Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Zainab tayi.

Sai la'asar sannan suma mota ta kwashe su zuwa gida.

Bayan Amina ta gyara part ɗinta, ta dinga tunani a kan yadda zata ɓullowa al'amuran.

"Lokaci yayi, da komai zai zo ƙarshe da yardar Allah!"




AYSHERCOOL
08081012143GABA DA. GABANTA
              NA
AISHA ADAM AYSHERCOOL



65


Daddy bai dawo ba sai bayan magariba, abin da ya bashi mamaki, bai wuce yadda ya tarar da su Hajiya Turai a gidan ba. Suka bishi da kallon banza. Wanda a baya har rige-rigen gaisheshi suke yi.
Bai kulasu ba, ya wuce sashinsa, inda Amina take.

Tun daga hanyar sashin, wani irin sassanyan ƙamshi na musamman yake dukan hancinsa, ya shiga falon da sallama, amma bata nan.
Ya miƙa ya nufi bedroom ɗin, yana buɗewa kunnuwansa suka jiyo masa sautin muryar Amina tana rera Karatun Alqur'ani mai girma.

Zuwa ya yi ya zauna a kusa da ita, ta cigaba da karatunta, a hankali ya kwanta a kan cinyarta, ya lumshe idanunsa yana jin yadda take zuba karatun Alqur'ani da ka.
Sai da ta kai aya ta idar, sannan ta kalleshi ta ɗan shafi gemunsa ta ce "Babyna, sannu da zuwa"

"Yauwa sayyada, kamar kar ki daina karatun nan Meenal"

Murmushi tayi ta shafa kansa ta ce "Meyasa baka dawo gida ba kaci Abinci?"

"Bana son na takura miki ne, naga kina da baƙi, naje na saka a gyara in da aka sauki baƙi, na tarar sun gyara komai fes, ya kika ga familyn namu, ina fatan dai ba wata matsala?"

"Ba wata matsala, naji daɗin zuwansu sun ɗebe mini kewa sosai, yaushe zaka kaini Dutse?"

"Very soon, ina son muje honeymoon ko 2weeks ne, da mun dawo sai na kai ki"

Amina ta ce "Mmm, meye Honeymoon?"

"Ban sani ba, Baby zamu samo" dariya tayi tana jan hancinsa, sannan ta ce "Amm na manta, ga kayan garata can, ina son a ɗebar musu nasu, a samu ko aika musu ne ayi"

Tashi yayi zaune da mamaki ya kalleta ya ce "Gara kuma, wace irin gara?"

"Gara mana da ake yiwa mace idan tayi aure"

"Haba Amina, wato zuwa kika yi kika saka Baba a gaba yayi miki gara ko, ni nace miki ina son gara ne?"

Tsuke fuska tayi ta ce "To ni na san zasu kawo ne, kawai fa gani nayi an kawo"

"Na san halinki, ki gaya mini gaskiya"

Kwaɓe fuska tayi za ta yi masa kuka, ya ce "Ya isa shikenan, zan saka a kwashe a mayar gaskiya, ai abin kunya ne a gareni ace dan na auri 'ya sai an mata gara"

"Yanzu Daddy ko kara ba zaka yi mini ba sai kasa a kwashi kayan a mayar? Wato kafi ƙarfin iyayena su bamu abu ko? Kar ka manta ni kaɗai suka mallaka komai suka samu dole ni zasu yiwa, amma bakomai na gode"

Ganin tayi fushi ya sanya ya sassauta murya ya ce "Babyna ba haka nake nufi ba, kiyi haƙuri dan Allah, na fasa a mayar ɗin komai ya wuce please"

Sake haɗe rai tayi ta kawar da kai.

Ya sake kwantar da murya ya ce "Haba tawan, smile mana, i have some candy for you"

"Cin hanci zaka bani"

"Eh, mana in dai zai sanya ki huce"

"Hmmm to shikenan, na haƙura tashi muje aci Abinci" ya miƙe ta riƙo hannunsa suka fita falo.

Bayan ya gama cin abincin ya nutsu ta ce "Daddy lefe na yayi kyau sosai, Allah ya ƙara arziƙi, ina ga da zai yiwu da Khalil ma ya tara nasa a wurin Anty Maryam, ba laifi ta iya zaɓe ta san kan kaya"

Daddy ya ce "Haka ne, wannan kuma ke zaki baki shi shawara, ni yanzu damuwata gininsa da ya tsaya yi masa iyayi da ƙaƙale, ya hanzarta yayi abin da zai yi ayi bikin, tun kan uwarsa ta hana"

Amina ta ce "Ta hana kuma, Daddy sai ka bari a fasa auren idan ta hana duk da kaje kayi magana ka kai musu kuɗin aure?"

"To Meenal ya zan yi? Kina kallon yadda nake ta fama da ita ai, tunda Allah ya sanya ta san aure muka yi, take tayar mini da hankali, ita kanta taƙi bari nata hankalin ya kwanta, na ma rasa yadda zan yi"

"To ai koma menene yake faruwa duk laifinka ne"

"Laifina kamar yaya?"

"Da ita da yaranta duk a ƙarƙashin ka suke, amma ka sakar mata ragamar gidan, sai abin da ta zartar, yakamata ka dinga tauna tsakuwa dannaya taji tsoro, ba a komai ya kamata ka dinga bari ana jayayya da kai ba, ba zigaka nake ba amma when it comes to serious issues, you have to be so serious, ba wai sai abin da suke so ba, batun auren Khalil idan ka bari aka fasa saboda mahaifiyarsa ba ayiwa yarinyar adalci ba"

Daddy ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Haka ne maganarki, in Allah ya yarda babu wani abi da zai faru, za ayi auren da yardar Allah, ni ban gaya miki wani abu bama, wani abokina ne da matarsa ta rasu, yake neman ya samu mace mai hankali wadda zata iya kula masa da yaran, duk da yaran ba ƙanana bane ba duk sun manyanta, wallahi nayi masa sha'awar auren sirikar Khalil, matar ba wata babba bace tana da ƙuruciya sosai gata jajirtacciya kuma nutsatsiya, bana son yin magana taga kamar na yi mata wulaƙanci ko na rainata, da na haɗa su"

Amina ta gyara zama ta ce "Kai amma naji daɗi, nifa tun da ka gaya mini halin da suke ciki, nake jin rausayinsu wallahi.
Yanzu abin da za ayi shi ne, ka yiwa abokin naka maganarta, amma sai ka ɗauke shi kuje a matsayin kun je da niyyar batun auren su Khalil, irin ko suna buƙatar wani abu, ko kuma dai makamnacin haka, kaga zai ganta a nan, idan tayi masa daga baya shi sai ya koma, idan ta amince shikenan idan bata amince ba shikenan".

Daddy kawai yayi shiru yana kallon Amina.

"Ya kuma naga kana kallona?"

"Kawai ina jinjinawa basirarki ne, ke har kin lissafa kin samo solution, to shikenan hakan za ayi, Allah ya sa su daidaita".

"Amin Daddy, kaima Allah ya baka lada"


Da daddaren ya sake komawa wurin Hajiya Zainab, wannan karon ya tarar da ƙofarta a buɗe.

"Meyasa kike rufe ƙofar ki ne?"

"Saboda bana ƙaunar ganinka"

Daddy ya ce "Ai ba sai kin faɗa ba na sani. Na zo ne na sauke nauyi, duk da yakamata na haɗaku nayi muku nasiha, amma na san halinki sai kinyi abin da zaki zubarwa da kanki mutunci a gaban yarinya, dan haka nazo na sameki ni da ke. Ina magana ne a kan batun rabon kwana ke da abokiyar zamanki, tunda babu buƙatar spending seven days ɗin nan, tunda koma dai menene ya riga ya faru".

"Dawa kake tunanin zaka raba kwana ni? Ba dai ni ba ka daina wannan tunanin kuma ka tashi ka bar mini ɗakina tun muna sheda juna da kai, kaje na sallama mata bana buƙatar ka"

"Idan ke ba kya buƙatata, ni ina buƙatarki, ba zaki saka in zalunceki ki barni da hakkinki ba"

Ta kalleshi sheƙeƙe ta ce "Au, wai kai nan har wani hakki ka sani, ka san daida da ba daidai ba? Kai ko kunya ba ka ji ba, dan Allah ɓace mini daga ɗakina, bana buƙatar ko kallon fuskarka"

"Shikenan, kiyi abin da kike so, ni zan yanke abin da naga ya dace, sannan ina saka ran next week zamu bar ƙasar nan tare da Amina, amma ba zamu daɗe ba, baifi muyi 2weeks ba mu dawo".

"Ku bar duniyar ma idan kaga dama, aikin banza kawai, kuma wallahi ina sake jan kunneka a kan auren da zaka yiwa Khalil, wallahi idan baka janye Maganar nan ba komai ya biyo baya ka kuka da kanka"

Daddy ya girgiza kai ya ce "Ɗanki ne dai, idan kika yi masa baki Allah ya jarrabeshi da auren mace irinki, kanki abin zai dawo"

A fusace ta miƙe ta ce "Me kake nufi da auren mace irina? Kana nufin ni mutuniyar banza ce?"

"Wannan kuma ke zaki wa kanki alƙalanci" ya juya ya fice ya bar mata ɗakin.

"Kan uba, lallai ma mutumin nan"


Daddy wurin Khalil ya nufa, ya tarar da shi a falonsa, yana ta waya har Daddyn ya shigo bai sani ba.

"Kai Magana na zo muyi fa" Khalil yayi firgigit, ya katse wayar ya hau sosa kai ya ce "Yi haƙuri Daddy, ban san kana nan ba.

"Dama ina zaka san na zo, kana nan kana soyayya" shafa kai Khalil yayi yana shafa kansa.

Daddy ya zauna a kusa da Khalil ya ce "Ya 'yar tawa, ina fatan tana nan lafiya"

"Tana lafiya lau, kalau Daddy, tana cewa ma in gaisheka"

"Amma ai baka gaya mini" Khalil yayi murmushi yana shafa kai.

"To yanzu kai meye shirinka? Kasan ba a saka wani dogon lokaci ba"

"To, dama Daddy batun ginina na ajiye cigaba da ginina saboda a baya naga kamar ba zan samu Hafsa ba, amma to yanzu dai zan cigaba da ginin, sai kuma batun kayan lefen".

Daddy ya ce "Ai kaine Khalil, wannan gida naka ka janyo ƙaƙale ƙaƙale da yawa, bana tunanin zai kammla kan lokacin, amma lefen Amina ta ce nata da Hajiya Maryam ta haɗa mata sun yi kyau sosai, ko kaima kuɗin zaka bayar idan ya so ta faɗi duk abin da take so a saya mata"

"Shikenan Daddy, duk yadda ka ce yayi, idan kuɗin ne sai na tura"

"To babu laifi, sai kuma magana ta biyu, duk yadda ake ciki ka tattara kayanka ka bar garin nan gobe in Allah ya kaimu, idan ba haka ba kuwa mahaifiyarka zata iya hana auren nan"
Khalil yayi saroro yana kallon Daddy.

Daddy ya ce "Ƙwarai kuwa, tun wuri ka koma duk abin da ake ciki ma dinga waya kawai"

Khalil yayi ajiyar zuciya, dan har ga Allah yana son cigaba da zuwa wurin Hafsa, dan su cigaba da samun shaƙuwa da fahimtar juna.

Jiki a sanyaye ya ce "To shikenan Daddy, zan koma in Allah ya yarda"

"Yauwa, Allah ya taimaka ya sanya albarka"

"Amin Daddy na gode sosai"

Daddy ya yi masa sallama ya koma wurin Amina.


Bayan tafiyar Daddy, Khalil ya ƙudurce gobe da Safe zai ɗau mota ya koma Abuja, ba sai ya jira jirgi ba, karma Mummy ta zo da wani batun da zai zama barazana ga aurensa.


Idan yana tare da Amina mantawa yake da komai, yaji kamar babu abin da yake damunsa, saboda yadda take tattalinsa take kula da shi, shi kansa har mamakin irin tsananin son da yake mata yake.
A duk lokacin da ta ganshi cikin walwala da fara'a ta kan yi amfani da wannan damar, wurin tuntar da shi abubuwa, da ɗora shi a kan hanyar da ta dace, yadda yakamata yayi wa kansa guzurin lahira a dukiyarsa tun yana raye.
A 'yan kwanakin da ya kasance tare da Amina, tunda ta tare duk wanda ya zo gidan nan, sai Amina ta bashi kuɗin mota, sai tayi girkin Abinci ta bawa mutum ya ci ya ƙoshi, sannan ya baka kuɗi.

Daddy yana ajiye kuɗi a ɗakinta sosai, kuma ya mata izinin yin amfani da su, dan haka ta samu damar yin kyauta sosai.


Washegari ta kasance Litinin ce, Khalil ya kintsa kayansa ya tafi wurin Mummy da sassafe zai yi mata sallama ya tafi.
Wani irin kallon bamza tayi masa sanan ta ce "Daga zuwanka har ka gama kwanakin zaka tattara kayanka ka koma ko Khalil. To ina sake jadadda maka ina nan daram a kan bakana, muddin kayi wannan auren sai dai ka nemi wata uwar, dan ba zan cigaba da amsa sunan uwarka ba, tunda ka zaɓi ubanka a kaina, shi yake hure maka kunne"

A sanyaye ya ce "Mummy ba haka bane ba, wurin aikine ake nemana"

"Rufe mini baki ni, koma waye yake nemanka kaje ka ƙarata, amma zaka dawo ka sameni, kuma aurene ba ka isa ka auri 'yar matsiyata ba, zan gani idan ina da muhimmanci a wurinka"

Jiki a saɓule Khalil ya tashi, ko wurin Abdul bai je ba, saboda safiya ce, balle Hafsa duk ya bari a ransa yayi musu sallama ta waya, shirye-shirye kuma sa cigaba da yi ta waya, amma jikinsa yayi sanyi da inkarin da Mummy take, na idan yayi auren nan ba shi ba ita.


Tayi mamaki ƙwarai, da Khalil bai nuna wata nadama ba, ya sa kai ya fice babu alamar zai janye batun auren nan.
Abin ya ƙular da ita sosai da sosai, miƙewa tayi ta nufi sashin Daddy, tana zuwa ta tsaya a ƙofar bedroom ɗin, ta dinga bugawa kamar zata karya ƙofar.

Amina ce ta fito da 'yar riga iya cinyarta, kanta ko ɗan kwali babu tana mutsutsuka idonta.

"Malama lafiya kike mana wannan bugun da safiyar nan?"

"Ke! Ba wurinki na zo ba, wurin mijina na zo yana ina?"
Amina ta rufe ƙofar bedroom ɗin sannan ta ce "Mijinmu dai ko? Bacci yake yi bai tashi ba ya aka yi?"

"Ba ruwana da bai tashi ba, ki bani hanya na wuce"
Amina ta tare ƙofar ta ce "Uban da ya saka kika masa rashin mutunci, ki ka koro mini shi nan, sai ya sa ki haƙura zuwa lokacin da zai dawo wurinki, kya gaya masa koma menene"

"Ke ni kike gayawa haka, sa'arki ce ni? Zaki bani hanya ko saina make ki"

Cikin rashin kunya Amina ta ce "Ba zan matsa ba, gobe idan ya kuma wurinki ki koreshi, yana zuwa zan caraf da shi ni. Ai ni Allah ne yayi mini gyaɗar dogo ma samu mijin shashasha, wadda bata da ra'ayin kanta sai na ƙawa, idan basu sa kin kashe auren nan ba ba zaki yi hankali ba"

"Ni kike gayawa haka? Dan kin auri mijina gani kike ni sa'arki ce, wallahi sai nayi maganinki"

"Allah da yayi ni shine maganina, ba ke ba, Allah sarki rayuwa, ba zan taɓa manta ranar da na zauna a kan kujerar falon mijinki ba, kika ƙare mini zagi da cin mutunci, amma da yake Allah ba yadda bai iya ba, sai gashi ƙirjinsa ne matashina, a kan ruwan cikinsa nake kwana, kin gama yi mini komai da kika sallama mini shi, Baby ya iya soyayya" ba tsoro balle kunya, Amina take gasawa Hajiya Zainab maganganu masu zafin gaske.

Jikin Hajiya Zainab har rawa yake, saboda azabar ɓacin rai ta ce "Ni kike gayawa wannan maganar?"

"Uwata ce ke da ba zan gaya miki ba? Ko kin manta lokacin da kike cin mutuncin ubana a gabana, ai kaɗan kika gani, ba zan fasa yi miki abin da na ga dama ba, har sai na tabattar da zuciyata ta samu nutsuwa daga baƙin cikin da kika dinga tura mini a zuciyata, abu mafi zafi a rai shi ne zagin ubana a gabana da kike yi"

"Na zagi uban naki, matsiyata 'yan ƙauye"

Amina ta ce "Ai ba zanji haushi ba yanzu, dan kin zagi Babana mussman da na san asalin balbela, kema daɗinta naki uban ba wani bane ba, da miji kike taƙama idan har za a kira maigadi matsiyaci ban san da wani sunan za a kira mai faskare ba, koda yake koba komai ko da goma ta lalace tafi biyar albarka, saboda rayuwata ta ginu nawa uban ya dage yake jure duk wani cin mutunci ake masa a gidan nan"

Cikin tsananin fushi, da zafin nama Hajiya Zainab ta fizgo Amina, ta hankaɗata ƙasa.
Amina kuwa ta ware baki, ta kurma uban ihu tana kiran "Wayyo Allahna Daddy ka fito kar ta kasheni, Daddy!Daddy matarka zata illatani"

Duk da sama sama yake jiyo ihun Amina, a sukwane ya farka daga baccin da yake, ya fito daga bedroom ɗin, aikuwa yaga Amina a ƙasa hawaye ya wanke mata fuska, Hajiya Zainab kuma na tsaye a kanta tana huci.

Ita kuwa Fadila, ta gama shirin makarantarta, ta ƙudurce zata je ta yiwa Daddy maganar kuɗin registration ɗin ta na makaranta, dan haka bayan ta kintsa, ta ɗauko jakarta ta nufi sashin Daddy.


Daddy kuwa kan Amina yayi da sauri, ya ɗagota yana faɗin Meenalina, menene meyafaru?"

Cikin kuka Amina ta ce "Dukana za tayi, hankaɗe ni tayi ni ƙafata da bayana ciwo suke, dan kawai nace mata bacci kake yi ba zan tasheka ba"

Aikuwa ran Daddy ya ɓaci, ya kalli Hajiya Zainab ya ce "Wai meyasa baki da girma ne? Kina cewa nayi abin kunya na auri 'yar cikina, ke kuma me ki ka yi? Zaki yi dambe da 'yar cikinki? A irin haka fa kuka je ke da 'yar ki kuka saka tayi ɓari, duk kashedin da nayi miki a kan Yarinyar nan baki ji ba, so kike sai kin illata ta hankalinki zai kwanta?"

"Kai baka san meyafaru ba kawai daga fitowarka zaka hauni da masifa, kai wani irin mutum ne, na dake ta ɗin kayi abin da zaka yi"

"Zainab na gaji da kawar miki da kai, koma menene ke kika zo in da take ai, ba ita taje in da kike ba, zan aikata abin da baki tsammani ba, muddin kika cigaba da takurawa rayuwarta, ba ita tayi miki laifi ba, nine da na aureta, komai zaki yi mini, zanniya jurewa bai dameni ba, amna ba zan lanunci cin zarafin 'yar mutane ba dan kawai ina aurenki ba, ita ma matata ce dan haka ki kiyayeni"

Ai gaba ɗaya sai Hajiya Zainab taji kamar ƙafafunta sun gaza ɗaukarta.

Ya kalli Amina cikin kulawa ya ce "Sannu Meenal, tashi muga"

"Ni ƙafar ciwo take mini, ka ɗaukeni muje ka ja mini" ya sunkuya ya ɗauketa kamar 'yar baby, ta kalli Hajiya Zainab tayi mata gwalo.

Fadila da taji abinda ya faru, kawai ta juya ta fice kan Mummy ta fito tana kuka.
Ikon Allah ne kawai ya kai Fadila makaranta, saboda tuƙi take amma sam ba a hayyacinta take ba, kuka kawai take yi.

Daddy kuwa a kan gado ya sauke Amina, ya zauna yana matsa mata ƙafar yana cewa "Sannu, ince ko dai bayan ƙafar ba abin da yake miki ciwo?" Amina ta jinjina kai.

Ya cigaba da ja mata yatsun ƙafar, yana faɗin "Sannu babyna, kar ki dinga biye mata dan Allah, kar ta illata mini ke, idan tayi miki wani abun ni ki gaya mini na ɗau mataki, amma dan Allah karki dinga biye nata tayi miki illa"

Cikin shagwaɓa ta ce "Nifa ba biye mata nayi ba, kawai daga cewa bacci kake ta hankaɗeni"

"To kiyi haƙuri cutyna" yayi maganar yana shafar fuskarta zuwa kan hawayenta.

Hajiya Zainab kuwa har ta nufi ɗakinta zuciyarta na yi mata zafi, ta juyo ta dawo ta banka ɗakin.


Tana bankawa ta tarar da Amina ta ɗage rigar jikinta, ta ɗora santala santalan ƙafafuwanta a kan nasa, tana goge hawaye, shi kuma sai lallaɓata yake yana kwantar mata da hankali.


Kamar zata afka kans Hajiya Zainab ta ce "Kai Ahmad na gaji, na gaji wallahi, na gaji da wannan cin kashin da kake mini. Wallahi ko ni ko wannan sheɗaniyar yarinyar, zaka gane baku da wayo daga kai har ita"

Saroro suka yi suna kallon Hajiya Zainab, sai masifa take kamar ta haukace, sai da ta yi ta gama ta fice daga ɗakin.

Rarrashin Amina ya cigaba da yi, yana kwantar mata da hankali, a kan in dai yana nan babu abin da Hajiya Zainab za tayi mata.

A yadda Fadila ta shigo aji, idnuwanta jawur duk sun kumbura, gaban Yazid ya faɗi ya juya yana binta da kallo.

Haka aka yi lectures, yana yi yana kallon Fadila, tana ta share hawaye.

Haka suka yi lectures wuni guda, hankalin Yazid yana kanta, yana mamakin menene ya sanyata a wannan halin haka.

Ko fita cin abinci bai ga tayi ba, kuma tsawon awannin nan, hawaye take zubarwa, kowa sabgar gabansa yake a ajin.


Koda aka tashi ma, Yazid yana zaune yana kallon in da take zaune, kowa ya watse amma sai ɗaiɗaikun mutane, ita kuwa tana zaune ta kifa kanta.

Miƙewa yayi ya nufi in da take zaune, ya ɗan daddaki kan teburin, amma bata motsa ba.
Ya kira sunanta a hankali "Fadila" kamar wadda take bacci haka tayi firgigit ta tashi.

"An tashi kowa ya tafi, amma kina zaune, lafiya kuwa?"

Ta girgiza masa kai, ta fara duba jakarta.

Zama yayi a kusa da ita ya kalleta ya ce "Ukty meke damunki haka?"

"Ban sani ba" ta faɗa cikin tsiwa.

"Yi haƙuri, amma tun da kika zo fa kike kuka, me yayi zafi ne haka?"

"Na ce maka ban sani ba, ina ruwanka dani ne? Ba kace bani ba kai ba ka rabu da ni mana"

Yazid yayi murmushi ya ce "Eh na faɗa, amma ke kika fara ai. Zuciyata ta kasa daurewa, bana son ganin mutum cikin damuwa, yanzu haka ji nake kamar na tayaki, meke faruwa can You share it with me?" Kawai ta sake fashewa da kuka, har da sheshsheƙa.

"Fadila nima zaki sani kuka, dan Allah ko menene yake damunki, kiyi haƙuri yi ta maimaita innalillahi wa innalillahi raji'un" yayi maganar a raunane.

Kallonsa Fadila tayi, da gaske yake zai tayata kukan, saboda yadda idanunsa suka sauya.

"Ni gida zan tafi, bani wuri" tayi maganar tana share hawaye.

Jakarta ya ɗauka ya ce "Muje na rakaki mota" tashi tayi tai gaba, yabi bayanta.
Har suka isa motarta, kuka take bata fasa ba.

Yazid ha ce "Bana tunanin zaki iya tuƙin nan, bani mukullin na kai ki gida"

Abin mamaki bata yi masa musu ba, ta miƙa masa mukullin, ba tare da tana tabbacin ya iya jan motar ko bai iya ba. Ya karɓa ya buɗe motar ya buɗe mata ta shiga, shima ya shiga ya kunna motar.

Ya ɗan kalleta ya ce "Ina ne adress ɗin?"

Nan tayi masa kwatance, ya yi addu'a, sannan ya fara jan motar a hankali.

Ganin ta ɗanyi Shiru, tana kallon gefen hanya, ya sanya Yazid ya ce "Yanzu gaya mini, meke damunki kike wannan kukan?"

"Wai kai ina ruwanka da abin da yake damuna, bayan kace ba kai ba ni, meya dameka da ni?"

"Hmm kin ji babu daɗi kenan, ai ke kika ce mini zaren ba kalar yadin bane"


Cikin tsiwa ta ce "To da kalarsa ne?"

Ya ce "A'a sorry. Tunda kin daina kukan Alhamdilillah, ita rayuwa haƙuri ake yi da ita, kuma komai yayi zafi magainsa Allah"

Yana rarrshinta, amma ji take kamar yana fama mata abin da yake mata ciwo.

Yazid ya sha uban mamaki, ganin uban danƙareren gidan su Fadila, yayi horn aka buɗe masa gate, ya shiga da motar ciki.
Sai dai yana shiga da motar, taji kamar ya dawo da ita cikin baƙin cikin da take ciki tsundum.

"A ina zan yi parking ɗin?"

"Kayi a ko ina ne ma"

Yazid ya yi parking, amma kan ya farga, tuni Fadila ta buɗe motar ta fice.

Amina tana falo tana ƙoƙarin fitowa, Fadila ta dawo ta wuceta fuuuuu kamar korarriya.
Amina ko a jikinta ta fito, tana fitowa taga Yazid a tsaye da mukullin mota a hannunsa.

Yazid ya ce "Sannu dai"


Amina ta ce "Yauwa sannu da zuwa, wa kake nema?"

"Amm dama Fadila na kawo gida, kuma bata tsaya ta karɓi mukullin motar ba, naga ta fice ta shiga gida"

Amina ta ƙare masa kallo sannan ta ce "Ko kai ne Yazid?"

Yazid ya ce "Eh ni ne"

Amina ta ce "Masha Allah, sannu da ƙoƙari bani mukullin na bata"

Yazid ya bawa Amina mukulli, har zai juya ya tafi ta ce "A'a ka tsaya a baka ko ruwa ka sha mana"

Yazid ya ce "A'a na gode"

Amina ta ce 'A'a ba zanji daɗi ba gaskiya, dan Allah ka jirani ina zuwa"

Yazid ya ce to.

Amina ta nufi cikin gida, tana wani irin murmushi da ita kaɗai ta san ma'anarsa.




AYSHERCOOL
08081012143GABA DA GABANTA
NA
AISHA ADAM AYSHERCOOL




66

A falo Amina taga Hajara tana aiki, Amina ta ce "Hajara, ɗan biyoni dan Allah zaki tayani wani ɗan aiki"

Hajara ta ce "To uwar ɗakina" tabi bayan Amina. Hajara ta tsaya a falo tana jiran Amina.

Amina ta shiga bedroom ta buɗe wardrobe ɗin Daddy, ta ɗauko galla gallan shadda guda biyu, da turare ta saka kuɗi a envelope ta fito ta miƙawa Hajara ta ce "Biyoni" suka fito in da ta bar Yazid a tsaye, ta karɓi kayan hannun Hajara ta miƙawa Yazid ta ce "Gashi muna godiya sosai da sosai"

Yazid ya ce "A'a gaskiya ba zan karɓa ba, na gode sosai"

Amina ta ɗan tsuke fuska ta ce "Meyasa, ka san babu kyau a baka kyauta ka ƙi karɓa faɗar maznon Allah Sallallahu alaihi Wasallam ce"

Ba dan Yazid ya so ba ya karɓa ya ce "Na gode sosai"

"Bakomai malam Yazid, Allah ya saka da alheri" Yazid ya jinjina kai, yayi gaba ya fita daga gidan.

Hajara ta ce "Uwar ɗakina, wannan kuma waye?"

Tayi murmushi ta ce "Nima dai ban kai ga sani ba tukuna, amma wani abu ma shirin faruwa, da zai bawa kowa mamaki"
Cikin rashin fahimta, Hajara ta ce "Ban gane ba"

"Zaki gane ne Hajara" daga haka ba ta kuma cewa komai ba, ta wuce sashinta.

Fadila bayan ta gama koke-kokenta, ta shiga tayi wanka,

Please Login or Register in order to submit comment