Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

shi ka ɗai a dining.

"Kana ta kallona idan na faɗi fa?" Amina tayi maganar tana jere plates ɗin hannunta.

"Nace ki kawo Abinci in kuma ganin lalle, amma kika turo wata ko?"

Amina ta girgiza kai ta ce "Bani na turota ba"

Ya ce "Well, mu ga lallen"

Ta ɗago masa dogayen yatsunta, da suka lalle baƙi da ja.

"Wow Masha Allah, a yiwa lallen nan kuɗi zan saya"

Ta ce "Ai an riga an biya mai lallen, Babar ƙawata ce ta biya"

"Na san an biyata, wani biyan zan yi ai na musamman"

"Ni dai a'a ka daina bani kuɗi haka"

Muryar Hajiya Zainab suka jiyo tana waya, nan da nan Amina ta nutsu ta fara ƙoƙarin barin wurin, Da kallo Daddy ya raka Amina, yana jin ba daɗi zuwan Hajiya Zainab ta katse musu hira.

"Nifa gaba ɗaya na kasa gane kan yaran nan, kowanne da salon tsirfar da ya tsira, shi wancan yayi zuciya ya bar gida ya daina kula kowa, ita wannan ta tsiri zaman ɗaki, da rashin walwala na tambayeta wai pressure ne na karatu wannan wane irin abu ne?"

Daddy ya ce "Wani abu na damunta ne?"

"Yo ni ina na san mata, 'yar ganin dama, koma wani abu na damunta sai ta ga dama ai zan sani"

Alhaji Ahmad ya miƙe ya ce "Ba zai yiwu wani abu na damunta, kuma a zura mata ido ba.

Ɗakin Fadila ya nufa, yayi knocking sannan ya shiga, tana zaune a kan Carfet ɗin ɗakinta, hannunta riƙe da littafi tana kallo.
Alhaji Ahmad ya ƙarasa yana faɗin "Autana, karatun kike yi haka?"

"Eh Daddy" ta faɗa a sanyaye.

Shi kansa ya karanto damuwa a tatare da Fadilan, duk da gwnaace wurin iya tsiwa da surutu idan ta ga dam, but her silent part dominate the other side of her.

"Amma ya ban ganki a dining wurin Dinner ba?"

Tayi murmushi ta ce "Bakomai Daddy, kawai ina son yin karatuna a cikin nutsuwa ne, da kuma cin abincin nikaɗai kar wani abu ya ɗauke mini hankali"

Daddy ya ce "No, i want see you by my side, ta so muje in tabattar kin ci Abinci, sai ki zo ki cigaba da karatunki kinji sweetheart"

Tamkar ƙaramar yarinya, haka Daddy ya lallaɓota suka fito, ya riƙo hannunta zuwa dining yana yi mata hira.

Mummy ta kallesu ta ɗan yatsuna fuska ta ce "Eh, da yake babanki ne ai gashi nan kin fito, ni da kika raina ce mini ki kayi in ƙyaleki ai"

Daddy ya ce "Please Madam, karki damar mini baby" yayi maganar yana zaunar da Fadila a kan kujera.

"Ka mayar da ita cikinka, ƙarewar Baby ma"

"Eh ba ruwanki da mu" Alhaji Ahmad yana matuƙar ɗaukar al'amuran Fadila da muhimmanci, dan wasu lokutan bai fiye damuwa da Khalil kamar yadda ya damu da ita ba, yake gudun abin da zai ɓata mata rai ba.

Sosai ya dinga ƙaƙalo hirarraki yana yi mata, a haka har ta ɗan saki jiki ta ci Abinci sosai, har zuciyarta ta fara raya mata ko ta gaya wa Daddy, abin da ke faruwa amma kawai ta share, ta kamala cin abincin ta tafi  ɗakinta.

Rana bata ƙarya sai dai uwar ɗiya ta ji kunya, yau ne Amina zata je garinsu, tun bayan watanni tara da ta shafe bata garin nasu duk da ba rabuwar daɗi aka yi ba, kuma bata san wane irin karɓa za suyi mata ba, hakan bai hanata yin murna da farin ciki ba, na zuwa ganin gida da zata yi, musamman ganin Inno, da shi ne babbar damuwarta.
Da Asubar fari, ta ɗau akwatinta ta kai jikin motar da za su yi tafiyar a ciki, ta tsaya suna gaisawa da Zakiru, Zakirun hana tsokanarta "Ke fa yau kamar salla take a wurinki, zaki je gida"

"Zakiru waya ƙi gida, kowa ya bar gida ai ba bisa son ransa bane ba, gida akwai daɗi sosai"

Zakiru ya ce "Haka ne, Alhaji yayi mini maganar zan cigaba da koya miki karatu yana biyana, yaushe zamu fara ne?"

"Ehh, nima mun yi maganar da shi, ka bari in dawo daga ƙauye, sai mu sanya lokaci, yadda ba zai shafi aikin da muke ba, kar ya zama abin magana".

Zakiru kamar Amina ta taɓo masa in da yake masa ƙaiƙayi ya ce "Ke dai bari, wannan gida Allah ya nuna mana iyakar wannan mata, ke dai kije ki shirya da wuri, yanzun nan mu kama hanya"

Gyaran murya suka ji a bayansu, Zakiru ya ɗa rikice yan risunawa ya gayar da Alhaji Ahmad.

"Bamu wuri" Daddy ya faɗa ransa a haɗe, Zakiru ya bar wurin, Amina ta tsaya tana kallonsa.

"Can't you greet me?" Yayi maganar yana tsareta da ido.

Ta ce "To ai gani nayi ka haɗe rai"

"Ba dole in haɗe rai ba, kawai kin zo nan kina ta zuba da wani"

"Daddy Akwatina fa kawai na kawo ya saka a mota"

"Eh daga nan kuma kika tsaya surutu ba, kin gama shiryawar ne?"

Ta ɗan gyaɗa kai ta ce "Eh, na shirya kaya kawai zan saka"

Ya ɗan tsareta da ido sannan ya ce "Ki kula sosai, zan dinga kiranki a waya in ji idan kun sauka"

"To in sha Allah" tayi maganar tana kallon ƙasa.

"Yauwa, banda yawo idan kin je ki zamanki a gida idan ba in da ya zama dole ba, bana son yawo ki zamanki a gida kin ji"

Ta ɗaga masa kai alamar eh.

"Talk"

"To Daddy" ta faɗa a shagwaɓe.

"Idan ma kika tafi yawo, za a gaya mini kuma zan haɗu da ke, maza kije ki ƙarasa shiryawa kiyi breakfast, kuzo ku tafi" Amina ta jinjina kai, ta wuce ciki.

Cikin lokaci ƙalilan, ta kammala kintsawa, ta karya tana ta murna, Hajara ta rakota, har suka fito Hajiya Zainab bata tashi ba, dama lokacin tashinta bai yi ba.

A kan baranda suka tarar da Daddy, yana tsaye yana danna waya, Baba kuma yana gefensa a tsaye.

Murmushi Amina ta yiwa Baba ta ce "Baba tare zamu tafi?"

Baba ya girgiza kai ya ce  "Ai ni naje na kuma komawa, ke kaɗai zaki tafi"

Tare da Daddy suka rakata har mota, cikin ƙasa da murya Daddy ya ce "Saura kije ki saki baki, kiyi ta hira da shi a mota" ba ta ce komai ba tayi shiru.

Ya ce "Safe journey"
Ta amsa masa da "Thank you"

Amina ta shiga mota, tana ɗaga musu hannu, suka tafi.

Gaba ɗaya Fadila damuwa ta fara shafar karatunta, saboda rashin sanin a wani hali Yazid yake, saboda tana matuƙar tausayin halin da yake shiga idan ba shi da lafiya.
Da ko ba komai da yana nan yana takura mata, ajiyar zuciya ta ɗan sauke tana kallon agogon hannunta, ranar Litinin zasu fara jarrabawa, amma babu Yazid babu dalilinsa.
Saura mintuna goma lokaci ya cika malamin da suke da shi ya shigo, babu zato babu tsammani ta ji aji ya kaure da hayaniya.
Babson ne da Captain, tare da Yazid a tsakiyarsu, Captain ya riƙo side ɗin Yazid na hagu, Yazid yana takawa a hankali yana murmushi.
Ba ƙaramin faɗuwa gaban Fadila yayi ba, Yazid ya rame fiye da tunani, ga wani irin haske gauuu da yayi, sai sajensa da ya ƙara yawa. Kana ganinsa ka san yaji jiki, koma yana kan sha, amma kasancewar ya zame masa jiki murmushi ne kwance a fuskarsa.
Mutanan ajin ne suka fara yi masa sannu, suna masa ya jiki, sai gaisawa da mutane yake, yana musabaha da mazan. Fadila ta zuba masa ido, sai dai ta kasa ko motsawa daga in da take, sai dai ƙasan zuciyarta da take murna kasancewar babu wani babban abu da ya same shi.

Kankiya ne dama zai shigo ajin, ya shigo ajin fuskarsa a haɗe ransa babu annuri sam, hakan baya rasa nasaba da canza lamba da yayi ya kira Fadila, tayi masa wankin babban bargo ta ci mutuncinsa.
Ya shigo yana ta muzurai, da hura hanci, da fari bai lura da Yazid da ke zaune a ajin ba, sai daga baya bayan ya yi rubutu a kan board ya juyo.

Ya sauke idonsa a kan Yazid, sake haɗe rai yayi ya kalli  ce "Me kake yi a class ɗina?"

Yazid yayi shiru bai ce komai ba.

"Zo ka fita ka bar mini aji, dan baka da mutunci shi ne zaka zo ka zauna mini a aji, zo ka bar mini aji, kuma ka sa a ranka ba zaka zana jarrabawata ba, come and leave my class usless"

Kalmar usless ɗin nan ba ƙaramin ƙonawa Fadila rai tayi ba, ji tayi kamar ta zagi Kankiya.

Captain ya ce "Sir kayi haƙuri ba shi da lafiya ne, yau ya dawo"

"Shut up! Nace ka sa mini baki ne? Ai ya riga ya san na hana shi zama a ajina, tashi ka bar mini ajina"

Yazid ya ja jikinsa a hankali, ya tashi tsaye, sai da ya tashi Fadila ta lura da Cannula a hannunsa, a hankali yake jan ƙafarsa, tare da dafe gefen cikinsa ya fice daga ajin.
Kankiya yayi tsaki ya ce "Nonsense"
Miƙewa Fadila ma tayi, ta ɗau jakarta ta nufi hanyar fita, tana jin Kankiya na kiranta amma tayi masa banza ta bar ajin da sauri.

Hajiya Zainab ce ta shigo ɗakin Daddy tana masifa "Wai ni ina wannan sakaran direban naka ya tafi? Tun ɗazu nake nemansa, yazo ya karɓo mini saƙo a wurin Hajiya Salma.

Cikin ko in kula Daddy ya ce "Na aike shi ne"

"Zuwa ina? Jiransa nake yi ni akwai in da zani"

"To ke ki ɗauki mota kije ki karɓo da kanki mana, ko ta yi miki aike"

"Haba Baban Khalil, ina gaya maka uzurina kana gaya mini wani abu daban, dan Allah ka kirashi ya zo ya je mini aiken nan"

Alhaji Ahmad ya tashi zaune ya ce "Na aiki Zakiru Shanono, zai kai Amina gidansu"

"I don't get you, and what does that mean? Meyasa zaka aike shi ya kaita ƙauye, a matsayinta na wa?"

"Mahaifinta ya nemi hakan, dan ba zai yiwu ya bar yarinya ita kaɗai ta tafi ba"

Rai a ɓace ya ce "I don't care, me yasa zaka yanke wannan hukuncin ba tare da na sani ba, 'yar aiki tafi aikin gidana muhimmanci kenan? Ubanta ya kaita mana, yanzu waye zai je mini aiken nawa?"

Miƙewa tsaye Daddy yayi ya ce "Zainab, ba Khalil bane da Ahmad kike Magana, duk wanda yake aiki a ƙarƙashina yana da damar ya nemi alfarma a wurina nayi masa" ya fice ya bar mata ɗakin.


MASU BUƘATAR SHIGA VIP GROUP, SUNA IYA TUNTUƁATA A KAN LAMBAR WAYATA DA KE ƘASA, DOMIN SU BIYA A SAKA SU


AYSHERCOOL
08081012143GABA DA GABANTA

AISHA ADAM AYSHERCOOL


44

Ganin Alhaji Ahmad ma ya ɗau zafi sosai, ya sanyata saurin saukowa daga nata fushin, dan da wuya yayi fushi amma idan yayi fushi wahalar sha'ani ne da shi fiye da tunani.
Dan haka ta ce "Naji shikenan ya wuce, na haƙura da saƙon na san yadda zan yi"
Bedroom ɗinsa ya wuce ya barta, tabi bayansa tana cigaba da lallaɓa shi, amma ya shareta ya ƙi saurarta.

Ba ƙaramin yarfa Kankiya Fadila tayi ba, ganin yadda yake muzurai ake tsoronsa amma Fadila ta yarfa shi a gaban ɗalibai, hakan ba ƙaramin ɓata masa rai yayi ba, kuma hakan ya jefa zargi a zukatan ɗaliban, mai zai sa Fadila ta tsinka malamin haka duk da yadda ake tsoronsa.

"Yazid, Yazid" tsayawa yayi ya waiwaya da jin muryarta a cikin dodon kunnuwansa.

Ta ƙarasa in da yake da sauri, bai ƙosa ba ya jira har ta cin masa.

Cikin damuwa ta ce "Sannu, ya jikin naka? Ashe baka da lafiya?"

"Eh, amma da sauƙi sosai Alhamdilillah"

"Wai meya sameka ne?"

"Rashin lafiya ne" ya bata amsa.

"Wane irin rashin lafiya?" Ta kuma tambayarsa cikin kulawa.

"An mini aikin appendix ne, sai kuma asma da ta dameni shikenan amma da sauƙi sosai"

"To yanzu ina zaka daga nan?"

"Gida zan tafi"

"Ok, to muje in sauke ka"

Da sauri ya girgiza mata kai ya ce "A'a ki bari na gode zan tafi"

"Ba ka ganin a yadda kake tafiya, kazo muje in sauke ka"

"Na gode, amma ba zan hau motarki ba, ban kai in hau mota irin wannan ba, ba ta dace da hawan talaka kamata ba" daga haka ya juya yana tafiya a hankali.

Tsayawa tayi tana cigaba da kallon yadda yake tafiya a hankali, har ya ɓacewa ganinta.

Tafe suke suna hira jefi jefi ita da Zakiru, yana bata labarin yanayin zamantakewar gidan kafin zuwanta.

"Ai nake gaya miki, ko 'yan uwan maigidan nan duk zumuncinsu sun haƙura sun daina zuwa, sun zuba masa ido, shi kansa sai lokaci lokaci yake zuwa, dama bata yadda yaranta suje ba, kuma fa 'yan gari ɗaya ne, saboda azabar baƙin halinta, duk son sa da yayi taimako sai dai yayi bata sani ba. Ai matar nan bana zaton tana son taga Annabi"

Amina ta ce "A'a karka ce haka, amma ina mamakin ita ko nata 'yan uwan basa zuwa sai ƙawaye"

"To ina taga wasu 'yan uwa ma, sukan zo wasu lokutan suna ba wani kallon arziki take musu ba, amma a hakan tana jidar kaya ta bani in kaiwa wasu daga 'yan uwanta, ai ita idan kika ga tana rawar kai tana nan nan da kai, to mai kuɗi ne kai, duk ta kanainaye maigidan baya jin maganar kowa sai tata, ai har gara yanzu a kan da, sanyinsa yayi yawa, sai ya fito cikin mutane ya fito yana taƙama baki Ga yadda ake girmama shi a waje ba, amma a gidansa ba shi da kataɓus ga shegen son 'ya'ya kamar masifa, waccan tsigalaliyar 'yar ta sa idan ta zauna tana taɓara abin takaici, gata halinta ɗaya da uwarta na rashin mutunci, ba kunya idan nayi kuskure take ƙare mini zagi, ai Alhaji Ahmad yayi ta kowane fanni amma a gidansa dai damisar kwali ne"

"Zakiru ya isheka haka, wasa yayi wasa banda tsikarin uwar miji da taɓarya" tayi maganar ranta a haɗe.

Zakiru ya ce "Kamar yaya kenan?"

"Ina ruwanka da abin da ke faruwa a gidansa kake ce masa damisar kwali, kai waya san yadda taka matar ke juyaka, ya isheka bana son wannan hirar"

Zakiru ya yi murmushi ya ce "Allah ya baki haƙuri, tuba nake"

Amina ta basar da shi ta haɗe rai.

Message ɗin Daddy ne ya shigo wayarta.
"Yaya hanya, kun isa kuwa?"

Tayi masa reply "A'a muna hanya"

"Ina fatan ba kya jin yunwa, idan kina jin yunwa ya tsaya ki ci Abinci"

"Ka manta na karya kafin mu tafi, mun shiga Shanono, mun kusa gida in sha Allah"

"Ok, to Alhamdilillah, ki gaishe su"

"Thank you, za su ji" ta ɗan yi murmushi ta ajiye wayar.

Hajiya Zainab ce zaune a ɗakinta tana waya da Hajiya Salma "Dan Allah Salma ki ƙara haƙuri, kwanan nan duk na kasa gane kan babansu Khalil, ya ce zai bani kuɗin amma sai wasa yake mini da hankali, da abu ya ɗan haɗamu sai ya hau fushi, a yadda yake ɗin nan idan na matsa, zai iya hana kuɗin nan, kuma ni kinga na tattare kuɗin hannuna na yi order kaya, kuma ba zai yiwu in kwashe sauran kuɗin hannuna in baki ba, saboda suma juyasu nake".

Hajiya Salma ta ce "Ni yanzu ya zan yi? Turai ta bani aron million biyu, dama na wajenki nake jira da million bakwai coustom suka ce zan bayar a sakar mini kayana, da ƙyar suka bari a 5million, kuma kinga Alhaji  kwanan nan ya ƙara mini jari ya ce ba zan samu ba"

"Kiyi haƙuri, zan cigaba da lallaɓa shi saina karɓa zan baki in Allah ya yarda, kuma ina ga zan je Abuja a satin nan in Allah ya yarda"

"Too, Zainab me zaki yi a Abuja kuma?"

Hajiya Zainab ta ce "Wurin yaron nan Khalil mana, gaba ɗaya ya ɗauki gaba da ni, ubansa kawai yake tuntuɓa, ba ruwansa dani"

"Kaii yaran zamanin nan, anya ba asiri suka yi masa ba, duk yadda Khalil yake miki biyayya, amma yanzu a kan wannan yarinyar ya daina shiga harkarki"

"Bari kawai Hajiya Salma, bana son babansa ya gano actual abin da nayi masa, kin san halinsa a kan 'ya'yansa, gaba ɗaya ina cikin damuwa dole in je Abuja"

"Ke Zainab, ai ba a yiwa yaran zamanin nan haka, ba ke yakamata kije ba, ki kai yarinyar wurin malamai, idan ma wani abun suka masa a karya shi, sannan ki nemo masa wata matar, akwai 'yar ƙanwata  Hajiya Badi'a ai kin santa Kursum ki haɗa shi da ita kawai"

"Kin kawo shawara haka za ayi, zai ga tsiya"

"Ai kawai ba sai kinje ba, sai bayan an kai kuɗi da komai, ki ce masa ya zo ga mata shine zaki hukunta shi ki nuna masa ke uwace"

Hajiya Zainab ta ce "Hakan ma yayi, na gode sosai Salma, zan zo gidanma da kaina mu ƙarasa tattaunawa"

"To shikenan, sai Allah ya kawoki" suka yi Sallama Hajiya Zainab na jin ta gamsu da shawarar da Hajiya Salma ta bata.

Amina tayi ta kwatantawa Zakiru hanya har ƙofar gidansu, suna parking ta buɗe motar ta tafi da gudu cikin gida, wasu daga yaran su Kawu Bala suna ƙofar gida suka bi motar da aka kawo Amina da kallo, dan ɗaya ce daga irin jibga jibgan motocin da Alhaji Ahmad yake hawa ne aka kawota.
"Inno! Inno!" Amina ta dinga ƙwalawa Innon kira.

Inno ta saki ƙwaryar hannunta, ta buɗe hannayenta Amina ta zo ta rungumeta, Inno ta ƙanƙame Amina kamar zata mayar da ita ciki, Amina kuwa kuka ta fara yi tana jin tsananin kewar Inno.

"Amina, Amina na rasa mema zance"

"Inno, yaushe rabon da in ganki?"

Inno ta ce "Yau ai gashi kin ganni"

Tuni wasu daga cikin yara har da 'yan matasa na maƙotansu, suka cika tsakar gidan suna kallon Amina.

Suka shiga ɗakin Inno, Amina sai sake ƙanƙame Inno take yi.

"Amina ya gida ya karatun bokon?"

"Karatu lafiya lau Inno"

Inno ta riƙe haɓa ta ce "Ohh, Amina buri ya cika ana can ana boko"

"Inno kenan, ai zaki ga ribar boko in Allah ya yarda, bari in yiwa Zakiru magana ya shigo ku gaisa"

Inno ta ce "Waye shi kuma?"

"Direban gidan da nake aiki ne"

"Au ai na zata siriki ne"

Dariya Amina tayi ta ce "Ba wani siriki"

Amina taje ta kira Zakiru, ya shigo gidansu Amina, suka gaisa da Inno, daga nan suka ɓige da hira kasancewar Inno ta san garinsu Zakiru yayarta tana aure a can.

Mutane sai shigowa suke suna sun zo yiwa Amina sannu da zuwa, nan kuwa gulma suke zuwa yi, suna ta maganganun Amina ta zama ƙatuwa, gashi ta yi fresh ta zama 'yar gayu, ga uwar waya a hannunta.

Zakiru ya kalli Amina ya ce "Amina ko zaki haɗani da wanda zasu tayani kwaso kayan da ke motar"

Amina ta miƙe tana faɗin "Ai ko nima sai in ɗauka"

Ya kalleta ya ce "Ki ɗauki me? Zo muje ki gani fa" Amina tabi bayan zakiru zuwa mota.

Ya saka hannu ya buɗe mata boot, waro ido tayi ta buɗe baki da tayi tozali da abin da ke cikin Boot ɗin.

Kayan Abinci ne kamar za a buɗe kanti, ta kalli Zakiru ta ce "Zakiru, wannan fa?"

"Aike Amina kin ciri tuta a gidan nan, shekaranjiya ya saka na ɗau motar nan muke je da shi muka sayo, jiya da daddare ya ce mini a wannan motar zamu tafi, kar in bari ki san da kayan"

"Na shigesu ni Amina, Zakiru kalli uban kayan fa"

"Ke ki gode Allah, Allah ne ya baki, da waccan matar ta sani ba zata bari a baki ba"

Amina ta ce "Zakiru kaima ka ɗiba"

"A'a nima ya sallameni, bari in kira wasu su tayani"

Haka aka dinga kwasar kaya ana shiga da su gidan su Amina, nan da nan sai ga matan su Baffa Lawan da yaransu sun cika gidan suma.

Sai da Zakiru ya tabattar da an gama kwashe kayan an shiga da su, yayi musu sallama ya ajiye musu bandir kuɗi ya ce in ji Alhaji Ahmad.

Gaba ɗaya Mamaki ya gama kashe Amina, amma ta basar kamar bata wani damu ba.

"Ohh Amina, kalli yadda kika koma, lallai yanzu kin wuce ajin Jarmai, birni ya karɓeki" Cewar Amaryar Kawu Bala.

Suka yi ta yaba Amina, suna son jin ƙwaƙwaf, ance musu gidan da Baba yake aiki a nan Amina ma take yi, amma shi tun da yake bai taɓa zuwa da wanan kayan ba, kuma ba a taɓa kawoshi a irin wannan mota ba sai Amina. Suna ta son su tanbaya suyi tsegumi, amma Amina ta haɗe rai ta haye Gadon Inno tana latsa wayarta, dan ba zata manta wulaƙanci da rashin mutuncin da suka dinga mata ba a baya.


Gaba ɗaya Fadila ji daɗin reaction ɗin da Yazid yayi ba, ji tayi gaba ɗaya bata son zaman makarantar, dan haka ta ɗauki motarta ta wuce gida.


Zuwa azahar sai ga su Baffa Lawan, an je har Gona an sanar da su, ga Amina can an kawota a wata ƙatuwar mota daga birni.
Basu ƙara tsinkewa da lamarin ba, sai da suka ɓangaren su Amina, suka tarar da uban kayan Abinci fal tsakar gida, cikin ɗaki kuma kayan sawa ne da kayan ciye-ciyen da Daddy ya saiwa Amina.

"Ke ina Aminar take, wanann kayan kuma na menene?" Cewar Baffa lawan yana shafa buhun shinkafa.

Inno ta ce "Bismillah Baffa ku shigo"

"Ba zamu shigo ɗin ba, ina Hassan ɗin ma tukuna?"
Inno ta fito tare da faɗin "Ai ita kaɗai ta dawo ban da shi, shi ya zazzo a 'yan kwanakin nan"

Bala ya ce "Ina Aminar ne?"

"Tana ɗaki"

"Eh lallai, rashin tarbiyyar ta ta har ta kai ta kasa fitowa ta gaishe mu?"

Inno ta ce "A'a ba haka bane ba, ke Amina fito mana" banda Inno ta saka baki babu abin da zai sanya Amina ta fito.

Gaba ɗaya suka bi ƙofar ɗakin Inno da kallo, Amina ta yi ƙiba, fatarta ta ƙara haske.

"Ina wuninku"

Kawu Bala ya riƙe baki ya ce "Ba shakka, yanzu dama irin wannan rayuwar Hassan ya zaɓi kiyi, shi ya sanya ya tattaraki ya kai ki birni? Ko in ce kuka haɗa baki kika gudu, yawon ta zubar ai shikenan gaki ga duniyar nan, kin ƙi sunnar ma'aiki kin shiga duniya bin yaran yahudawa"

"Kawu Bala, Tazubar kuma?"

"Eh yawon ta zubar mana, idan ba haka ba wani irin aiki ne kike yi haka da kika samo wannan kayan, tun da uban naki yake aikin a birni ya taɓa zuwa da makamancin haka ne?"

Ran Amina yayi bala'in ɓaci, kawai ta tashi ta bar musu tsakar gidan, dan idan ta cigaba da zama zata iya rama cin zarafin da suke mata.

"Ka gani ko Yaya Bala, wai mu muke mata magana ta tashi ta tafi, idan ba bariki ba mai zai kawo haka?" Ita dai Inno tayi mus shiru, suka gama cin mutuncinsu suka tafi.

Inno ta koma ta samu Amina a ɗaki ta ce "Amina kiyi haƙuri, wallahi tun da kika tafi suke surutai da ƙanann maganganu"

Amina ta ce "Aikuwa sai sai suyi, dan bani da lokacinsu, na gaba ya riga yayi gaba, kuma Inno a ɗibar musu wani daga kayan Abincin nan a basu, aniyarsu ta bisu"

Da yamma Amina ta shirya, ta tafi sada zumunci wurin sauran 'yan uwa, kowa sai son ya ganta yake yi, masu ƙananan maganganu kuma suka cigaba da yi.
Su Bala kuwa da aka ɗebi kayan Abinci aka basu, lumi suka karɓe duk da suna iƙrarin kayan haram ne.

Da daddare Amina da Inno suna tare, Amina tayi musu girkin dare, suna ta hira Inno na bata labarin abubuwan da suka faru bayan tafiyarta, haka ita ma Amina ta dinga bawa Inno labarin birni makaranta da yanayin rayuwar mutanen birni.

"Gaskiya Inno an mana nisa, cigaba yana birni, in Allah ya yarda a dalilin karatun nan nawa sai garin nan ya samu cigaba na gaske"

"To Allah ya sa, amma da fari nima naso kiyi aurenki duk da ba Jarmai na ke so ki aura ba, amma yadda na ganki ɗin nan naji daɗi sosai, kin san bayan tafiyarki Jarmai mata biyu ya aura ya saka"

Amina ta ce "Allah ya rufa mini asiri, da tuni nima ina ciki"

Wayar Amina ce ta fara vibrating tana kawo haske, ganin sunan Daddy ya sanya ta kalli Inno ta ce "Ina zuwa"

Ta miƙe ta bar ɗakin ta koma wani, ta zauna sannan ta amsa wayar tare da yin sallama.

Sai da yayi ajiyar zuciya sannan ya amsa ya ɗora da cewa "Da ba zaki ɗaga bane?"

"Wace ni in ƙi ɗaga wayarka, ina tare da Inno ne ina cin abinci"

"Ok, nayi zaton kin yi bacci ai"

"Ai dare bai yi ba sosai"

Daddy ya gyara kwanciyarsa Sannan ya ɗora da cewar "Ina fatan kin ci kin ƙoshi"

"Na ƙoshi sosai ma, gani ga Inno muka ci fa, nayi kewarta sosai"

Yayi murmushi ya ce "That's good, ni kuma na kasa cin Abincin"

Ɗan waro idonta tayi ta ce "Me yasa?"

"Ba a bani wanda nake so ba, fruit kawai naci na kwanta"

Cikin damuwa da tausayawa Amina ta ce "Meyasa baka sa an dafa maka wanda kake so ba? Kar ka kwana

Please Login or Register in order to submit comment