Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

'Taɓ dama kin san abin da ya dace da wanda bai dace ba?'

Fadila tana nan tana zaman jiran Daddy ya kirata, sai sannu take jerawa Yazid, shi kam Yazid yayi shiru bai cewa komai, sai taron ɗalibai 'yan ajinsu dake tsaye a wajen suna mayar da yadda aka yi.

HOD ɗin su suka gani ya tunkaro in da suke, da shi da wasu malamai guda biyu.

Yana zuwa ya kallesu a ɗan rikice ya ce "Wacce Fadila?"

"Gani"

"Ke ban da abinki, idan kina da wata Matsala ba sai kizo ki mini bayani ba a san yadda za ayi, amma kawai kina nema ki kunno mana wuta daga sama haka ake yi, ina shi wanda aka krɓarwa takarda?"

Yazid ya sauk mask ɗin fuskarsa ya ce "Gani sir"

HOD ya kalleshi ya ce "Yazid kai ne?"

"Eh nine sir"

HOD ya kalli malaman da suka zo tare ya ce "Baku gane wannan yaron ba? Ya taɓa jan sallar juma'a ranar da Imam bai zo ba, Yazid ya aka yi wannan matsalar ta faru, ya aka yi aka kamaka da satar amsa"

"Wallahi sir ban saci amsa ba, ga class mate ɗina nan a tambaya aji?"

"Wallahi Sir ka san Yazid ba zai yi satar amsa ba, the overaller of the year, ka sani sir" cewar Captain.

HOD ya ce "Naji, kuje za a san abin yi, ke Fadila da kai malam Yazid ku shigo na kira Kankiyar a waya ai"

Captain ya ce "Allah ya ƙara maka lafiya Baba HOD, Allah ya tsare mana kai, wallahi mun yarda in dai Yazid na da laifi a hukunta shi".

"shikenan, kuje za a kula da komai in sha Allah"

Bayan sun shiga Ofishin HOD, Vice ɗinsa sai masifa yake yi, a kan dan me za a goya musu baya, su kai ƙarar malami?.

HOD ya ce "Daga sama aka bada umarnin faɗaɗa bincike, dan haka sai ka ja bakinka kayi shiru".

Fadila da kanta ta janyowa Yazid kujera, ta goge masa ya zauna a hankali.

Ɗaya malamin ya ce "Shi bashi da hannu ne?"

Fadila ta ce "Ba shi da lafiya ne"

"Meya same shi ga mutum garau da shi?"

"An masa aiki ne, kuma yana da Asma, baya son ƙura"

"Lallai kam"

Shi dai Yazid babu abin da ya iya cewa.

Kankiya da yaga kiran HOD, ya gama tsara ƙarairayin da za suyi shi da TJ, bai zaci abin ya girmama ba, sai da ya tarar da Exam officer da student affairs ga kuma Yazid da Fadila, a take ya sha jinin jikinsa. Gaba ma she akwai gabanta.

Suka nemi wuri suka zauna, nan aka shiga bin diddigin abubuwan da ya faru, da har ya sanya aka yi waya daga sama a kan case ɗin.

Nan Fadila ta warware komai, hatta chats ɗin su da Kankiya, da yadda yake takura mata da waya, da warning a kan Yazid, sai data nuna musu da wasu daga recordings ɗin wayar da suke yi.
Shi kansa Kankiya sai a lokacin ya san waye mahaifin Fadila, Yazid kansa yayi sanyi da jin Fadila 'yar waye, bai taɓa zaton hakan ba, kawai dai ya zata 'yar masu kuɗi ce, amma mutumin da ya taɓa riƙe ministan albarkatun ƙasa, kuma sananne bai zai gaza sanun kowace irin alfarma yake nema a ƙasa ba.
Aka koma ɓangaren Kankiya ko yana da abin cewa, da kuma TJ ya bada hujjar cewa Yazid ya saci amsa, amma kowanne ya gaza kare kansa.

Nan aka ce sallami su Fadila, amma Fadila ta ce ya batun jarrabawar Yazid? Ta fito da takrdarsa da aka duƙunƙuna, EO ya karɓa ya ce su tafi an sallamesu.

HOD ya ce "Dan Allah dan gaba idan abu irin wannan ya faru, kan a gayawa father a fara zuwa a samemu muyi maganin abin, ba sai an kunno mana wuta daga sama ba" Murmushi kawai Fadila tayi.

Yazid ya kalli malaman ya ce "Sir na gode sosai da sosai, Allah ya saka muku da Alkhairi ya biyaku da aljanna"

Student affairs ya ce "Kar ka damu, Allah yayi muku albarka"

Suka amsa da Amin.

Yazid ya fito yana ta jera ajiyar zuciya, yana godewa Allah yadda yake tsallakar da shi tarko da sharrin mutane daban daban.

Fadila ta kalleshi ta ce "Nayi farinciki da Allah ya sanya wahalarka ta semester nan bata tafi a banza ba, Allah ya ƙara kiyayewa"

"Amin, na yaba da namijin ƙoƙarin da kika yi a kan ganin ba aci mutuncina ba"

"Kar ka damu, idan na bari aka tozarta ka kamar ni aka yiwa, kuma koma menene ai a kan gaskiyarka ne, bari in kira Daddy in yi masa godiya"

Yazid ya jinjina mata kai. Ta ciro wayarta ta kira Daddy.

"Hello yaya aka yi, komai ya daidaita ko kuwa?"

Ta faɗaɗa murmushinta ta ce "Daddy komai yayi daidai, an kiramu an warware komai, muna godiya Allah ya saka da alheri"

"Amin, sannan idan na dawo gari zan zo makarantar ta ku, dole ayi miki tsakani da wannan malamin, ba zan lamunci irin haka ba, kuma daga yau kar ki sake ɓoye abu makamancin wannan"

"To Daddy in sha Allah, mun gode sosai"

"Never mind sweetheart, ayi karatu da kyau Allah ya bada sa'a"

"Amin Daddy"

Ta mayar da dubanta kan Yazid ta ce "To yaya, muje in sauke ka ne?"

"A'a, ina jiran Sir Kankiya ya fito ne, zan bashi saƙo"

"Saƙon me?"

"Ki jira zaki gani"

"Ko mu samu wuri ka zauna, saboda jikinka?"

"A'a bakomai, zan iya tsayawa"

Ba su wani ɗau lokaci ba, sai ga Kankiya ya fito fuskarsa babu annuri, ga wani gumi a goshinsa shi da TJ, aka yi sa'a kuwa su biyu ne kawai suka fito.

Yazid ya tari Kankiya ya ce "Sir kayi haƙuri a kan abin da ya faru, ni da a son raina ne, ba zan taɓa yin abin da zai ja maka ɓacin suna ba, sai dai ka sani duk wata halittar ubangiji da ke doron duniya duk talaucinta muninta, kayanta ko arzikinta, ko da kafiri ne Allah yana son halittarsa, ba kuma zai bar zalunci ba, ka tsangwameni ka takurawa rayuwata duk saboda Fadila. Dan Allah Sir idan har kana son Fadila da gaske kaje gidansu ka sami mahaifinta, ka cireni daga wanda ke barazana ga soyayyar ka, ni kawai na ɗauketa a matsayin'yar uwata da muke aji ɗaya. Fadila tana da komai na gata da jin daɗin rayuwa, Amma Bani da komai sai Allah sai karatuna, idan ka durƙusar da ilimina ka durƙusar da rayuwata baki ɗaya, in dai yanke alaƙata da Fadila zai sama maka nutsuwa na yanke duk wata alƙata da ita, zan mayar da hankalina a kan abin da ya kawoni, amma ka dubi Allah ka tausayawa maraya, ka bar ni in samu ilimin da na zo nema cikin kwanciyar hankali" yayi maganar tare da haɗa hannayensa biyu alamar magiya.
Daga haka ya juya ya fara tafiya, Fadila ji tayi kamar ta shaƙe Kankiya ta huta.

Jikin Fadila yayi sanyi, tabi bayan Yazid da kallo, ga wani irin tausayinsa da ya mamaye zuciyarta, ta mayar da kallonta ga Kankiya da ya ƙame a wurin, tayi masa wani mugun kallo ta bar wurin, a can harabar ajinsu suka tarar da ɗalibai a tsaye suna jiran su ji yadda ta kaya game da jarrabawar Yazid.
Yazid ya basu tabbacin cewa komai ya daidaita, na suka dinga yi masa son barka, tare da cewa Fadila ta cika ƙawa ta gari.
Sai dai bai tsaya wani abu ya kuma haɗashi da Fadilan ba ya bar Wurin.

Debate ɗin yau babu Amina a ciki, sai dai a quiz tayi participating, shima cikin ikon Allah makarantarsu Amina tayi nasa zuwa mataki na gaba.
Daddy har mamakin ƙwaƙwalwar Amina yake yi, ta burgeshi matuƙa gaya, a ransa yake jin ko nawa ne zai kashe ya kaita ko ina ne a faɗin duniya tayi karatu, ba zai taɓa barin wannan ƙwazo nata ya tafi a banza ba.

Ana tashi daga quiz ɗin wurin Daddy ta nufa, kan ta ƙaraso ya fara tafa mata, sai da ta rufe fuskarta tana murmushi.

"Gaskiya kin birgeni, ban san yadda zan misalta miki fatincikin da na shiga ba, Allah ya ƙara hazaƙa Allah ya baku nasara"

"Amin Daddy, duk wata nasara dana samu a harkar karatuna, ba zan taɓa mantawa da gudumuwarka ba, Allah ya biya maka buƙatunka na alkhairi ya kula da zuriyarka, sai da na zubda hawaye a lokacin da naji nawa kake kashewa a kan harkar karatuna, bani da bakin....

"Ya isa haka, zo mu tafi ai kun gama" ya katseta ba tare da ta gama maganar ba.

"Wai Daddy duk lokacin da ka yi mini abu ba zaka barni nayi maka godiya ba, bana jin daɗin hana.

Ƙiri ƙiri ya basar da zancen ya ce "mu tafi ko" ba yadda ta iya haka tayi shiru ta fito suka tafi.



Gaba ɗaya jiki babu ƙwari haka Fadila ta koma gida, haka nan ta rasa abun da yake mata daɗi.
Ba dan tana jin daɗin komai ba, tayi wanka ta ci Abinci ta fara karatunta.

Wajen ƙarfe biyar na yamma sai ga Mummy ta dawo, ta tarar da Fadila tana zaune tana duba litafinta.

"Ashe kin dawo"

Fadila ta ce "Eh na dawo, ai exams muke a school"

"Yayi kyau, ke Albishirinki?"

Fadila ta ɗan kallk Mummy sannan ta ce "Mummy duk wannan fara'ar ta mecece?"

"Ke dai ki amsa mana, ai dole kiga farinciki a fuskata"

Fadila ta rufe littafin, ta tattara dukkan nutsuwarta a kan Mummy ta ce "Goro"

"Ina kyautata zaton, na kusa yin sirukai very soon, na yiwa Daddynku maganar Kursum, ya ce mini in bari mu dawo daga umara, zai zauna da mahaifinta, and finally ɗa gidan Hajiya Salma yana iya dawowa a kowane lokaci, dan yana ta bada saƙon gaisuwa a baki, da ya takura ma a bashi lambarki amma ta hana, ta ce kar ya ɗauke miki hankali kina karatu ne yanzu, ya bari ya dawo tukuna, dan har ta yiwa mahaifinsa magana"

Fadila gaba ɗaya zancen bai mata ba, ta ce "Ohhh my Goodness, yanzu a kan wannn maganar ne kike ta wannan murnar for God sake, Mummy ko ganinsa fa ban taɓa yi ba, har ya yiwa babansa magana, dan Allah a ajiye wannan maganar aside"

Ɗan tsuke fuska Hajiya Zainab ta yi ta ce "Ban gane a ajiye maganar nan aside ba, am trying to make your tomorrow better ke da ɗan uwanki, yadda ko bayan ba ranmu na san na kafaku abokan rayuwarku ba zasu zame muku liability ba, ba ruwansu da abin da kuka mallaka, ta nuna mini hoton yaron ba shi da wani aibu, kuma already yana da sana'arsa a can in da yake karatu, idan kun yi aure can zaku tafi gaba ɗaya"

Tura baki Fadila tayi ta ce 'Ni gaskiya Mummy am not going anywhere, karatuna fa?"

"To karatun dama ba a waje muke yi burin kiyi ba, amma mahaifinki ya hana ba yanzu ga dama ta samu, ba sai kije ki cigaba da karatun a can ba"

Sake tura baki Fadila tayi tana noƙe kafaɗa, dan tun bata ga gayen ba taji lamarin bai yi mata ba sam.

Mummy ta kwantar da murya ta ce "Haba autar, am sure you will like that guy, yaron yana da hankali ba zaki shiga wahala ba zaki huta sosai, Please don't disappoint your mum, na san type ɗin mijin da kike so, I know you are classic that's why I chose him for you"

Fadila ta tashi tsaye ta ɗau littafinta ta ce "Mummy, we should discuss it later, let me first concentrate on this one" tayi maganar tana nuna wa Mummy littafin hannunta.

"Ok dear, good luck"

Fadila ta amsa da thank you ta bar wurin.





"Minister" Amina ta faɗa tana leƙa fuskar Daddy, dan taga reaction ɗinsa.
Shareta yayi ya cigaba da kallon tagar mota.

"Minister am talking fa"

"Kinga ki kiyayeni tom"

Murmushi tayi ta ce "Ka san me nake sha'awar ci kuwa?"

"A'a, ki faɗi ko meye kan mu isa gida sai mu tsaya a nema a hanya"

"A'a ni ba na sayarwa ba, wainar fulawa zan soya in ci"

Ya waiwayo ya kalleta ya ce "Ina kika ga kayan wainar fulawa a gidan?"

"Ban gansu ba amma sai a nemo"

Daddy ya ɗan ƙura mata ido ya ce "Ni ne zan nemo"?

"A'a ni na isa in ce haka, wace ni ranka ya daɗe, dan Allah ka saka a samo mini kayan yi, ni zan yi da kaina"

"Sai dai a ajiye ki, ke kije ki nemo"

"Idan na ɓata fa, ko wanan karnukan suka cinyeni a hanya"

Ya kasingiɗa da jikin seat ya ce "Da na huta kwana biyu, da yawan surutunki da rigimar tsiya"

Ta ɗan marairaice ta ce "Kenan takura maka nake"

"Eh to ba nace ba, surutunki bai fiye takura mini ba, kamar gaddama da rigimar rashin dalili"

"To ka saka a mayar da ni in da ka ɗauko ni tun da haka ne"

"As you wish, bari in yiwa direban magana ya sauke ki sai in ɗoraki a babur ki tafi"

Kwaɓe fuska tayi zata yi kuka ta ce "Au yanzu da gaske takura maka nake yi, kuma sai ka mayar da ni?"

Dariya yayi ya ce "Ji mini yarinya da rikicin gangan, ke fa kika ce na mayar da ke in da na sa aka ɗauko ki"

"To ni ba in da zan koma" ta faɗa tana haɗe rai tare da gyara zamanta.

"Haba Meenalin, meye na fushin kuma? Za a nemo kayan wainar fulawa idan ma cewa ki kayi in soya miki, sai in ɗaura zani in soya miki"

Dariya ce ta ƙwace mata ba tare da ta shirya hakan ba, ta ce "Wa yaga Daddy na soya wainar fulawa, da sai na maka hoto a haka" Dariyar ta ta kawai yake kallo, gwanin burgewa kamar kar ta daina.

Ya gyara zamansa ya ce "Kin san gidan ne tun da ba zama nake a cikinsa ba, ba bu kayan masarufi a ciki, tun lokacin da na riƙe muƙami a gwamnatin baya aka bani shi, idan ba na shigo Abuja ba bana zama a cikin sa, na cewa Khalil ya zauna a ciki, ya ce yayi masa nisa da wurin aikinsa, sai mun zo hutu kawai muke zama".

"Gidan me kyau kuwa, to a can Lagos ɗin ma kana da gida?"

Ya ɗaga mata gira alamar eh.

"Mmm lallai Daddy, kana jin daɗinka, ka dinga sawa ana Abincin sadaka kana rabawa mabuƙata, ka godewa Allah, Allah bai jarrabeka da tashin hankalin rashin muhalli ba" tayi maganar tana duba wayarta, ba da wani serious tayi maganar ba, amma maganar yaji ta shigeshi sosai.

Har ta manta da tayi maganar sai kuma ta ɗora da cewa "Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya ce 'Dukiyar me bayarwa bata taɓa tawaya saboda yana bayarwa. Ka lura a duk lokacin da ka yayewa wani damuwa, sai kafi wanda ka yiwan shiga farinciki, kyauta akwai daɗi, ka bawa mutum abu kaga yana murna, saifa ka gama shekarunka kana salla ba a karɓa, amma cikin rahamar ubangiji a sanadiyyar faranta ran bawansa ɗaya, sai ya yafe maka, ai shi Allah gafuru rahim ne"

"Haka ne sayyadata, shi yasa bana manta lokacin da kika mini kyautar fura da Nono da zan yi tafiya, tun daga lokacin kika ƙara kima a idona"

Tayi murmushi ta ce "Allah ya ƙara arziki, ka ci kaita bayarwa"

"Ameen ya Allah"

"Daddy na ji kace Khalil a garin nan yake aiki, ba zaka je ka ganshi ba, naga ha daɗe bai je gida ba"

"Aikuwa Yakamata in je ɗin, dan ya daɗe yana magiyar in je in ga gininsa, amma Allah bai sa na shigo Abuja ba, bari in kira wayarsa in ji, idan yana nan anjima sai in je"

Amina ta gyaɗa kai, Daddy kuma ya nemi wayar Khalil ya kira.

Sai da ga kusa yankewa sannan ya ɗaga, cikin numfarfashi yayi sallama.

"Khalil, lafiya kuwa naji kana numfashi da kyar?"

"Lafiya lau Daddy, bana jin daɗi ne kawai"

"Subhanallah, meke damunka?"

"Nima ban sani ba, ji nake dai kamar zuciyata ce take ciwo, bana iya numfashi sosai"

A rikice Daddy ya ce "Kana wane Asibitin?"

"Ina quarters ni banje Asibiti ba"

Daddy ya katse kiran yana mita "Wannan wane irin shahsahnci ne, ya zauna a gida yana fama da ciwo, yi sauri muje mu ajiyeta, mu wuce can wurin Khalil ɗin" yayi maganar cikin damuwa.

"Daddy ka kwantar da hankalinka, Allah ya bashi lafiya, ni ka sani a napep a kaini gidan"

Ya girgiza kai ya ce "No, muje a kai ki tukuna"

Amina ta ɗan ƙura masa ido sannan a ranta ta ce "let me see if I can do something, Hajiya Zainab Gaba akwai gabanta"



AYSHERCOOL
0808102143GABA DA GABANTA
               BY
AISHA ADAM AYSHERCOOL


49

Sake kallon Daddy Amina tayi, taga yadda damuwa ta mamaye ilahirin annurin da yake ci da, ta ɗan yi ƙasa da muryarta ta kira sunansa "Daddy"

Ya waiwayo ya kalleta, ba tare da ya amsa mata ba.

"Dan Allah ka kwantar da hankalinka, in sha Allah yana nan lafiya, naga duk ka shiga damuwa"

Ya ɗan sake kallonta ya ce "Yanzu har damuwa ta bayyana a fuskata?"

"Eh mana, ga damuwa nan kwance a fuskarka ina gani"

Ya ɗan shafi fuskarsa ya ce "Dole in damu, yanzu kamar Khalil da girmansa da komai, ba shi da lafiya amma ya kasa zuwa Asibiti, kuma ya ƙi gayawa kowa haka ake yi, idan ya cutar da rayuwarsa fa, wannan ai shirme ne"

"Haka ne, amma ka kwantar da hankalinka, ka fara jin ta bakinsa kafin ka yanke masa hukunci, ka bi komai a hankali ka gano kan rashin lafiyar ta sa, akwai malaminmu da ya gaya mana, akwai cututtukan da sukan faru da basu da alaƙa da magani, nutsuwa da kwanciyar hankali kawai mara lafiyan yake buƙata"

Daddy ya gyɗa kai ya ce "Haka ne"

"Yauwa dan haka dan Allah ka kwantar da hankalinka, idan kaje kar kayi masa faɗa, sannan kuma ka ɓoye wannan damuwar da ke fuskarsa kar ka sa ya karaya, kuma kaga kai ma baka da cikakkiyar lafiya"

Kallon Amina yake yi, 'yar ƙarama sai hikima, tana ta ƙoƙarin taga ta kawar da tasa damuwar.

Ya ɗan ja numfashi ya sauke ya ce "To shikenan, na gode sosai"

Hakan yayi daidai da tsayuwar motar a ƙofar gidansa, har zata sauka ya ce "Ki rubuta duk abin da kike buƙata, ki bawa Joseph, zai sayo miki"

"To wanne ne Joseph ɗin?"

"Dogon mai suma"

Amina ta jinjina kai ta fice daga motar.

Kai tsaye quarters ɗin Khalil yake su Daddy suka nufa, suna zuwa Daddy ya tarar da wani abokin aikin Khalil ɗin tare da shi.
Khalil ya rame yayi baƙi, cikin girmamawa abokin Khalil ɗin ya gaida Daddy, Daddy ya amsa masa sannan ya mayar da dubansa kan Khalil ya ce "ya aka yi ka zauna haka ba ka je Asibiti ba?"

"Daddy naje, idan na sha maganin bana jin komai, shi ya sa na daina zuwa"

A fusace Daddy ya kalleshi ya ce "Kuma saboda shirme, da rashin sanin ciwon kai ka kasa kirana ko mahaifiyarka ka sanar mana, kawai kayi zamanka kana fama da ciwo, da sa dai ace mini in zo in ɗau gawarka? To idan kai baka buƙatar rayuwarka ni ina buƙata, ku kenan ku biyu Allah ya bani ka zana kana wasa da lafiyarka, tashi mu tafi ni muje Asibiti"

Khalil wani irin jiri yake fama, da ƙyar ya iya miƙewa tsaye, ƙarshe sai sa shi aka yi a mota, suka tafi Asibiti.
Suna zuwa aka yi masa gwaje-gwaje aka tabattar da jininsa ne yayi ƙasa sosai Hypotension, haka sugansa ma saboda rashin cin abinci.

Nan da nan likitoci suka yi ta kai kawo a kan Khalil, ana saka masa ruwa da allurai, sai ga shi ya ɗan farfaɗo har yana iya zama da kansa, Daddy da kansa yaje ya nemowa Khalil Abinci, ya zauna ya sa shi a gaba, yana zare masa ido ya ci, kamar wani ƙaramin yaro (Iyaye masu daɗi, Allah ya ƙarawa iyayenmu lafiya da nisan kwana, wanda suka rasu kuma Allah ya yi musu rahama)

Sai da ya tabbatar Khalil ya ƙoshi, har ya iya shiga banɗaki yayi alwala ya dawo ya yi salla.
Daddy ya cigaba da yi masa faɗa.
"Ni ban san ma dalilin da yasa ko gida da kake zuwa ƙarshen wata ka daina ba? Gaba ɗaya ka ɗauko wasu sabbin ɗabi'u, nema ma kake ka cire kanka daga cikinmu, mahaifiyarka na ta complain a kan ko kiranta baka yi a waya"

Kamar Khalil zai kuka ya ce "Daddy ya zan yi, ko na kirata a waya sai ta nemo abin da za tayi mini faɗa, ta rabani da yarinyar da nake so, wai yanzu wata zata aura mini"

"To sai me, a kan hakan kake nema ka kashe kanka? Ba zaka yi mata biyayya ba, naga dai ba zata zaɓi abin da zai cutar da kai ba" Shiru Khalil yayi Daddy ya cugaba da banbanminsa, dama ya san Daddyn ba zai goyi bayansa ba, duk abin da Mummy ta shirya masa shi kawai yake aiwatarwa.
Sai bayan sha ɗayan dare aka sallami Khalil, a kan sharaɗin, zai koma washegari ya sake ganin likita.

Daddy bai koma gida ba sai sha biyu saura na dare, abin mamaki yana zuwa ya tarar da Amina a falo ba tayi bacci ba tana jiranshi.

Da sauri ta tashi tana masa sannu da zuwa.

"Ya aka yi baki kwanta ba?"

"Ai kona kwanta ba zan iya bacci ba, baka dawo ba kuma ban san a wane hali Khalil ɗin yake ba, nayi ta ƙoƙarin kiranka a waya, amma bani da network gaba ɗaya"

"Jikinsa da sauƙi sosai, na mayar da shi gida ma sun sallemshi daga Asibitin".

"Allah ya bashi lafiya, kaje ka kintsa ka zo ga Abinci na maka"

Ya kalli inda ta nuna masa fulasan abinci ya ce "A ina aka samu Abinci?"

Ta ce "Sautun kayan wainar fulawata nayi da kuma abin da zan dafa maka, ga tuwon Alkama nan da miyar kuɓewa sai kuma Coffee, sai kuma Fruit ka ci duk wanda kake so"
Lumshe ido yayi, Amina duk ta gama sanin abubuwan da yake so, da kuma lokacin da yake son su.
Ya ɗan buɗe idonsa ya ce "Me zance miki ne Meenalina? Allah ya saka miki da alkhairi, idan kin yi Aure ya baki ikon yiwa mijinki biyayya"

"Yaushe zan yi Auren bayan ka hanani yin saurayi" Murmushi yayi yayi gaba, dan baya son ta ƙaƙalo rigima, ya shiga ɗakinsa yayi wanka ya canza kaya, ya fito ya sake tarar da ita a zaune tana jiransa.

Sai dai kallo ɗaya tayi masa ta ɗauke kanta, kasancewar dogon wando ne a jikinsa sai shirt baƙa. Yana ankare da ita amma ya basar ya kunna Tv sannan ya zauna ya ce "Yauwa serve me"
Kamar mara gaskiya haka ta sunkuyar da kai tana zuba masa Abincin, cikin son kawar mata da yanayin da ta shiga, ya fara bata labarin irin sakarcin da Khalil ya yi.

Ta kalleshi ta ce "Yanzu ba shi da lafiyan kayi masa faɗa?"

"Ba dole in masa ba, kin ga yadda yaron nan ya koma kuwa?"

"Hmm, to ka tambaye shi meyake damunsa?"

"Shiritarsa ce dai, wai babarsa ta hana shi auren wata wadda zata aura masa daban"

"Eh ai da gaskiyarsa, gaskiya yakamata kayi wani abu a kai"

Ya ce "Me zan yi a kai?"

"Ka duba abin da yake so kayi masa idan har bai saɓawa Shari'a ba, ba ita kaɗai take da haƙƙi a kansa ba, yakamata a ce...."

Kan ta ƙarasa maganar ya ce " Ɗan ki ne ko ɗanta? Ta fiki sanin ne ya dace shi, haryanzu yaro ne bai san meye ya dace da shi ba"

Sak Amina tayi tare da yin shiru, ba ƙaramin ɓata mata rai maganar ta sa tayi ba, ta ɗan jinjina kai ta ce "Haka ne, ɗanku ne bai kamata in dinga shishshigi a kan abin da bai shafeni ba, amma idan ka cigaba a haka watarana zaka ga abin da ba ka so a gidanka" ta tashi fuskarta ɗauke da ɓacin rai ta bar falon.

Dan haushi tana zuwa ɗakinta, ta haye gado, ta ja bargo tana jin yadda zuciyarta tayi mata babu daɗi da abin da Daddy yayi mata.

Sam bacci ya kasa ziyartar idanunta, tana ta saƙawa da warwarewa, ji tayi an turo ƙofar ɗakin, sake dunƙulewa tayi cikin tsoro, dan bata san waye ya shigo ba.
A hankali ya tako ya ƙaraso gaban gadon, ya sanya hannu zai janye bargon, ta riƙe bargon gam tare da sakin ihu, da sai da ta ɗan razana shi.

"Ke lafiyarki kuwa?"

"Meyasa zaka zo mini ɗaki yanzu ka yaye mini bargo, ka san a halin da nake?" Tayi maganar da iya gaskiyarta.

Ya ce "Haka ne, ban kyauta ba, tashi muyi magana".

"Ni ba wata magana da zamu yi, bacci zan yi".

"Idan baki tashi ba zan yaye bargon, and I mean it"

Buɗe ido tayi ta ce "To ɗauko mini hijjabina gashi can a ninke"

Kallonta yai ya ce "Are You commanding me?"

"Idan baka ɗauko mini na saka ba, zan yi kwanciyata"

"Ok shikenan, bari in yaye bargon in ɗauko

Please Login or Register in order to submit comment