Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sun ishe ni, na kula da mijina da sabgogina, yanzu admission nake jira, kema kar ki zauna da kin samu dama ki cigaba da karatunki kawai in dai zai yarda".

Hafsa ta ce "Eh zai yarda, yana ma yi mini zancen, amma ya ce na bari ya nutsu daga hidimar bikin nan da yayi"

Amina ta ce "Haka ne biki akwai hidima kam, Allah ya baku zaman lafiya"

Har bayan la'asar ita Mummy ma sam bata san Hafsa na gidan ba, baga tafi ba, Bayan la'asar Khalil ya dawo, a lokacin ma Daddy ya dawo.
Daddy yayi murna sosai da ganinsu, mussaman Hafsa yayi ta yi musu Addu'a da saka albarka, tare da yi musu nasiha a kan haƙuri da juna.
Sai da aka yi sallar isha'i sannan suka rako su Khalil, har mota.

Fadila da taga wucewarsu abin ya bata mamaki, dan bata ma san sun zo ba.
Sashin Mummy ta tafi, tana mamakin yadda suka zo, amma basu zo wurin Mummy ba.

"Mummy"
"Na'am ya aka yi?"

"Mummy Yaya Khalil na gani da matarsa, zasu tafi yanzu kuma banga sun zo wurinki ba"

Cikin mamaki ta ce 'Ban gane sun zo zasu tafi ba dama basu tafi ba?"

Fadila ta ce "Dama kin san sun zo ne?"

"Eh na sani, amma ni korarsa nayi"

"Taɓ, aikuwa suna wurin waccan Yarinyar, gasu can Daddy da ita sun yi musu rakiya"

A fusace ta ce "What! Yaron nan kuwa yana da tunani? Au wurinta ma ya koma?. Gaba ɗaya Khalil bashi da tunani ba shi kuma da hankali, amma na san abin da zan yi, zan yi maganinsa kuma ita kanta sai na ja mata kunne a kan Khalil, munafuncin Yarinyar nan ya isheni"

Fadila ta jinjina kai ta bar ɗakin Mummy.

Bayan su Hafsa sun je gida ma, rarrashi da nasiha Khalil ya cigaba da yi mata, dan babu wanda za a yiwa abin da Mummy ta yi wa Hafsa ya ce zai ji daɗi.

Cikin sanyin jiki ta ce "Amma auren nan zai yi mana albarka kuwa, tun da har Mummy bata so"

Khalil ya ce "In sha Allah, zai yi mana kuma ita ma zata sauko" Hafsa dai kawai jinsa tayi, amma ba dan ta yarda da abin da yace ɗin ba.

Ko da Hafsa suka yi waya da Mama, ta gaya mata sunje gidansu Khalil, amma am bata gaya mata yadda suka yi da Mummy ba, dan bata son ɗagawa Maman hankali.
Sati guda da Bikin Hafsa, Mama ma ta tare a gidan Alhaji Ilyas, cikin ikon Allah dama yaran nasa ba ƙanana bane ba, duk da girmansu, dan haka suka yi ta murna da auren da mahaifinsu yayi.


Haka rayuwa ta cigaba da juyawa, cikin jujjuyar lokaci sakannin zuwa mintun, awanni zuwa sa'oi kwanaki da kuma satuttuka suka dinga shuɗewa.
Hafsa ta yi wata guda a gidan Khalil, cikin tsananin so da ƙaunar junansu, sai tattalata yake yi yana nuna mata ƙauna, gefe guda kuma a tsorace take, saboda iƙrarin Mother a kan za ta yiwa Khalil aure, shikenan idan ta yi wa Khalil aure ta kaɗe, dan ta san budurwa zata aura masa, kuma 'yar masu kuɗi, shikenan ita ma ta san wannan rawar kan da yake a kanta, dan yanzu ya aureta ne, amma da ya samu wata zai daina tattalinta.

Ranar da ta cika wata biyu, ya ɗauketa ya kaita har gida wurin Mama, Mama tayi murna sosai da ganin Hafsa, tayi sharrr da ita ta sha kwalliya, ita kanta Hafsa tayi murnar ganin Mama, alamu suka nuna tana cikin kwanciyar hankali tare da mijinta da 'ya'yansa. Da suka tashi dawowa gida, sai da ya kai Hafsa gidansu Abdul suka gaida mahaifiyarsa.

Washegari kuma, Khalil ya saka Hafsa ta kira Amina, dan ta basu kwatancen gidansu a Shanono zasu je gaida Baba.
Amina kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha, sai murna take bakinta yaƙi rufuwa.
Tayi musu kwatance sannan ta ce "Khalil, Dutse fa yaushe zaku je?"

Ya ce "A satin nan in Sha Allah"

"To yayi kyau, na gode sosai da sosai, dan Allah idan kunje Dutse har gidan 'yan uwan mamanku kuje, kai kayi zumunci da su".

Khalil ya ce "In sha Allah, ko kina da saƙon da za a kai Shanono"

Ta ce "A'a, ai baifi sati biyu naje, na gode sosai"

Ya ce "Babu komai, kar ki damu"

Ta kaste wayar, Daddy na fitowa daga wanka, tayi tsalle ta rungume shi.

Ya ce 'Tooo, ya aka yi ne?"

"Su Khalil ne zasu garinmu, wai zasu je gaida Babana"

Yayi murmushi ya ce "Ai yayi kyau, yakamata su faranta miki, kamar yadda kika yi tsayin daka a kan kiga bikinsu ya yiwu"

"Kai Alhamdilillah, ji nake kamar nayi rawa wallahi"

Yayi murmushi ya ce "ai kin saba dama"


Su Khalil sun samu karɓuwa sosai a garinsu Amina, Inno ta karrama su sosai da sosai ita da Baba, Khalil yayi musu alheri da yamma suka juyo Kano, Inno kuwa ta haɗa musu kayan tsaraba sosai tana musu Addu'a.
Amina suka yi waya da Baba, ya sanar mata ai su Khalil sun zo, ta dinga murna tana jin daɗi.
Shi kam Khalil ba zai taɓa mantawa da abin da Amina tayi masa ba, ko iya ƙoƙarin ta na samun Hafsa da yayi, ya isa ya dinga ganin kimarta.

Bayan sun huta kwana biyu, Khalil ya kuma ɗaukar Hafsa zuwa Dutse su gaishe su, kuma suyi musu bangajiya, nan ma sun ga kara da karamci, suka dinga murna dan haka nan gari banza Khalil baya zuwa Dutse.


Salim kuwa biki ya nata ƙaratowa yana shiri, sai dai ya fara ƙuluwa da abubuwan da Fadila take yi masa, na wulaƙanci da cin mutunci, dan haka ya fara gaya wa Babarsa abubuwan da Fadilan take yi masa.
Hajiya Salma taji haushin hakan matuƙa, dan haka ta kira Hajiya Zainab a waya.

Hajiya Zainab bata kawo komai ba a ranta ta ɗaga wayar tana faɗin Hajjaju.

"Kin ga Zainab, abin nan idan mai yiwuwa ne ayi, idan ba mai yiwuwa bane ba a bar shi kawai, kince a haɗa auren ɗanki da 'yar 'yar uwata abu bai yiwu ba, zamu haɗa auren yaranmu amma Fadila sai wulaƙanci take yiwa yaron nan, idan fa bata so kawai a bar sabgar nan".

Hajiya Zainab ta ce "Me yayi zafi haka ke kuwa? Mu bi komai a sannu dan Allah, zan yi mata magana" Mummy tayi ta bata haƙuri, ta katse wayar ta tafi ɗakin Fadila.

Da mamaki Fadila ta kalleta ta ce "Mummy, ya na ganki a ɗakina yanzu?"

"Ban sani ba, wato dama munafuntata kika yi, kika ce mini zaki auri yaron nan, amma kike wulaƙanta shi ko? Hajiya Salma ta kirani rai a ɓace ta ce kina wulaƙanta mata ɗa. To kin kyauta kema kije kiyi duk abin da kika ga dama, kuyi ta cusa mini baƙin ciki ke da ubanki da ɗan uwanki tun da haka kuka zaɓa. Ba kwa ƙaunata ba kwa kishina, wai Khalil ya wanke ƙafa ya tafi garinsu yarinyar can, ya kuma je Dutse duk ba tare da sanin na ba, ga baƙincikin babanki kema kuma gashi kin tsiro da naki, na gode" ta juya fuuuuu ta fice ta barwa Fadila ɗakin.

Dafe kai Fadila tayi, kawai ta fashe da kuka, tama rasa me za tayi, 'yan kwanakin nan ni ko bacci bata iya yi, saboda tunanin auren nan, ga Mummy sai shirin biki take, ga shi shi kuma munafuki ya na kai ƙararta.
Take taji wani irin mugun takaici ya tokare ƙirjinta, tayi jifa da littafin hannunta ta cigaba da kuka.

Alhaji Ahmad yana ta shirin komawa Lagos, amma yana tunanin yadda zai bar Amina da Hajiya Zainab a gida, dama a yanzunma yana nan ɗin ba shiri suke ba.
Kwanciyar hankalinsa shine yana wurin Amina, amma duk lokacin da yake a wurin Hajiya Zainab, kwanan tashin hankali suke yi.



Hafsa na kwamce a kan doguwar kujera, Khalil ya ce ta zauna ta huta, yana ta ɗan yin aikace-aikacen da zai iya yi, Hafsa sai dariya take yi masa, yana mopping tana cewa 'gaskiya wannan mopping ɗin, to kar dai in ce a bar mini abina nayi aji haushi, amma gaskiya ba haka ake yi ba"

Yayi dariya ya ce "Aikuwa sai nayi, kuma idan na gama sai kin mini godiya, in gama in je in ɗora girki"

Hafsa ta ce "Kaiii, ashe yau ciki zai ɓaci, za ayi ta gudawa"

"Aikuwa sai na dafa, kuma sai kin ci"


Kamar an wurgota sai ganin Hajiya Zainab suka yi a tsakiyar falon.

Miƙewa Hafsa tayi, gaba ɗaya jikinta ya ɗau rawa, ga 'yar rigar jikinta ba in da ta kai.

"Mu..mu... Mummy sannu da zuwa" Hafsa tayi maganar cikin rawar murya.

Wani kallon banza tayi mata ta ce "Ba shakka, kin zo kin samu wuri kin miƙe ƙafa, kai kuma har ka zama bawa ko? Wato Khalil saboda baka neman albarka saboda ka nuna mini ban isa ba, ka wanke ƙafa ka tafi har Shanono wurin wancan matsiyatan ni kake wulaƙantawa ko Khalil".

Jiki ba ƙwari Khalil ya ce "Mummy ba haka bane...

"Rufe mini baki, munafuki" ya sunkuyar da kansa ƙasa, yana sake mamkin hali irin na mahaifiyarsa.

"To bari kaji in gaya maka, wallahi ba za a taru a mallake mini kai ba, ban haifawa kowace mace bawa ba, ka tattara kayanka ka koma wurin aikinka, wallahi na bincika baka koma ba, hukuncin da zan maka sai ya baka mamaki, kuma ban yarda ka bar garin nan da ita ba, ke kuma ki fara lissafa kwanakin da suka rage miki a gidan nan, dan yadda yake wannan rawar kan a kanki, nan gaba sai abin da Allah yayi, ina ga zai iya dukana ma saboda ke".

Khalil ya haɗa hannayensa biyu ya ce "Mummy dan Allah kiyi haƙuri, kinga bama ta jin daɗi, na miki alƙawarin da ta ji sauƙi zan koma"

"Au har ya kaimu ga fara jayayya ko Khalil? Da kan ka aureta sai ka tafi ka shafe kwanaki ban saka a idona ba, amma saboda ita ka fara yi mini musu ko? Khalil kar ka ƙure ni nayi maka baki fa"

A gigice ya ce "Shikenan, Kiyi haƙuri zan koma in Allah ya yarda".

"Kar ma ka koma kaga yadda zan yi da kai, sakarai" yadda ta shigo ta zazzage musu masifa, ko zama ba tayi ba ta juya ta fice. Dama tsarin da tayi, idan ya bar garin zata san yadda zata yi ta kori Hafsa, dan bata ƙaunarta ko kaɗan.


Mummy fa ta tatara Fadila ta fita a sabgarta, hakan ya sake jefa Fadila cikin tsananin damuwa, ko Abinci bata iya ci, karatunma ta ajiye bata iyawa gashi test suke yi a makarantar.

Da ƙyar a daddafe ta iya yin test ɗin yau, saboda azabar ciwo da kanta yake yi.

Bayan sun gama test suna da sauran lectures, sai dai ba zata iya jira ba, kuma gaba ɗaya ko son zuwa gida ba tayi, saboda ta san damuwa zata je ta kuma tarar wa.
A hankali ta tashi ta bar ajin, saboda yadda hayaniya tayi yawa a ajin.

Wani ajin da babu kowa taje ta samu ta zauna, sai da kanta ha cigaba da yi mata wani irin matsanancin ciwo, ga ƙirjinta yayi nauyi, da ƙyar take numfashi.

Har Yazid ya shiga aji, suna jiran malamin da zai shigo musu, yaga kiran Fadila.
Ɗaga wayar yayi yana mamakin dalilin kiran nata, dan harara ce take haɗa shi da ita a kwanakin nan.

Yana ɗagawa yaji muryarta sama-sama ta ce "Dan Allah ka zo level 4, bani da lafiya ka zo ka kaini gida"

Cikin hanzari Yazid ya tashi, ya bar ajin ya nufi level 4, a can ƙarshen ajin ya hangota ta kifa kanta.
Ya ƙarasa in da take da sauri yana kiran sunanta. Ɗago idonta tayi sun yi jawur, hawaye ne kawai ke fita daga idonta.

"Subhanallah, Fadila meyafaru ne?".

"Bani da lafiya, na kira Yusra bata ɗauka ba ina ga suna lectures ne, dan Allah ka kaini gida kaina zai fashe, dishi-dishi nake gani"

Yazid ya ce "A'a mu dai je Asibiti, in da kika taɓa kaini ɗin nan, ta so muje" jiki na rawa ta tashi tsaye, ya sa hannu ya karɓi jakarta, sai dai jiri ya kwashe ta, Yazid ya riƙeta.
Aikuwa ta fashe da kuka ta ce "Bana gani sosai fa"

Yazid cikin damuwa ya ce "Sannu, tashi mu tafi daure".

Da ƙyar ta iya tsauwa, ta riƙe gefen rigarsa suka fito a hankali.
Suka ƙarasa wurin motarta, ya duba jakarta ya ɗau mukulli ya buɗe motar, ta shiga shi kuma ya zagaya mazaunin direba ya kunna suka bar makarantar.
Kan su kai Asibitin duk Fadila ta firgice, sai koke-koke take yi, tana riƙe kanta.
Yazid ji yake kamar ya cire mata ciwon, ya dawo da shi jikinta, yadda take yi ɗin nan zaka tabattar tana jin jiki sosai.

Suna zuwa asibitin aka karɓesu da gaggawa, kasancewar sun san Fadila nan da nan suka karɓeta, aka kwantar da ita.
Doctor Aliyu na ganin Yazid ya ce "A'a mutumin, yau kuma kai kawota?" Yazid ya ɗan yi murmushi.

Sosai take kuka tana kiran sunan Mummy.
Doctor Aliyu ya ce "Fadila ya isa haka, meyake damunki?"

Cikin kuka ta ce "Ni ka ƙyaleni, ina Yazid?"

Aliyu ya ce "To Yazid ɗin ne zai baki magani ko ni?"

"To ba kana kallona ba, ka ƙi yi mini komai, Zid ka mayar da ni gida in mutu a can"

Yazid yayi ƙasa da murya ya ce "Zan maida ke, Addu'a nake yi miki, amma kiyi shiru kin ji" ta fashe da kuka ta ce "Bana gani sosai"

"Zai daina in sha Allah, kiyi addu'a"

Ta ce "To, amma kaje gidanmu ka kira mini Mummy"

Ya ce "To shikenan, zan je in sha Allah" tana ta wannan surutan, gaba ɗaya Yazid ya shiga damuwa, ya zuba mata ido sai rawar sanyi take saboda zafin zazzaɓi"

Doctor Aliyu ya ce "Ka kwantar da hankalinka, zafin ciwo ne amma nayi mata allurar bacci, za tayi bacci zazzaɓin ma zai sauka"


Yazid ya ce "Allah ya sa"

Doctor Aliyu ya auna Bp ɗin Fadila, amma ya ganshi ya hau sosai.

Doctor Aliyu ya ce "Ya aka yi jinin Yarinyar nan ya hau haka?"

Yazid ya ce "Ban sani ba, nawa ya nuna?"

Aliyu ya ce "160/90mmgh, ya hau sosai, bari in je in Kira babanta yakamata su sani, ina ga a nan zamu riƙeta"

Jiki a sanyaye Yazid ya ce "To shikenan"

Bayan fitar Doctor Aliyu, Yazid ya matsa gaban gadon ya zuba mata ido. Sai yanzu ya lura da yadda ta ƙara ramewa.

Kamar mai raɗa yaji tana kiran sunansa.

A hankali ya matsar da kunnensa bakinta dan jin me take cewa.

"Yazid! Bana son sa ka gaya wa Mummy!!"

Ras gaban Yazid ya faɗi, ya kira sunanta amma yaga bacci take she's unconscious, amma tana ta nanata "Bana son shi!!"

Tofa!



AYSHERCOOL
08081012143LITTAFIN KUƊI NE, MAI BUƘATA YANA IYA TUNTUƁATA A KAN LAMBAR WAYATA.
08081012143



72


Jiki a sanyaye Yazid ya ce "Fadila, me kike cewa ne?"

Kasancewar bata hayyacinta bata san meya ke faɗa ba, a cikin baccin ta cigaba da kuka tana cewa bata son shi.

Tunani ya shiga yi, waye bata so ɗin ko Kankiya ne? Amma ai Kankiya ya bar makarantar ma tun bayan da abin nan ya faru babu daɗewa. Ya bawa kansa amsa.

Doctor Aliyu ne ya shigo ya miƙa wa Yazid takarda, ya ce yaje Pharmacy ya karɓo maganin.

Yazid ya karɓa je Pharmacy aka bashi maganin, ya tambayi kuɗinsa aka ce masa ai akwai kuɗi a family file ɗin ba sai ya biya ba.

Ya koma ya kai maganin ya tambayi, doctor Aliyu ya kira gidansu Fadila.

Doctor Aliyu ya ce "Na kira su, lambar mamanta a kashe babanta kuma bai ɗaga ba".

Yazid ya koma wurin Fadila ya zauna, yana ta saƙa da warwara, ya ɗan zuba wa Fadila ido, tayi rama sosai da sosai.
'kenan dalilin damuwarta kenan, kusan kullum cikin kuka?'.

Haka yayi ta wasi-wasi har la'asar Fadila bacci take, bata farka ba, Yazid ya tashi yaje yayi salla ya biya ya sayo wa Fadila fruit da kwalin exotic, in da Allah ya taimake shi da 'yan kuɗi a jikinsa.

Cikin ikon Allah ya koma babu daɗewa, ta fara motsi zata tashi.

Yayi saurin ƙarasawa gaban gadon nata, yana kiran sunanta.

Miƙa tayi, Yazid ya kawar da kansa ƙasa, ta kalli Yazid ta ce "Baka tafi ba?"

Ya ce "Eh, sannu ya jikin?"

"Da sauƙi ina, Doctor Aliyu?"

Ya miƙe ya ce "Bari naje nayi masa magana, ko zaki ci wani abun kan yazo?"

Ta ɓata rai ta ce "Ni bana ci, ka kira mini shi".

Yazid ya tashi, ya kirawo mata Doctor Aliyu.

A tare suka shigo ɗakin da take, Aliyu ya kalleta ya ce "Sannu ya jikin?"

"Da sauƙi, ka kira mini Mummyn?"

Aliyu ya ce "Wayarsu bata shiga, amma zan sake kira meya yake yi miki ciwo yanzu?"


"Kaina ne yake ciwo haryanzu wallahi, ga ƙirjina yayi nauyi"

Doctor Aliyu ya zauna ya ce "Yauwa yanzu gaya mini, yi min bayani, meke damunki jininki ya hau?"

Ta waro ido ta ce "Hawan jini kuma?"

"Eh, jininki ya hau, gaya mini meke damunki?"

Jikinta ya ɗanyi sanyi, amma ta kasa magana.

Aliyu ya ce "Talk mana"


Ta ɓata rai ta ce 'Bakomai, ni ka sallameni kawai in tafi gida"


Yazid ya ce "Jikin naki a haka zaki tafi?"

"Eh ni gida zan tafi"

Yazid ya ce "Dan Allah kiyi haƙuri ki zauna"
Ta galla masa harara ta ce "Ba zan zauna ɗin ba"

Aliyu ya ce "Ke masifaffiya, yana ta ɗawainiya da ke tun da ya kawo ki yake zaune yana kula da ke, amma kina masa masifa ba za a sallame ki ɗin ba"

"Kar ka sallame nin, tafiya zan yi da kaina"

Aliyu ya ce "Sannu Yazid, kana haƙuri da wannan fitsararriyar, ka fasa da ita zan baka ƙanwata"

Duk da yadda take fama da kanta, wata uwar harara ta gallawa Aliyu ta ce "Koma wace kai ka sani, na gaya maka ni ba saurayina bane ɗan ajinmu ne"

"To, Allah ya baki haƙuri, bari na sake trying lambar gidanku, ki samu ki ci wani abu, kan a baki magani"

Ba tace masa komai ba, Doctor Aliyu ya fice daga ɗakin.

Ta kalli Yazid ta ce "Ka daɗe sosai a asibitin nan, ka tashi ka tafi na gode"

Yazid ya girgiza kai ya ce "Kar ki damu, kinga ga Fruit na sayo miki ko zaki iya sha"

Haka nan taji ya bata tausayi, ta ce "Bani ayaba in ci"

Ya ɗauka ya miƙa mata, sai ɗan yamutsa fuska take yi.

Ya kalleta cikin kulawa ya ce "Ya aka yi, ya naga kina yamutsa fuska?"

Kamar za tayi kuka ta ce "Zazzaɓin ya sauka, amma kaina ciwo yake yi, kuma wai jinina ya hau ni abin ya bani mamaki"

Ya kwantar da murya ya ce "Meke damunki har haka da jininki zai hau? Meyafaru ne?"

Kawai sai hawaye ya fara bin fuskarta, har da sheshsheƙa.


Yazid ya ce "Yi haƙuri, dan Allah ki daina wannan kukan ya isa haka, kinga baki da lafiya".

"Ni ka ƙyaleni nayi"

Ya ce "No, ba zan iya ba, bana son ganin kukanki, ci ayabar su zo su baki maganin"

Ya dinga lallaɓata sai dai tana ci tana kuka, yana cigaba da rarrashinta.

Sai bayan la'asar daf da magariba sannan Aliyu ya samu Mummy a waya, ya sanar mata da Fadila fa tana Asibiti tun wurin sha biyu.

A rikice ta ɗau mota ta bazamo Asibiti wurin Fadila.

Tana zuwa ta nufi Vip rooms tana dubawa, dan ko Doctor Aliyun bata nema ba, cikin sa'a a ɗaki na uku taga Fadila a ciki, gefenta kuma ga Yazid a zaune.

Da sauri ta ƙarasa gaban gadon da Fadila take kwance tana faɗin "Fadla, lafiya kuwa? Meyasameki garin yaya aka kawo ki asibiti?"

Kasa Magana Fadila tayi, sai kallon Mummy da take yi, hawaye fal idonta.

Yazid ya risuna yana gayar da Mummy.

Ƙarewa Yazid kallo tayi, daga sama zuwa ƙasa ta ce "Waye wannan?" Ta tambayi Fadila maimakon ta amsa gaisuwar Yazid.

"Ɗan ajinmu ne" Fadla ta bata amsa.

Still bata amsa masa ba ta ce "Fadila maimakon ki kira gida, sai a kawoki Asibiti ba wanda ya sani?"

"To Mummy ba duk an kira lambarku bata shiga ba, ke taki bata shiga ba, ta Daddy kuma baya ɗagawa"

Mummy ta ce "Dama ya za ayi ya ɗaga, yana ta waccan banzar yarinyar" ta kalli kayan Fruit ɗin dake kan drower a gefen Fadila ta ce "Wannan kayan fa, waye ya kawo su?"

"Yazid ne ya saya mini" ta bata amsa.


Hajiya Zainab ta kwaɓe baki ta ce "Waye kuma hakan?"

Fadila ta ce "Gashi nan, a kusa da ke"

Ɗan guntun tsaki tayi ta ce "Wai meyasameki ne ma?"

Fadila ta ɓata fuska ta ce "Kaina ne yake ciwo, da ƙirjina".

Yazid ya miƙe ya ɗan risuna ya ce "Mummy ni zan tafi, Ukty as'alullahil azim, rabbil arshil azim an yashfiyaki".

Fadila ta ɗan yi murmushi ta ce "Na gode sosai, na zaunar da kai ka gaida gida".


Yazid ya yi murmushi ya ce "Bakomai, Allah ya ƙara sauƙi"

Har zai fita Mummy ta ce "Kaga, zo ka kwashe wannan kayan ka tafi da su, ka ƙarasa su ka cinye"

Fadila ta ce "A'a bar mini ina so, zan ci"

Mummy ta ce "Ke ba sai a sai miki wani ba, ai naga shi mabuƙaci ne"

Yazid a ƙasan ransa bai ji daɗin abin da Mummyn tayi masa ba, amma ya maze ya ce Bakomai Mummy, Allah ya bata lafiya.

"A'a ba Mummy ba, Hajiya Zainab" Yazid ya jinjina kai ya fice.


Mummy ta mayar da kallonta ga Fadila ta ce "Ke wai waye wannan?".

"Mummy na gaya miki ɗan ajinmu ne, wannan Yazid ɗin ne da nake baki labari kwanaki"

Hajiya Zainab ta tsuke fuska ta ce "Meye alaƙarki da shi?"

Fadila ta ɗan numfasa ta ce "Kamar dai yadda na gaya miki a baya Mummy, bakomai, Yazid yana taimaka mini sosai a harkar karatu, iyakacinta kenan. Amma ba abin da nake tunani bane ba.


"Au ai kema na ɗauka gajiyayyen zaki ɗauko mini, bayan da sa ranarki a ka, kalli wani matsiyacin takalmi a ƙafarsa, yadda idaunsa suka yi fici-ficin Nan da gani yunwa yake ji"


Yazida data fara ƙosawa da mitar Mummy ta ce "Ki kwantar da hankalinki, ni ba son Yazid nake ba, ba tsarar aurena bane ba, kawai dai yana da kirki ne"

Doctor Aliyu ne ya shigo shi da wasu Nurses guda biyu, yana ganin Mummy yayi murmushi ya ce "Hajiya, ashe kin ƙaraso"

Mummy ta ce "Eh, na zo tun ɗazu, ya aiki?"

"Alhamdilillah, Hajiya ki ritsa ta tayi miki bayanin meke damunta, jininta ya hau sosai"

Hajiya Zainab ta ce "Innalillahi wa innalillahi raji'un, kamar ya hawan jini?"

"To gata nan dai ki tambayeta"

Hajiya Zainab ta kalli Fadila ta ce "Fadila garin yaya jininki ya hau, a wannan shekarun naki haka?"

Shiru Fadila tayi a ranta ta na jin dama zata iya gaya wa Mummy abin da yake damun zuciyarta. Amma tayi shiru ta ce ita ma bata san dalilin hawan jinin ba.


Bayan sallar isha'i Daddy yana zaune yana cin Abinci, suna hira da shi da Amina, ta ce "Baby, ɗazu da ka bar samsung ɗinka a gida an kiraka, amma dai ban ɗaga ba.

Yayi murmushi ya ce "Meyasa baki ɗaga ba?"

"To na sani ko wayar ta sirri ce?"

Ya kalleta ya ce "Kina tsoron ko wata ce ta kirani a wayar?"

Amina tayi murmushi ta ce "Idan ma watan ce ta kiraka ina ruwana, normal ne ai"

Ya ce "Ba wani normal, kizo ki isheni da mita da kumbura baki saboda kishi ba"

"Ba wani kishi da zan yi, kowa iya allonsa ya wanke kawai, ni dai na san na riga na sha kwana a nan" tayi maganar tana ɗora hannunta a ƙirjinsa.

Ya saka nasa hannun a kan nata hannun yana kallonta ya ce "Tabbas hakane, kin riga kin sha kwana a zuciyar mijinki Amina, Ahmad na matuƙar ƙaunar ki sosai Meenal, kin kawo haske na musamman a rayuwata, kin fitar da ni daga cikin wani duhu da ya dabibaye rayuwata a kan Zumunci da kuma ciyar da dukiyata. Ina alfahari da ke Allah ya yi miki albarka"

Tayi murmushi ta kalleshi ta ce "Ni yakamata nayi maka godiya, da ka bani fitilar haska rayuwata ta ilimi, ka dinga kula dani, ka nuna mini nima 'ya ce, duk da yadda iyalanka ke ƙyamata, amma baka ƙyamace ni ba, ka aureni, kake ta nuna mini kulawa ni da iyayena. Ni yakamta nayi maka godiya"

Ture kwanukan Abincin yayi, ya ɗorata a kan cinyarsa, ya rungumeta sosai a jikinsa, yana cigaba da gaya mata yadda yake sonta.

Kamar ba babban mutum ba, ya ce "Sweetyna".

"Na'am Daddy" ta amsa tan jan gemunsa a hankali.

"Zan biya mana umara, mu da mutum biyar, kiyi selection wanda kike ganin ya dace mu tafi tare da su".


"Wayyo Allahna daɗi, Allah ya ƙara maka arziƙi Daddy, abin da nake ta buri a rayuwata, ina burin zuwa makka".

"Da Hajji na so biya mana, amma na san maybe lokacin Babyna yana cikin ki, tafiya ba zata yiwu ba" yayi maganar yana shafa cikinta

Tura baki tayi tana murmushi, ya ce au dariya ma na baki, wataƙila

Please Login or Register in order to submit comment