Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sake ɗiba ta ci, taji yayi mata daɗi sosai da sosai.
Jan kujera tayi ta zauna, ta dinga tsamar naman nan tana ci, kan kace meye wannan ta ci ya kai rabi.

Hajiya Zainab kuwa sai lallaɓa Daddy take yi, tana yi masa kwarkwasar da sai zai bata kuɗi yake ganinta.

Ta sha uwar kwalliya, sai ƙamshi take tayi masa jagora zuwa falo, sai hira take yi masa.

Turus tayi lokacin da suka ƙaraso dining, taga Amina zaune da spoon a hannunta tana cin naman da ta tanada saboda Alhaji Ahmad.

"Ke, wani irin wulaƙanci ne wannan da rainin hankali, na girka wa Mijina abun ki zo ki zauna kina ci?" Ɗan saroro Amina tayi sannan ta ce "Dan Allah kiyi haƙuri, wallahi ban zaci ke kika dafa masa ba, nayi zaton Hajara ce......

"Ko kuma uwar Hajara ba, saboda tsabar rashin mutunci ko Hajarar ce ta dafa ba kya bari a baki iznin ci ba, zaki zauna na yiwa mijina girki ki cinye"

Amina ta ce "Ya salam, amma nace kiyi haƙuri ni wallahi ban san ke kika girka ba, saboda ban taɓa ganin kin yi ba, raina ne ya biya amma ba damuwa ai sai na girka masa wani".

A cikin tsananin fushi Hajiya Zainab ta kalli Daddy ta ce "Wallahi tun wuri ka taka wa Yarinyar nan burki, wannan wane irin iskanci ne da rashin mutunci,? Yaya za ayi na dafa abu saboda kai ta zauna ta na ci, yanzu nayi magana ace na fiye kishi da neman rigima ita kuma wannan me tayi?"

Daddy ya kalli Amina ya ce "Meenal, meyasa ki ka ci bayan kin san ba ke kika ajiye ba, kin san fa bana son neman magana"

"Wallahi Daddy ban san naka ne ta ajiye maka ba, ji nayi ina son ci shiyasa"

"Eh tunda gaki mayya ba, dangin mayu kinga nama idan baki ci ba mutuwa zaki yi".

Amina ta ce "Ni ba mayya bace, danginmu kuma babu mayu, dan hak.... Ba ta ƙarasa ba Daddy ya ce "Ya isa haka, ki bata haƙuri kawai a wuce wurin"

"Amma Daddy tunda kuka fito fa nake bata haƙuri, me kuma take so nace mata?"

A ɗan hasale ya ce "Ki bata haƙuri nace, bana son gardama"

Amina ta sunkuyar da kanta ta ce "Dan Allah kiyi haƙuri, ban san ke kika girka ba"

Daɗi ne ya kama Hajiya Zainab, ganin yadda Daddy ya fara acting, ya sanya taji a ranta ai maganinta ya fara ciksa, dan ma bai ci wannan naman ba, in da Allah ya taimaketa akwai sauran maganin.

Ta haɗe rai ta ce "Gaskiya dai ka sake ja mata kunne, kar ta sake yi mini irin haka, idan kuma ta kuma komai nayi mata ita ta saya"

Daddy ya ce "Kiyi haƙuri, ba zata sake ba in Sha Allah, kuma in dai nine kar ki damu, na karya haka na gode sosai da kulawa"
Amina kuwa miƙewa tayi, ranta babu daɗi garin ta bar wurin, ta kifar da sauran naman ya zube a ƙasa.

Daddy ya kalleta ya ce "Ina zaki? Ba zaki zauna ki karya ba?"

Hajiya Zainab ta ce "No, bana buƙatarta a nan, daga ni sai kai nake son muyi breakfast, ta samo dai abu ta gyara wannan abin da ta zubar" ko sauraransu Amina ba tayi ba, tai musu banza tayi tafiyarta.

Ɗaki ta koma ta nemi wuri ta kwanta, taji yadda naman da taci yake taso mata, ga shi taji kamar tana ƙaurin hayaƙin nan da ta fito ta tarar ya turnuƙe falo.
Guntun tsaki ta ja ta na juyi a kan gadonta, daga bisani wani irin bacci yayi awon gaba da ita.

A cikin baccin nata ne, taji yadda cikinta yake murɗawa, ta farka ta tashi zaune, abu kamar wasa cikinta ya dinga murɗawa, ta dinga juyi a kan gadon nan, daga baya kuma sai amai. Tun tana iya tashi daga kan gadon ta tafi toilet, har ta nemi wuri ta zauna a toilet ɗin, ta dinga kwara aman nan ba ƙaƙƙautawa, duk ta fita hayyacinta kamar wadda tayi cholera.

Babban abin da ya bata haushi bai wuce yadda Daddy ko ya leƙo yayi mata sallama kan ya fita ba, alhalin idan yana wurinta, sai ya je yaga Hajiya Zainab koda kuwa zata ci masa mutunci ne.

Bayan fitar Daddy, Hajiya Zainab ta ɗau waya take bawa su Turai labarin abin da ya faru a group. Suka tayata murna saboda alamu ya nuna kamar maganin ya fara aiki, amma Hajiya Turai ta ce "A gaskiya naji haushin cin naman nan da wannan shegiyar 'yar tayi, Allah ya sa shi ne ajalinta"

Salma ta ce "Amin dai, sai ki sake dafa masa wani, amma ki tabattar daga ke sai shi a ɗaki, ki bashi ya ci".

"Haka za ayi, na fara na turaren nan ma, ni na naman na damu ya ci, kuma shi yafi son kifi fa a kan nama, saboda hawan jini"

Turai ta ce "Haka nan zaki lallaɓa shi, sai yaci, mu dai fatanmu buƙatar mu ta biya"

Ta ce "Haka ne, in Allah ya yarda zan duk mai yiwuwa, naga na bashi ya ci, sonake naga ya kori Yarinyar nan korar wulaƙanci a gidan nan"

"Kar ki da mu, ke dai ki civaba6da gwada maganin" suka cigaba da zigata da baga shawarwarin yadda zata ɓullowa al'amuran.



Khalil kuwa ya dage sai shiri yake, yana narka kuɗi a gininsa, kamar wanda zai auro 'yar wani gwamna ko sarki, sannan yana turawa Hajiya Maryam kuɗi domin yi masa sayayar kayan lefe.
Sunata cigaba da tsara yadda biki zai kasance.
Abdul ya ga yakamata ya sanar da Khalil batun soyayyarsa da Yusra, kar ya zo yaji a wani wurin yaji babu daɗi.
Dan haka bayan sun gama hirar yadda abubuwa zasu kasance a bikin Khalil, sai Abdul ya fara sako masa nasa zancen ta hanyar cewa "Malam nima fa na kusa kai kuɗin Auren nan". Khalil ya ce "Are You serious?"

"Da gaske nake maka"

"Amma gayen nan baka da kirki, amma baka taɓa gaya mini ba, ko ka haɗani da ita mu gaisa ba"

Abdul ya ce "Ai ba wata bace a nesa, ta gida ce"

"Ok, wacece?"

Abdul ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Yusra ce, ƙawar Fadila".

Khalil ya ce "Ohhh Allah, Allah mai yadda ya so, lallai zaka sha iyayi da rawar kai, ka rasa Fadila amma kusan halinsu ɗaya Allah ya baka wuyanka ɗauka"

"Amin na gode da fatan alkhairi"

"Ahh haba bakomai, amma gaskiya ku bari a fara nawa sai ayi naku"

Abdul ya ce "Saboda wayo, to ban yadda ba"

Gaba ɗaya Abdul bai yi zaton Khalil zai ɗau abin so simple haka ba, a zatonsa zai nuna bai ji daɗi ba, saboda a baya ƙanwarsa ya nuna yana so.


Yazid kuwa ya kuma haɗuwa da Fadila a makaranta, sai dai fuskar nam babu yabo ba fallasa, da fara'arsa ya ƙarasa gareta yana mata murmushi.
"Alhamdilillah, naji daɗi da ban ganki kina kuka ba, amma ya aka yi kwana biyu baki shigo school ba?" Yayi maganar yana ƙoƙarin zama, amma ta matsa gefe dan bata son yadda jikinta ke rawa da sun samu kusanci.
Fasa zaman yayi ya ce "Ohhhh sorry, ina fatan yanzu kin watstsake?"

Ta ɗan gyaɗa kai ta ce "Yes Alhamdilillah"

"Tsarki ya tabatta ga Allah, mun gode masa bisa ni'inominsa da jarabbwowinsa. Kin san ita rayuwa sai ana yi ana taɓa ɗan Adam yake sake samun kusanci ga mahaliccinsa, kuka ba mafita bane ba sam, Addu'a da miƙa lamari ga Allah su ne mafita kin ji?"
Kallonsa tayi amma bata amsa ba.

"Ya kika yi shiru?"

"Ina jinka ai"

Ya ce "Alright, yauwa dan Allah ina sake godiya da alherin da aka yi minina gidanku"

"Kaga bakomai kar ka damu kawai" ta katse shi.

Bai sake cewa komai ba ya bar wurin, ita ji tayi ma gaba ɗaya ta tsani zaman ajin, dan haka ta tashi ta ɗau jakarta ta fice.

Yusra ta kira a waya, Yusra ta sanar mata tana common room, dan haka ta wuce ta je ta tarar da ita a can.

Ta je ta samu Yusra a can, tana zuwa ta zauna ba tare da ta ce mata komai ba.

Yusra ta kalleta a nutse ta ce "Beb, meke faruwa ke ba a rasaki da damuwa menene?"

Kaar za tayi kuka ta ce "Komai ma Yusra, gaba ɗaya gidanmu babu daɗi, wannan yarinyar ta ɓata mana jin daɗin rayuwa, ko kin san Mummy sai da ta bar gida kwana huɗu ba wanda ya san in da take"

"Subhanallah, amma dai an ganta ko, ai ni baki gaya mini ba"

"Ta dawo jiya, baƙin ciki da ɓacin ran da Daddy yake sakata ne ya ta tafi, ba wanda ya san ina taje sai jiya ta dawo, Yarinyar nan munafuka ce, last week tunda na zo school ɗin nan nake kuka, baki ji cin kashin da take yiwa Mummy ba, kuma Daddy yana goya mata baya, da aka tashi daga school yazid ya kaini gida, saboda munafurci ta bashi abu ni ban san me ta bashi ba yake ta ayi mata godiya, da ni na bashi ba lallai ya karɓa"

Yusra ta ce "Au kun shirya da Yazid ɗin ne?"

"Ke oho masa, ni ba shi ya dameni ba, Yaya Khalil fa ko a jikinsa abin da Daddy yayi wa Mummy, yama koma wurin ta ita da Daddy, duk yadda zan gaya miki ba zaki gane yadda gidanmu ya tarwatse ba"

"No, ki daina faɗar haka, gidanku ba zai taɓa tarwatsewa ba, kuma komai zaa wuce da yardar Allah"

Fadila ta ce "Allah ya sa, ni ji nake dama muna da wasu 'yan uwa da muke zuwa gidansu, da can zan koma ba zan iya jure wannan tashin hankalin ba"

"Fadila Addu'a ita ce mafita a kan komai, dan haka ki miƙa lamuranki ga Allah, ki manta da komai"

Fadila ta nemi wuri ta kwanta a cinyar Yusra, tana ganin Yusra ba zata gane halin da take ciki ba.




Amina ba ƙaramin ƙulewa tayi ba da Daddy bai shigo ba, ta sha wahala sosai da ƙyar aman da take ya tsaya.
Wajen azahar taji ana bubbuga ƙofar bedroom ɗinta, da ƙyar ta taso ta buɗe. Sai taga Hajara a tsaye.
Hajara ta ce "Naga gaba ɗaya banga kin fito ba, shine nace bari na zo na duba ko lafiya".

Amina ta ce "Wallahi Hajara bana jin daɗi ne, dan Allah ida da gasarar kunu, ki damo mini ki kawon in samu na sha"

"Subhanallah, Allah ya sauwaƙe kina ɗaki baki fito ba shiyasa ba wanda ya sani, bari na kawo miki"

Amina ta ce "Yauwa na gode" ta koma taje ta kwanta.

Mintuna talatin da ɗoriya, sai ga Hajara ta dawo, ta kawowa Amina kunu, ta karɓa tayi mata godiya, ta zauna ta sha kunun sosai dan tana ji yunwa, amma bayan ta gama sha, tana tuna naman nam da ta ci, taji cikinta ya kuma hautsinawa taje ta amayar da shi.

Amina ta ce "Na shiga uku ni Amina, anya wannan naman da arziƙi ne, naje na ciyo wa kaina masifa da kaina"

Haka ta wuni tana malelekuwa, da kyar aman ya tsaya. Duk ta fita hayyacinta.
Wajen ƙarfe shida da rabi, tana kwance bacci ya ɗauketa, taji ƙamshin turaren Daddy. Ta buɗe idonta a hankali ta ganshi zaune a kusa da ita yana shafa kanta.

Kallo ɗaya tayi masa ta ture hannunsa, ta juya masa baya.

"Meenal lafiya kuwa?"

Amina ta ce "Ni ka ƙyaleni"

Ya kwantar da murya ya ce "Haba 'yar babyna, nine fa Daddy ne"

"Ba wata 'yar babynka, da ka mini wulaƙanci a gaban matarka, ka goya mata baya dan an dafa maka abu na ci, har da wani yi mini faɗa naman ma da naci ya kusa kasheni, kuma wai wunin yau ko ka leƙo ka ganni, bayan idan kana wurina ko zata maka wulaƙanci ita kana leƙawa ka ganta wuni nayi ina ciwon ciki amma banga ka zo in da nake ba"

Cikin rarrashi ya ce "Haba Meenal, ya zan bata rashin gaskiya bayan kin san kin yi laifi, zata dinga ganin bana yi mata adalci. Wallahi ina ƙoƙari Amina idan na biyewa son zuciyata ba zan muku adalci ba, saboda na san ina miki son da ni kaina yake bani mamaki. Kuma naje mun yi maganar auren Fadila ne da iyayen wannan yaron, ban zaci zan daɗe haka ba, amma dan Allah kiyi haƙuri" banza tayi masa tana cigaba da zumɓura baki.

"Babyna, ko in tsuguna ne? In dai hakan zai saki farinciki sai na durƙusa na baki haƙuri, dan Allah ki daina fushin nan wallahi ni kaina wunin yau babu daɗi nayi shi, nayi missing ɗinki abubuwane suka sha kaina dayawa, amma am sorry Dear"

Ya ƙarasa maganar yana juyo da ita ta fuskance shi.
Saboda tsabar shagwaɓa sai ta hau kuka har da hawaye, tana tura baki, Daddy kuwa ya lalace a wurin rarrashinta, yana share mata hawaye.

Sai da ta ɗan samu nutsuwa sannan ya ce "Yauwa Meenalin Daddy, ko ke fa saura kuma ki yi mini murmushi zuciyata ta samu nutsuwa"

Ta noƙe masa kafaɗa.

"Please Baby"

Ta ce "Ina da sharaɗi"

"Wane sharaɗin ne?"

"Gaskiya kar ka sake ka ci nama a kwanakin nan, ka san dai kana kan dokokin likita ko?"

"In dai wannan ne, shikenan ba zan ci ba i promise, yi murmushin na gani"

Murmushin tayi tana share sauran hawayen fuskarta.
Murmushin shima yayi ya ce "To yanzu me zaki ci?"

"Gasashen Kifi nake so, manyan nan mai miya"

"To shikenan, amma taso muje ki ɗan tattaka, ko kya ji dadin jikin ki".

Ta ce "Ni ba tattakawa zan yi ba, ban yi wanka ba, duk jikina ciwo yake mini saboda ciwon ciki"

Daddy ya miƙe, ya cire babbar riga, ya saka Amina gaba zuwa toilet.

Har mai shi ya shafa mata, ya taimaka mata ta sanya wasu kayan, ya kalleta ya ce "Ko muje Asibiti dai, naga jikinki yayi weak?"

"Ai ya daina yi mini ciwon, ka sayo mini kifin kawai"

"To shikenan, kwanta ki huta yanzu zan dawo"

Ta ce "To a dawo lafiya"

Ya jinjina mata kai ya fice, yan fita falo ya haɗu a Hajiya Zainab, ta kalleshi ta ce "Dama kana gidan nan tun ɗazu? Nifa bana son munafunci, amma dai ka san yau a wurina kake ko?"

Alhaji Ahmad ya ce "Haba Zainab, dan ina wurinki shikenan ba zan leƙa in ga ya take ya ta kwana ba? Yarinyar nan tunda na fita ashe bata da lafiya, hakkinta a kaina yake dole naje naga jikinta"

Cikin ɓacin rai ta ce "dole ko? Yayi maka kyau" ta wuce fuuuu ta bar shi a wurin.

Da fari ji yayi kamar ya bita, da ya tuna Amina ko Abinci bata ci ba wunin yau, kawai sai ya fice ya tafi saya mata kifinta da ta nema.


Hajiya Zainab iya ƙuluwa ta ƙulu, amma ta danne saboda ta sake dafa wani namn, so take ya ci.

Amina kuma zaman ɗakin ne ya gundureta, ta ɗan ji daɗin jikinta, dan haka ta fito da niyyar zuwa kitchen, ta dafa tea idan Daddy ya kawo mata kifin, ta samu abin haɗawa.
Sai dai kamar ɗazu da safe, yanzu ma falon warin wannan hayaƙin yake yi.

Da sauri ta ƙarasa kitchen, saboda jin yadda tari ya fara taso mata.
A gurguje ta dafa tea ɗin, ta koma ɗakinta tana tsaki, saboda ita bata ga amfanin wannan hayaƙin ba, bata san ta ina yake shigowa falon ba, dan sam bata yi zaton Hajiya Zainab ke kunna shi ba.

Da magariba Daddy ya dawo da kifin Amina, ta dinga murna da ganin kifin nan, ya zauna ya sata a gaba ta ci sosai sannan ya ce "Alhamdilillah, tun da kin samu kin ci kifin sosai, Allah ya baki lafiya, gobe in Allah ya kaimu nake son muje mu yiwa 'yan uwa bangajiya, har Shanono nake son muke, jibi in Allah ya kaimu kuma, zamu je Dutse ta can zamu tashi".

Murmushin fuskarta ne ya ƙaru cikin murna ta ce "Amma naji daɗi sosai, Allah ya kaimu da rai da lafiya"

"Amin ya rabb, bari na tashi naje wurin Yayarki"

Ta gyaɗa kai ta ce "Ok, shikenan kace ina gaisheta"

"To zata ji" ya tashi ya tafi. Ta ji daɗin jikinta mussaman yanzu da ta samu ta ci wani abin ya zauna a cikinta.

Tashi tayi ta duba littafinta da take rubutun Alqur'ani a ciki, ta sanya hijjabinta ta ɗau biro ta zauna, tana karantawa a hankali tana rubutawa.


Ba dan Hajiya Zainab ta so ba, ta saki fuskarta, bayan Daddyn ya rarrasheta a kan Amina ce bata jin daɗi.
Ta kawo masa abinci tare da wani farfesun naman, ya kalli naman ya ce "Naman nan a bar shi, zuba mini Abincin kawai"

Ta kalleshi ta ce "Saboda me?"

"Likita ya hanani cin jan nama, saboda shekaru da yanayin jikina"

Ta ɗan rausayar da murya ta ce "Amma sai da ka bari na dafa zaka ce ba zaka ci ba, dan Allah ko kaɗan ka ci mana" ganin duk ta damu ta ɓata fuska, ya sanya ya ɗau fork ya ɗebo naman, murmushi yayi kan ya kai bakinsa, ya tuna da tare za su ci Abinci da Amina, zai fara cin Abinci ƙura masa ido za tayi sai taji yayi Bismillah, idan kuwa bai yi ba sa ta riƙe masa hannu tana haɗe rai kamar wani ɗanta.
A hankali yayi Bismillah, ya kai yanka ɗaya bakinsa, sai ya tuna alƙawari yayi wa Amina ba zai ci ba, dan haka ya ce ya ishe shi.
Kissar duniya da rarrashi ba wanda Hajiya Zainab ba tayi ba, amma ya ce ba zai ƙara ba ya ƙoshi.

Ji tayi kamar ta tsinke shi da mari ta huta, amma ta shareshi.

Abu ɗaya ne ya ɗan faranta mata rai, shine maganar da yayi mata na cewa iyayen Salim sun zo ya haɗu da su, sun ce zasu kawo kuɗin Aure da zarar ya dawo, shi kuma ya ce ya basu, sannan zai cigaba da saurarensu.
Wannan maganar ce ta ɗan faranta mata rai, amma duk da haka ta shareshi, saboda rashin cin naman nan ba ƙaramin ƙuluwa tayi ba.

Da daddare har sun kwanta, yake gaya mata cewar gobe in Allah ya kaimu zasu fita shi da Amina, jibi kuma za suje Dutse daga nan zasu bar ƙasar kwanaki goma ma kawa za suyi su dawo.
Sai da Daddy ya gwammace bai yi nata zancen ba, saboda azabar bala'in da ta dinga yi masa a ka, tamkar zata dake shi. Ƙarshe sai juya mata baya yayi, tayi mai isarta ƙasan zuciyarta kuma tana Mamakin yadda aka yi maganin bai fara aiki yadda take so ba.



Hajiya Zainab tana can tana bacci, Daddy ya lallaɓa ya tafi wurin Amina, dama ranar girkinta ne, yayi wanka ya shirya ko karyawa ba suyi ba, ya ɗauketa suka fice.
Ɗaya gidan nasa suka tafi, ta haɗa musu breakfast, bayan sun kammala suka sake shiri a tsanake suka fita.
Gidan Ammi suka fara zuwa, Ammi tayi murna da ganin Amina, ta yi ƙiba sosai ta ƙara kyau.

Amina ta hau yiwa Ammi mitar, ita bata dawo ba, Azima ma bata je ba.
Ammi ta ce "Ai bai kamata mu dinga yi miki zarya a wannan ƙadamin ba, ita ma nan suka shirya da 'yan ajinku da zasu je miki, nace kar suje tukuna kar wannan abokiyar zaman naki ta tsinkaki a gabansu"

Amina ta ce "Ni da yake ma bata tata nake yi ba, idan tayi mini ba raga mata zan yi ba, kullum ni ba mai zuwa wurina, ita Azima ai da ko ita sai ta dinga zuwar mini".

Azima ta ce "Ni rabani da zuwa gidan matar aure, ta koreni ta ce mini mijinta ya dawo"
Bata wani jima ba, Daddy ya kirata ya ce ta zo suna da wurin zuwa sosai, haka tayi sallama da Ammi da Azima suka tafi.
Daddy gidajen wasu daga abokansa na Kano, ya kai Amin suka gaggaisa da iyalansu, tare da yi musu bangajiyar zuwa walimar bikinsu.
Amina tayi mamakin yadda Daddy yake da jama'a, amma babu mai iya takawa gidansa saboda masifar matarsa.

Sai azahar suka ɗauki hanyar Shanono, Amina sai daɗi take ji, kamar yau zata fara zuwa garin.

Inno da bata san da zuwansu ba, ta rasa ina zata ajiyesu dan daɗi, nan da nan aka yiwa Baba waya aka ce Amina ta zo, Baba ya rufe shago ya nufo gida cike da ɗokin son ganin tilon 'yar ta shi.
Abin kunya sai ga su Baffa Bala, sun biyo sahun masu zuwa su gaida mijin Amina, kamar ba iyaye ba sai gasu suma.
Sai a yau Amina taga sabon gidan da aka sayawa su Baba, manyan gidaje biyu ne aka saya aka haɗesu, aka ƙawata su, ga aiken kayan Abinci da Daddyn yake yi musu.
Ba ƙaramin kima Daddyn ya daɗa a wurin Amina ba, ita a rayuwarta duk wanda yake son iyayenta to ya samu zuciyarta.

Aikuwa duk wanda ya zo akwai alherin da Daddy zai yi masa, Amina ta sake sosai a gida tare da Inno da Baba, suka yi ta hirar yaushe gamo.

Bayan sallar la'asar suka nufo cikin garin Kano.


Hajiya Zainab kuwa bayan ta farka ta nemi Alhaji Ahmad ta rasa, ta kira wayarsa ya sanar mata yayi sammako sun fita da Amina.
Haka ta dinga zage-zage ita kaɗai a gida, ta zari mayafi ta tafi gidan Hajiya Turai, suka sake tattaunawa a kan batun magungunan wurin malamin, aka tambayeshi ko za a iya amfani da maganin a kifi, ya ce musu a'a lallai a Nama ake so.

Har ta dawo da yamma su Amina basu dawo ba, ta zauna a falo ta kasa tsare tana jiran taga ta ina zasu shigo.

Aikuwa tana nan zaune, sai gashi sun dawo, Daddy na riƙe da jakar Amina, Zakiru kuma ya shigo da kayan tsaraba, da suka zo da su daga ƙauye.

Ba kunya ba mutunci haka Hajiya Zainab ta cigaba da tsigale masa a gaban kowa.
Amina tafiyarta tayi ta bar su, dan ta lura ita dai Hajiya Zainab idan har za a biye mata kullum sai an yi tashin hankali da ita.

Amina bata san yadda suka ƙare ba, dan tana zuwa sashen ta rage kayan jikinta tayi, ta shiga tayi wanka tayi alwala ta zo ta tada salla.
Bayan ta idar Daddy ya shigo, sai dai yanayinsa ya nuna mata yana cikin damuwa, kuma ta san Hajiya Zainab ce ta kunno shi.

Ya zauna yayi shiru ya rasa abin da yake masa daɗi, Amina ta ninke abin sallar, ta je ta zauna a kusa da shi, ta rungumo kansa jikinta, tana ɗan shafa bayansa cikin sigar rarrashi ta fara magana "Sweetheart, ni da yaranka da duk masoyanka muna buƙatar ranka da lafiyarka, dan Allah kar ka cutar mana da kanka, saboda wata damuwa da zaka iya ajyeta a gefe muyi rayuwarmu. Damuwarka na jefa ni cikin damuwa nima duk sai na rasa meyake mini daɗi, kayi haƙuri ka ji?"

Da fari ji yake kamar zuciyarsa zata tsaga ƙirjinsa ta faso, amma kalaman Amina suka dinga kwantar masa da hankali, sai da taga ya ɗan nutsu, sannan ta ƙyaleshi yaje yayi salla, ya nemi wuri ya kwanta.
Washegari yayi shahada ya je wurin Hajiya Zainab yi mata sallama saboda doguwar tafiya da za suyi, tana fara zage zagenta, ya fice ya tafi ya barta.


Ko da suka Dutse, danginsa tamkar zasu goya Amina, Amina gata da saurin sabo, ga ungo uban kayan zaƙi na gararta da aka kai musu kawai sai santi suke. Wasun su har suna ita wannan da ake gani ga karkara ce har da abin arziƙi na gara, uwar mulki kuwa ko barbaɗen gishiri ba ai kai mata ba.

Amina ta yadda Alhaji Ahmad ɗan gata ne, kuma ɗan dangi gaba da baya, amma saboda tsabar son zuciya na Hajiya Zainab ta sa ya watsar da kowa sai ita.

A family house ɗin su Daddy suka kwana, ya ɗauko mata hotuna yana nuna mata hotunan iyayensaa da 'yan uwansa da ya rasa, sai da ya zub da hawaye, saboda iyaye wasu duraku ne masu girman gaske a rayuwar kowane ɗan Adam.

Washegari da Azahar, aka kai su Alhaji Ahmad airport, inda jirginsu ya ɗaga zuwa Dubai.



Alhaji Ahmad ya samu isashshen lokacin hutawa, da nuna wa 'yar babyn amaryarsa kulawa da soyayya sosai da sosai, ya ɗan samu releif daga yawan hayaniya da tashin hankali da yake fuskanta na Hajiya Zainab.
Amina lallaɓa abinta take, ta mayar da shi kamar yaro dai-dai da shekarunta.
Ya dinga yawo da ita wuraren shaƙatawa daban daban yana kashe mata kuɗi.


Hajiya Zainab saboda azabar baƙin ciki da kishi, gaba ɗaya ta manta bata gayawa Fadila batun maganar aurenta ba, sai ma shirin sake komawa nijar da suke yi a karo na biyu, dan yin wani asirin tunda wannan bai yiwu ba.
Sai da taje tana yiwa Fadila sallama, tana sanar mata in da zata tafi ne, Fadila ta ce "Mummy, me kuma zaki je yi a nijar? Muda bamu da kowa a can?"

Mummy ta ce "Sirikarki zamu

Please Login or Register in order to submit comment