Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

account, sannan yakamata ke ma ki yi sayayya abubuwa da zaki amfani da su saboda tafiyarku Abuja, musamman kayan sawa, dogayen rigunan nan naga kina san su sosai, kuma suna miki kyau, amma naga Atamfa ma tana miki kyau"

"Daddy"

"Yes" ya amsa tare da kallon wurin da take zaune.

"Idan aka tambayeni waye yake bani wannan abubuwan me zance?"

"Waye zai tanbayeki?"

"Baba mana ko mutan gidan"

"Mutanen gida babu wanda zai tambayeki ina kika samo kaya, Baba ma haka, na baki amsa and keep your mouth shut" haka Amina tayi shiru tana zancen zuci.

Har zuwa bayan sallar magariba, Fadila na dakon wanda zai ce gashi yaje inda Yazid yake duba shi, sai ma ƙorafi da 'yan ajin suka dinga yi a kan cewa babu wanda ya san gidansu, kuma lambar wayarsa ba ta shiga sam.

A layi Daddy ya sauke Amina, dan yana tunanin ko Hajiya Zainab ta dawo, Amina tayi mamakin rashin ganin Baba a bakin gate, a 'yan kwanakin nan tana mamakin in da Baban yake zuwa.
Hajara dake Kitchen taga gilmawar Amina da leda, saura ƙiris ta yanke da wuƙa saboda son ganin ƙwaƙwaf, ta yasar da abin da take tabi bayan Amina tana ƙwala maga kira. "Amina! Amina!!"

Amina ta tsaya ta waiwayo ta ce "Lafiya?"

"A'a lafiya lau, ina kuka je ne haka ke da Alhajin, na ganki da uwar leda haka, ina kuka je?"

Amina ta kalli Hajara rai a ɓace ta ce "Yana sashinsa, zaki iya zuwa ki tanbayeshi, zai fi baki amsa yadda yakamata"

Hajara ta haɗe rai ta ce "Ke Amina, kar mini rashin kunya mana"

"Hajara wace irin rashin kunya, da muka fita da mutumin nan kin san ina muka je, ana ta shirin tafiyarmu Abuja ne, kuma Yanzu tare kika ga mun dawo da zaki titsiyeni da wasu maganganu na daban"

Hajara tana jinjina yadda Amina ta ƙware a iya rainin hankali, da sauya zance, amma ta basar ta biye mata ta hanyar cewa "Wannan ledar a makarantar aka baku kenan, bari in zo a kwanceta da ni"
Banza Amina tayi mata tana tunanin yadda za tayi maganin Hajara da saka idonta.

Abdul ya kira wayar Khalil har ya gaji, baya ɗaga wayar, har ya fara tunanin ko wani abun ne ya samu Khalil ɗin.
Ba tsammani yaga kiran Khalil ya shigo wayarsa, ya ɗaga wayar yayi sallama, Khalil ya amsa sannan ya ɗora da cewa "Abdul yakake?"

Abdul ya ce "Dalla ware, kawai ka kashe wayoyinka, na kiraka na kiraka ka ƙi ɗaga wayata".

Khalil ya ce "Yi haƙuri, bani da lafiya ne"

"Ya salam menene ya sameka?"

Khalil yayi ajiyar zuciya sannan ya ce "Bari kawai Abdul, tun da na baro gida da ƙyar na samu Hafsa ta ɗaga wayata sau ɗaya, itama ashe babu lafiya, yarinyar nan ta tubure, da gaske take ba zata aureni ba" ya ƙarasa maganar cike da damuwa.

Abdul ya ce "Dama banda abin ka Khalil, ka sawa ranka salama a kan yarinyar nan, mahaifiyarka bata so. Kuma dan shirme ka koma wurin aiki baka sanar a gida ba, sai da na mayar da motarka sannan suka sani, baka ga faɗan da Mummy tayi mini ba"

"Abdul ba zaka gane bane, gaba ɗaya Mummy bata damu dani ba, ta tatarani ta watsar da ni, ko kiranta nayi na gaisheta sai dai mu ƙare babu daɗi tayi ta mini faɗax.

"To ai haƙuri zaka yi, tun da ta nuna bata son abu kayi haƙuri da shi kawai"

Khalil ya ɗan numfasa sannan ya ce "A zahiri na rabu da Hafsa, amma zuciyata ga kasa Abdul, ka san me ma Mummy ta ce? Wai ba zan zaɓi matar da zan aura ba sai wadda ta zaɓa mini"

"Khalil, ni dai babu abin da zan iya ce maka, sai dai kayi haƙuri, iyayenmu ba zasu taɓa zaɓa mana abin da zai cutar da mu ba, sannan dolenka kayi haƙuri ka cigaba da yi mata biyayya, komai zai wuce in sha Allah"

Khalil ya ce "Kaga ni ba wannan ba, dan Allah so nake kaje ka duba mini ita"

"Khalil, ba zaka haƙura da batun Hafsa ba ko?"

"Ba haka bane ba, ni dai dan Allah kaje ka duba mini ita"

"Shikenan, naji zanje in Allah ya yarda"

Khalil ya ce "Yauwa na gode sosai, dan Allah idan kaje ka haɗani da ita"

Abdul ya ce "Shikenan, zanje in sha Allah".

Sai wuraren ƙarfe tara na dare, sannan Hajiya Zainab ta dawo gida, ta sha hidima duk ta gaji, tayi wanka ta rama sallolin da bata samu yi ba, ta fito falo ta bawa Amina umarnin dafa mata indomie da tea ta kai mata sashin Daddy.
Ganin tun da ta dawo Fadila bata fito ba, kuma rabon da ta ganta tun kan ta fita da ga leƙa taga tana bacci, ya sanya ta tafi ɗakin Fadila.

"Autar ko nemana ma ba kya yi ko?" Fadila data mayar da hankali a kan litattafanta a zahiri, wanda a baɗini tunani ne fal ranta, ta ɗago ta kalli Mummy ta ce "Mummy kin dawo?"

Mummy ta ce "Eh mana na dawo, amma ko kizo ki mini sannu da zuwa"

Fadila ta ɗan yamutsa fuska ta ce "Mummy karatun exams nake ne, mun kusa farawa"

"Amma dai dan kizo ki ganni kawai, shikenan Allah ya bada sa"a ya karatun?"

"Alhamdilillah"

"Fadila na so kin rakani wurin bikin nan, mates ɗinmu duk da yaransu wasu suka je, gwanin sha'awa ke kuwa ba kya son shiga mutane sam, sai kace daddawar sata kullum kina ƙule a ɗaki"

"Mummy, ni kin san bana son abin hayaniya ne gaba ɗaya, gara in zauna a gida in karatuna"

"Aishikenan, amma dai ai gara ki dinga shiga mutane, da haka ake sabawa, wai ni ya na ganki duk wani iri ne, meke damunki?"

"Mummy me kika gani?"

"Kamar ya me na gani, gaba ɗaya mood ɗinki ya canza yayi wani iri"

Fadila ta ce "Kawai gajiya ce Mummy"

"To ki dinga hutawa kanki dai, bari inje in ci Abinci" ta tashi ta tafi sashin Alhaji Ahmad, ta tarar da shi yana aiki a system.
"Sannu da gida" ta faɗa tana zama a kusa da shi.

"Yauwa sannu da zuwa ya hanya?"

"Lafiya lau, ya jikina naka?"

Ya ɗan kalleta ya ce "Ina ruwanki da ya jikina, da kika iya ficewarki kika barni"

Tsuke fuska tayi ta ce "Zaka fara ko?, Yanzun da naje na dawo meye ya sameka nifa bana son neman rigima daga dawowata Yanzu"

Girgiza kai kawai yai ya ce "Ba zaki camza ba Zainab"

"Eh ba zan canza ba ɗin, yauwa ni dama ina son muyi magana, ina son ka ƙara mini jari ne"

Banza yayi mata ya cigaba da aikinsa.

"Sweetheart magana fa nake maka" tayi maganar tana kashe murya.

Still bai kulata ba, ta sanya hannu ta saƙalo kafaɗarsa ta ce "Talk mana"
Amina tayi sallama hannuta riƙe da kular Abinci da teaflask.

Gabanta ne ya faɗi da taga Daddy tare da Hajiya Zainab, wani abu taji yana ƙoƙarin taso mata. Innalillahi wa innalillahi raji'un tai ta maimaitawa a ranta.
Ta ajiye ta ce "Bari in kawo miki kofi da plate" tayi maganar muryarta har sarƙewa take yi, ta juya ta bar ɗakin.
Murmushi Alhaji Ahmad ya yi, dan ya lura da halin da Amina ta shiga.

"Wai ya naga kana murmushi ni kuma kaƙi kulani?"

Ya ce "To ba ina jinki ba"

"To kayi Magana"

"Me kike son ince miki, wato bani da wani amfani a wurinki sai lokacin da kike buƙatar kuɗi ko wani abu a wurina ko?"

"Haba dai, ba haka bane taimakawa zaka yi Please Baban Khalil" tayi maganar tana sake shigewa jikinsa.

Amina ce ta kuma dawowa, yanzu ma kanta a ƙasa har da tuntuɓenta.

Alhaji Ahmad na ganin haka ya rungumo Hajiya Zainab ya ce "Nawa kike so?"

Gyar zama tayi tana murmushi cike da duniyanci ta ce "Ni ko million uku ce, wasu sarƙoƙi zan order da takalma"

Ganin Amina taƙi kallonsu, kuma tana ƙoƙarin tashi ta tafi, ya sanya Daddy ya ce "Buɗe fridge ki bani coc"

Kallon Daddy tayi da sauri, dan daga dokokinsa da aka saka masa an hana shi shan lemukan nan. Yana ganin ta kalleshi, ya kashe mata ido yana kuna rungume Hajiya Zainab, Amina bata san lokacin da ta watsa masa wata uwar harara, ta nufi fridge ɗin, maimakon ta ɗauko masa coc sai ta ɗauko masa ruwa.

Daddy ya ce wa Hajiya Zainab "Zan duba inga nawa zan baki, amma ba wannan watan ba"

"A'a gaskiya ni yanzu nake so"

Ya ɗan tsuke fuska ya ce "Bafa na son rigima"

Ko da Amina ta kawo ruwan dire masa tayi a wurin, ta fice daga falon, Ba tare da ta kuma ko kallonsu ba.

Gaba ɗaya haka Amina ta dinga jin ranta babu daɗi, musamman da Amina ta lura da gayya yayi, dan ya bata haushi.
"To ma ni ina ruwana" ta faɗa cike da basarwa.

Abu kamar wasa Yazid ya kwashi kusan kwanaki bakwai bai zo makaranta ba, kuma babu wanda taji ya ce gashi ya san ga a halin da Yazid yake, ta san ba ƙaramin abu ne zai hana shi, zuwa makaranta ba, ta so tayi zancen da Yusra amma ta san halin Yusran, yanzun nan zata fara kawo mata wasu zantukan na banza da zasu ɓata mata rai.
Gefe guda ga Kankiya ya addabi rayuwarta, ta so ta yiwa Mummy zancensa, but she knows what she can do, Mummy bata ɗaukar al'amura irin wannan da sauƙi, ba ta ƙi ta rufe kanta taje ta sameshi ta yi masa tatas ba a kan Fadilan, koma ta kunno masa wutar da ba zai iya kashewa ba, wanda ita kuma Fadila ba ta son hakan, dan haka ta sak duk lambobinsa a blacklist, yadda ba zai iya samun damar kiranta b, amma ya canza lamba ya cigab da uzzura mata.
Gaba ɗaya Fadila a yanayin Activities ɗinta zaka gane cewar tana cikin damuwa, amma ta ƙi gayawa kowa meke damunta.

Amina tana kallon saƙonnin Daddy, yana mata magana amma ta shareshi, dan haka kurum haushinsa take ji.

Kamar yadda Khalil ya buƙata, Abdul ya je gidansu Hafsa domin dubata, sai dai ya tausaya mata, ta rame tayi zuru-zuru, suka gaisa cikin mutuntawa, Sannan ya ce "Dama Khalil ne ya ce in zo in duba masa ke, wayarki ta daina shiga gaba ɗaya"

Hafsa ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Yaya Abdul, dan Allah ka dinga gayawa Khalil gaskiya, ka nuna masa muhimmancin yiwa iyaye biyayya, mahaifiyarsa ta nuna ba ta son alaƙarmu, har wurin sana'ata suka ,o ita da wasu, a kan in rabu da shi mai zai sa ya cigaba da dagewa a kan lallai sai mun cigaba da alaƙa?"

Abdul ya numfasa ya ce "Haka ne Hafsa, kuma nima kaina ina gaya masa, sai dai kiyi masa uzuri tun da na san Khalil ban taɓa ganin macen da Khalil ya nuna ya ce ga budurwarsa ba sai ke, duk da ana nuna ana son sa, a kanki ya fara cewa wannan mace ce da tayi mini nake son na aura, dan haka abin zai masa wuya rabuwa da ke lokaci ɗaya, shima yana can ba shi da lafiya, amma Hafsa ku cigaba da addu'a, idan da Alkhairi sai kiga kun yi auren"

"Anya Yaya Abdul? Kamar yadda mahaifiyarsa ta faɗa ni ba tsarsr aurensa bace, haka ne ni ɗin ban dace da shi ba, ko ya aureni ba zanji daɗin zama cikin family ɗinsu ba"

Abdul ya ce "Ai shi lamarin Allah, ba ruwansa da wani yana so wani baya so, idan ya ƙaddara abu zai yiwu sai ya yiwu, ki cigaba da Addu'a, Amma Khalil ma yana cikin wani hali, kiyi masa Addu'a"

Jiki a sanyaye ta ce "Allah sarki Khalil, mutumin kirki ne zan cigaba da yi masa da Addu'a".

Abdul ya ce "Bari in kirashi ku gaisa" tayi saurin girgiza masa kai ta ce "A'a na samu nutsuwa kwana biyu, idan muka yi waya zan kuma shiga damuwa" tayi maganar idonta fal hawaye.

Wani irin tausayin su ne ya kama Abdul, sun shaƙu da juna, Mummyn Khalil ba ta da tausayi kanta kawai ta sani.

Abdul ya cigaba da rarrashin Hafsa, ya shiga har gida ya gaida Maman Hafsa, yayi musu alheri sai dai da ƙyar ya samu suka karɓa ya tafi.


Amina tana ta shirya kayanta da wuri, saboda tana ɗokin zuwa ganin gida, ranar Litinin da safe, bayan Daddy ya idar da sallar asuba bai dawo gida ba sai ƙarfe shida saura, saboda ya tabattar a wannan lokacin zai ga Amina, tana aikin gida saboda zata tafi makaranta.
Aikuwa yana zuwa ya tarar da ita da duku-dukun nan tan mopping a falo.

Wutar falon aka kashe, hakan ya sanya ɗakin ya gauraye da duhu, da sauri ta waiwaya dan ganin meke faruwa.
Taku taji ana tunkaro in da take, sai dai ko ba a gaya mata ba, ƙamshin turarensa ya sanar mata da shi ne.

Sai da ya zo in da take sannan murya ƙasa-ƙasa ya ce "Good morning"

Shiru tayi taƙi Magana.

"Am talking fa, kuma kina jina"

Cikin basarwa da shagwaɓa ta ce "To meye yasa zaka tsorata ni?"

"Saboda abin tsoron baya baki wahala ko? Wai me nayi miki ne kike wani fushi da cin magani?"

"Ni ba fushi nake ba"

Yayi murmushi, ya sake sunkuyowa daidai tsawonta har tana jin numfashinsa a wuyanta ya ce "Faɗi gaskiya dai, idan ba fushi kike ba, meye na ignoring messages ɗina, ko dai ko dai?"

"Ko dai me?" Ta faɗa a tsorace saboda yadda jikinta yayi sanyi.

"You are jealous dear, stop pretending"

Kunna wutar lantarkin falon da aka yi ne, ya sanya su ɗagowa.



DOMIN SAMUN POSTING KULLUM GARZAYO KI BIYA KUƊIN VIP, KU TUNTUƁENI TA KAN LAMBAR WAYATA

AYSHERCOOL
08081012143.GABA DA GABANTA

BY
AISHA ADAM AYSHERCOOL

AREWABOOKS AYSHERCOOL7724
WATPAD AYSHERCOOL7724

43

Gaba ɗaya suka waiwaya dan ganin waye haka? Gaba ɗaya hankalin Amina ya riga ya gama tashi, Hajara ce a tsaye a wurin makunnin ƙwan, ganin duk suna zuba mata ido kuma sai ta hau kame-kame tana faɗin "Amm.... Ban san.."

Ɗauke kai Daddy yayi daga kallon in da Hajara take, ya mayar kan Amina ya yi ƙasa da muryarsa ya ce "Karki manta anjima zan aiko a kai ki banki, a buɗe miki account"

Noƙe faɗa tayi ta ɗan tura baki ta ce "Ni ba zani ba"

"Me kika ce?"

"Bakomai" ta faɗa taka sake tura baki.

Murmushi ya yi ya wuce sashinsa, Amina ta cigaba da mopping ɗin ta suka mayar da Hajar daidai da kujerun da suke falon.
Gaba ɗaya Hajara rasa abin yi tayi, a baya tunane tunanenta sun fi karkata ga zargi, amma a yau ta sake tabattar da abin da ke tsakanin Alhaji Ahmad da Amina wata alaƙa ce mai ƙarfi da girman gaske, wadda da alama alaƙar tayi ƙarfi sosai da sosai.

Kamar yadda Daddy ya ce, da kansa yaje makarantar su Amina, bayan an tashi sukaje banki, aka yi mata duk abinda yakamata, ya saka kuɗi a ciki naira dubu ɗari biyu.

Mamaki ne ya cika Amina ta ce "Daddy wannan maƙudan kuɗin me zan yi da su, idan Baba ya gane fa?"

Daddy ya ce "Ta yaya Baba zai gane, sai dai idan kece zaki gaya masa, kuma ai ba wasu kuɗi ne masu yawa ba, Zakiru zai kai ki ki sayi duk abin da kike so, ban fiye son shiga wurare bane saboda identity ɗina, ba dan ke ba wurare da yawa ba zan iya zuwansu ni kaɗai ba, kuma ni bana son a takura rayuta duk in da zaka sai da masu baka kariya"

"Amma meyasa baka so a ganka? Kar a ganmu tare aje a gayawa Maman su Khalil ko?"

Ya ce "Eh, kin san bana son ɓacin ranta da damuwarta"

"Eh amma ni kana son ganin nawa" tayi maganar da iya gaskiyarta.

"Mhmm, me yasa kike haɗa kanki da ita? Ita matata ce ke kuma"
Sai yayi shiru.

A ƙule Amina ta ce "Eh ita matarka ce, ni kuma 'yar aiki ba talaka mara galihu"

"Yauwa Ashe kin sani, amma ni bance miki talaka mara galihu ba" yayi maganar da salon ya sake kunna Amina.

Aikuwa ta kai ƙololuwa dan taji haushi ba kaɗan ba.

"Banda rigima irin taki, ina na taɓa ganin wannan ƙarfin hali in ba a wurinki ba, nace kina son mijinta kince me zaki da tsoho".

Cikin tsiwa ta ce "Allah ya kiyaye in yi kishi da wannan matar, ta kasheni da bala'i wadda ba ta san darajar ɗan Adam ba"

"Zaki fara ko? Ban gaya miki bana so ki dinga duk wata magana da zata shafi matata ba".

Amina ta ce "Amma ai kai ka fara bani ba, wallahi Daddy seriously yakamata ka kula sosai, Allah ya baka dukiyar da zaka amfanar da al'umma, amma an gindayeta wuri ɗaya daga ita sai iyalanta, duk wanda ya raɓoka zai mora an dinga yi masa gori kenan da kallon banza, wallahi idan baka gina lahirarka ba daga ranar da ka mutu, wanan dukiyar aka raba musu, su sadaka ma Allah ya kai ladan kabarinka sai wanda ya dubi Allah.
Na san naganganuna sun yi tsauri da yawa, amma dan Allah kayi haƙuri Daddy, wallahi gaskiya nake gaya maka. Dan Allah yanzu dan Allah ya baku arziki ya dace aje aci mutuncin 'yar mutane dan Khalil ya ce yana sonta, ba a gabana aka yi ba, amma yadda ya zo yana faɗar zancen naji zafi sosai saboda nima tsatson talaka ce, da na motsa a gidan nan sai kyara da gori, wallahi Daddy kaf mutanen da ke aiki a cikin gidanka suna yi ne dan basu da wata sana'ar da zasu samu su rufawa kansu asiri, ban da haka mai zai sa ka zauna a gabanka ana kiran mahaifinka nusari, soko da sauran miyagun maganganu?" Ta ƙarasa maganar hawaye mai ƙarfi suka ƙwace mata.
Ba ƙaramin tasiri maganganun Amina suka yi a zuciyarsa ba, duk da ba wata babba bace ba, amna wasu lokutan tana da matukar hangen nesa da son faɗar gaskiya. Yana jinta tana kukan Amma bai rarrasheta ba kuma bai ce mata komaia ba, har tayi ta gama tayi shiru.

Wasa² rashin sanin halin da Yazid yake ciki ya addabi Fadila, tun tana dannewa har ta kasa ya kai ga ta kira Yusra a waya. Ta zayyanewa Yusra duk abin da ke faruwa.
Yusra ta ce "To ni yanzu da kika kirani me kike so in yi miki? Da kina da lambarsa ne ma sai a kirashi, ko kuma ki tanbaya a 'yan ajinku ko akwai mai lambarsa"

Cikin damuwa ta ce "An bani lambar na kira baya shiga"

"Wai to meye duk kika bi kika ɗaga hankalinki?"

Fadila ta ce "Haba Yusra, kamar ba a gabanki kinga halin da yake shiga idan ba shi da lafiya ba, ko da yake ke lokacin da kika zo ya farfaɗo, ni da muka kaishi Asibiti ban zaci zai rayu ba, yau fa ina miki maganar yafi sati baya zuwa school, aikuwa duk abin da zai san ya yaƙi zuwa makaranta ba ƙaramin abu bane ba"

"Na gane, yanzu dai ki kwantar da hankalinki, ki cigaba da Addu'a Allah ya sa yana lafiya, da an san ko unguwarsu ne ma da anje an tambayi in da gidansu yake"

Fadila ta ce "Ni banji wanda yace ya san unguwarsu ba, shikenan dai sai anjima" ta ajiye wayar tare da dafe goshinta, gaba ɗaya tana cikin zullumi.

Khalil dauriya kawai yake yi, ko yaje zuwa wurin aiki sai dai baya iya wani abin kirki, lamarin Hafsa ha tsaya masa a rai nesa ba kusa ba, yana matuƙar sonta da tausayinta, baya son ta faɗa hannun wanda bai san ƙaddara ba, tsananin yardar da tayi da shi ne ya sanya ta gaya masa wani babban sirri na rayuwarta, da baga gayawa kowa ba sai shi, yanzu gashi Mummy ta shiga ta fita, yanzu da wani ta gayawa wannan sirrin ba shi ba, ha zamana kuma bai aureta ba, shikenan haka zai ta kallonta da abin koma yayi ta yaɗawa a gari.

Duk shirin da Amina take yi na zuwa ƙauye, da hidmar da take tayi da kuɗi babu wanda ya tambaye ta ina ta samu kuɗi, hatta wayar hannunta da aka wayi gari aka ganta da ita, Hajiya Zainab bata tuhumeta a ina ta samo ba, sai tsananin saka idanu da take fuskanta daga wurin Hajara.
Ita kuwa Fadila abin da ya dameta daban dan baka ba ta Amina take yi ba, dan idan ta ga dama sai ta wuni a ɗaki bata fito ba balle su haɗu.

Musamman da aka tashi daga makaranta, Amina ta tafi gidansu Azima, mamansu ta sa aka kaita wurin masu gyaran kai, aka wanke kan aka yi mata kitso ƙanana masu kyau, aka yi mata lalle ja da baƙi, sai bayan la'asar ta dawo daga gidansu Azima.
'yan kwanakin nan Daddy ya auri zaman falo, saboda kawai ha dinga ganin Amina, yana zaune shi da Hajiya Zainab Amina ta shigo gaba ɗaya ya mayar da hankalinsa kan Aminar, ba tare da Hajiya Zainab ta lura ba.

Amina na zuwa ɗakinta ta ajiye jakar makaranta, ta tsaya a gaban mudubi tana kallon kyan da kitson kanta yayi.
Wayarta dake kan mudubi ce tayi vibrating. Ta janyo wayar ta duba, sai taga saƙon Daddy ne "Lalle yayi kyau sosai, ki shirya mana dinner a dining yau, ina son zan sake gani"

Murmushi Amina tayi tana sake kallon lallen, tare da mamakin ya aka yi harya ga lallen nan.

Emojin murmushi ta tura masa tare da saƙo kamar haka "Ya aka yi har kaga lallen nan?"

"I watch everything about you, dan haka ba abin mamaki bane, zan jira a dining ki kawo Abincin dare in kuma gani"

Tana daga tsaye sai murmushi take tana bashi amsa, ta tura masa "A gajiye nake, Hajara ce zata shirya dining"

"Kin mai da ni kamar wani kakanki ko? Idan baki zo ba ba ke ba zuwa ƙauye, and i mean it"

Ɗan kwaɓe fuska tayi ta masa reply da "Tuba nake ranka ya daɗe, ba zan iya ɗaukar wannan hukuncin ba, zan zo in sha Allah"

Murmushi ne ya suɓuce masa da ganin abin da Amina ta rubuta masa.

"Ba zan haƙura ba, a haɗa mini fruit salad"

Tayi masa reply da "An gama as you wish"

"Wai dariyar me kake tayi ne kai kaɗai, ka tattara hankalinka a kan waya gaba ɗaya?"

Daddy ya ɗago ido ya kalli Hajiya Zainab ya ce "Ke ma ba taki wayar ce a hannunki ba, hira nake da mutane na"

Ta haɗe rai ta ce "Mutanenka suwa kenan?"

"Nika ɗai nake rayuwa a duniyar ne, babu abokai da 'yan uwa da zan hira da su in murmushi?" Yayi maganar ransa a haɗe, tuna tana lallaɓa shi dan ta karɓi kuɗi a hannunsa ne ya sanya ta bar zancen ta sauya akalar zancen zuwa wani.

"Baban Fadila anya Khalil yana da hankali kuwa?"

Cikin rashin fahimta Daddy ya ce "Kamar yaya kenan?"

Ta ɗanyi ƙwafa sannan ta ce "Ko kiran wayata fa ba yayi, fushi yake da ni kenan?"

"I don't know, bana ce ba, ya kan gaisheni ni dai ta chat"

"Lallai Khalil, aikuwa zan nuna masa nice uwarsa, a kan yarinyar talakawa zai ɗau fushi da ni?"

Daddy ya ce "Idan yana sonta ki ƙyaleshi mana, Khalil fa ba yaro bane ya mallaki hankalinsa, he knows what is right for him, ki ƙyale yara su zaɓi abin da ya dace da rayuwarsu"

A fusace ta ce "Over my dead body, yarinyar fa a bakin titi take sayar da kayan shirme, ai ba kimar gidan nan bace kaje nemawa ɗanka aure gidan matsiyata, Allah ya suttura, haryanzu Khalil bai san me ya dace da shi ba, dan haka ni zan zaɓa masa mace 'yar gidan daraja ya aura"

Daddy ya ɗan gyaɗa kai sanan ya ce "Ba kya ganin hakan zan haifar masa da matsala? Karki aura masa 'yar mutane ya wahalar da ita, tun da ba shi ya ce yana so ba"

"Shi ya isa ya tsallake umarni na? Yaje ya yi ta fushin kar ya fasa, zan maganinsa ne"

Daddy dai be kuma cewa komai ba, ya cigaba da taɓa wayarsa.

Kamar yadda Daddy ya gaya wa Amina, yana dawowa daga sallar isha'i ya nufi dining yayi zamansa, yana jiran Amina.
Sai dai ko da Amina ta kammala girkin, ta shiga tayi sallar isha'i, Hajara ta je ta fara shirya kayan Abinci.
Ba tare da ya kalli Hajara ba ya ce "Turo mini Amina ta ƙarasa kawo Abincin"
"To" ta amsa gwiwa a saɓule.

Ta tarar da Amina a Kitchen, ta zuba ruwa tana sha, "Alhaji ya ce ki ƙarasa kai sauran Abincin"

"Ban da abu irin naki dama Hajara, ni da ki ka barwa girki nayi ai sai ki bari in ƙarasa ladana, amma na zo na tarar kin fara kaiwa" ta wuce ta ɗauki plates, da jug ɗin da ta yi fruit salad ta fice.
Hajara tayi ƙwafa ta ce "Ayi dai mu gani, Allah ya tona muku asiri muga ƙaryar iskanci"

Cikin sa'a Amina ta tarar Hajiya Zainab da Fadila ba su fito cin abincin ba, sai

Please Login or Register in order to submit comment