harabar gidan da harararrakin haj hadiza da ruwaida suka fara cin karo. Sunata doka musu ita. Ciki harda tagomashin ta yaran su dake gefe suma sun dakko halin.


Haj hadiza tayi gaba tana jan dogan tsaki. Badan amb junaid yace lalle su tafi a ayari dukan su ba kar wanda yayi gaba yabar wani da tuni sun dade da tafiya.


"Shafaffy da mai." Ta fada hadi da waiwayawa baya ta sake bankama haj jameelah harara da amaal.


A haka suka karasa sashen Hajiya Maryam mahaifiyar su Amb. Junaid.


Tuni har wasu yan uwan sun sun zo wajen hajiyar dubada motoci dake faffake na alfarma...


___
_ADVERT👇_


_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_


_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._


_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._


_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_


_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_


_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_


*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥




*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*


_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*




FURAR DANKO
Billyn Abdul


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at👇


1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k




_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥
[8/9, 1:37 AM] Hafsaat💞: _BM_




_NA:_


_NANA HAFSATU_




_09_






Bakunan su dauke da sallama suka shiga babban parlorn Hajiya. Wasu daga cikin iyalin ta sun zo suna zazzaune.


Amb. Junaid na daga gefen hajiyan a a kasa yana zaune. Ya sanya hannun sa duka biyun yana yiwa kafafun hajiyan tausa.


Amsa sallamar yan parlorn suka yi naki daya. Domin a ranar ne mahaifin su zaa dawo da shi daga kasar south Korea inda aka kaishi don yo masa eani aiki a hakarkarin sa.


Dukkanin yaran na sa sun hallara da sauran yan uwa da 'ya'yayan su.suna tsammatar dawowar tasu


Hajiyan na zaune ne a babbar kujera me cin mutane uku.


Sai Babban wansu Alhaji Nuraddeen, 'Ya'yan yan uwa nace da shi, Bappah na kandemi, Sai kanin sa da ke binsa a kusa da shi, Honorable Minister of finance, Alhaji Jalaludden Muhammad anace da shi Bappahn Hajiya... Sunan kanin hajiyar yachi mai rasuwa.


Sai ta ukun su wato mabiyar Alhaji Jalaludden... attorney general ce ta kasa, Justice Fateemah suna ce da ita (Gwaggon court)..


Sai Bappah Abdullahi. Wato farfesa/professor Abdullahi suna ce da shi Bappahn Istanbul. Saboda ya zauna a Istanbul.


Daga gefen wasu tumtum da suka sha kawaatuwa da wani irin kyalkyalin beza kuma Dr. Aisha ce a zaune ta mike kafafun ta. Gaban ta da kofin tangaran ne dauke da kunu aciki tana juya shi da sukarin data zuba.


Baki daya dai yaran hajiyan sun hallara....


Su Hajiya hadiza suka karasa shjga cikin parlorn suka zaazauna. Daya bayan daya suka fara gaggaushe da juna..


Amj Junaid na daga gefen Hajiya shi dai yana mai cigaba da matsa mata kafafu.. wasun su sun amsa musu fuskokin su a sake wasu daga ciiki kuma fuskar nan tasu babu yabo babu fallasa.


Alhaju Jalaludden wanda shine babban Yayan su bayan Alhaji Nuraddeen. Mikewa yayi yana gyaran zaman babbar rigar jikin sa.


Amb junajd ya daga idanu ya dube shi alokacin ya kai kansa ga agogo yana son yaga lokaci


Wata harara mai tattare da tsantsar tsana da kyamata ya zuba wa amb junaid. Ya karasa wajen hajiyar tasu ya zauna daga gefe har yana mirje yatsun amb junaid dake maya tausa abisa sani kuma ya take sun.


"Hajiya ni zan dan fita..."


Hajiya bacci ya fara fusgar ta. Da sauri ta dan bude idanun ta,


"Iyye? Magana ake?"


"Jalaludden ne hajiya..."


"Ina zakaje kuma?"


"Zan dan futa ne Hajiya na shawo iska....."


"Ba zaka jura su dawo ba?"


"A kofar gidah zan dan huta . Nan din ne acike."


"Toh shikenan Allah yayi albarka."


"Aamin Hajiya."


Mikewa yayi daga zaman da yayi a gefen ta. Ya fuce da sauri. Yana fita.Alhaji Nuraddeen yabu bayan sa.


Professor Abdullahi ya daga idanu ya dube su ya mayar kasa kawai yana jujjuya kai. Kasan makoshi yake furta,


"Allah ya kyauta...."


Amb junaid baki daya jkkin sa sai ya sake masa sanyi. Ya rasa wacce iriyar wutar kiyayyayar ce ke sake ruruwa a zukatan yan uwan na sa dake suke uwa daya uba daya.


"Junaidu kaga yadda nake renovating asibitina kuwa?" Cewar gwaggo indom wato dr Aisha.


Ta karkato masa kan iPad din nata yana kalla... Murmushi yayi sosai. Kafin ya mike ya koma inda take zaune ya saka hanu ya karbu ipad din yana zooming hotunan asibitin farfajiya da cikin sa..


Ma shaa Allah Allah yasa an fara a sa'a..Allah ya temaka Amin."




"Aamin suka hada baki."


Suna dai zazzaune baki daya wasu na magana wasun su na daddanna wayoyin hannun su ya yin da wasu ke kallon shirin da ake haskawa a talabijin na tashar Aljazeera.


"Zo nan takwara ta ...." Hajiya Maryam ta kira Amaal da ke gefen mahaifiyar ta a zaune.


"Tohm Hajiya.." Ta mike da sauri ta nufi wajen hajiyan ta tsugunna


Hajiyan ta kamo hannun ta ta rike cikin nata tana mai duban idanun ta,


"Sannu takwara... Je ga daki can zaki ga magogin goro a gefen gado ki dakko mun."


"Tohm Hajiya."


Tashi tayi da sauri ta nufi dakin ta dakko ta kawowa Hajiya.


"Bari na goga miki."


"Allah yayi albarka..."


"Ina safwanu mai gidan nawa?" Hajiya ta tambaya tana duban inda sauran yaran suke a zazzaune..


Hajiya hadiza ta dashare baki. Da dazu da hajiyan ke yiwa Amaal magana ita kadai sai kumbura fuska take amman da ke hajiyan ta tambayi nata dan yanzu sai washe hakora take kaman gonar auduga..


"Kai tashi Hajiya na kiran ka.."


"Kyale shi idan ya na hutawa... Ga kuma Abubakari, ga Na'eelah nan ga ...."


"Najwa..." Haj Hadiza ta amsa ta tanata murmushi ita ga mai tarin 'ya'ya..


"Ga kuma biyu kyautar Allah ...Ikram da Ikhlas.." Ta saka yatsa tana mai nuni da yan biyun Hajiya Ruwaida


Hajiya Ruwaida ma sai kuma fuskar ta ta gauraye da farin ciki.


Duk dai Hajiya ta kamo sunayen su daya bayan daya tana musu wasa. Duk kuwa da dattijuwa ce me kamewa, batada rikicin tsufa sannan bata wasa da jikoki irin wasan nan da yake wuce gona da iri. Tana da matukar kwarjini shi yasa ko jikokin nata suke nutsuwa idan suna tare da ita..


"Ku tashi mu lalleka a gaysa." Cewar amb. Junaid daya mike daga inda yake a zaune.


Ya isa wajen Hajiya ya durkusa cikin girmamawa yace,


"Hajiya bari mu shisshiga gidajen a gaysa."


"Toh junaidu sai jun dawo. A gayshe su da dakyau."


"In shaa Allah hajjaju."


Yana gaba suna biye da shi a baya suka nufi sashe sashen da ke cikin gidan suna gayshe da su


Duk inda suka je anyi maraba da ganin su. An kuma kakkarbe su hannu dubu bama biyu ba...


Sai da suka gama gayshe da kowace ahali na zuriyar ardo kandemi da ke cikin kandem estate sannan suka koma sashen Hajiya.


Yaran Gwaggo indo da basa cikin estate din suma sun kawo ziyara, hakama iyalin Gwaggon court.


Tuni suka fara hirar yaushe gamo da yaran Amb. Junaid. Gwanin ban sha'awa. Sai hirar zumunci suke.


Alhaji jalaludden na daga kujera ya dawo ya zauna sai muzurai yake yana yamutsa fuska musanmam da yaga Amb Junaid ya zauna a kusa da Hajiya...


"Wai har yanzu abun na su bai kammala ba?" Hajiya ta juya ta dubi jajaludden tana tanbayar sa


"Sun kusa waiwayowa gidah gaba daya Hajiya. Matsala aka samu ne da visa din musty. Amman su nan da sati uku zasu dawo gaba daya. Da sun dawo kuma shikenan ba komawa. "


"To Allah ya kawo su lafiya. "


"Allahumma Aameen Hajiya .."


Suna dai zazzaune kowanne da abunda yake yi. Zaman jiran dawowar shi da yan rakiyar sa kawai suke ... Mahaifi agare su, wato Grand Kadi/Chief Justice/Alkali "Alhaji Muhammad Mahmud Kandemi ..."


__
_ADVERT👇_


_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_


_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._


_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._


_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_


_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_


_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_


*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥




*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*


_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*




FURAR DANKO
Billyn Abdul


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at👇


1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k




_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥
[8/9, 2:09 PM] Hafsaat💞: _BM_


_NA:_


_NANA HAFSATU_


_PAGE:10_


_BM vip arewabook👇: https://arewabooks.com/book?id=64a96774d6e097b6d856cfb9._


___


_ARDO KANDEMI INT.. AIRPORT_


*Ardo* kandemi international airport ne dake birnin Nukaa a kasar najeriya. Yana daya daya cikin manyan airports din da ake ji dasu a fadin najeriya da ketare..


Airport ne daya ci sunan marigayi me garin kandemi wato Ardo kandemi wanda daga yankinsa ne gwamnati ta tsakura ta saka sunan birnin Nukaa. Nukaa state kenan..


Jirgi ne samfurin private jet wato ba mallakin gwamnati bane ko na kasa, jirgi ne wanda masu hannu da shuni ke mallakar su, ko manyan siyasa, Yan kasuwa, Manyan malamai da ake damawa dasu. Da ma masu babban matsayi na jam'iyu ta kasa da ketare


Sosai mutane sukayi dafifi wajen son ganin sa. Masu gadin da masu tsaro sun sha mamaki kwarai matuka na ganin mutanen duk kuwa da baa sanar da dawowar sa ba. Haka zalika ko a ya uwa ba kowane yasan da waiwayowar tasa gidah ban amman masoyan sa sun cika airport din don tarbar sa..


Face mask yaja ya lullube hancin sa har wajen idanun sa, gaba da bayan sa kuwa dakaru ne dake zagaye da shi suna kare shi.


Kafafuwan sa ne lokaci daya suka shiga yi masa rawa, Gabansa ya tsananta bugawa. Kansa ma ya shiga masa ciwon. Jikinsa take ya hau rawa, Wani abu ya fara masa yawo kaman tafiyar kiyashi a jikin sa.


Jikin sa ne ya tsananta har ya kasa wani takun. Masu tsaron sa suka yi kansa


"Ranka ya dade..."


"Sir"


"Yallabai"


"Alhaji"


"Boss."


Haka dai sukai ta kiran sunan sa. Tuni ya yanke jiki ya fadi akan wani me
tsaron sa. Suka rike da sauri duka suna kiran kawun sa dake bayan su yana cike wasu takardu.


Da sauri ya karaso wajen shima yana gyaran zaman gilashin idanun sa. Cike da tsantsar firgici ya shiga taba jikin dan uwan na sa.


"Karami... Karami? Karami?"


Girgiza shi ya shiga yi da iyakar karfin sa amman ba wani canji.


"Ku temaka mun."


A tare suka tallabo shi sosai suka yi waje dashi ta wata kofa da take kebantacciya ce ba kowane ya santa ba sai kana da babban mukami ko kai wani ne a kasar ... Ko kuma idan emergency ya faru na gaggawa to ana amfani da ita...


Kai tsaye suka yi wajen mota da shi suka saka shi acikin wata motar yan kwana kwana (ambulance). Dandazon mutane har sun fara taruwa amman ina tuni suka ja motocin su suka fita daga cikin airport din.


Duk na'urar air conditioner din dake tirara motar da sanyi.. Hakan be hana jikin Alhaji Muhammad yin gumi ba. Wani irin gumi ne ke tsattsaga daga jikinsa mai tsananin kuna da yauki.


"Sir kaga ruwan da yake fita daga jikin sa."


Wani dan sanda ya fada yana mai nunawa Alhaji Adamu jikin Alhaji Muhammad.


Kasa magana Alhaji Adamu yayi .ya janyo wayar sa dakyar yana duba lokaci. Gefe daya yana duban yadda ma'aikatan lefiyan kwana kwanan ke bashi temakon gaggawa


Gashi ba tare suka taho gaba daya ba da sauran wanda suka tafin.


Wani abu ya taho ya tokare masa a wuya. WhatsApp ya shiga. Da saqon amb junaid ya fara cin karo yana masa ya jikin mahaifin na su?


Nan da nan ya sanar masa ai sun dawo ma ga abunda ya faru. Alokacin amb junaid ya mike daga zaunen da yake don dama yana online wayar sa na hannun sa..


"Meya faru?" Cewar Hajiya Maryam


"Ba bakomai Hajiya Ina zuwa."


Futa yayi da saurin sa har yana cin tuntube yayi kofar gidan tsabar tashin hankali kafar sa daya da warin takalmi daya baby.


Ma'aikatan na ganin sa suka tashi


"Yallabai lafiya?"


"Ina sarkin mota?"


"Ya fita da su Hajiyan Makama"


"Ba wani direba a kasa?"


"An tafi dakko tara makaranta. Su hambali sunje cikin gari."


Yaja dogon tsaki yana dartse idanun sa.


Yana juyawa ya hangi su Alhaji jalaludden zasu shiga motar su, Dama yaga sun futo daga parlorn dazu ba dadewa, da sauri ya karasa wajen su,


"Wajen su baba zaku?"


Alhaji jalaludden bai amsa shi ba. Sai Alhaji Nuraddeen.


"Eh ... Shigo muje."


Ya bude gidan gaba ya zauna. Alhaji jalaludden na owners coner sai Alhaji Nuraddeen a gefen sa direban Alhaji jalaludden na tukawa a gaba, sai amb junaid a kujerar gefe,


"Suna wani asibiti? Yaya?"


"Bansanj ba Junaid .... Kawu yace kai ya fara fadawa. Kafin ya mana forwarding."


"Bana online ne sai da na hau, Amma...Ai"


Bai karasa fada ba Alhaji jalaludden dake jinsu ya ja dogon tsaki, ya dubi Alhaji Nuraddeen cike da bacin rai yace,


"Bansan meyasa zaka ce mu taho da mutumin nan ba. Ko dai yayi shiru ko na futa na bar masa motar."


Amb Junaid ya juya ya kalle shi. Direban ma dik sai jikin sa yayi sanyi kansa a akan titi.


"Menene haka jalaludden?"


"No Yaya ai gaskia ne....Duk wannan shekarun sai daya tabbatar ya gama kitsa komai sannan zai waiwayo kandemi? Wanene yasa jikin baba a wannan matsanancin ciwon idan ba shi ba."


"Subhanallahi yaya jajaludden me kake fada haka? Wallahi wallahi bansan me kake nufi ba. Menayi? Meya faru? Wane ciwo na saka baba? Yaya Nuraddeen ka wayar dani me Yaya jalaludden yake nufi?"


Alhaji Nuraddeen ya girgiza kai kawai yama rasa me zai ce..


"Kuyi hakuri dan Allah. Hakan duk bata taso ba. Yanzu dai duka zukatan mu na cikin damuwar ciwon mahaifin mu. Shine agaban mu. Koma menene sai ya biyo bayan samuwar lafiyar mahaifin mu.."


Amb Junaid daya juya yana kallon su sai ya mayar da jikin sa ya koma kallon titi kawai.


Tarun damuwar dake cinsa ta sake masa tasiri. Baki daya maganganun Yayan su jalaludden ce ke masa yawo a kwanyar kansa.


Dai dai lokacin da saqo ya shigo wayar sa da unknown number. Tamkar ba zai bude ba sai kuma ya bude sakon daya kunshi,


"Barka da dawowa zuri'ar kandemi. Ambasada mai murabus. Na haneka da kada ka soma sanya kafa ka dawo amman kayi fatali da magana ka dawo. To abunda ya faru yau wasa ne farin girki. Sannu da zuwa ne ka fara cin karo da shi kafin asalin babban wasan ya fara.... Ka tattara iyalin ka ku koma inda kuka fito. Idan ba haka ba......"


Runtse idanun sa yayi da sauri . Dai dai lokacin da suka shiga babban asibitin da ke na kudi kuma shine wanda yake na babban likitan estate din..


Nan motar yan kwana kwanan ta kunna kai ciki itama .


Ma'aikatan kafiyan suka kai musu temako kan wani gado suka dora shi da sauri sukayi ciki da shi da gudu...


Suka furfuto daga cikin motar bayan direba ya faka motar awajen adana motoci da ke farfajiyar asibitin.


Dukkanin su wayoyin su na hannun su. Ya dube su na dan wani lokaci ya kauda kansa da sauri don zuciyar sa ta fara kiyasta masa wani zato na daban a kan su. Don haka da sauri ya fara kamo addu'oi yana yi kasan makoshi... Don bayasan kyautata zato. Don zato zunubi ne ko da ya zamanto gaskiya.


Cikin asibitin suka shiga da sauri kowanne hankalin sa a tashe. Sukayi bangaren emergency unit da akayi da shi.....


_ADVERT👇_


_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_


_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._


_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._


_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_


_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_


_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_


*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥




*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*


_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*




FURAR DANKO
Billyn Abdul


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at👇


1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k




_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥
[8/10, 1:36 AM] Hafsaat💞: _BM_


_NA:_


_NANA HAFSATU_


_PAGE:11_


_BM vip arewabook: https://arewabooks.com/book?id=64a96774d6e097b6d856cfb9._


___


*Dakin* gaggawa na marasa lafiya magashiyan aka nufa da shi. Manyan likitocin suka shiga ciki suna bashi temako.


Ya yin da su Amb junaid ke daga wajen kofar dakin gaggawar a tsaitsaye. Kawu Adamu yanata kaikawo daga kofar dakin zuwa karshen corridor.


Kana ganin fuskokin su kasan suna cikin madaukakiyar damuwa marar misaltuwa.


Ba a wani dau tsawon lokaci ba likitocin su biyu sika fito daga cikin dakin. Daya ya zare safar hannun sa ya jefar daya kuma ya nufi wajen wani famfo yana wanke hannun sa.


"Barkan ku da yammaci." Daya daga ya fada..


"Barka kadai."


"Barkan mu.,"


"Sannu ku da kokari doctor."


Suka shiga amsa masa daya bayan daya..


"Dr gwanzam zai muku bayani game da komai. Muna fatan Allah yabashi lafiya ya tashi kafadunsa cikin gaggawa ya kuma sa kankarar zunubai ce Amin. zan je rounds ne."


"Aamin Aameen Dr. Faysal."


Ya karasa fada yana mai basu hannu daya bayan daya suka gaisa sannan ya tafi.


"Makusancin Alhaji nake son magana da shi." Dr gwanzam ya fada.


"Ai duka nan likita, kowanne daga cikin mu makusancin sa ne. Wadannan 'yayan sa ne.. Sannan ni dan uwa ne kuma makusanci matuka agare shi."


Kawu Adamu ya fada cike da damuwa marar misaltuwa.


"Alright...Ku zo muje ko?" Dr gwanzam ya fada yayi gaba suna biye dashi ta baya.


Wani daki ya shiga suka bi bayan sa. Dauke yake da kujeru da kayan kallo gefedaya kuma da drwer ta cika fal da littafai a jajjere.


Sai wasu hotuna dake dauke a kusuruwoyin dakin.. Hotunan sikelaton ne dana hanjin ciki. Sai wani dake nuni da sassan jikin dan Adam da wasu rubutu a jere da manyan baki


"Bismillah ku zazzauna."


Ya nufi kujerar sa ya zauna. Suma suka zazzauna a kujerun gefen sa.


"Likita Allah ya saka da alkhairi..."


"Aamin... Allah yabashi lafiya yasa kaffarane."


"Aameen"
Suka hada baki wajen amsa shi.


"Ai kafin zuwan ku prof (Babban likitan mai asibitin) ya sanar mana komai."


"Allah sarki.... Yana can Ashe bai dawo ba."


"Ya kusa in shaa ALLAHU."


"Ma shaa Allah.. Allah ya temaka Amin"


"Aamin Aamen.."


"Allah ya biyaku da irin dawainiya da kokarin da kuke ga marasa lafiya." Cewar amb junaid.


"Allahumma Aameen..mahaifin ka ne amman ko kamar ta baci?" Dr gwanzam ya tambaye shi


"Mahaifin mu ne." Ya amsa shi yana murmushi.


Alhaji jalaludden ya daga kai ya masa wani kallo yana yamutsa fuska. Cikin hasalewa yace,


"Likita muna son sanin halin da mahaifin mu yake ciki...."


"Ko zan iya sanin matsayin ku awajen sa saboda magana ce mai matukar muhumman ci. Sannan zatafi dacewa idan da na kusa da shi mukai."


"Baka che Dr. Nogan ya fada muku ba?"


"Eh ya gaya mana cewar vvip patients zasu zo. Tunda mu ba mu wani dade a asibitin nan da fara aikin mu ba kusan ni daga baya na dawo kasar ma a Paris nake. Yace mu baku duk wata kulawa data dache.. already akwai history na ciwon ma mun duba sosai munyi nazari akai. To Amma dai ko wani fanni abunda nakeson fada yana da sirri da kuma amana. Don haka asibiti na da tilashen lullube sirrin cutukan marasa lafiya da ke karkashin sa inde ba sanin hakan ne ya zama tilashe ba gaskia baa futar wa wanin wani yanayin ciwon sa..shi yasa muke son sanin ku din su wannene ya yan uwantakat taku ta ke? Tunda akwai 'yayan kanne ai suma na jini ne, akwai kuma 'ya'yan da aka haifa na ciki.. Kuyi hakuri da ni"


Alhaji jalaludden yaja dogon tsaki yana cije baki. Duk sukai shiru. Dr gwanzam ya sake cewa,


"Ku gafarce ni dan Allah yanayin aikin ne yazo da haka."


Alhaji Adamu ya sauke katuwar bahaguwar zuciya ya nisaa ainun kafin yace,


"Mun fada muku na lura kaman baku amintaa ba...."


"Ba haka bane ranka ya dade... Kawai munason tabbatarwa ne..."


"Wadannan duka su ukun 'yayan sa ne na cikin sa. Uwar su daya uban su daya, shine mahaifin su... Wannan shine na fari awajen sa Alhaji Nuraddeen. Wannan ma dan sane jalaludden, wannan shine karamin dan sa gaba daya. Ambasada Junaid.. Nasan zaka iya sanin su duka ba bakin fuska bane."


"Nasan wannan dai minister ne..wannan ma na san ya rike jakada a akasashen waje. Wannan ne dai ne dai bansani ba." Dr gwanzam ya fada yana dan murmusa fuska..


"Kanne na ne duka...ni ne babban su kamar yadda Kawu ya fada..."


"Ma shaa ALLAHU.... To a zahirin gaskia Alhaji Muhammad idan muka che ga abubuwan da sike damunsa gaba daya min san su gaskia munyi karya. "


"Doctor wata babbar cutar ce dashi?"


"A'a ka kwantar da hankalin ka Kawu.... Ina nufin abubuwan dake faruwa dashi na rashin lafiya suna da yawa bazaar iya cewa ai abu daya be ko biyuu sike damun sa ba. Sannan kada kusa damuwar hakan a ranku. Shi ciwo dama lokaci daya yake shiga. Fitar sa ce ke daukar tsawon lokaci."


"Haka zancen ka yake."


"Tabbas hakane."


"Yauwa! Dan Allah ku kwantar da hankulan ku"


"To ai likita dole ne mu saka tsoro da farbaba azukatan mu. musanman da kache abubuwan da ke damun sa da yawa.,"


"Masana suka ce, Allah bai sauki kowane cuta ba fyace sai da maganinta ko?"


"Hakane"


"Wannan gaskia ne"


"Sannan Allah baya dorawa dan Adam abunda yafu karfin sa."


"Tabbas."


"To sai mu cigaba da addua. Mu kuma dora da magunguna da sauran bincike..in shaa ALLAHU komai yazo karshe. Zai samu waraka da yardar Allah. Cuta ai kankarar zunubai ce. "


"Allahu ya sa likita."


"In shaa ALLAHU."


"Yauwa.... Magana ta farko dai nasan kunsani kuuma.. Alhaji yana dauke da cutar ciwon zuciya da hawan jini.. sai kuma bayan nann nasa da ke masa physiotherapy na lumbar sacral spine..shima da sauki Alhamdulillah. Ba kuma shi da calcium yayi kasa sosai. Sai kansa da mukai CT scan akwai jini daga gefe da zamu cire. Kusan wannan sune abubuwan da muka Gano a bincikemu na yau. Kuma aikin da

Please Login or Register in order to submit comment