Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

raka, zamu je harkar wani business ne"

Cikin mamaki Fadila ta ce "Sirikata kuma? Wacece sirikata?"

Mummy tayi murmushi ta ce "Hajiya Salma mana, ni mana manta ban gaya miki ba fa, iyayen Salim sun zo sun yi magana da babanki, ya ce ya basu kuɗi kawai zasu kawo a saka rana".

Saroro Fadila tayi tana kallon Hajiya Zainab, ta ce "Mummy yaya za a ba dani ga mutumin da duk abin nan da ake yi ko ganinsa ban taɓa yi ba"

Mummy ta dafa kafaɗar Amina ta ce "kar ki damu, an tura masa lambarki, za kuyi magana, ai na san ba zaki bani kunya ba, shi ya ce kin masa ai, bari in tafi kar suyi ta jirana, idan na samu dawowa a yau shikenan, idan ban samu ba, sai dai mun yi waya" ta ɗau jakarta ta nufi hanyar fita, ta bar Fadla da wani yanayi da ta kasa gane kanta, takaici ne ko mamaki.



Amina tana cikin bacci, tayi mafarkin wata baƙar mage, ta biyota, tana ta gudu tana kiran sunan Allah, amma duk da haka magen tayi tsalle ta kafa haƙoranta a cikin Amina.


"Innalillahi wa innalillahi raji'un, Daddy ka taimakeni" Daddy da yake banɗaki yana wanka, kansa yayi wata irin sarawa, sai da ya dafa bango, da ƙyar ya iya lalubar towel ya ɗaura ya fito.
A gigice ya ƙarasa gadon da Amina take, wanda gaba ɗaya ya wanke da jini, ga jikinta sai rawa yake, kan ya ƙarasa in da take yaji jiri yana neman kayar da shi.


WANDA KUKE FITAR MINI DA BOOK, NA GODE SOSAI 🙏 ALLAH YA NA KALLONMU DUKA, DAN BA MUYI HAKA DA KU BA.

AYSHERCOOL
08081012143NA KUƊI NE ₦500 VIA 0009450228
AISHA ADAM JAIZ BANK
SAI EVIDENCE OF PAYMENT TA
08081012143

68

Dafe kai Daddy yayi, ya ɗan jingina da bango, yana kallon Amina, yana kallon yadda jikinta ke ta karkarwa, 'yar rigar baccin jikinta, duk ta ɓaci da jini, farin bedsheet ɗin da ke kan gadon shima yayi kaca kaca da jinin.

Da ƙyar Daddy ya ja jikinsa, kansa na cigaba da sarawa.

A hankali ya furta "Meenal"

Yayi maganar yana ƙarasawa in da take kwance. Ƙanƙame shi tayi tana kuna, jikinta na cigaba da rawa.

"Meenal meyasameki haka?"

"Daddy tsoro nake ji"

"Tsoron me?"

Muryarta na rawa ta ce "Wata mage ce take cizona"

Bai damu da yadda ta ɓata shi da jini ba, ya sake ƙanƙameta ya ce "Meenal ba wata mage a wurin nan"

"Kayi mini Addu'a, zafi nake ji sosai"

Ya jinajina mata kai, amma ya kasa furta komai da sunan Addu'a, sai kansa da yake ta juayawa, yaga komai na juya masa, suka sake ƙanƙame juna, ji take kamar numfashin ta zai ɗauke, mararta kamr zata haifi dutse haka take jinta.

Amina ce tayi ƙarfin halin fara karanta Adduoi a zuciyarta, a hankali kuma ta fara furtawa a kan harshenta.
Sun daɗe a haka, kan daga bisani su ji su tamkar wanda suka farka daga barci.

Jin kan ya ɗan lafa masa ya sanya ya ɗan ɗaga Amina daga jikinsa, idanunta duk sun yi wani iri saboda kukan da tayi.

"Ya jikin naki?"

Tayi ajiyar zuciya ta ce "Da sauƙi"

"Bari in taimaka miki ki gyara, sai mu tafi Asibiti"

Daddy har tausayi ya bata, saboda yadda shi ma yake fama da kansa, amma sai kaiwa yake yana komowa, da kansa ya wanketa tsaf, ya gyara bedroom ɗin.

Duk da jikinsa babu daɗi, haka ya saka Amina a gaba suka tafi Asibiti, Daddy yayi mamaki da aka gwada sigansa da jininsa duk lafiya lau, duk sauran teses ma da aka yi masa komai ya nuna lafiya lau.
Sai dai babban abin da ya tayar masa da hankali, bai wuce yadda aka sake tabattar masa da cewar Amina ta sake samun ɓarin juna biyu ba. Shi baya sanin da cikin sai dai yaji ɓari, ji yayi kamar yayi kuka, saboda yana daga abin da yake buri shi ne samun yara.

Ɗakin da take kwance ya shiga, ya tarar da ita da drip a hannunta, ta ƙurawa wuri ɗaya ido.
Sallamarsa ce ta dawo da ita daga tunanin da take yi. Ya ƙarasa ya zauna a kusa da ita, ya riƙo hannunta a cikin nasa ya ce "Sannu Meenal"

"Yauwa Daddy, ya jikin naka? Ina fatan ba wata matsala?"

Ya jinjina mata kai ya ce "Eh, sun duba komai normal, amma sun gaya miki meyafaru da ke?"

"Eh sun gaya mini, wai na kuma samun abortion ko?"

Cikin tausayawa ya ce "Eh haka ne, amma kiyi haƙuri ki kwantar da hankalinki"

Ta yi murmushin ƙarfin hali ta ce "Daddy, ai bakomai Allahn da ya bani shi ya karɓa, duk na san ina son na haifi abin da ke cikin, amma Allah ya san dalilin da ya sa suke zubewa"

"Haka ne Meenal, amma Meyasa baki gaya mini kina da juna biyu ba?"

Ta ɗan gyara kwanciyarta ta ce "Nima ban san akwai ba, tunda nayi wancan ɓarin, ban sake period ba, ban san ina da wani cikin ba"

Ya shafa kanta ya ce "Shikenan, Allah ya bamu mai amfani, ina ga zamu ɗan ƙara kwanaki kan mu koma Nigeria, sannan ina son idan mun koma muje kiga ƙwararen likitan mata"

"Amma meyasa zamu ƙara zama a nan, kaga a gida baka gaya mata ba"

"Amina, bana son damuwa ne, na shafe shekaru ina karatu, neman kuɗi, kula da iyali da suaran hidindumu ina buƙatar hutu ƙwarai da gaske, yanzu muna komawa gidan, ba zata sauya zani ba, zata cigaba da tayar mini da hankali ne kawa, dan haka ki barmu mu huta sosai ma koma, kinga kya ga likitan matan ma a nan kawai"

Haka Amina ta haƙura ta ƙyaleshi. Duk gwaje-gwaje da yakamata an yiwa Amina, babu wata matsala da ta nuna cewar ita ke haddasa mata ɓari, a ka sallameta aka bata magunguna suka koma gida.

Ita kanta Amina tayi mamakin yadda aka yi hakantake faruwa, cikin farko dai ta san faɗuwar da tayi ne, na biyun nan kuma daga wannan mafarki ta tashi ta ganta cikin jini.
'ko dai aljanu ne zasu shafeni, dan amce suna saka mutum ɓari?' tayi wa kanta tambayar a zuciyarta.
Da sauri ta kawar da tunanin ta bawa kanta amsa da ai tana azkar, dan haka babu abin da zai sameta sai abin da Allah ya ƙaddara mata.

Kwanaki biyu a tsakani suka ware, suka cigaba da shan soyayya ita da Daddy, ta mayar da shi tamkar ƙaramin yaro daidai ita, yayi ta biyewa shirirtarta, yawo kuwa wuri wuri hake suk tafiya, wataran suyi tseren keke, da makamantansu wanda hakan ya ke ƙara musu kusanci da kuma ƙaunar junansu.


A gida kuwa Hajiya Zainab taje ta kuma karɓo wasu asirin, gaba ɗaya hankalinta baya kan Khalil yanzu burinta shine ta wargaza auren Daddy. Sai dai ta jefa Fadila ma a cikin cakwakiya, dan tunda tayi mata zancen za a kawo kuɗin aurenta da mutumin da bata sani ba, ga shiga tashin hankali, dan sam bata jin ƙaunar abin a ranta.
Kamar yadda Mummy ta gaya mata, sun bawa Salim lambar wayarta, dan har ma yayi mata magana ta what's app, amma yaƙi tura mata hotonsa, gaba ɗaya sam a tsarin yanayin kalamansa ma bata ji yayi mata ba, hakan ba ƙaramin jefata yayi a damuwa ba.

Mummy ta sakata a gaba, tana ta tsara mata yadda zata shiryawa bikinta, domin daga shi ta san ba zata kuma aurar da ɗa ba, amma taga gaba ɗaya Fadilan ta ɓata rai.

"Fadila, wai meyake damunki ne?"

Kamar ta taɓo wa Fadila in da yake mata ƙaiƙayi ta ce "Ni wallahi Mummy bana son auren nan, dan Allah ki barni in cigaba da karatuna kawai"

Mummy ta ce "Haba Fadila, so kike na mutu banga jikokina ba, meye aibun kiyi auren yanzu ki cigaba da karatun naki a gidansa?"

"Ni Mummy auren ne bana so, dan Allah kawai a bar maganar nan"

"To yanzu Fadila so kike naje na samu Hajiya Salma nace mata ba kya son auren, bayan an riga anyi magana? Ki duba kiga abin da babanki da yayanki suka yi mini, kema watsa mini ƙasa a ido zaki yi kenan? Duk cikinku babu wanda zan raɓa naji daɗi, hankalina ya kwanata kenan?"
Ganin yadda gaba ɗaya mood ɗin Mummy ya sauya ne, ya sanya Fadila a sanyaye ta ce 'Mumny kiyi haƙuri dan Allah, ba haka bane ba, shikenan naji na haƙura zan aure shi in dai zaki ji daɗi".

"Yauwa 'yar autata, ai na san ke ba zaki bani kunya ba, ba zaki zuba mini ƙasa a ido ba, Allah yayi miki albarka, shi kuma ɗan uwanki shi ma ina nan ina faɗi tashi, dan ba za ayi auren nan ba"

Fadila dai bata sake iya cewa komai ba, ta tashi ta koma ɗakinta, ji tayi kamar ta saka hannu a ka ta kurma ihu, saboda amsawa Mummyn da tayi zata auri Salim, alhalin har ga Allah ita bai yi mata ba sam.

Gaba ɗaya yanayin da take ciki ya nemi ya shafi karatunta, sam bata mayar da hankali, ɗan karatun da take ƙoƙarin yi ma ta kasa, da ta fara sai tunani, Yazid yana ankare da ita, sai dai baya son yawan shiga sabgarta tana yarfa shi, amma kowa ya kallta ya san akwai damuwa a tare da ita.

Ɓangaren Maman Hafsa kuwa, tana ɗan shirninta, da ba a rasa ba, duk da an ɗauke musu kayan ɗaki, amma hankalinta ya kasa kwanciya, saboda bata ajiye ba, ba kuma ta bawa wani ajiya ba. Dama ta san dangin mahaifin Hafsa babu uwar da zasu tsinana musu, mutanen da suka ƙi karɓar kuɗin aurenta, suka dinga ɓata ta a wurin sirikinta, yaushe za a sanya ran zasu yi musu wani abu.
Ga unguwa ta ɗauka, wai Liman ne ya karɓi kuɗin auren Hafsa, sa ƙanan maganganu suke yi, wai anya ma kuwa tana da uba, 'yar halak ce, dan idan da dagaske mahaifinta rasuwa yayi, ba za a rasa danginsa da zasu karɓi kuɗin Aurenta ba.
Wasu abubuwan ma dai, Hafsan ce take kwantarwa da Maman hankali a kan wasu abubuwan.

Khalil kuwa ya zage sai faman ƙoƙarin hattama gininsa yake da kayan lefe, dama gini ne ya ɗauko shi na manya, dan haka sai fama yake yi, 'yan uwan Daddy da abokanansa sai bashi gudunmuwa suke yi. Shi da Abdul suke tsara komai, kayan lefe dama Hajiya Maryam yake turawa kuɗin tana saya wa Hafsa, idan ya tambayeta me take so ayi mata a gidanta, ko na lefe sai ta ce masa ita komai ya sakamata ta gode, juyin duniya Hafsa ba zata taɓa ce masa ga abin da take so ba.
Akwai abubuwa da yake buƙatar shawarar Hajiya Zainab, amma ba halin ya tuntuɓeta, ko kiranta a waya baya iya yi, saboda yana tsoron abin da ka iya haifarwa. Aikuwa hakan ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba, ga Daddy da ya ce zai yi kwana goma ya shuɗa, ko nemanta a waya baya yi, shima Khalil ɗin haka.
Da kanta ta kira Khalil a waya, yana ganin wayarta ya shiga cikin tashin hankali, dan bai san dalilin kiran ba.

Aikuwa kamar ya sani, dan yana ɗagawa ta dira masa bala'i.

"Khalil ka zama ɗan kanka ko? Gaba ɗaya ka mayar da ni a bar banza, bani da wata kima a idonka, bani da mutunci saboda ubanka ya goya maka baya ka auri 'yar matsiyata, to duk abin da kake ka ajiye ka dawo gida ina son ganin ka"

A ɗan rikice  Khalil ya ce "Mummy, aiki yayi yawa a nan, sai na nemi excuse tukuna"

"Ba ruwana da wani excuse, kai ta shafa, ka dawo mini gida, ina son ganinka"

Jiki a sanyaye ya ce "To shikenan, zan dawo in sha Allah"

Tayi tsaki ta kashe wayarta.

Alhaji Ahmad dai sai da ya shafe sati uku shi da Amina, daga kwana goma, sannan suka yi shirin dawowa Nigeria, tunda suka fara shirin tahowa Nigeria, Daddy ya shiga cikin damuwa, saboda ya san da sun dawo zai cigaba da fuskantar tashin hankali daga Hajiya Zainab.

Amina ta lura da yanayin da Alhaji Ahmad yake ciki, kuma ta san bai wuce a kan Hajiya Zainab bane ba, ba ta fiye son yi masa shishshigi a kan abinda ya shafe shi da Hajiya Zainab ba.

Haka suka gama shirinsu, suka koma Nigeria.
Ko da suka sauka, gidan babu kowa, Fadila tana makaranta, Hajiya Zainab ta tafi nata gantali.

Hajara ce ta tari su Amina, cikin murna da sakin fuska, nan da nan ta shiga Kitchen, ta fara ƙoƙarin dafa musu Abinci.

Amina ta fito falo, ba laifi ko ina a gyare, Hajara tana ƙoƙarin kulawa da komai.
Daddy kwanciya yayi a sashin Amina yana bacci, dan ya samu ya ɗan huta.

Tun wajen sha biyu na rana suka dawo, Zakiru ya ɗauko su a airport, amma har biyar Hajiya Zainab bata dawo ba.
Daddy ya shirya zai ɗan fita, Amina na falo, tana ɗan cin abinci, hakan yayi daidai da shigowar Fadila falon daga makaranta.
Tana ganin Amina a zaune a falo, ta kalli Amina, ta ja wani uban tsaki, da ba tayi ma tsammanin ganin Aminan ba, dan basu san da daowarsu yau ba.

"Ke Fadila" taji Muryar Daddy ya kira sunanta.

Tsayawa tayi cak ta waiwayo, Daddy ya kalleta ya ce "Wa kike yiwa tsaki?"

Fadila tayi shiru ba tace komai ba.

"Da ke nake wa kike yiwa tsaki?" Yayi maganar a kausashe.

Ta ɗan razana ta ce "Daddy ba kowa"

"Ai naga abin da kika yi, me tayi miki? Kawai kin shigo kin tarar da ita a zaune, ke baki mata sannu da zuwa ba kawai kin yi mata tsaki. Fadila ki kiyayeni fa, idan kika wulaƙanta Amina tamkar ni kika wulaƙanta, tunda ni na aureta na ajiyeta, ba ita ta ajiye kanta ba, dan haka ki kiyayeni, bata haƙuri" wani abu ne ya soki ƙirjin Fadila, wannan 'yar yarinyar ƙanwar ƙanwar bayanta za a kalla ace ta bata haƙuri?.

"Ba magana nake miki ba?"

"Kiyi haƙuri" Fadila ta faɗa a taƙaice.

"Allah ya ƙara nuna mini kin mata tsaki ko makamancin haka, idan ba zaki mutunta ba to ban lamunci ki shiga sabgarta ba, balle ki ci mata mutunci, na sani mahaifiyarki ke zigaki, amma idan na tattara na aurar da ke, na yiwa tufkar hanci, da sun kawo kuɗin Aure ni ba zan saka lokaci mai tsawo ba, na gaji da halinku"

Kasa ɗaga ƙafafuwanta Fadila tayi, jin yayi batun aurar da ita, ga kuma furucinsa na ƙarshe, wai ya gaji da halinsu, duk tarin soyayya da tattali na Daddy a garesu, yau a saboda yayi aure yake musu wannan cin kashin.
Da ƙyar ta ja ƙafarta, ta nufi sashinta tuni hawaye ya wanke mata fuska.

Amina kuwa cewa tayi, Baby a dawo lafiya.

"Yauwa Meenal, Allah ya sa"

Bayan fitar Daddy, ita ma sallar tayi, ta dawo ta ɗan kunna turaren wuta a falon.

Kamar daga sama sai ga Hajiya Zainab, kamar an korota, Amina ta ɗago kai ta kalli Hajiya Zainab, ta ɗauke kanta ta cigaba da ƙoƙarin kunna Tv.

"Baƙar munafuka, na kusa kawo ƙarshenki" Mamaki ne ya kama Amin, ba ko sallama kawai ta fara maganar zata kawo ƙarshenta"

"Ni bani da lokacinki, an barwa karnuka faɗa" Amina tayi maganar a hankali, tana cigaba da aikinta.

"Ni kike cewa karya?"

Ta miƙa hannu zata janyo Amina, Amina tayi maza ta kauce ta ce "Karki kuskura ki kai hannunki jikina, ba ruwanki da ni, ba fa tsoronki nake ji ba da nake yi miki shiru, wallahi kika dakeni sai na rama"

"Bari na dakekin, naga uban abin da zaki iya, 'yar matsiyata wadda basu gaji arziƙi ba"

Amina ta ce "Daɗinta dai mai faskare bai isa ya nunawa maigadi arziƙi ba, idan har maigadi matsiyaci ne ban san me za a kira mai faskare ba"

Kan Amina ta kuma yi a fusace, zata daketa Amina ta kuma sake ja da baya, sai surfa uwar ashariya take kamar bamagujiya.
Fadila ce ta fito, bata san Mummy ta dawo ba, sai ganinta tayi a falo tana zage zage tayi kan Amina.

Da sauri ta ƙarasa in da Mummy take ta riƙeta, tana faɗin "Mummy dan Allah ki bari"

"Ƙyaleni, ki rabu da ni in ci ubanta, ni zata kalla ta zagi ubana?"

"A'a fa, ni ban zageki ba, ba faskaren ne sana'ar babanki ba?"

Cikin tsawa Fadila ta ce "Ke Amina, karki kuskura ki zagar mini uwa, ki shiga hankalinki"

Amina ta ce "Babarki zaki gayawa ta iya kanta, kar ta kuma zagina, sannan ke kuma karki sake ɗaga mini murya"

Hajiya Zainab ta sake ƙuluwa, tana miƙa hannu zata daki Amina.

"Kai! Meye haka Zainab a gidana? Me kike yi haka?"

Waiwayowa tayi ta kalli in da Daddy ya ke ta ce "Sannu shugaban munafukai, dole kace haka mana, ka ɗauki yarinya kaje ka shafe kusan wata guda, ko ta kanmu baka bi, wallahi idan baka ji tsoron Allah ba sai ka wulaƙanta".

"A gaban 'yata kike ce mini munafuki ko? Yanzu abin da kike koya mata ita ma taje tayi nata gidan mijin kenan? Ke idan bance kiji tsoron Allah ni kya gaya mini haka? Kin haɗu ke da 'yarki zaku daki 'yar mutane saboda kawai ina aurenta, shikenan na san matakin da zan ɗauka"
Ya ture Hajiya Zainab ya janyo Amina, ya ce "Ina fatan ba abin da suka yi miki?"

Amina ta ɗaga masa kai alamar eh, ya janyeta suka bar falon.

Hajiya Zainab ta nemi wuri ta zauna, ta dafe kanta, gaba ɗaya tayi mamakin yadda gaba daya Asirin da take bai yi aiki ba.

A ɗaki kuwa Daddy, rarrashin Amina yake yi "Meenal kinga dalilin da ya sanya nace miki na raba muku gida kenan, ban san me Yasa Zainab ta kasa haƙuri ta karɓi ƙaddara ba"

"Daddy, bana son ka ware mini gida, ka gaza yi mini adalci, yanzu na san da anyi wa Fadila aure maybe a samu sassauci a wasu abubuwan"

Ya ce "Haka ne, zan san abin yi. Gobe in Allah ya kaimu kuma zan je gidan sirikan Khalil ni da Alhaji Iliyas, mubi shawararki ya ganta idan tayi masa"

Amina ta ce "Allah ya daidaita su"

Ya amsa da Amin.

Daddare duk da yana cikin zullumin tunani, a kan karɓar da Hajiya Zainab zata yi masa, haka ya tunkari sashenta.
Sai dai sam bata kula shi ba, balle ta saurareshi, yana zaune a falonta yana duba wayarsa, ta shige bedroom ɗinta, ta saka key ta bar shi ya kwana a falo.

Tun da suka dawo Hajiya Zainab ta saka su a gaba, da tashin hankali da rashin mutunci. Da Sassafe ko Amina bai yiwa sallama ba, ya shirya ya bar gidan.

Ɗaya gidan nasa yaje ya samu ya ɗan huta.
Shi da Alhaji Ilyasu suka je gidan su Hafsa, domin magana a kan shirin bikin su Khalil, suka je a kan su faɗi zaɓin da suke na furnitures, Maman Hafsa ta ce ba su da wani zaɓi, komai aka yi musu sun gode.

Kasancewar da biyu suka je, Alhaji Ilyasu yaga maman Hafsa tayi masa, gata nutsatsiya ba zaka ce ma ta haifi Hafsa ba.

Alhaji Ahmad ya ce wa Maman Hafsa karta damu kanta a kan shirin bikin nan, zasu ɗauke komai za ayi, karta damu.

Mama tayi ta musu godiya, tare da yi musu Adduoi su da magabatansu.

A hanya Alhaji Ilyas, ya dinga yaba Maman Hafsa, yana cewa Daddy shi dai tayi masa yana sonta.

Daddy ya ce masa "To ni dai tunda na kaika ka ganta, sai ka yiwa kanka sauran aikin" Alhaji Ilyas yayi masa godiya, sannan Daddy ya tafi gida.

Dama Daddy ko karyawa bai yi ba, ko zuwa gidan baya son yi, dan ya fara deciding ya koma Lagos, ya huta da tijarar Zainab.

Kasancewar a wurinta yake, ba shi da wani zaɓi da ya wuce ya fara zuwa wurin nata, idan ta ga dama ta bashi abinci, idan kuma ta hana shi, ya je ya ci a wurin Amina.

A falonta ya tarar da Khalil a zaune a gaban Hajiya Zainab, tana ta zuba masa faɗa ko haɗiyar yawu bata yi.

Alhaji Ahmad ya kalli Khalil ya ce "Kai meya dawo da kai?"

Khalil da idanunsa suka yi ja, ya ɗaga kai ya kalli Daddy ya ce "Mummy ce ta ce tana son ganina".

"Tashi ka je" ya kalli Hajiya Zainab da ta tsare shi da ido.

Daddy ya ce "Ka tashi ina yi maka magana"

Khalil ya tashi, yana yi yana kallon Hajiya Zainab ya fice daga falon.

Hajiya Zainab ta ce "Wallahi duk masifarka, ɗa dai nawa ne, kuma baka isa ka aura masa yarinyar matsiyata ba wadda bana so ba"

Alhaji Ahmad ya gazgata maganar Amina, na ya yiwa iyalinsa illa da ya bar ragamar gidansa a hajiya Zainab, bai taɓa tunanin fuskantar irin wannan zazzafar ƙiyayya daga gareta ba.

A haka ya lallaɓa yai kwanakinsa biyu a ɗakinta, sai dai a falo yake kwana, dan kulle bedroom ɗin ta take ta bar shi a falo.

Komawarsa wurin Amina ne, ya samu sauƙi dan tana ɗaukar lokaci da shi, tana rarrashinsa tana tattalinsa da kwantar masa da hankali.

Dama can Hajiya Zainab ba tambayarsa take ba, idan zata fita amma yanzu abin nata ya ƙazanta sai ta wuni bata gida, ba tare da ya san inda ta tafi ba.
Ta gama wuninta bata gida, ta dawo suna falon sashinta ita da Fadila suna tattaunawa.

Daddy ya shiga da sallama, hannunsa riƙe da leda, Fadila ce kawai ta amsa sallamar a ciki.

Ya ƙarasa gaban Hajiya Zainab, ya ajiye mata ya saka hannu a aljihunsa, ya ɗauko kuɗi bandir ɗaya ya ce "Na rage lokacin bikin Khalil, ga invitation ne mun gama komai, nan da sati biyu ne bikin, idan da wani shirye shirye da zakiyi ne shikenan kya sanar da ni. Nayi magana da iyayen wancan yaron, sun zo ɗazu ga kuɗin auren 'yarki nan, dubu ɗari na tsayar da Magana wata biyu kawai na saka!!!

AYSHERCOOL
08081012143LITTAFIN NAN NA KUƊI NE, KU TUNTUƁENI TA LAMBAR WAYATA KUYI PAYMENT.



69

Gaban Fadila ne yayi wata irin mummunar faɗuwa jin ance wai an karɓi kuɗin aurenta, ita fa gaba ɗaya wannan Salim ɗin bai yi mata ba, bata son shi, kuma dan cin mutunci da ƙasƙanci, wai dubu ɗari aka kawo kuɗin aurenta.
Wani irin gumi ne ya shigo tsatstsafo mata, ji take ina ma mafarki take yi, wannan wane irin abu ne haka, dama da gaske Daddy yake yi, da ya ce zai aurar da ita ya huta, wato ya gaji da ganinta kenan ya daina sonta, saboda yayi aure?.

Hajiya Zainab ta miƙe tsaye, ta watsawa Alhaji Ahmad invitations ɗin a jikinsa "Ka kwashi tsiyarka Ahmad, kaje can dama kai ka nema masa auren, kaje ku ƙarata, ba da yawuna ba wallahi"

A sanyaye Fadila ta ce "Mummy dan Allah ki bari, Daddy ne fa"

"Dalla can rabu da ni, idan ke ubanki ne ni ubana ne? Da ni kake zancen mu zuba mu gani, shege ka fasa tsakanin ni da kai"

Girgiza kai kawai yayi, ya fito daga sashinta, ta biyo shi tana cigaba da surfa masa bala'i, Amina kuwa kulolin Abinci ne a hannunta da zata kai dining.
Kawai taga Daddy ya fito, Hajiya Zainab ta biyo shi tana watsa masa sauran invitations ɗin.

Idanunsa sun yi jawur, tamkar ya zubda hawaye saboda baƙinciki, a gaban 'yarsa take masa wannan tijarar.

Da taga watsa masa invitations ɗin bai isheta ba, ta shiga jan rigarsa tana cigaba da gaya masa duk maganar da ta ga dama.

Zare babbar rigar yayi, ya bar mata a hannunta yayi gaba, aikuwa ta kuma cukuikuye rigar ta jefe shi da ita, dafe kansa yayi da yaji yayi masa nauyi yayi waje.
Ajiye kulolin hannunta Amina tayi, tabi bayansa tana kuka.
Tabbas kowane rai akwai irin jarrabwarsa, amma yana daga cikin babbar jarabtar da Allah zai maka, ya haɗaka da abokin zama wanda bana gari ba.

"Daddy, Daddy" Amina ta bishi tana kiran sunansa, ta ƙarasa da sauri in da yake, tana zubar da hawaye ta ce "Daddy dan Allah kayi haƙuri"

Murmushin ƙarfin hali yayi ya ce "Me kika yi mini kike bani haƙuri"

"Daddy abubuwan da suke faruwa a gidan nan basa yi mini daɗi, zuciyata bata jin daɗin abin da ake maka, Daddy ko ka haƙura da ni, idan har hakan zai dawo muku da farinciki a cikin gidan nan"

Ajiyar zuciya yayi ya ce "A da ɗin ma ba a cikin farin ciki nake ba, zuwanki ne ya samar mini da shi, ina ga Albarkacin biyayyar da na yiwa mahaifiyata na aureta ne ya sanya, ya kawo mini ke cikin rayuwata, komai zai faru ba zan rabu da ke ba, sai dai mutuwa ta rabamu, ina sonki sosai kuma ni ba abin da kika yi mini, muna tare in sha Allah"

"To kazo mu koma cikin gidan, kar ka fita a haka dan Allah"

"Bakomai ki bari, zanje na huta ne"

Amina ta ce "Ni dai ban yadda ba, kazo mu koma" tayi maganar cikin marairaicewa.

Amina ta ja hannunsa suka koma, sashinta tayi masa wurin zama

Please Login or Register in order to submit comment