Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta gaji.

Kasancewar tafiyarsu ta ƙarato, ya sanya Amina ta duƙufa cigaba da bitar karatun da tayi, ana sallar isha'i, ta shige ɗakinta, hatta Abinci a ɗakinta ta ci.

Wajen sha ɗayan dare ta ga kiran Daddy, ta ɗaga ta saka wayar a handsfree taƙi magana.

A hankali ya ce "Meenalin Daddy"

"Na'am"

"Au na zaki kulani ba, ki ka ɗaga wayata ki ka yi shiru?"

"Ai kaima watarn haka kake mini"

"To naji, zan samu tea?"

Amina ta ɗan tura baki ta ce "Ni gaskiya a gajiye nake, daga dawowata aka sani canza labulaye da Carfet, da nayi niyyar ko girki na yi maka, amma ko akwatina ban ajiye ba aka sani aiki"

"Waye ya saki aikin?"

"Ai kai ma ka sani"

"To shikenan naji, da safe idan Allah ya kaimu, ki mini girki kin ji Meenalina, am missing your delicious food, kuma kinga kin fi kowa sanin Abincin da ya dace da ni"

Ta yi wani murmushi kamar tana gabansa ta ce "I Will in sha Allah"

"Ranar Wednesday zaku tafi, so ki cigaba da shiri, idan da wani abu da kike buƙata ki sanar da ni"

"Eh, abu ɗaya nake so"

Cikin zaƙuwa ya ce "What it is?"

"Your presence their" tayi maganar a shagwaɓe.

"Rigimar ce ko, sai da safe" ya kashe wayar. Ajiye wayar tayi tana cigaba da mita, ta mayar da hankali ga karatunta.



Cikin rashin samun mafita, da rashin karsashi Khalil ya kira Mummy a waya, sai da ta kusa katsewa sannan ya samu ga ɗaga.

"Yau ka ga dama ka neme ni kenan?" Yaji muryarta maimakon ko gaisawa ta bari suyi.

A saɓule ya ce "A'a ba haka bane, bani da lafiya ne"

"Eh, ko ba baka da lafiya ba? Kana fama da ciwon so ko, gubar Asirin da suka zuba suka baka a Abinci bata sake ka ba, to ka sani in kai sun shanye ka ni basu shanye ni ba".

"Mummy dan Allah duk a bar wannan maganar, ni kiranki nayi na gaisheki"

"Ka riƙe gaisuwarka bana so, jibi in Allah ya kaimu zanje naga iyayen yarinyar da na zaɓa maka, next za a kai kuɗin Aurenka da ita"

"Innalillahi wa innalillahi raji'un, dan Allah Mummy kar ki mini haka"

"Ai tuni ma an riga an yi, idan ka ga dama kayi mini biyayya, idan ba ka ga dama ba kabi 'yar matsiyata mai awara a hanya!!


AYSHERCOOL
08081012143GABA DA GABANTA

BY
AISHA ADAM AYSHERCOOL


46

Baki na rawa Khalil ya ce "Dan girman Allah Mummy ki tsaya ki ji"

"Ubanka zan ji, rufan baki zaka gane kurenka"

Ta kashe wayar, Khalil ya dafe kansa yana jin wasu zafafan hawaye suna zubo masa, ba tausayin kansa yake ji ba, tausayin Hafsa ya fi cika masa zuciya, saboda bai san wane irin mutum Allah zai haɗa Hafsa da shi ba.


Kankiya ne zaune a office ɗinsa tare da wasu abokan aikinsa, suna ta hayaniya da surutu.
Suka ɗan tsagaita Kankiya ya ce "Wallahi baku ga rashin mutuncin da yarinyar nan tayi mini ba, duk yadda ɗalibai ke shakkata amma ta yarfa ni yarinyar nan, wallahi ban da ina sonta da saina wahalar da ita wallahi"

"To kai Kankiya, ya aka yi ka bari har ta rainaka haka ne?"

Kankiya ya ɗan taune leɓensa na ƙasa ya ce "Bari kawai TJ, ni ban taɓa ganin yarinyar da na nuna ina so ba, sai ita, amma sai wulaƙantani take yi, ta tsaya tana saurar wani sakaran yaro, dan ina sonta ne, ba yadda zan iya da ita, kuma da alama babanta mai faɗa aji ne, shi Wannan Yaron zan wulaƙanta in ga ta tsiya"

TJ ya ce "Ka bari sai exams, kai ta gara shi, kana dawo da shi"

"Ai ba sai ka faɗa ba, nace no Attendence no exams, kuma na hana shi zama a ajina, naga idan na taɓa shi tana jin haushi"

Suka cigaba da tattaunawa a kan Yadda Kankiya zai yi da Yazid.



Kamar yadda Daddy ya buƙata, da sassafe kan Amina ta tafi makaranta, tayi girki, ta je ta shirya a dining.
Ta koma ɗakinta ta tura masa saƙo "Na gama Abinci, ka fito in ganka kan in tafi"

Yana zaune ya idar da azkar, yana duba muhimman saƙonni a wayarsa, saƙonta ya shigo ta what's app.

Murmushi yayi ya kirata video call, tana tsaye ɗaure da towel, tana jira ko zata ga saƙon Daddy kan ta shiga wanka, sai ga video call ya kirata, bisa rashin sani tayi zaton Voice call ne, kawai ta ɗaga kiran.
Da fari bata lura ba, ta ajiye wayar tana neman comb, tana ta hello. Sai da ta ɗago ta ga kyakkyawar fuskarsa ta bayyana a kan screen ɗin wayarta. Wata 'yar ƙara ta saki ta cilla wayar kan gado, tare da dafe ƙirjinta, gaba ɗaya ba ta sa Video call ne ba ta ɗaga kiran, ya ganta babu mayafi yanzu kuma ya ganta daga ita sai towel.
Wani Irin haushi ne ya kama Amina, gaba ɗaya taji wata irin kunya da haushin kanta sun kamata, tare da zargin kanta mai yasa bata duba ba ta ɗaga, yanzu ma sai ya yi zaton ko tana sane ta ɗaga kiran.
Jiki a sanyaye haka tayi wanka, ta fito ta shafa mai ta saka uniform, ko karyawa ba tayi ba, ta ɗau jakarta, ƙarfe bakwai da kwata ta lallaɓa ta fice, tana fatan kar su haɗu. Sai dai tana fitowa ta ganshi a kan kujerar da ke facing ɗin ƙofar da zata fito, ya zubawa ƙofar ido.
Ji tayi tamkar ta koma ciki da gudu, amma ya riga ya ganta, ta fito kanta sunkuye, ko ɗago kai ta kasa yi balle ta kalleshi, ta dinga jin tamkar ƙasa ta tsage ta shige ciki.
Kanta a ƙasa haka ta ce masa ina kwana, amma ya ƙi amsawa ya cigaba da kallonta. Har ta kai ƙofa ya ce "Amina" ta tsaya cak bata waiwayo ba.

"Zo" yayi maganar fuskarsa babu wasa.

Ta juyo ta dawo kanta a ƙasa, ta zo gabansa ta durƙusa.

Yayi ƙasa da muryarsa ya ce "Mun yi faɗa ne?" Ta girgiza masa kai.

"To ba faɗa meye yasa kike sunkuyar da kai ko kulani baki ba?"

"Ai na gaisheka baka amsa ba"

"Banji bane, kince in zo ki ganni, kuma na fito baki kulani ba"

Amina ta ɗan yi Jimm ta ce "Dama ba komai"

Fadila ce ta fito, hannuta riƙe da mukullan motarta, da kuma jakarta.

"Daddy good morning"

Cikin sakin fuska ya ce "Morning dirling, how are you?"

Ta kalli in da Amina ke durƙuhe a gaban Daddy, ba ta kawo komai a ranta ba ta ce "Daddy bari in karya in wuce school"

Ya ce "Ok, yaushe za kuyi hutu ne, a fara shirin tafiyarku ke da Mummynki?"

"In the next couples of week in sha Allah"

"Shikenan, Allah ya taumaka ya bada sa'a"

"Amin Daddy" ta nufi dining domin ta karya.

Ya kalli in da Amina ta sunkuyar da kai ya ce "You can go" Amina ta miƙe ba tare da ta ɗago ta kalleshi ba, ta juya ta bar falon.

Amina ta fara zuwa suka gaisa da Baba sannan ta tafi makaranta, da aka tashi sai da ta biya gidansu Azima, ta haɗa Maman Azima da Inno a wayar Ammin Azima suka gaisa, ta bawa Ammin Azima tsarabar.
Ammin Azima ta na matuƙar son Amina, jin ta take tamkar 'yar da ta haifa, sai la'asar sannan Amin ta tafi gida.
Sai da Baba ya yambayeta a ina ta tsaya, ta gaya masa taje gidansu Azima ne ta kaiwa Mamanta tsarabar da Inno ta bayar a kaimata.

Wasa-wasa aka shiga wasan ɓuya tsakanin Amina da Alhaji Ahmad, in dai ta san zata ganshi, ba ta fitowa kuma ta kashe wayarta gaba ɗaya, dan karma ya kirata.

Hajiya Zainab tare da Turai da Salma, suka shirya suka je gidan ƙanwar Hajiya Salma, wato Hajiya Badi'a.
Gida ne na alfarama, kai da ganin gidan ka san suna da abin hannunsu, Mummy ta washe baki, dan irin mutanen da take son su haɗa zuriya kenan, bata fatan talakawa su raɓi zuriyarta sam.

A katafaren falon Hajiya Badi'a tasa aka sauke su, ba laifi ta karɓesu cikin mutuntawa, dama sun san juna Hajiya Zainab da Hajiya Badi'a, su kan haɗu a sha'anin Hajiya Salma, amma ba ta taɓa sanin tana da 'ya mace ba.

A lokacin Hajiya Salma ta yiwa Mummy bayanin cewa, Kursum ba ta gari ne tana karatu a ƙasar waje, shi ya sanya bata santa ba. Sun taɓa hira sosai, sannan Hajiya Badi'a ta kira Kursum dan su gaisa.
Duk ramar Fadila Kursum ta fita, ga ta da wani irin haske gauuu babu kyan gani, kai da ka gani ka san ba farinta bane, tayi fixing nails ta musu fenti, haka ta fito soƙai-soƙai kamar raƙumar dawa.

Cikin iyayi ta ɗan lanƙwasa ta ce "Ina wuninku?"

Suka amsa mata da lafiya ƙalau.

Ta kalli Hajiya Salma ta ce "Mummy, yau nace zan zo gidanki"

"Ba wani nan, dan kin ganni ne shi ne zaki wani ce yau zaki zo gidana"

Nan suka gabatar mata da Hajiya Zainab, da abin da suke buƙata, har muƙaman Alhaji Ahmad sai da aka gayamata, suka nuna mata hoton Khalil.
Ba kunya a gabansu ta ce musu ta amince, da ma duk samarin nata ba wani tsayayye sai watsatstsu, ga Khalil ya haɗu ta ko'ina, a nan Hajiya Zainab ta tabattarwa da Hajiya Badi'a cewar kan su tafi umara, ko da zarar sun dawo, za a kawo kuɗin Aure.

Kursum ta ce "To amma shi yaushe zai zo?"

Hajiya Zainab ta ce "Kar ki damu, da zarar ya shigo Kano, zai zo ku gaisa"

Hajiya Salma ta ce "Kaga mara kunya tambaya ma kike yaushe zai zo ko?"
Kursum ta tashi tana murmushi ta bar falon gaba ɗaya.



Makarantar su Amina suna ta preparing ɗinsu a kan tafiyarsu, suna ta gaya musu ƙa'idojin da zasu kiyaye, da jadadda musu ranar tafiya kar wanda ya makara.
An tashi daga makaranta, Amina na tafe da ita da Azima, wata Perfect ta sanar da Amina ana nemanta a Office ɗin director.
Ba tayi tunanin komai ba, ta cewa Azima ta jirta ta je ta dawo, sai dai tana shiga da Daddy ta fara tozali, idonsa cikin nata, tayi saurin ɗauke idonta ga sunkuyar da kai ƙasa.

Ta ƙarasa ciki, ta gaida director ta gaida Daddy ya amsa mata yana kallonta.

Director ya ce "Amina, an zo musamman ana kafa mana dokoki a kanki, mu kula da ke sosai".

Amina dai ta sunkuyar da kai tana wasa da yatsun hannunta.

Daddy ya ce "Idan kun isa can Abuja, in kun sauka, za a tura direba ya ɗuke ki sai lokacin da zaku fara competition ɗin za a dinga kai ki, ba zaki zauna a hotel ba"

Ta jinjina masa kai kawai.

"Shikenan tashi mu tafi gida" ta miƙe ta bar Office ɗin, Daddy yayi sallama da director, ya bi bayan Amina.

Azima kuwa da ta gaji da jira, sai tayi tafiyarta, saboda kwanan nan kusan kullum cikin kiran su Amina ake, saboda tafiyar da za suyi.

Daddy ya ƙaraso ya buɗe motar, ta shiga shi ma ya zaga ya shiga.

Gaba ɗaya ta zama wata iri, kamar ba ita ce take masa surutu kala-kala ba, ta koma kamar wata baƙuwa ta kasa sakin jikinta, ko haɗa ido taƙi bari su yi.

"Kin gama guje-gujen?" Ta girgiza kai.

"Yi magana mana" tayi shiru ba tace komai ba.

Murmushi ya yi ya ce "kawai kiji kamar babu abin da ya faru, banga komai ba ki manta" wata Kunya ce ta sake kama Amina, ya dai ganta da towel ɗin kenan?.

'yanzu gaya mini me kike buƙata, mai zan saya miki?"

Zumɓura baki tayi ta ce "Ni bana son komai"

"Meyasa?"

"Bayan kace ba zaka ba"

"To ai Khalil zai je, zai wakilceni"

"Ni Khalil ɗin da baya kulani, ni kai nake son ka zo"

Ya ɗan shafi gemunsa, wanda hakan ya zamo kamar ɗabi'arsa ya ce "Ni wurin aiki zan koma, idan Khalil ɗin ma ya zo ai duk ɗaya ne"

Ɗauke kanta tayi tana tura baki, ita ba haka take so ba.

Ɗan leƙa fuskarta yayi ya ce "Meenali na"

"Ba wata Meenalinka"

Yayi murmushi ya ce "Tawa ce mana"

"Amma na roƙi abu ka ƙi yi mini" tayi maganar tana masa wani irin kallo, da yake kai wa zuciyar Alhaji Ahmad wasu irin saƙonni.

"Ke idan baki yi rigima ba ba kya jin daɗi ne?"

"Kaifa kace in dinga tambayarka abin da nake so"

"To ai duk cikin abin da kike tambaya wannan ne kawai ba zai yiwu ba"

Ta ce "Ai shikenan" tayi maganar tana sake ƙanƙame jakarta, tana kallon titi.


"Meenal, idan kunje ki kula da kanki sosai, ban da yawo, banda rashin ji, ki yi ta Addu'a Allah ya baku nasara, ya sa a samu abin da aka je nema"

"Amin, zan kiyaye idan Allah ya yarda"

"Yauwa Meenalina, yau zan samu Coffee ɗin dare?"

Ta ce "To, amma a dining zan ajiye maka, ka fito ka sha, ni bana son abinda zai haɗani da ita, kuma ni gaskiya tsoro nake ji, kullum in dinga zuwa falonka, ga Hajara ta saka mini ido, kuma idan matarka ma ta ga ina yawan zuwa wurinka ta ritsani ni me zance mata?" Sai da ya bari ta gama wassafa bayananta sannan ya kuma cewa "Can i get a Coffee tonight?"

A duk lokacin da yayi irin wannan, ta san yana son tabattar mata he is serious. Jinjina masa kai tayi alamar eh, ya cigaba da tuƙinsa sannan ya ɗan nisa ya ce "Idan na baki umarni, ko na nemi abu a wurinki, bana buƙatar ki kawo mini ko wane irin excuse, ina fatan kin gane?"


"Eh na gane, kayi haƙuri" bai ce mata komai ba suka cigaba da tafiya.


Gaba ɗaya a wannan karon karatun jarrabawa ba ya yiwa Fadila daɗi sam, dan abubuwa da yawa idan Yazid ya koya mata tafi ganewa kuma ta riƙe, amma wannan karon ita kaɗai take karatunta, gashi wayar ta sa ma taƙi shiga gaba ɗaya, kullum sai a ce mata tana rufe. Tana matuƙar tausayinsa da jin damuwar rashin zuwansa makaranta, amma babu wanda ta gayawa, ciki har da Yusra, dan ita bata son Yadda Yusra ke ƙoƙarin nuna mata cewar tana son Yazid.



Yau kamar Hajiya Zainab ta san Alhaji Ahmad ya shirya ganin Amina, taƙi yafiya ta je ta kwanta, ta saka shi a gaba a kan lallai sai ya bata kuɗin da ta nema a wurinsa na zata ƙara jari, shima kuma kamar ya san da wata a ƙasa sai ja mata rai yake, ya ce yau ya ce sai gobe, ba kuma dan ba shi da su ba, sai dai ya ce a cikin satin zai bata, sannan hankalinta ya kwanta, ta amince ta sako masa wata hirar kuma.

"Baban Khalil, yau na yiwa Khalil mata"

Daddy ya ce "To, Mata a ina kenan?"

" 'yar ƙanwar hajiya Salma ce, yarinyar nutsatsiya da ita, na yaba da ita sosai ga ta 'yar babban gida"

Ya ɗan kalleta sannan ya ce" Shi Khalil ɗin ya amince da hakan ne?"

"Ai kamar punishing ɗin sa zan a kan abin da yayi mini, kuma na san ba zai ƙi ba zai so ta ya manta za waccan yarinyar"

Ya ɗan ɗage kafaɗa ya ce "Ok, shikenan, Allah ya tabattar da Alkhairi"

Ta gyara zamanta ta ce "Amin, amma nan kusa nake son a kai kuɗin aure, ko kan mu tafi umarar nan ne"

Daddy ya ce "No, akwai wani abu da nake yi, sai na kammala zuwa idan kun dawo daga umarar, zan ga uban yarinyar tukuna"

To shikenan na gode sosai. Tayi maganar tana murmushi, ita dai idan har kaga walwala a fuskarta, to an biyewa ra'ayinta ne, ko da kuwa son zuciya ne. Suna nan zaune suna hira, Amina tayi sallama ta kai masa tea.

Hajiya Zainab ta kalleta a wulaƙance ta ce "Waye ya saki wannan aikin, an ce miki muna buƙata ne?"

Daddy ya yi saurin cewa "Ni nayi musu Magana ɗazu, na ce a kawo mini tea, zan yi aiki da daddaren nan"

"Ok ban sani bane" tayi maganar ba tare da zurafafa bincike ba. Amina dai ta ajiye kayan shayi tayi waje abinta, taji daɗin tarar da Hajiya Zainab da tayi, ba damar Daddy ya tsareta ya hanata tafiya.


Ana ya gobe su Amina za su yi tafiya, Baba ya kira Amina, ya zaunar da ita ya dinga yi mata nasiha mai shiga jiki sosai.

"Uwata, kinga ni dai zuwanki birni na barki ne dan ki samu ki cika burinki, na yin karatu, bani da burin da ya wuce ki samu ingantaccen ilimi, ki samu miji nagari, kin san ɗauki ba daɗi da kuma irin miyagun alkaba'in da aka dinga janyo mana, duk saboda na goyi bayan ki zauna da ni a nan kiyi karatu, dan Allah Amina kar ki bani kunya, kinga in da zaki tafin nan, baki da kowa sai Allah, dan Allah ki mayar da hankalinki, ki nutsu kiyi abin da kika je yi, ki riƙe mutuncinki, ba danni ba ba dan halina ba ki kula da kanki Amina, ki kula da mutuncinki, kije lafiya ki dawo lafiya, dan Allah kar ki watasa mini ƙasa a ido".
Gaba ɗaya jikin Amina yayi sanyi, ta ce "In Allah ya yarda Baba, ba zan baka kunya ba, ba zan aikata duk wani abu da ya saɓawa abin da ka ɗorani a kai ba in sha Allah"
"To madalla, Allah ya bada nasara, Allah ya kiyaye ku, Allah ya kaiku lafiya ya dawo da ku lafiya, ya bada abin da aka je nema, da salularki zaki tafi ko?"

"Eh Baba, sunce zamu iya zuwa da ita"

Baba ya ce "Yauwa, na dinga kiranki, in ji abin da ake ciki, zan so in rakaki ko makarantar ne, amma kin san idan nayi yinƙurin hakan, mutan gidan za su kya cewa nayi laifi"

Amina ta ɗan gyaɗa kai ta ce "Zan so ka rakani Baba, amma bakomai Allah ya nuna mini ranar da zan rabaka da aikin nan, mu ci gashin kanmu"

Baba yayi murmushi ya ce "Amin uwata"
Sosai nasihar Baba ta ratsa Amina sosai, ta koma cikin gida, gefe ɗaya tana murna za tayi doguwar tafiya ta bar Kano a karo na farko a rayuwarta, wani sashin na zuciyarta tana fargabar ba ta san yadda tafiyar da competitions ɗin su zasu kasance ba.

Amina tayi ta saka ido, ko Daddy zai yi mata sallama ko su haɗu amma bai nemeta ba, gaba ɗaya sai taji babu daɗi hakan, har ta shirya da sassafe cikin goggagun uniform ɗinta, tayi kyau sosai, amma Daddy bai fito ba, a wannan karon Hajara ce ta kai mata Akwati har gaban mota, Fadila na kallonsu suna ta shirin tafiya, amma ko kallo ba su isheta ba. Baba yayi ta yi mata nasiha da Addu'a.

A wannan karon ma, Zakiru ne ya kai ta har makaranta, tuni an fito da zungureriyar motar makarantar su, sauran ɗaliban da ba da su za a je ba suka fito harabar makarantar ana kallonsu, ana ɗaga musu hannu, su Amina suka ɗuru a motar makaranta, suka kama hanya.



KU BIYONI BABBAN BIRNIN TARAYYA DOMIN JIN YADDA ZATA KAYA.
AYSHERCOOL
08081012143GABA DA GABANTA
BY
AISHA ADAM AYSHERCOOL



47

Hausawa suka ce tafiya mabuɗin Ilimi, Amina ta ga abubuwa da dama, wanda tun da take bata taɓa barin garin Kano ba, amma sai gata a hanyar babban birnin tarayya Nigeria wato Abuja, suna tafe a hanya ana tsayawa masu uzuri su yi da cin abinci, Baba yana ta kiranta a kai a kai yaji ya hanya, haka ma Ammin Azima tana kiranta, sai kuma ita da take kiran Inno, sai dai sam Daddy bai kirata ko sau ɗaya ba.

Sai Azahar su Amina suka sauka garin Abuja, a wani katafaren hotel da aka kama saboda saukar ɗaliban, Amina ɗakin da aka ajiyesu su uku ne a ciki.
Amina taji shiru, Daddy ya ce mata za a zo a tafi da ita gidan Abokinshi in da zata zauna, amma taji shiru, ita ba rashin tafiya da ita gidan abokin nashi ne ya dameta ba, rashin jin ɗuriyar Daddyna ne ya dameta.

Har zuwa dare bai kirata ba, dan haka ita tayi kasadar kiransa, domin jin ko lafiya.
Sai da ta kusa tsinkewa sannan ya ɗaga wayar, cikin kamilalliyar muryarsa ya yi mata sallama.

Ji tayi kamar ta kashe wayar, dama yana nan normal amma yaƙi kiranta yaji ko sun sauka lafiya.

Muryarsa ta ji ya ce "Yaya kuma ki ka yi shiru? Akwai damuwa ne?"

Wani haushin ne ya sake kamata, wasu lokutan Daddy akwai iya kunna mutum.

"Bakomai" ta bashi amsa a taƙaice.

Ta kasa kuma cewa komai, shi ma kuma bai sake cewar ba duk suka yi shiru, ƙarshe Amina ta gaji ta kashe wayar ta ajiye.

Jin ta kashe wayar ya sanya Daddy sauke wayar daga kunnensa, ya bi wayar da kallo yana murmushi, ya ɗan kashingiɗa ya ce "Meenal kenan, dole ki saba da shiga damuwa a duk lokacin da kika mini laifi, na fuskanci wannan shi ne hukuncin da ba kya so"
Ya sake ɗaukar wayar, ya shiga gallery lock ɗinsa, in da yake adana hotuna, yana kallon hotunan ta, wasu hotunan shi ne yayi mata su, wasu kuma shi ya saka ta tura masa, ya dinga kallon hotunan yana murmushi, ya tsaya a kan wani hotonta da take sanye da uniform, ta goya jakarta tana murmushi, ƙuruciyarta ta fito sosai musamman yadda ta riƙe hannun jakar bayan ta goya jakar.

Ɗora wayar yayi a kan ƙirjinsa, yana jin wani al'amari yana fuzgarsa a game da Aminan.

A yau ne su Fadila zasu fara jarrabawar second semester, sai dai ta kasa zaune ta kasa tsaye, saboda rashin ganin zuwan Yazid, haka nan taji hankalinta ya tashi, bata son ya rasa jarrabawar nan.
Kan ta shiga ajin ta samu wuri ta tsaya, ta kira shi a waya, sai dai wayar tayi ringing bai ɗaga ba.
Haka ta shiga ajin ta zauna, aka farra jarrabawa, amma babu Yazid babu dalilinsa gaba ɗaya sai ta kasa nutsuwa ta kasa rubutun jarrabawar, ji take ina ma zata iya yi masa jarrabawar bata manta taimakon da yayi mata a baya ba.

Jin ɗaya daga cikin invigilator ya ce "Sheikh sai yanzu?" Ya sanya Fadila ɗagowa da sauri.

Kasancewar har da TJ abokin Kankiya, a malaman da suke invigilating ne ya sanya ya dakawa Yazid tsawa ya ce "Get out, saboda ba ka san darajar jarrabawar ba, shine sai yanzu zaka zo jarrabawa, ka yi asararta kuwa, gobe idan kana so ka zo da wuri"

Ɗaya malamin ya ce "A'a yi haƙuri, na san ba zai makara intentionally ba, ya aka yi ka makara Sheikh" Kasancewar malamin sukan haɗa jam'i da Yazid a masallacin makaranta, ya sanya ya san shi.
Yazid ya ɗan yi murmushi ya ce "Afuwan Sir, na biya Asibiti ne an yi mini dressing, idan na makara ba za su yi mini ba"

Malamin ya ce "Meya sameka ake maka dressing?"

Yazid ya ɗan juya ya ɗagawa malamin rigarsa, sai ga plasta da aka saka a rufe masa wurin da aka yi masa aiki ya ce "An mini aiki ne, har sau biyu a wurin, ina zuwa ana wankewa duk bayan kwana uku"

Fadila kuwa sai leƙawa take kamar ita yake nunawa. Cikin tausayawa malamin ya yiwa Yazid sannu, tare da bashi wurin zama, ya bashi booklet ya kai masa question paper da Attendence har wurin zamansa duk yayi, ya yiwa malamin godiya, ya fara jarrabawar sa.

Sai da Fadila taga Yazid ya nutsu ya fara jarrabawa, sannan hankalinta ya kwanta, ta cigaba da tata jarrabawar, sai kuma ta tuna ai akwai abubuwa da yawa da aka yi baya nan, da yaya zai yi jarrabawar? A take ta tuna gwanancewa irin ta Yazid, ba abune mai wahala a wurinsa ba ya cinye jarrabawar ba.

Sai da tayi wannan tunanin, ta samu cikakkiyar nutsuwar cigaba da rubuta jarrabawata cikin nutsuwa.

Suna nan suna jarrabawa, Kankiya ya shigo yana zazzagaya su, yana wani muzurai da zare da ido, ya zo kan Fadila ya tsaya, yana kallon abin da take rubutawa, haushi ne ya kama Fadila, dan ko san ganin Kankiya bata yi, ta janye takardarta ta ajiye biron tare da haɗe rai.

Yayi ƙasa ƙasa da murya ya ce "Ina son ganinki yau, idan kun gama jarrabawa"

Ɗagowa tayi ta kalleshi ta ce "Ba zan zo ba"

"Kin san me rashin zuwan naki yake nufi kuwa?"

"Ban damu ba, kaje kayi duk abin da kaga zaka iya yi".
Yayi murmushi ya ce "Kar in ɗau matakin da zuciyarki ba zata iya ɗauka ba"

"Nace kaje kayi duk abin da ka ga dama, kuma ka matsa daga kaina kan in yi Magana da ƙarfi in janyo hankalin mutane kanmu"
Ganin da gaske take zata aikata abin da ta ce, ya sanya shi yin gaba, yaje ya tsaya a kan Yazid ma, ya ƙure shi da ido, amma Yazid bai

Please Login or Register in order to submit comment