Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kandemi..... Bayan zuwan hausawa da basu iya fayyace sunan ba saboda harshen fulatanci ne a hausan ce sai suke cewa da shi 'Ado Kandem...' a haka kuma sunan ya zamo ya tumbatsa har ya zama cibiyar kasuwanci. Allah ya sanyawa yankin albarka ake ce da gurbin kasuwar kandem...


Bayan sun hayayyafa sun tara iyalai masu tarin yawa. Sai ya zamto sun mamaye ilahirin yankin da gaurayen sa. Sai ake kiran wajen yankin kandem...


Daga nan bayan samuwar yanci da zaman lafiya ya yawaita sai aka basu masarautar garin baki daya tunda su suka samar da yankin ake cewa da wajen garin kandem..


Daga nan bayan mulkin damokaradiyya sai ya zamto an yarje musu. Kasa ma ta san da birnin sosai. Ya zamto shine cibiyar kasuwanci ta kasar baki daya.


Ardo kandemi wato kakan kakan kakannin usulin dangin ya zamto yana da matan sa na aure biyu. Akwai yafendo asalin sunan ta 'Nusaibatu.' Sai Yagwalgwal ita kuma usul din sunan ta 'Kausar'...


Alokacin da kasar ta samu yancin kanta ... A baya lokacin mulkin sojoji kenan, Sai wanda yake a matsayin shine shugaban sojojin da ke mulkar kasar sai ya zamto ya sanyawa yankin kandem suna. Da farkon sunayen matan Ardo, wato Nusaibatu da Kausar... Ya yi masa laqabi da birnin 'NUKAA'


Masarautar kuma sai ake cewa da ita masautar kandem... Wanda zuriyar Ardo kandemi ke karagar mulki suna mulkar garin...


To a hakane cikin ikon Allah da buwayar sa da hikimar sa zuri'ar marigayi Ardo kandemi ta tumbatsa tayi reshe tayi ya'ya da jikoki da tattaba kunne da uhumhum masu tarin yawa da albarka ..


Har ya zuwa lokacin da Nigeria ta karbi yancin kai ta nada Lagos a matsayin babbar birnin ta ya zuwa sanda akalar komai ta koma birnin Abuja...


Zuri'ar Ardo kandem ta wuce duk inda ake tunani. Sun zama reshe da ko'ina yayi ya'ya. Duk wani bangaren alkalanci na kotu, likitanci, injiniiyoyi, frofesosi, masu aikin gidan jarida da na tv, gidajen rediyo, Yan siyasa, hakimai da sarakai da dakatai, Yan kasuwa , jakadun Nigeria dake sauran kasashe... Kai da duk ma wani babban mukami na gidah dana waje idan aka duba kashi chassa'in cikin dari zuri'ar Ardo kandem ne. Allah ya sanya musu tarin albarka da dimbin nasibi mai tarin alkhairai...


Wasun su na zama ne a kasashen waje, wasun su na wasu garuruwan, wasu na wadansu anguwoyin acikin garin Nukaa din wadanda aure ya sauya musu wajajen zama. Ma'ana mafi yawan matan dangin dake auro wasu mazan da ga wasu dangin... Duk kuwa da kashi tamanin na cikin dari auren zumunci suke yi. An taba samun sabani ne sau biyu akan wasu auren da aka hada na zumunta. Har abun ya fara kawo tangarda da son rabuwar zumuntar. Dakyar aka iya sasantawa aka kuma kawo karshen hadin auren zumuntar. Ya zama dik me son auren babu takura yaje waje ya auro...



×××××



Hancin motocin su Amb. Junaid ne da iyalan sa suka shiga dandatsetsen katafaren babban gidan na kandem estate.


Babban gidah ne daya ci sunan a kira shi da 'aljannar duniya' komai yaji. Domin tsayawa ma a baku labarin yadda gidan ya kawaatu da komai na rayuwa tabbas bata lokaci ne. Sannan zuciya zata iya tantama akan hakan.


Masu gadin suka tashi da sauri suka yo kan motocin da number jikin plates din motar ke rubuce da manyan bakin kandem 01 zuwa kandem 05...


Tsayawa motocin sukayi. Amb junaid ya bude kofar mazaunin da yake. Masu gadin da maaikatan gidan maza sukayi dafifi akan sa. Sanin shi mutum ne mai karamci da adalci, dattako ya kamata, da Kuma kyautatawa da jikin sa, gumin sa da kuma aljihun sa.


Haka ya rika basu hannu suna musaba. Bakin sa abude yanata musu murmushi suma suna rissina masa cike da girmamawa.


Sai da ya tabbatar ya gaysa da kowa acikin su sannan ya daga musu hannu . Suka rufe masa murfin motar direbobin suka ja motar zuwa ciki.


Kai tsaye motocin sukayi bangaren mahaifiyar sa... Wanda shima nasa gidajen a sashen suke. Gate ne kawai ya raba su. Nata yayi dama nasa ya kalli hagu. Amma da yar tazara a tsakani.


Motocin suka danna kai cikin gate din. Suna karasa parking suka furfuto daga cikin motar . Shine agaba suna biye da shi a baya...


Ya doka sallama ya shiga cikin babban parlorn. Dattijuwar hajiyar na zaune akan wata kujera samfurin Italy. Babban Qurani ne a hannun ta. Fuskar ta saqale da gilashin kara ganin ta.


"Hajjaju na.... Hajiya ta" ya fada da sauri cike da madaukakiyar murna marar misaltuwa


Ta dago ta kalle su tana amsa sallamae. Murmushi tayi faffada. Ta mayar da kanta kan quranin da take karantawa. Ka'dane sai ta kai aya take ajiyewa. Allah ya temaka tana karshen shafin tana karashewa kuwa ta daga hannun ta tana addua kamar ko da yaushe . Suma suka daddaga hannuwan.


Amb Junaid nata kada kai yana cewa,


"Aamin, Allah ya amsa... Allah ya amsa Hajiya... Amin Amin."


Karbar Qur'anin yayi ya ajiye a inda take ajiyewa.


Tayi murmushi tana kallon su daya bayan daya,


"Allah yasa Qur'ani ya cecemu. Amin"


"Amin Hajiya"


"Aamin Amin"


"Allahumma Aamin hajia."


Suka shiga amsa adduar da tayi. Domin Hajiya Maryam akwai Ibada da yawon karanta alqurani. Tunda kananuna shekarun ta har girman ta. Shi yasa Allah ya amince duk tsufan ta ganinta bai tafi ba. Tana iya karanta komai idan rubutu yayi karanchi ne take karawa da temakwan gilashin karatu na kara girman ganin rubutu.


"Hajjaju barka da Rana... Mun same ku lafiya? Ya jiki hikin na ki? Fatan komai da komai kalau Hajiya? Allah ya saka miki da mafificin alkhairin sa yasa kifi ha ka, Amin...."


"Amin junaidu, Allah ya maka albarka, Allah ya maka albarka, Allah ya maka albarka junaidu."


"Amin Hajiya Amin."
Ya matsa daf da ita. Hawayen dadi daya nabin daya a fuskar sa. Duk girman sa idan yana gaban hajiyar su ganin sa yake dan karami.


"Allah ya albarkaci zuriyar ka junaidu. Allah ya albarkaci dukiyar ka junaidu, Allah ya albarkaci komai na ka junaidu. Allah Amin."


"Aamin Hajiya... Aamin."


Nan da nan daya bayan daya suka rika tasowa suna gaishe da Hajiya tanata amsa musu. Amb Junaid yaki matsawa daga gaban ta sai ma sake gyara zama da yayi sosai yana jin sa cikin wani irin nishadi marar misaltuwa


Amaal ce karshen tasowa ta nufi wajen hajiyan tana murmushi. Hajiya Maryam ta bude baki tana murmushi.


"Ahh takwara ta ce? Zo nan yar albarka..." Ta janyota jikin ta tana shafa kanta,


"Hajiya ya kafar ta ki?" Ta tanbayeta tana mammatsa mata su


"Da sauki maryama. Nagode kinji? Je ki huta Allah yayi albarka Amin."


"Bangaji ba Hajiya."


"To ai shikenan idan sarkin agaji yazo ka kyale."


Suka saki dariya baki daya idan aka tsame hadiza da iyalan ta da kuma ruwaida da nata yaran da ke ta kumbura zasu fashe...


Wayar sache tayi kara. Ya janyota da sauri ya shiga wajen sakonni. Dubada ko da yaushe sai an ajiye masa saqo kala kala ta kafafai da dama na social media da ma text message ta ainihin number sa.


Amma duk da tarin lokutan da aka diba bai taba ko sai daya ba zuwa dan a bincika masa mai bibiyar tasa ba, Ya dai barwa kansa sanin koma wanene, BAKON MUNAFIKI!! ne wanda (BANA MUTUM DAYA BANE)


Dubada yan uwa da dama sun juya masa baya ciki harda wadanda suka fito ciki daya wato uwa daya uba daya ..Ya Kuma tabbatar wa kansa BAKON MUNAFIKIn ne ke qissima komai. Amman koma wanene ko ma wacece da sannu gaskiya zata bayyana.. Domin komai nisan dare gari zai waye. Allah zai bayyana mai gaskia .


Sakon ma dariya ya bashi alokacin daya kai karshen karantawar. Ya sake karantawa daga farko yana girgiza kai kawai cike da rashin bacin rai,


"Ban hane ka da kada ka waiwayo zuriyar kandem ba? Ba ka ji ba sai da ka dawo gidah ko? To ka sani cewa ka debo ruwan dafa kan ka.... Ka jira ka ga abubuwan da zasu biyo baya....."


Kashe wayar yayi baki daya ya zurata a aljihu. Ya saka hannun sa duka biyun ya janyo kafar mahaifiyar sa daya ya dora akan cinyar sa. Ya yinda amaal ke matsa mata daya kafar.


Heat Balm din da ke hannun sa ya bude ya lakuta ya shafe kafar hajiyan da ita ya shiga matsa mata ahankali. Yana ta mata hira..


Tuni maaikatan suka shiga kawo musu abinci da sauran abubuwan sha dana motsa baki. Suka cikata gaban su da shi....


Kowanne ya shjga diba yana ci yana korawa da lemo da ruwa mai sanyi... Yayin da maaikatan ke ta kai kawo akan su sunata hidima akan su......




_Afuwan abisa rashin ganin cigaban paid pages na littafai biyu daga cikin ZAFAFA BIYAR. Hakan ya faru ne sanadiyar rashin lafiya da ta riske mu. Muna baku hakuri dan Allah. In shaa Allahu da mun karasa samun sauki zaku ji mu duka da yardar Allah.... Mungode da zabin litattafan zafafa biyar. Allah ya kara budi_


_ADVERT👇_


_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_


_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._


_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._


_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_


_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_


_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_
[8/7, 7:27 PM] Hafsaat💞: _*BAKON MUNAFIKI!!!*_
_(BA NA MUTUM DAYA BANE)_
_👺🏡👩‍👩‍👦‍👦_




_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_




_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
_®️NANA HAFSATU (MSS XOXO)_


__AREWABOOKS:MSSXOXO_
_WATTPAD:MISSXOXO00_


_PAID PAGE:07_


_________
Sai sha biyu saura kwata na dare tukun sannan suka fara yiwa Hajiya sai da safe suka nufi sashen su.


Amb. Junaid ya gyara zaman sa sosai a gefen Hajiya daga kasa. Ya cigaba da matsa mata kafafun nata ... Tana ta shi masa albarka.


"Allah yayi maka albarka.... Nagode nagode nagode. Ka je ka huta."


"Ai ban gaji ba hajjaju. Ko dai bacci kike ji?"


"Baccin ma ina jin sa.. Kun shisshhga wajen yan uwan kuwa?"


"Wallahi bamu zazzagaya ba Hajiya. Nan kawai muka yada zango..Da safe in shaa ALLAHU zamu jajje. Da ke sanda muka zo din nasan yawanci suna wajen aiki. Basu dawo ba da yawan su shi yasa."


"Toh Allah ya temaka... Idan Allah ya kai mu goben sai ku shisshhga."..


"Aameen hajjaju"


Dan gyangyadi ta fara yi. Charbin hannun ta da take ja har ya fadi kasa, da sauri amb junaid ya sanya nasa hannun ya gyara mata natan da kuma carbun daya fadi a kasa yadakko ya ajiye mata a gefen ta.


Ta farko da sauri tana sosa gefen idon ta na dama,


"Junaidu.."


"Naam Hajiya..."


"Ba dai bacci ka fara ba ko.?"


Dan murmushi kawai yayi ya girgiza kansa cike da girmamawa.


"Kaje ka kwanta dare ya ja."


"Toh Hajiya in shaa ALLAHU..."


"Kunyi magana da yan uwan na ka kuwa?"


"Eh munyi a group chat."


"Na'am.. Guru me?"


"Afuwan... A kafar sadarwa ta yanar gizo dinnan da ake yanzu.."


"Ma shaa Allah! Allah ya kara hade kawunan ku Amin."


"Amin Hajiya... Kuna samun su baba kuwa a waya ko har yanzu?"


"Ana samun su mana... Dazu ma nan an kira sadiya ta kawo mun muka gaisa. Wani abun ya faru ne? Kar ka boye mun"


Yayi saurin girgiza Kansa. Don ba yaso ko kadan ya sanyata cikin damuwa.


"Babu abunda ya faru hajiyar mu...Allah ya dawo dasu lafiya Amin."


"Allahumma Aameen."


Ya sake gyara zaman sa cike da girmamawa ya ce,


"Hajiya bari naje.... Kema gwara ki kwanta. Allah ya kara miki lafiya da nisan kwana da imanin Allah."


"Allahumma Aameen... Junaidu. Tare da ku duka. Allah ya tashe mu lafiya."


"Allahumma Aameen.."


Mikewa tayi ahankali da ga kishingiden da take... Tashi yayi ya dakko sandarta da ke gefen tv..


"Hajiya muje ko?"


"Da ka bari sadiya ta mun rakiyar ai."


"A'a Hajiya ... Bari nima na yau samu ladan."


Dariya sukayi baki daya. Ta rike gefen sandar. Ahankali ya shiga temaka mata har suka karasa dakin nata


Ya bude marikin ya tura suka shiga ciki. Ko'ina a tsaftace yake a dakin sai karatun Qur'ani ne ke tashi a jikin wata mp3.


Da sallama a bakunan su. Ahankali ya karasar da ita bakin babban gadon nata me lallausar katifa da babban bargo me laushi shima.


"Sannu Allah yayi albarka kaji?"


"Nagode Hajiya. Allah ya saka mkli da alkhairi."


"Allahumma Aamin"


"Ko zaki shiga makewayi?(bandaki)"


"Sadiya zata ..."


"Ai Hajiya yau so nake na kwashe duka ganimar ladan da sadiyar nan ke samu dai. A temaka dai."


Batai musu ba tayi murmushi kawai hadi da saka hannunta akan sandar ya temaka mata ta mike. Ya kaita har cikin bandakin bayan sunyi adduar shiga bandaki.


Kan wata kujera da take zama aciki saboda ciwon kafafun ta ya zaunar da ita akai. Ya janyo babbar buta duk kuwa da ruwa a famfo ya cika ta mata ya ajiye a gabanta.


Sannan ya koma dakin yazauna zaman jiran ta. Data kammala ta dauro alwala ta saka sandar ta ta dogara har wajen kofar dakyar yana jiyo motsin ta ya tashi da sauri ya bude ya temaka mata suka koma cikin dakin.


"Allah yayi maka albarka..."


"Amin hajiyar mu."


Kwankwan Kwan...
"Salamu alaikum."


"Waalaykm Salam sadiya shigo."


Nan matashiyar budurwar ta shigo sanye cikin riga da zani . Da hijabi har gwiwa.


Tana shigowa ta dafe kirji tayi hamdala,


"Alhamdulillah.."


Hajiya tayi murmushi tana kallon ta,


"Kinata nema naa ko?"


"Eh saboda da kikace na bari su tafi sashen su tukun. Na fito naga ba kowa wallahi bakiji rai na na."


"Allah sraki sadiya. Bappan naku ne yace daren yau bari wai shima ya samu lada. Ya temaka mun na yo komai sai sallah da zanyi ta nafila sai na kwanta "


"Ma shaa ALLAHU... Barka da dare bappah."


"Barkan mu dai sadiya. Sannu da kokari da dawainiya da Hajiya Allah ya saka miki da alkhairi."


"Wallahi itace ke dawainiya da ni banida bakin godiya sai fatan Allah ya cika a mizani ya biya bukatu na alkhairi."


"Allahumma Aameen."


"Bari naje Hajiya zan dawo."


"To sadiya."


"Wallahi kaganta nan yarinya mai hankali da nutsuwa. Wannan yaron (Dan ta na fari) shine ya je har cikin shukaa na kandemi tahada jini da bappan ku Nata'ala (Dan uwan ta).. Ya auri kanwar mahaifiyar ta. Mai dakin sa ta uku. Gatanan komai ta dauke mun ga temako duk inda zani bata gajiyawa da rakiya."


"Allah sarki. Allah ya saka masa da alkhairi shima. Sadiya kema Allah ya saka da alkhairi. "


"Amin" suka hada baki wajen amsawa..


Ta fita daga dakin ta rufo musu kofar. Amb juanid ya mike shima bayan ya jira hajiyan ta yi nafila.


"Toh Hajiya bari na tafi. Allah ya tashemu lafiya"


"Aamin junaidu. Sannu da lokari kaji?"


Dan murmushi kawa yayi. Cike da girmamawa ya sake cewa,


"Allah ya kara miki lafiya da imanin Allah."


Ya sake dukawa yayi mata sai sa safe sai kma ya fiche ya nufi nasa sashen shi da iyalan sa.


Bayan ya shjga cikin bangaren na sa. Parlorn sa ya wuche ya zauna. Abubuwa masu tarin dama nata kwaranyo masa. Take kansa ya fara wani zugi da radadi kan barazanar fado masa saboda azabar ciwon da ya fara yi masa na kaife daya.


Kansa ya daga sama yana tuno ko yau da safe ya kira lambar mahaifin na sa bata shiga kwata kwata. Haka sauran yan uwa da suke taren da mahaifin nasa kusan sati daya kenan a jere yana kira ba sa daukar wayar ta sa. Har gwara Kawu Adamu shi yana ce masa baya kusa dasu ya fita...


Girgiza kai kawai yayi shi kadai. Ya saki murmushi mafi kuna a cikin zuciyar sa.


Ahankali cikin sanyayyar muryar mai sauke da tarin damuwa marar misaltuwa can kasan makoshi yace,


"Toh Allah ka shiga lamuran mu... Ka yafe mana kurakuren mu Amin.."


Ya sake sauke wata ajiyar zuciyar a karo na uku kafin ya mike yana runtse idanun sa yayi cikin gidan.dake parlorn nasa shine a farko da bandaki sai kuma babban corridor dake dauke da flower vase da wani mudubi sai babbar kofar gidan mai kallon parlorn na sa. Dake daga wajen sa ana iya shiga sauran wajajen...


Dakin sa ya wuche kai tsaye. Bandaki ya fada ya tsaftace jikin sa hadi da daura alwala. Qur'ani ya dakko ya shiga karantawa.


Kafin bayan wani lokaci ya kai aya. Sai ya tashi yayi nafila. Ya bi lafiyar gado bayan yayi adduoin sa.


Abubuwa barkatai suka shiga masa yawo akai. Ya jima ainun yana tunane tunane kafin bacci barawo ya sache shi...




_Afuwan..... Ma biya zafafa biyar..🙏_




*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥




*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*


_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*




FURAR DANKO
Billyn Abdul


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at👇


1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k




_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥
[8/8, 9:45 PM] Hafsaat💞: _BM_


_08_


_NA:_
_NANA HAFSATU_


_______


Ahankali ta shiga bude manyan idanun ta tubarkAllahbda ke mata nauyi saboda baccin da ke neman rinjayar ta.


Dai dai lokacin da liman ya fara kirayen assalatu. Ta tashi da addua a bakin ta tana mai mike hannuwan ta sama.


Mikewa tayi ta shiga bandaki ta yo tsarki hade da dauro alwala. Tun da safe da aka kammala gyaran gidan aka kintsa ko'ina..don hatta sallayar da zatayi sallar akai an shimfida an ninke hijabi an ajiye shi daga gefe. Ga kuma charbi da wasu littafai na islama. Sai Qur'ani akan abun ajiyewar sa


Ta hau kan sallayar bayan ta zura hijabin ajikin ta. Nan da nan ta dau niyya ta da sallar.


Ko bayan data idar bata tashi ba tana zaune akan sallayar tana azkhar. Cikin haka aka kwankwasa kofar dakin


Tana daga zaunen ta mike ta bude kofar.. mahaifiyar tache ta shigo ciki.Ta tsugunna har kasa cikin girmamawa ta shiga gayshe da mahaifiyar ta ta.


"Alhamdulillah Amaal. Da fatan kin kwana lafiya?"


"Alhamdulillah..."


"Ma shaa ALLAHU! Ai inata sauri nache ko baki farka ba."


"Ah na tashi.. Na ma ruga alarm din tashi."


"Ma shaa ALLAHU... Allah yayi albarka"


"Amin Hayateey. "


"Kin kai kayan naki ne?"


"Ina?" Saboda baki daya ta manta .


"Dakin ku mana..."


Nan da nan fuskar ta ta sauya. Har ga Allah batasan kasancewar ta a dakin nan. Tasan kullu yaumin ranta ne zasu dinga bataa mata shi.


"Ina miki magana kinyi shiru..."


"Yi hakuri Hayateey. Wallahi banason zama tare da su."


Hajiya jamila ta sauke ajiyar zuciya. Ta sanya hannun ta kamo amaal suka zauna akan gado.


"Ya sunan ki na ainihi?"


"Maryaam."


"Sunan wa kika chi?"


"Sunan Hajiya.."


"Wacece Hajiya?"


"Mahaifiyar su abbiey..."


Haj jameelah ta kada kai kafin ta cigaba da cewa,


"Lokacin da abbieyn ku ya yanke dawowar mu Nigeria gaba daya. Da zama acikin kandem estate wayace ya roke shi alfarma daya hade kan kawunan iyalin sa ko dawowa akayi kada a rarraba kan yara. Son samu a hadesu waje daya don samun jituwa da wanzuwar zaman lafiya a tsakani. Waya ba abbieyn ku shawara ya amince batare da ya musa ba ko sau daya? Uhm waya bashi shawara?"


"Hajiya ce ta bashi shawarar."


"Ma shaa Allah! Hajiyar nan mahaifiyar sa ce, Kuma mafi soyuwa awajen abbieyn na ku. Abu na biyu kin manta biyayya ga bin nagaba da kai musanmam ma iyaye ? Iyayen ma mahaifi agare ki. Don haka kar ki kuskura kice ke a'a ko da kuwa zaki halaka sai ki hakura ki fawwalawa Allah lamuran ki.. Domin komai nisan dare gari zai waye Allah zai bayyana mai gaskia. Bugu da kari kada ki manta ma sunan Hajiya kikachi... Banason na sake jin cewar bakyasan kasancewar ki atare da su. In shaa Allah alkhairi ne zaman na ku. Kuma da yardar Allah Allah zai kare ki ki cigaba da addua. Kinji?"


Daga kai tayi. Hawaye daya na bin daya. Ta dubi dakin da take ciki wanda yake da a matsayin nata ita kadai yanzu kuma zata koma su dinga kwana tare da yan uwanta da suke uba daya


Hawa na uku agidan aka gyara akayi wani irin katafaren hadadden babban daki me girma sosai da babban parlorn sa aciki. Da bandakuna har biyu. Da kitchen da store da balcony.


Gadaje ne a jere kowa da nasa da durowar sa. Da kujera da computer ta aiki akan desk sai mini fridge karami a gefen gadaje biyu. Sai bookshelves guda uku manya a jere dauke da littafai.


Daga gabas kuma makekiyar tv ce plasma ta bango da setin kayan kallon. Kitchen dinsu ma babu abunda babu harda kayan abinci bayan kuma cikin agidah zaa dafo a kawo musu. Nasun kuma an ajiye musu ko saboda gaba zasu bukache su dafa dan wani abun


Sai wani daki daga gangaren bene, Shi kuma kayan motsa jiki ne kala kala acikin sa.


Sai wani babban daki daga hanyar fita an rubuta study agaban kofar dakin. Kana shiga zaka dora idanun ka akan kujeru kowanne da benchin sa agaban sa. Ga Qur'anai nan a ajiye da sauran littattafai na addinin islama.


Da makekiyar dispenser da disposable cups a gefe. Da manyan sallayoyi masu matukar laushi da carbi suma a gefe.


Gwanin ban shaawa dai ko'ina a tsare a kuma killace. Dakin gaban sa kuma babban daki ne shi ma da manyan katifu biyu da tv ta zaune da karamin firji a gefe. Da babbar fanka ta tsaye.


Dakin manyan masu aikin su ne da aka dakko musanmam saboda sa ido akan su da kuma tayasu ayyukan wasu abubuwan. Su uku ne. Manya biyu sai budurwa guda daya.


Su kuma bangaren mazan yana daga can baya idan an fita daga kofar sashen na iyayen su matan da na su Amaal.Anan akayi musu nasu bangaren suma kamar yadda na su amaal din yake.


Sai da su dakunan su kowanne daki mutane biyu ne aciki. Dakin da ya zamana a bangaren su Amaal din maaikatane aciki su kuma dakin ya zamana na Yaya babba wato sadeeq . Babban da ga amb. Junaid..


°°Bayan wayewar gari sosai ainun. Amb. Junaid da kansa ya kikkira matan na sa awaya ya sanar musu shi fa tun asubah ya koma bangaren Hajiya. Dan haka achan zai karya kumallo zai kumayi wanka.


Ya nanata musu cewar idan sun ci abindin safen su hanzarta su yiyyi wanka su shrya don zasu zagaya gidajen yan uwa da basu shisshiga ba. Kasancewar daren jiya yaja sosai shysa basu shiga ko'ina ba.


Maaikata ne suka kakkai musu abincin karin kumallon. Duk abunda zasu bukata an tanadar musu. Wani abincin ma ko tabashi ba suyi ba.


Tuni kowannen su ya fara shiri. Masu shiga bandaki nayo wanka. Masu rage ciki nayi. Masu saka kaya da sauran su. Kowanne dai ya zama cikin shiri.


Hajiya. J ta shiga wajen Amaal dake tsaye tana bottling din buttons din doguwar rigar da ke jikin ta. Tundaga saman rigar har zuwa kasanta wasu manyan botira ne masu girma da kyakyali. Sai kananan botiran a hannun rigar ta da ake maqale su. Mayafin rigar ma ya sha adon botiran gefe da gefe.


"Wai baki gama ba amaal? Ni meyasa ne kike da shiririta? Kinfi so kullum dai ache keche da lefi? Sarkin makara. Kullum ke ake bari a karshe a shirin komai. Sanyin jikin ki yayi yawa. Matso nan ni na karasa saka miki."


"Hayateey kiyi hakuri." Ta fada hade da matsawa wajen mahaifiyar ta ta. Ta kama hannun rigar ta na sakala mata botiran


"Gyara sanyin jikin nan zaki Amaal.. Kinga dai abbiey din ku yace sai kun maimaita ss2-ss3 anan saboda university. Don haka doke ki zama mai shirya wa da wuri. Yanzun kin ga makaranta daya zai saka ku. Ba kamar can ba ne da makaranar ki daban. Nan yana cewa ba zakuyi karatu waje daya ba zaa fara sukar sa. Duk kuwa da su ne kecin zalin ki. Kinji ko?"


"Tohm Hayateey in shaa Allah. "


"Allah ya miki albarka. "


"Aamin Hayateey tare da ke."


"Yauwa muje naga sun

Please Login or Register in order to submit comment