Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

na koyar da su ɗalibaina ne"

Ta ce "Au sunana ma haka kake faɗa kai tsaye Fadila ko, to ɗaliban naka sun zo har da budurwar ka"

Ya waro ido ya ce 'Ni ɗin, ni ina naga wata budurwa? Wallahi Fadila ɗalibaina ne"

Kicin-kicin tayi da fuska ta ce "Oho maka dai, ga abin da suka kawo can a ajiye maka"

Gaba ɗaya Yazid ya shiga damuwa, ya zauna a gabanta ya riƙe hannunta ya ce "Wallahi Fadila ni bani da wata budurwa, ɗalibai na ne kawai ni bakomai a tsakanin mu" murmushi ta yi ta ce "To shikenan na yarda".

Murmushi yayi ya ce "Meyasa ba kya son nayi budurwa?"

"Au budurwar zaka yi? Wallahi duk ranar da na tabattar da kayi wata budurwa sai dai ka dawo ka tarar bana nan"

Murmushin sa da ya saba yayi ya ce "Babu ma abin da zai kaini, dan Allah Fadila kina sona?" Yayi maganar cikin marairaicewa.

Kallonsa ta yi ta kwashe da dariya, har hularta na cirewa daga kanta.

"Fadila meye ya baki dariya kuma?"

"Bakomai, miƙo ledar nan na ga me 'yan matan naka suka kawo mana"

"Ba zaki daina wannan zancen 'yan matan ba ko?"

Rungumeshi ta yi ta ce "Gwani ɗan Inna"

Lumshe idonsa yayi yana jin daɗin yanayin.

"Dan Allah ko sau ɗaya Fadila, bana son na cigaba da zama da ke ina takura miki ba kya sona"

Miƙa masa hannunta ta yi ta ce "Biyani sai in gaya maka ina sonka ko bana sonka"

Gani ta yi jikinsa yayi sanyi, yana cigaba da kallonta.

Ta kai hannunta fuskarsa tana cigaba da murmushi.

"Fadila da kin san matsayin da kike da shi a wurina kuwa, da kin san matsayin da kike da shi a nan da baki ɗau maganata wasa kina dariya ba" yayi maganar yana nuna saitin zuciyarsa.

"Meye a nan ɗin da ka nuna" tayi maganar tana dariya.

Yazid ya ce "Irin abin da yake cikin ƙirjinki"

"A'a gaskiya da banbanci ƙirjina da naka ba ɗaya bane, kenan bani da maraba da maza" a tare suka yi dariya yana cewa Allah ya shiryeki.

Yau ko makaranta bai je ba, Ya sa Fadila ta shirya suka fara zuwa gidan Hajiya, sannan suka wuce titi ya samar musu napep, wani store suka shiga, Fadila ta ɗan sai abin da take buƙata, suka wuce ya sai musu Abinci sannan suka dawo gida.
Fadila ta ji daɗin fitar da suka yi,haka kurum ta tsinci kanta cikin nishaɗi. Sai da suka dawo suka ci Abincin dare sannan ta bi ta kan kayan da ɗaliban Yazid suka kawo mat, turaren wuta ne suka kawo mata, fal da humra.
Ta turawa Yazid gabansa ta ce "Ga abin da 'yan matanka suka kawo wa matarka"

"Ai ke suka kawowa bani ba"

"Ai sai ka yi musu godiya, idan ma dai 'yan matanka ne ba damuwa fa, da na ƙara gaba sai ka yi aurenka".

Shiru yayi mata, duk sai da ta ɗan gane bai ji daɗin abin da ta ce ba.

Ya ƙi kulata, ta shirya kwanciya ta kwanta, shi kuma yayi zamansa ya buɗe Alqur'ani ya fara tilawa.

Kusan awa biyu, amma ba shi da niyyar tashi. Dan haka ta fito daga net ɗin ta dawo kusa da shi ta zauna.

Miƙa hannu ta yi ta rufe Alqur'anin, amma ya shareta ya cigaba da yi da ka.

"Ka shiga time ɗina fa sir" ta faɗa tana riƙe masa hanci.

Yazid ya ce "Ke, sai kin ƙarasani tukuna? Ke da ba kya so na wane time ɗin naki na shiga?"

"Ni zaka yiwa wayo, fushi kake da ni ko?"

Ya ce "Ni na isa na yi fushi da ke?"

Ta ɗan sauke numfashi ta ce "Zid ina gane wa idan abu bai maka daɗi ba, amma sai ka danne fushi da murmushi, shikenan dai mu je ka kwanta"

Kamar ƙaramin yaro ya noƙe mata kafaɗa.

"To ƙaddara ina sonka, shikenan"

"Ba shikenan ba, anjima kuma sai ki ce ba kya so na"

Murmushi Fadila ta yi ta ce "Bayan ka gama tofeni da Addu'a cikin dare, kana sa mini hannu a riga ai ina jinka wataran".

"Sharri zaki mini"

"To ka ce ba ayi ba mana, kana ta tofeni da Addu'a, ka mallekeni"

Yace "Ni addu'a kawai nake miki ta kariya, ni ban san zancen da kika gama ba"
haka suka kwanta Yazid yana jin farincikin ganin Fadila na nuna masa kulawa da soyayya.

Sannu a hankali ta gama sakin jiki da shi, ta rungumi rayuwa a yadda ta zo mata, ta rungumi Yazid da sai a yanzu ta gano yadda take mutuwar son sa.



Sai da Amina suka yi wata da sati uku, da tafiyarsu Lagos zuwa umara, sannan suka dawo Kano.
Tun da suka dawo Daddy yake fargaba, dan ya san halin Zainab sarai.
Jin labarin su Amina sun dawo, ya sanya maƙwabta suka dinga shigowa sannu da zuwa suna yi wa Amina sannu da zuwa.
Zakiru da Hajara kuwa duk garuruwansu suka wuce, domin suma su samu su ɗan huta sannan su dawo bakin aiki.

Kamar yadda Daddy ya tsammata, haka Hajiya Zainab taje ta titsiye shi, cikin faɗa da tashin hankali, a kan lallai ya gaya mata in da Fadila take, amma still ba ta samu wata gamshashiyar amsa daga gareshi ba, hakan ya ƙara tunzarata, tayi masa cin mutunci san ranta ta koma sashinta ta zauna ta dinga kuka kamar ƙaramar yarinya.

Washegari da sassafe Hajiya Zainab ta shirya ta nufi Dutse,bata tsaya ko ina ba, sai gidan kawun Alhaji Ahmad, gaba ɗaya mutan gidan bin ta ska dinga yi da kallo, dan rabon da ta tako taje Dutse har sun manta, balle ta je gidansu, amma yau suka ganta a gidan.
Ta sanar musu da wurin Kawu ta zo, suka je suka yi mata iso a wurnsa.

Shi kansa mamakine ya kama shi, tare da tambayarta ko lafiya?

Fashewa da kuka Mummy ta yi ta ce 'ƙarar Ahmad na kawo maka, yau an kusa shiga wata na uku, ya ɗauke mini Fadla ya kaita in da ban sani ba, nayi-nayi ya ƙi gaya mini in da take"

Kawu ya ce "Ke Zainab ban da abinki wannan ai abin da zaku iya sasanta kanku nex.

"Nifa na yi iya yina, amma yaƙi saurarata ni dai ku saka baki ya gaya mini in da 'ya ta take".

Kawu ya ce "Shikenan, zamu zo gidan naki in sha Allah, ki koma gida" jin ya bata tabbacin zai zo ya saka Alhaji Ahmad a gaba ya gayamata in da Fadila take, hankalinta ya ɗan kwanta, ta fito ta fice.

Tana ƙofar gida tana shirin kunna mota, sai ga wata ƙanwarta, tana ganinta ta ce "Laa Anty Zainab, dama kin shigo Dutse Baba Auwalu ya dawo daga umara mun ji abin arziƙi Allah ya saka"

Ko saurarata ba tayi ba, ta ja motarta ta bar wurin, dan ga san ta tsaya ne ta gaya mata Baba Auwalu ya dawo dan gulma, tunda sun san kishiya ce ta saka aka biya masa.




Fadila kuwa ta kwantar da hankalinta, tana rayuwarta sannu a hankali da Yazid, wata irin soyayya suke yi kamar su cinye juna take, ji take yi Allahn da ya haɗata da Yazid ne kawai zai iya rabata da shi, saboda yadda yake kulawa da ita ne da yake da biye mata da yake yi, ya sanya take taɓararta son ranta.
Tana matuƙar tausaya masa saboda labarin rayuwarsa da ta ji, yayin da shi ma yake tausaya mata na wannan sauyin da ta samu lokaci guda.
Yau ma suna kwance ya gama yi mata ƙarin Alqur'ani, da litattafan Addini.
Fadila ta fuskanci cewar ƙarancin ilimin addini ya taka muhimmiyar rawa a rayuwarsu, da ya sanya suke aikata wasu abubuwan.

Suna kwance Fadila ta ɗora masa ƙafafuwanta a jikinsa. Yana jinta tana neman magana amma yayi mata shiru.

Can ya kira sunanta "Matar"

"Mmmm"

"So nake muje Rano" Yazid yayi maganar yana murginawa kusa da ita.

Fadila ta ce "Mu je mu yi me?"

Yazid ya ce "Muje kiga 'yan uwana da dangina mana, idan Allah ya bamu haihuwa ma kinga kin san in da dangina suke"

Fadila ta ɗan yamutsa fuska ta ce "Waye zai haihun?"

"Ke mana Habibty"

Fadila ta ce "Taɓ, gaskiya na yi ƙanƙanta da wata haihuwa"

Yazid ya ce "Au Ba zaki haihu ba amma kin iya zuwa ki sakani gaba kina a baki time ɗinki ko kina lallaɓani?" Yayi maganar cikin zolaya.

Dariya Fadila ta yi ta ce "Nake lallaɓaka ayi me? Ka jika har da sharri abin naka, to amma dai ka san ba a haka aka kawo maka amanata ba ko? Saliha ce ni ba abin da na sani"

"Mhmm shiyasa idan na zauna kusa da mutum a makaranta yake rawar jiki ko?"

Buɗe baki tayi ta ce "Laaa wai haka ka iya sharri Zid?".

"Kice ba ayi haka ba? Kullum kina liƙe da ni, ni matsa ki bani wuri na yi bacci" rasa me zata yiwa Yazid ta huce tayi ta ɗau pillonta tana kwaɗa masa.

Dariya yake yi, ya ja hancinta ya ce "Ki kwanta kar mu kasa tashi gobe in Allah ya kaimu".

Fadila ta tura baki ta ce "Wallahi zan rama, dani kake zancen" ya rungumeta yana murmushi.

Wuta aka kawo, haske ya gauraye ɗakin Fadila ta ɗan rintse idanunta ta ce "Dama baka kashe fitila ba"

"Eh, tashi ki kashe mana"

"Naƙi ɗin" ta faɗa tana lumshe idanunsa.

Gani yayi ta zabura ta tashi da sauri, shima ya tashi zaune ya ce "Wifey menene?".

"Zid kaina ne ya fara yi mini irin wannan ciwon da na kwanta a asibiti"

A gigice ya ce "Subhanallah ko jinin naki ne ya hau?"

Ta girgiza masa kai ta ce "Zid kaina zai fashe, duhu fa nake gani".

Take ya gigice "Fadila menene?" Yayi maganar yana riƙeta.

Fizge-fizge ta dinga yi tana neman ta fita hayyacinta.

Yazid ne ya fara yi mata addu'a yana tofa mata, amma sai mimmiƙewa take tana wani irin numfashi.

"Bana ganinka fa Zid, duhu nake gani kaina zai rabe biyu, bana gani fa"

Sosai ya rungumeta a jikinsa, ya ɗora hannunsa a kanta yana karanto mata addu'a.





Su Kawu ne zaune a falon gidan Alhaji Ahmad, ga Hajiya Zainab duk suna zaune a falo.

Kawu Hamza ne da Kawu Ali ƙannen mahaifin Alhaji Ahmad, da suka yi wancan zaman tare da su lokacin da za a gaya mata auren Alhaji Ahmad.

Kawu Hamza ya ce "Ahmad, kar kace mini ba tare da saninta ka yanke hukunci da ka yanke ba, ace tsawon wannan lokaci ba ta san in da ka kai mata 'ya ba?"

Daddy ya ce "Kawu ban yi mata haka ba dan na wulaƙanta ta, sai dan sanin cewa idan na gaya mata zata iya ɓata komai"

A fusace fuska duk hawaye ta ce "Ni bana son wani dogon jawabi, ka gaya mini in da 'ya ta take, saboda rashin tausayi da imani ka ɗauke mini 'ya ka kaita wani wurin, kuma ka ɗau matarka kayi tafiyarka ka barni ko na mutu ko na rayu ba ka damu ba, ina ka kai mini 'ya ta?"

Daddy ya ce "Na aurar da Fadila ne ha mutumin da ya dace da rayuwarta"

Cikin rashin fahimta ta ce "Kamar yaya?"

"Kamar yadda nake gaya miki, Fadila na ɗakin mijinta yanzu haka"

Kawu Hamza ya ce "Haka ne, a Dutse aka ɗaurawa Fadila aure, sai dai mu bamu san ne gaya miki ba!!!


Ayshercool
08081012143LITTAFIN KUƊI NE, MAI BUƘATA YA TUNTUƁENI A KAN LAMBAR WAYATA.

81

"Ahmad kana cikin hayyacinka kuwa? Ko dai ka sha wani abun ne?"

Daddy ya ce "Tun da nake da ke na taɓa shaye shaye ne?"

Cikin ƙunar rai ta ce "Zata iya yiwuwa ka fara a 'yan tsukin kwanakin nan, wace irin maganar banza ce haka kake yin ta? ta yaya zaka yiwa Fadila aure babu sani na, aure ba shiri bakomai kamar auren dabbobi"

Daddy ya ce 'Ai dama nine nake da alhakin aurar da ita ga mutumin da ya dace ba ke ba. Da fari kin kawo naki zaɓin kun dawo kun janye, kun zubar mini da mutuncina a idon a duniya, dan haka na aurata ga wanda na ga ya dace"

Ta kalli Daddy ta ce 'Ahmad so kake ka ga na haukace ina bin bola saboda baƙin cikinka ko? To da ikon Allah, sai dai kaga haka a kanka, kuma na baka nan da awa ashirin da huɗu duk in da 'ya ta take ka fito mini da ita, idan ba haka ba wallahi kotu zan kai ka azzalumi mara imani Ahmad ka kasheni ka huta kawai mana"

Kawu Ali ya ce "A'a Zainab ba a haka, bai kamata kiyi haka ba uban 'ya'yanki ne fa, dan Allah ku zauna kuyi sulhu a tsakanin ku"

A fusace ta ce "Babu sulhu a tsakanina da wannan mutumin, dama ai kune kuke shirya kowane munafunci, kuma kuke ƙara goya masa baya, komai yayi ai daidai ne a wurinku, tunda ni ba 'yar ku bace ba dole ku dinga goya masa baya, to wallahi na gaji da baƙin cikin da mutumin nan yake ƙunsa mini a cikin gidan nan, wallahi ƙararsa zan kai muddin bai dawo mini da 'ya ta ba, ai ba shikaɗai ya haifeta ba" ta tashi fuuuu ta bar falon.

Su Kawu sun yiwa Daddy faɗa sos6, tare da nuna masa rashin kyautawar abinda ya aikata na aurar da Fadila ba tare da ta sani ba, ko a lokacin su kansu sun yi masa magana a kan wannan wane iri aure ne bagatatan kamar yaƙi, amma ya ce musu yana da dalili, ya yi ta basu haƙuri dai suka tafi.

Ba ƙaramin tausayin Hajiya Zainab ya ji ba, shi kansa ya ga uwar ramar da tayi bayan dawowarsu, ya san tana cikin damuwa, amma yanzu da zarar yayi wani yunƙuri ci masa mutunci za ta yi, amma bai haƙura ba, ya nufi sashinta, duk dan ya samu a zauna lafiya, amma yana shiga ta dinga zazzaga masa masifa da tashin hankali, sai da ya gwammace bai je in da take ba. Yana bata haƙuri da lallaɓata tana buntsirewa tana cin mutuncin sa dana kwaunnan sa. Take ya ji zuciyarsa ta kuma bushewa, bama ya dana sanin auren da ya yiwa Fadilan, a ransa ya sake ganin hakan shi ne daidai.
Da ya aurar da ita ta je tana irin halin mahaifiyarta, gara da Amina ta bashi Shawarar yin haka.
Yana zuwa sashin Amina kuma, ya tarar da ita a toilet, tana ta sheƙa uban amai, kamar zata amayo kayan cikinta. Take ya manta da zafin da Hajiya Zainab ta haɗa masa, ya tattara hankalinsa a kan Amina, ya shiga toilet ɗin ya taimaka mata ta gyara jikinta suka fito yana mata sannu.
Ta kalleshi ta ce "Dear ina su Kawun ko har sun tafi?"

Daddy ya ce 'Eh sun tafi"

Ta ce "Subhanallah, yanzu ya kuka yi ni da muka dawo gani nayi ta rame sosai, yakamata kawai a gayamata gaskiya in da Fadila take"

"Meenal, kin san halinta lokacin da ake lallaɓata a lokacin take wulaƙanci, dan haka ki nar wannan zancen tukuna tun yaushe ne ba ki da lafiya?" Tunani tayi idan ta ce masa ta kwana biyu zai ji babu daɗi, dan haka ta ce masa "Yaune kawai na tashi cikina babu daɗi, nake ta amai"

Ya ce "Shirya muje Asibiti a duba mini ke, na tsorata da wannan aman".

Babu musu ta shirya, suka fita domin zuwa Asibiti, a hanya ne Amina take bashi shawara yakamata ya kira Yazid ya ji suke, idan da dama ma ya je da kansa ya duba su"
Daddy ya ce "Ai da muna Lagosa na kirashi, ya ce mini babu matsala, ba zan je ba yanzu zan kuma kiransa dai a waya, ko na gayyace shi gida na ji abin da yake wakana, amma ba zan je ta ganni ba zan iya mayar da aikin baya"

Amina ta ce 'Kuma haka ne, to Allah ya jishe mu alkhairi"

Ya amsa mata da Amin.

Bayan gwaje-gwaje da yakamata ayi mata, likita ya tabattar da tana da ciki. Dama ita ta sani, Daddy sai murna yake yi, sai dai ta wani fannin Amina bata wani murna, saboda zata fara zuwa makaranta, gashi da alama cikin mata ya zo da laulayi, sai dai ba ta son ta ɓatawa Daddy rai, dan haka ta biye masa yana ta murna yana Addu'a Allah ya bar masa.


Wata irin miƙa Fadila take tana nishi, sai jujjuya kai take yi, Yazid ya dinga karanta mata Alqur'ani ta dinga mimmiƙewa tana wani irin gunjin kuka, ya daɗe a rungume da ita yana yi mata Addu'a, kan Allah ya taimake shi jikinta ya saki ya yi sanyi ta hau bacci.
Mamaki ya shiga yi, dama Fadila na da iska ne? Amma shi bai taɓa ganin alamar hakan a tare da ita ba to yaya aka yi haka ta faru?

Hajiya Zainab kuwa ji tayi kamar ta sha guba ta mutu dan baƙin ciki, ta rasa in da zata saka kanta bata san da me zata kwatanta irin abin da Alhaji Ahmad yayi mata ba.
Kamar yadda ya zame mata kamar wahayi duk abin da ha sameta sai ta sanar da su Hajiya Salma, haka ta ɗau mota ta tafi shagon Hajiya Salman, aikuwa ta tarar da ita da Hajiya Turai duk suna tare.
Suna ganin a yadda ta zo suka san akwai damuwa. Aikuwa ta zazzage musu duk abin da yake faruwa.

Hajiya Salma ce ta kwarara ashar ta ce "Ban taɓa ganin azzalumin mutum da baya tsoron Allah ba, yanzu ƙiyayyar har ta kai ga haka? 'yar da ya haifa, wallahi mutumin nan baya tsoron Allah, kuma ko ki yarda ko karki yarda wannan sheɗaniyar Yarinyar da yake tare da ita, ita ce take yi masa asiri, gara tun wuri ki bazama ki nemi abin yi, idan ke ba zaki iya ba mu sai muje mu nemo miki taimako. Kina kallo yanzu ko kuɗaɗen da kike samu a wurinsa yaushe rabon da ki samu? Duk ta toshe komai ita kaɗai take samun komai ta nayar da ke hoto, wai ma wa ya aurawa Fadilan?"

Jiki a sanyaye Mummy ta girgiza kai ta ce "Nima ban sani ba"

Hajiya Turai ta ce "Ni na ma rasa bakin magana, ƙarshen raini da wulaƙanci dai yayi miki shi, dole ki san duk yadda zaki yi ki nemo 'yarki"

Yadda suka dinga zigata suna nuna mata Daddy ya gama wulaƙantata ne ya sanya ya kuma hawa, har take jin a duniya ta ƙara tsanar uban 'ya'yan nata.




Yazid kuwa kusan raba dare yayi yana yiwa Fadila Addu'oi. Da Asuba ko sallar asuba bai fita ba a gida yayi salla, ya tasheta tayi salla, da yayi mata batun ya jikinta? Sai ta ce masa ai ita lafiyarta ƙalau babu abin da ya sameta gaba ɗaya.
Yazid ya bar maganar a ransa, sai da ya saka mata ido sosai, wurin kula da ibada da Addu'oi, duk da wasu lokutan sai sun yi faɗa dan tana cewa ya takura mata.
Kwana kusan biyar, ta ware sosai ya kuma taso mata da maganar za suje Rano.
Ita kwata kwata bata son zuwa Ranon nan, dan ba ta ga abin da Yazid zai koma yayi a garin da suka nuna basa buƙatar sa ba.
Ita kanta Hajiya mita ta dinga yi, a kan Yazid ya haƙura da Ranon nan, amma yayi ta lallaɓata yana bata haƙuri.

"Dan Allah Hajiya kiyi haƙuri ki bari na je, na kai musu Fadila ma su gaisa, tun da 'yan uwana ne babu yadda na iya, yakamata ta san suwaye dangina, idan aka kwana biyu kuma sai mu je Jalingo"

Hajiya ta ce "Dan dai ka matsa ne Yazid, amma ni banga amfanin mutanen nan a tare da kai ba, bayan ƙiri-ƙiri sun nuna ba ƙaunarka suke yi ba"

Yazid ya ce "Duk da haka Hajiya, ko ina so ko bana so ai 'yan uwana ne"

"Eh na san 'yan uwanka ne, amma matarka da zaka ɗauka ka kai musu fa, dama ita ma gata ga yadda take, kuma kaje su kunyata ka a gabanta kai baka tunanin haka kwata kwata?".

Yazid ya ce "Hajiya ai ya san komai na gaya mata"

"Ka gaya mata kuma, shikenan Allah ya tsare, amma ban yadda ka kaita ku je ka kwanar musu da 'ya a wannan garin ba, kar su yi mata wani abun"

Yazid ya ce "In sha Allah ba kwana za mu yi ba, a ranar zamu dawo".

Washegari da sassafe Yazid suka shirya, suka nufi tasha.
Tun da Fadila take bata taɓa zuwa tasha ba, galibi a jirgi suke zirga-zirga, sai kuma Dutse da sukan je a mota.

Fadila tana cikin dogon hijjabi, har da face mask a fuskarta, ba a ganin fuskarta. Warin da wasu da ga cikin matafiyan suke yi ne da warin fetur, ya sanya zuciyar Fadila tashi, ta riƙo hannun Yazid ta ce "Zid"

"Na'am Baby, menene?"

"Zuciyata tashi take, wannan warin fetur ɗin ya dameni, ga wani wari da na kasa gane kona menene"

Cikin kulawa ya ce "Ko wani abun zan sai miki ki saka a bakinki?"

Ta ce "Eh sai mini"

Kafin su fara tafiya, Yazid ya sauka, ya sayo mata kwakwa da dabino, da aya fal, ya kawo mata.
Cikin hijjabinta ta shiga ta jingina da jikin Yazid, tayi ta ciye-ciyen ta, har aka fara tafiya.
Ƙarfe sha ɗaya na safe suka isa garin Rano, suka samu wata motar suka ƙarasa.
Garin gwanin ban sha'awa sun yi noman rani, ko ina koren ganye, ga su da hanyoyi masu kyau, ko ina titi ha fitlinsi na solar duk a kan titunan.

Duk da gidan su Yazid ginin ƙasa ne, amma tun daga ƙofar gidan zaka san me gidan yana da rufin asiri,ginin ya ginu doguwar katanga ce sosai. Ga soraye sun kai takwas kan ka dangana da cikin gidan.

Gidan yana ɗauke da ƙaton tsakar gida iya ganinka, da ɗakuna kashi-kashi a ciki. Ko da yake ginin na da ne, amma ka san talaka ba zai iya irin wannan ginin ba.
Suna wuce sorayen Yazid yana mata bayanin wasu daga abubuwan da suka faur a baya.

Da sallama suka shiga gidan, suka tarar da yaran gidan suna ta kaiwa da komowa a tsakar gidan.
Wata budurwa ce ta amsa sallamar, tana ƙarewa su Yazid kallo.

Yazid ya ce "Haulat ina mutan gidan ne?"

Wadda aka kira Haulat ta ce "Ba sa nan an kai Baba Uwani gidan mai magani, amma yanzu zasu dawo"

Ya ce "To bamu abin zama kan su dawo"

Ba musu ta shiga ta ɗauko musu tabarma, ta dawo ta shimfiɗa musu. Suka nemi wuri suka zauna.
Fadila na cigaba da ƙarewa gidan kallo.

"Zid ina ne ɗakin Inna?"

Yazid ya nuna mata da hannunsa ya ce "Gashi can, naga ma yanzu shirgi suke tarawa a ɗakin"

Ta ce "Allah sarki, Allah yayi musu rahama baki ɗaya"

"Amin my wife, na gode sosai"

Suka cigaba da hira, yana bata labari, kasancewar ya san yanayin gidan nasu sai a hankali, hatta ruwan da zata sha sai da ya saya mata.

Suna nan zaune suna hira, 'yan ƙanan jikokin gidan da yaran maƙota suna ta kaiwa suna komowa a gidan.

Hayaniya suka fara ji, ana ƙoƙarin shigowa da wani abu, gaba ɗaya hankalin Yazid da na Fadila ya koma kan hanyar shigowa.
Wasu samari ne suka shigo da abu a cikin tabarma, sai daga baya Yazid ya lura da yayyensa mata da suka shigo daga baya.
Abin da aka ajiye a cikin tabarmar ne ya ɗan tsorata Fadila, mace ce ƙafarta ta kumbuta himmm, da cikinta fuskarta duk wasu irin ƙuraje, gashi tayi baƙi sosai.
A gigice Yazid ya tashi ya nufi in da matar take yana faɗin "Baba Uwani, meya sameki haka?" Da ƙyar matar ta iya ɗaga kanta ta kalli Yazid ta ce "Gwani kai ne yaushe ka zo?"

"Tun ɗazu muka zo matar da na aura na kawo muku ku gaisa, amma meya sameki haka?"

Ta fashe da kuka, yayin da yayyen nasa kuma suke bin Fadila da ke zaune a gefe da kallo, fara tas da ita me kyau wai yake faɗin matarsa ce.
Ita kuwa Fadila ta haɗe rai, ta ja face mask ta rufe fuskarta, dan duk sai ta ji haushin su ya kamata, dan da alama yanayin tsayinsu da idanuwansu ya tabattar mata da yayyensa ne.

Matar ta riƙe hannun Yazid tana kuka ta ce "Yazid ka ga yadda Allah ya mayar da ni, hakkinka sai bibiyarmu yake yi ni da Hanne, yanzu ita tana can tana fama da ciwon miyagun baƙaƙen aljanu, jikana Sani ma an shanye masa hannu da ƙafa, nima ka kalli yadda Allah ya mayar da ni, kuma mai magani ya ce dole na nemi afuwar wanda muka yiwa asiri9"

Yaya Gaji da ke kusa da Baba Uwani ta ce "Baba dan Allah kiyi shiru, wannan ba abin da zaki tsaya kina faɗa bane ba dan Allah".

Baba Uwana ta girgiza kai ta ce "Bar ni Gaji, nikaɗai na san me nake ji ban sani ba ko gaya masan ya sanya na samu sauƙi"
ta kuma mayar da idonta kan Yazid da fuskarsa ta bayyanar da damuwa ta riƙo hannunsa ta

Please Login or Register in order to submit comment