Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kai sau biyu, amma Yazid na kan sallaya yana ibada.
Ita yawan ibadar Yazid har mamaki yake bata.

Ji tayi yayi shiru da karatun da yake yi, ya tattara hankalinsa a kan wani abu, da bata san ko menene ba.
Ƙasa ƙasa taji Kamar Yazid kuka yake yi.

Kasa kwanciyar tayi, har ta fito ta je daf da shi, bai sani ba. Hannu ta saka ta zare hoton da yake hannunsa.
Wata kyakkyawar Bafulatana ce a jiki,  mai matuƙar kyau na ɗaukar hankali.

"Wacece wannan?" Ta jefo masa tambayar.

Shiru yayi ya zuba mata ido, ya kasa furta komai.

Littafin kuɗi ne, ku tuntuɓeni domin saya.
Ayshercool
08081012143LITTAFIN NAN NA KUƊI NE, MAI BUƘATA YANA IYA TUNTUƁATA A KAN LAMBAR WAYATA 08081012143

76



Cikin ƙosawa ta sake cewa "Ka yi
magana mana, ka yi shiru kana kallona"

Ya saka hannu ya karɓi hoton daga hannunta, yana ɗan jujjuya shi sanyaye ya lumshe idanunsa sannan ya buɗe su ya ce "Wato Fadila, duk wanda ya rasa uwa yayi kuka. Shiyasa duk da ina murna na aureki, amma bana jin daɗin nesanta ki da Mummy da Daddy yayi ba. Ita uwa wata kyauta ce daga Ubangiji da bata da madadi.
Inna wuro kenan, ni kuma ina kiranta Innata. Kamar yadda na samu labari Bafulatana ce ta riga a can wani ƙauye a Jalingon jihar Taraba. Galibinsu fulani ne, sai dai galibinsu ba musulmi bane ba, rigar su Innarmu musulmi ne sai dai basu damu da ilimin addini ba, ba abin da suka sani sai kiwo da kuma tallan Nono. Inna tana da yayye mata biyu sai kuma ita ta uku, suke nan a wurin mahaifinsu. A wurin tallan Nono ne da suke shiga garin Jalingo yi Inna ta ci  karo da ilimin addini ta gane Cewar a duhu suke zaune na jahilci, addinin ma basa gudanar da shi yadda ya dace a rigarsu dan haka ta ɗau ragamar neman ilimi.

Idan taje tallan Nono, sai ta zauna cikin makarantu ta ɗau karatu. A lokacin babu wanda ya damu da sai an saka a makaranta kan kaje, ta samu wata makarantar islamiyya tana zuwa.
Ta ƙuduri aniyar yin karatun addini mai zurfi. Domin ya zama babbar malamar ita ma ko dan ta dinga wayar da kan 'yan ƙauyen su. Sai dai wannan buri nata bai cika ba, mahaifina ya haɗu da ita, lokacin da suka je rigarsu shi da wani abokinsa sayen shanu.

Kasancewar dama ba karatu suke yi ba, kuma 'yan uwanta duk da wuri ake yi musu aure, ya sanya ita ma mahaifinsu ya amince da mahaifina a kan ya kawo kuɗin aure a sanya ƙanƙanin lokaci.
Mahaifina yana da mata biyu, mahaifiyata ce ta uku, uwar gidansa Baba Uwani, sai kuma ta biyun Baba Hanne. Babban abin da ya damu mahaifiyata shi ne burinta na karatun addini babu lallai ya cika.
Bayan ta auri Mahaifina, ya tafi da ita garinsu da yake cikin Ranon jihar Kano ta tare a gidansa da ke ɗauke da matansa da kuma yaransa biyar da suka kasance duk mata.

Kalata ta wurin uba tana nan a raye, amma a lokacin bata garin Rano, tana wani wurin tana aure bayan rasuwar kakana, dan haka babana yana da yayye biyu maza, sai ƙanwarsa mace.

Mahaifiyata na da matuƙar haƙuri da kawaici, mabaifina yana sonta sosai da sosai, hakan ya sa ta bijiro masa da son ta koma makaranta, amma ya ce bai yadda ba abin zai zama surutu a gari.
Tun da mahaifina ya auro mahaifiyata matansa suka sakota gaba, suke nuna mata ƙiyayya a fili. Idan baya nan suyi ta sakata aiki mai wahala. Mahaifina tsayayyen mutum ne a kan gidansa, yana da rufin Asiri sosai a garinmu an san shi sosai yana da kuɗi, yana dillancin dabbobi har zuwa kudu da maƙotan Nigeria, gidanmu ba a yunwa ko rashin sutura, sai dai ba a damu da ilimi ba sam.
A na haka mahaifiyata ta samu juna biyu, sai dai ba wanda ya sani, saboda ba ta laulayi daga ita sai mahaifina suka sani.
Babu wanda ya farga mahaifiyata na da juna biyu, sai ganinta kawai suka yi tana naƙuda. Ta yi doguwar naƙuda bata haihu ba, Babana ya ɗauke ta zuwa Asibitin cikin gari, dan duk da rufin Asiri na mahaifina yana cikin karkara da iyalansa.
Mahaifiyata ta haifi ɗa namiji, Mahaifina yayi murna sosai da sosai, zai samu magaji, mahaifiyata kuma murnar da take yi, shi ne Allah ya cika mata burinta a kan yaron nan, ya zama masanin addinin Muslunci sosai.
Tun da suka koma gida sai ƙananan maganganu, mussaman da suka ga yadda mahaifina ke ta rawar kai a kan haihuwar.
Ranar suna mahaifiyata ta roƙi mahaifina ya saka mini suna Yazid.
Mahaifina bai sani ba, sunan wani babban malami ne a cikin garin Jalingo da Innata ke zuwa masallacin sa jim wa'azi.
Son da yake yiwa mahaifiyata ya sanya shi ya amince, ya sanya mini suna Yazid.

'yan garinsu mahaifiyata sun zo, duk da fulani ne amma wasunsu ba musulmai bane ba suka zo taron suna, mahaifina sai da ya yanka manyan raguna da saniya, aka dinga ci ana rabar da naman a garin, ko baka je suna ba, abu ne mawuyaci ka kasa cin naman da aka yanka da kuma abincin suna.
Matan Babana suka kuma mahaifiyata a gaba, abin mamaki a wannan karon har da facaloli, suna mata gorin wai 'yan uwanta maguzawa ne.

Mutanen gari suka dinga yi wa matan mahaifina Allah sarki, duk wannan wahalar yaransu mata ne, lokaci ɗaya daga zuwan mahaifiyata ta fara haihuwar namiji, idan babana ya mutu ba zasu samu komai ba.
Kasancewar mahaifiyata ba sawa ba fitarwa, ya sanya bata damu da abin da suke yi ba, sannan bata nuna kara a kaina kasancewata ɗan fari.
Ba abokan zaman mahaifiyata ba, hatta 'yan uwana yayyena, suke kishi da ni, basa son na raɓesu.
Tun ina ƙarami mahaifiyata ke mini kirana da Gwani Yazidu magajin malam.

Bayan na fara tasawa, ɗan abin da mahaifiyata ta sani na ilimin addini ta fara koya mini, hatta magana tayi iyaka ƙoƙarin ta bakina ya buɗe da la'ilahailallah. Irin koyon maganar nan na yara, da bisimilla istigfari ta dinga koya mini bakina ya buɗe da su, bana zuwa ko ina ba wanda yake ɗaukata kullum ina tare da mahaifiyata hakan ya sanya nayi saurin iyawa.

Shekaruna uku a duniya, Innata ta matsa a kan lallai mahaifina ya kaini makaranta, ya nuna mata nayi ƙanƙanta da yawa amma ta dage, da ƙyar ta bari na shekara huɗu. Ya sakani a wata makarantar addini da take ƙauyenmu, sai dai akwai nisa sosai daga gidamu zuwa makarantar dan haka mussaman yake biya malamin makarantar kuɗi, ya dinga sawa ana zuwa a ɗaukeni ko a dawo dani.

Cikin ikon Allah nan da nan, kasancewar ƙwaƙwalwar yarinta, na dinga ɗaukar karatun Alkur'ani da malamin ke tsaye a kaina yana koya mini.
Tamkar ɗan ƙaramin ɗansa haka ya mayar da ni, ya kan ɗorani har a kan cinyarsa yana koya mini karatun Alkur'ani.

Sai dai ƙiyayyar da ake nuna mini a gidanmu  ta sanya bana sakewa ko a cikin yara, dan ko tsakar gida na fito wasa, sai yayyena su ci zalina.
Kullum ina naniƙe da Innata ko ina makaranta.
Batun gata a wurin mahaifina ba a magana, duk abin da ya ɗinka sai ya ɗinka mini, ga mahafiyata ma bata wasa da Abincin da zan ci, bata bani cimar banza, gashi da ƙananan shekaruna amma girmamani take saboda sunan da aka saka mini.
Daga cikin abin da yake ƙonawa mahaifiyata rai, shi ne yadda abokan zamanta kan kirani da jikan maguzawa saboda a danginta akwai wanda ba Musulmi ba, cikin izgilanci idan ta kirani magajin Malam, sai suce ko kuma jilan maguzawa ba.


Sai da na shekara bakwai a duniya, sannan mahaifiyata ta kuma haihuwa, ta sake haihuwar ɗa namiji, aikuwa matan gidan nan tamkar su kasheta, saboda 'ya'ya maza take haifa. aka saka wa jaririn sunan Huzaifa.

Duk da Inna ta kuma haihuwa, hakan bai hana ta daina sona ba, tare da cigaba da kula da mu.
Ban fi shekaru goma ba, Mahaifina ya fara tafiya da ni wuraren kasuwancin sa, idan yana gari wasu lokutan haka yake zamansa yayi ta hira da ni, yana mini hirar kasiwancinsa duk da ba ganewa na ke yi ba. Ya biya aikin umara ni da shi ya tafi da ni.
Hakan ya ƙara rura wutar ƙiyayyata a zukatan matan gidan, kamar su cinye ni su huta. Inna tana yawan gaya masa ya dinga ƙoƙarin yin adalci a tsakanin yaransa bai kamata ya tafi da ni umara ba. Amma buɗar bakinsa ya ce mata "Su 'ya'yan su da nake aurarwa na ke kashe musu kuɗi nawa na taɓa bawa Yazid, ina adalci a tsakanin su"

Ƙanina Huzaifa shima ya fara tasawa, sai dai halina da na Huzaifa ba iri ɗaya bane ba. Huzaifa yaro ne mai ƙiriniyar gaske, ga ta'adin tsiya, Inna tana can tana aiki Huzaifa zai fita tsakar gida ya shiga neman magana a tsakar gida.

Su kama mutan gidan su kama Huzaifa su yi ta duka suna zagi, abin da yake matuƙar ƙona mini rai, in ga an daki ɗan uwana. Duk rashin maganata ina jin haushin in ga an taɓa gudan jinina.
A lokacin na kai shekaru goma sha uku, ina haddar Alqur'ani sosai da sosai, tun Huzaifa na shekara uku nake tafiya da shi makarantar mu. Idan muna gida kuma ina koya masa karatun.

Ba zan manta watarana ba, babbar yayarmu da aka yi mata aure tuni, mai suna Yaya Gaji ta zo ita da yaranta.
Suna cikin wasa tare da Huzaifa da yaranta, faɗa ya kaure a tsakanin sa da ɗanta Sani, yayyensa suka haɗu suka dinga dukan Huzaifa, da ƙyar na ƙwace shi, na kalli ɗaya daga cikin yayyena da har da su a dukan Huzaifa, abin da ban taɓa ba nace "Allah ya saka maka" ba tsammani na ji saukar mari yayata mariya ta mareni tare da ɗorawa da zagina. Duk ƙanƙantar Huzaifa da yaga an mari yayansa, haka ya fara kaiwa Mariya duka, haka na janye Huzaifa muka bar tsakar gidan.

Sai dai ko mintuna goma ba ayi da dukana da Mariya tayi ba, ta ƙone a hannu da ruɗen tuwo, a take ta kurma ihu, ba a ɗau tsawon lokaci ba hannun ya saɓule a take.

Mariya ta sha jinya dan kamar hannun ba zai warke ba, shi kuwa Huzaifa kamar an sake tunzura shi kullum rashin jinsa gaba yake yi.
Hatta Innarmu suna yawan yin faɗa da Huzaifa, ni kuwa ko Inna bana son na ga tana taɓa mini Huzaifa.

Gaba ɗaya hankalina baya kan kasuwancin da mahaifina ke ta janyo ni kan harkar. Ina nan na mayar da hankali a kan karatu na, tare da kula da ƙanina abin ƙaunata.
Kwatsam! Matan mahaifina suka tsiro da wani camfi, wai in dai aka taɓawa Inna 'ya'ya sai wata masifa ta afkawa mutum, bayan jikan maguzawa da suke kirana da shi, suka fara ƙoƙarin laƙaba mini maita ni da mahaifiyata.
Ina da shekaru goma sha huɗu, na sauke Alƙur'ani hadda, malaminmu ya fara batun a turani makaranta cikin gari, domin samun cigaba da karatuna na addini.
Mahaifina ya fara iƙirarin karatun ya isa haka, yana son ya sakani a kan kasuwancin sa sosai, amma mahaifiyata ta cigaba da lallaɓa mahaifina, a kan ya bar ni na cigaba da karatun.
Son da yake yi mata ya sanya wasu lokutan, baya son yin abin da zai sanya ta cikin damuwa. Makarantar da zan tafi ta kwana ce, amma zallar ilimin addini ne ake koyarwa a ciki.
Inna tana ta yi mini shirye shiryen tafiya, ni kuma kewarta da ta ƙanina ta fara damuna, ina son karatuna amma kuma ina ƙaunar iyayena da ƙanina. A nata shirin tafiyata ne, a lokacin  kuma Innarmu ta fara wata irin rashin lafiya, ga kuma tsohon ciki, ga wasu irin ƙuraje da suka fara fito mata a jikinta.
Nan na ji ba zan iya tafiya na bar sanyin idaniyata a wannan hali na rashin lafiya ba.

Inna ta dafa kafaɗata ta ce "Haba Gwani ɗan Inna magajin malam, ba ka son Inna ta yi alfahari da kai, ka zama babban malami?"

"Inna ina so, amma baki da lafiya fa"

"Bakomai, kar ka damu zan ji sauƙi in sha Allah"

Huzaifa ya kalli Inna ya ce "Inna, wai almajiranci za a kai yayana, ni gaskiya zan bi shi in da za shi"

Inna ta ce "A'a ba almajiranci bane ba, karatu zai je yi"

Huzaifa ya fara kuka ya riƙe ƙafar Yazid ya ce "Gwani Dan Allah kar ka tafi ka barni, dukana su Mariya zasu cigaba da yi, kuma wa zai kaini makaranta? Da wa zan dinga cin abinci?".

Na durƙusa na rungume ɗan uwana, ina rarrashinsa. Inna ta matsa na tafi makaranta.

Ta riƙe hannuna ta ce "Allah ya yi riƙo da hannunka, Allah ya shiga lamarinka ka mayar da hankali sosai Yazid, Allah ya baka ilimi mai amfani"

Baba da kansa ya kai ni makaranta, tare da Malamina na garinmu Malam Kabir, makarantar babbace, kuma boko ce da islamiyya a haɗe. Dama idan ɗaliban Malam Kabir sun yi sauka, wanda suke buƙatar ɗora karatunsu, wannan makarantar Malam Kabir ke tura ɗaliban sa, saboda yana da connection da su.
A nan shugaban makarantar ya yiwa babana bayanin makarantar an buɗe ɓangaren boko ma, idan yana buƙata in haɗa duka.
Baba ya ce a bani zaɓi idan ina so, nan na ce masa ina so, babana ya biya komai, kuɗin makaranta ta sai da Baba ya tafe na shekara uku, saboda Babana yana da arziƙi dai-dai gwargwado. Iya kayan Abinci da na tafi da su kuwa, ba a magana ya bani kuɗi masu yawa, ya rungumeni yana cewa Gwani Yazid zan yi kewarka sosai zan dinga zuwa ina dubaka.
Ni kaina na ji babu daɗi tafiyar Babana, ga kuma kewar Innata da ƙanina Huzaifa.

Na mayar da hankali sosai a kan karatuna, sai dai ni bokon nan tana mini wahala, dan makarantar kanta sun fi ƙarfi a kan ilimin addini, amma duk da haka ban sare ba, na ɗorawa raina ina son yin karatun.

A lokacin babu waya, dan haka ban san halin da Inna da Huzaifa suke ciki ba, duk da abin yana damuna, Baba yana zuwa kawo mini ziyara sai ya ce mini kowa yana nan lafiya ba sai na zo ba gida ba, in zauna in yi karatuna dan cika burin mahaifiyata.

Kusan watanni huɗu ina makaranta ban je gida ba, Baba ya hanani, gashi an shigar wata na biyar, Baba kuma ya shafe lokaci bai zo ba, na tayar da hankalina na ce zani gida.

A ka bani kwana uku a makaranta.

Sai kuma Yazid yayi shiru ya sunkuyar da kansa.
Cikin ƙosawa Fadila ta gyara zama ta ta ce "Cigaba mana"

Yayi ajiyar zuciya ya ce "Da na koma gida, Allah ya yiwa Babar Gwani rasuwa, wato Innarmu. Naƙuda ta kamata Baba baya gari, matan gidan nan aka rasa mai kaita Asibiti. Tun lokacin da take da cikin kasancewar mahaifinmu ya ɗan fara wayewa da wasu al'amura na zamani, ya bar Inna ta je awo, kuma a wurin awon an sanar mata da ta fara naƙuda ta je Asibiti kar ta haihu a gida, ni da ita take gaya mini haka, amma ba su taimaka mata ba, dama tana halin rashin lafiya naƙuda ta risketa, tayi jijjiga ta rasu, ta bar ɗan jaririn, kamar yadda na samu labari har ta mutu tana tsaka da naƙuda addu'a take yi mini, Allah ka cika mini burina a kan Gwani, Allah ka shirya mini 'ya'yana ka duba mini ka tsare mini shi, da shi da ɗan uwansa Allah ka zama gatansa. Da ire-iren wannan addu'a ta cika.

Baki ba zai iya bayyana halin da na shiga ba, na tarar da Huzaifa ya yi baƙi, ya rame na nemi a nuna mini mai ta haifa amma aka ce washegari shi ma ya koma.
Duk yadda na so na yi tawakalli na kasa, na shiga ɗakinta na tatarao kayanta na saka a gaba na dinga kuka.
Bayan an share zaman makoki, dangin mahaifiyata suka ce zasu tafi da Huzaifa, tun da yarone a ƙarami, bai fi shekara takwas zuwa tara ba, amma matan mahaifina suka ce, kar ya yarda a kai masa ɗansa cikin maguzawa. Aikuwa mahaifina ya hana su, mahaifiyarsa ta so saka baki, amma ta yi shiru saboda duk 'yan'yanta shi ne mai kuɗi ba ta son ɓacin ransa.
Sai dai tun a wurin zaman makokin Inna, na fuskanci sauyi daga wurin Baba, kamar ba ya son ganina, da ya ganni sai ya kawar da kansa, idan na zauna a wuri sai ya tashi, ya yi ta hantarata na rasa dalilin haka, amma na bar shi da kawai alhinin mutuwar Inna ne.

Duk da ƙarancin shekaru na Huzaifa, ya dinga ce mini "Gwani, Inna ta ce kayi karatu, ka cika mata burinta" Na rungume Huzaifa ina kuka, ina tunanin yadda zan bar shi a gidan shikaɗai.
Mahifina ya koma kan kasuwancin sa, ba tare da ya mini ko sallama ba. Ga wasiyyar Inna a raina ga tausayin Huzaifa, tabbas da ya dauke Alqur'ani da da shi zan tafi makarantar mu.

Tun ina gidan ban koma ba, abinci sai an ga dama ake bamu, a daddafe na kwan goma, Huzaifa yana nanata mini in koma makaranta.
Dauriya da juriya ce kawai ta sanya ni na koma makaranta, na ji duniyar ta isheni, ta daina mini daɗi, bana gane komai, karatunma da ƙyar nake yi, Allah ya jiƙan shugaban makarantarmu Malam Umaru mai allo, ya dinga rarrashina yana bani haƙuri.

A haka na cigaba da karatu, ina tunanin halin da ƙanina yake ciki, da ƙyar na yi watanni biyu, kayan Abinci na suka ƙare kaf, ga Baba ya daina zuwa makarantar gaba ɗaya ganina.
Wani ɗan makarantarmu da muka yi makaranta tare a garinmu da yaje gida ya dawo, yake sanar mini wai akwai matsala a gidanmu ƙanina babu lafiya. Ranar ko baccin awa guda ban ba, gari na wayewa na nemi izini na tafi garinmu. Da na je gidan mu ba wanda ya saurareni, balle ya iya gaya mini abin da ya faru, sai a waje ake gaya mini, wai Huzaifa na babban Asibitin cikin gari.
Kuɗin hannuna ba su taka kara sun karya ba, na tafi Asibitin da aka gaya mini, sai da ƙyar na gano a in da aka kwantar da Huzaifa.
Na tarar da shi Kansa da hannunsa duk bandeji, ga ƙafarsa ma haka.
Cikin tashin hankali na ƙarasa wurinsa, na riƙe shi cikin kuka na ce "Gwani Huzaifa, meyafaru da kai haka?"

Leɓensa a bushe ya kalleni, ya riƙo hannuna da hannunsa mai lafiya ya riƙe, amma bai ce komai ba sai hawaye da ke bin gefen idonsa.

Na kuma matsawa na ce "Waye yake zaune a wurinka"

Ya girgiza kai ya ce "Ba kowa, Baba uwani ce ta zo ta tafi, amma ba ta kula da ni ba ta bani ruwa"

Cikin kuka na ce "gayamini, meya sameka ƙanina".

Huzaifa ya ce "Zan gaya maka, amma kar ka gayawa kowa"

"Ba wanda zan gayawa"

Huzaifa ya yi ƙasa da muryarsa ya ce "Sani ɗan gidan Yaya Gaji ne, da muka je ɗiban ruwa bayan gari, ya hankaɗani a rijiya, ya gudu ya barni, ban san yadda aka yi na fito ba, na ganni a nan, wannan masu saka farar rigar sun ce na karye a hannu na da ƙafata, a biya kuɗi a gyara mini."

Na sake matsawa na rungumeshi ina kuka, shi ma cikin kukan ya ce "Baba bai zo ya ganni ba, kuma Inna Gaji ta ce ta gaji da zuwa wurina, dan Allah Yaya kar ka tafi ka bar ni a nan"

"Babu in da zanje Huzaifa, ina nan a wurinka".

Muna cikin wannan halin wani likita ya shigo, ya kalleni ya kalli Huzaifa ya ce "Ɗan uwanka ne?" Na jinjina masa kai alamar eh.

Cikin faɗa ya ce 'Amma 'yan gidanku ba su da mutunci, mun gaya musu a zo a biya kuɗi mu ɗora yaron nan, ayi masa hoton kai da na ƙirji da sauran tasa tasai, ya zubar da jini sosai kalli yadda fatarsa tayi haske saboda rashin jini, kuma idan yayi tari gudan jini ne yake fita, amma sun yi buris kamar an kawao dabba an ajiye,mai jinya ma babu, Mutanen karkara sai dai su haifi 'ya'ya amma ba a iya kula da su ba".

Na kwantar da murya na ce "Dan Allah likita ka yi haƙuri, ina ga babanmu bai sani ba, amma zai iya biyan ko nawa ne, bari zan je gida na gaya masa".

Likita ya ce "Ka hanzarta, dan muna buƙatar ganin baban naku, ance babar yaron ta rasu, amma ai yakamata ya sanya ido a kan yaransa, ya za ayi a tura wannan ɗan mistitsin yaron ɗiban ruwa a rijiyar ƙauye da bata da ɗauri balle murfi ba dole ya faɗa ba?"

Likitan nan ya yi ta sababi ina ba shi haƙuri. Da ƙyar na lallaɓa Huzaifa, ya haƙura na ninka na koma gida a ƙafa, saboda bani da kuɗin mota, na yi sa'a na tarar da Baba a gida. Na gaishe shi amma ya ƙi amsawa sai tsawa da yayi mini, yana tambayata ko lafiya?.
Nan na sanar masa da abin da likita ya ce, abin mamaki duk soyayya tarairya da kulawar Baba ga 'ya'ya musamman idan mutum ba shi da lafiya ba ga matan ba ba ga mazan ba, muddin ɗansa ba shi da lafiya sai ya shiga damuwa, amma a wannan karon sai ya hauni da faɗa, wai na tashi na ba shi wuri. Na shiga tunanin laifin da na yiwa Baba har na fusanci wannan wulaƙanci amma na kasa ganowa, na sake marairaicewa ina masa kuka da magiya, amma ƙarshe ya hau neman madoki.
Matan Babana da ke tsakar gida kuma suka saka shewa suna dariya. Wata uwar yunwa na sakata ta, amma ba ta abincin nake ba, na shiga ɗakin Inna na tattara samirunta, da kwallaye, na fita da su, na je na sayar na sai Abinci na yi kuɗin mota zuwa Asibiti, da niyyar na kai kuɗin idan ya so ko wani abun a fara yiwa Hauzaifa. Amma ina zuwa na tarar da ma'aikata a kansa yana ta aman jini, da wani irin numfashi, wata Nurse tana faɗin wannan yaron da wuya ya tashi, da alama da ka ya dira a rijiyar ko ya samu internal injury a cikin kansa ko kuma dai a ƙirjinsa!!!YAU TAKE JAJIBERIN ZAƁE A NIGERIA, MASU ƘURI'A A HANNU KU TAIMAKA KU ZAƁA MANA SHUGABANNI NA GARI MASU TSORON ALLAH, KUN GA DAI IRIN HALIN HA'ULA'I DA MUKA TSINCI KANMU A WANNAN RINTSIN, TSADAR KAYAN MASARUFI, RASHIN TSARO, YAJIN AIKI DA SAURANSU.
DUK DA BA WANI MUKE ZARGI DA SAMU A HALIN DA MUKE CIKI BA, JARABTA CE DAGA ALLAH.
MUNA FATAN UBANGIJI ALLAH YA ZAƁA MANA SHUGABANNI NA GARI AMIN.





77

Dariya ce ta kusa ƙwacewa Yazid ya ce "Banda ragon azanci, ya zaki saki kayan kuma ki hau rufe jiki? Me ma zan kalla? Ki shirya a nutse"
bin sa tayi da kallo, ta kasa motsawa balle ta ɗau kayan sai ɓoye jiki da take yi.
Ya ƙarasa ya ɗau kayan ya ɗora mata a kafaɗarta.

Cikin tsiwa ta ce "Ni ka fita na saka kaya"

Shiru ya yi mata, ya wuceta ya buɗe sip, ya ɗauko kayansa yana ƙoƙarin sauyawa, alhalin da ba haka yake yi ba, sai ya ɗebi kayansa ya tafi banɗakin tsakar gida.

"Wai me zaka yi haka?"

"Me kika gani a hannuna? Kaya zan saka"

"Kuma a cikin ɗakin nan a gabana?"

Yazid ya ce "Yau naga ikon Allah, kiyi harkarki nayi tawa mana, ina ruwanki da ni ne?"

Ya ƙarasa maganar yana zare singlet ɗin jikinsa.
Juya masa baya tayi, dama kaya ne suke rage masa girma kokuwa dai tsananin kwarjinin da yayi mata ne?.

Kwasar kayanta tayi, ta nufi ɗan mitsitsin banɗakin da ke cikin ɗakin, wanda da ƙyar take iya juyin kirki a cikin sa. Tana daf da shiga taji ya ce "Masha Allah, ƙafafuwanki gwanin ban sha'awa"

Ƙirjinta ne yake dukan uku uku, tana mamakin fitsarar da Yazid ya ke gwada mata, a haka kamar na ruwansa, abin da yayi mata jiya ta tuna a ranta ta ce 'Lallai ma mutumin nan'.

'wai kayan sun gagara ki saka ne, ko sai na shigo na taya ki sawa?"

Shiru tayi masa, ta gama sanya kayan sannan ta fito, ta wani haɗe rai karma ya kawo mata wargi.

Shima basarwa yayi, ya ɗauki mukulli suka fita.
Mamakin irin unguwarsu Yazid take, kasancewar yamma ce, galibin yaran unguwar suna gindin kwata suna suyar awara, wasu na sayar da dankali, wasu wainar fulawa.
Ga azabar lunguna da kwatoci ko ina, ga uban tumaki da awaki, kana tafe kana basu hanyar wucewa, banda kajin hausa da suke nasu shagalin tsakanin layukan.
Sai a

Please Login or Register in order to submit comment