Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

rana bayan dawowar Amina daga makaranta, ta shirya ta sha kwalliya, tana jiran dawowar Daddy sai kace matar gidan.
Da ya dawo, dai tarairayarsa take tana nan nan da shi, kasancewar rana ce sosai, Hajara tana can sashensu, Amina suka zauna a babban falo suka ci Abinci, Daddy ya ce idan aka yi sallar la'asar zai kaita tayi printing slip ɗin.
Amina babu kunya tayi ɗare ɗare a kan cinyar Daddy, yana biyewa shirirtarta.
Hajara kuwa da munafurci ke cigaba da cinta, ta leƙa ɗakin Amina taga bata nan, dan haka ta fito falo, dan ta lelleƙa ta ga ko yanzun ma suna tare.
Sai dai a wannan karon ma ta kuma katarin ganin Alhaji Ahmad da Amina tare, ya sanya ƙarshen chocolate a bakinsa, ita ma ta sanya ɗaya ƙarshen a bakinta, suna ci a hankali tana kallon idonsa tana murmushi.
Cak Hajara ta tsaya, ta dafe bakinta, kuma taƙi tafiya ta tsaya ganin ƙwal uwar daka.
Aikuwa suna cin Chocolate ɗin, suna zuwa tsakiya ya haɗe da bakin Amina yana murmushi.

A hankali Hajara ta koma, saboda a wannan karon bata san matakin da zai iya ɗauka a kanta ba idan ya ganta, ji tayi ina ma da hanyar da zata silale taje ta gayawa Baba ya zo ya gani da idonsa, amma sai ta tuna gargaɗi da kashedin da Amina tayi mata ɗazu da Safe.

Bayan sallar la'asar, Daddy yau ɗau Amina a mota, ya sanarwa da Baba cewar zai kaita su cire slip ɗin jarrabawa.
Bayan sun dawo, Daddy ya danƙawa Amina tarin kayan karatun da ta samu na kyaututtuka a wurin competition, sai kuma kuɗinta ya ce ba zai bata ba, sai dai ta faɗi abin da za ayi mata da su.

Ta ce "Ina son ka ɗauki dubu ɗari biyu, a kaiwa Inno dubu hamsin, Hajara da Zakiru a basu dubu ashirin, sauran idan zasu isa a saiwa Baba gida a bashi jari"

Daddy yayi murmushi ya ce "To ai duk kin rabar da kuɗin, kuɗin naki baza su a rabar haka ba sannan a saiwa Baba gidan ba, amma zan san abin da zan yi. Sannan ni kuma ki bar kuɗinki Amina ni yakamata na baki bake zaki bani ba"

"Saboda ka raina ko?" Tayi maganar tana haɗe rai.

"Ni na isa in raina? Ban raina ba"

"To ni dai a raba kamar yadda nace, sauran ko jarin a fara bawa Baba, so nake ya tsaya da ƙafarsa in raba shi da wannan aikin da yake"

"Yadda kike so haka za ayi ranki ya daɗe" murmushi tayi tana ɓoye fuska saboda maganar ta sa ta bata dariya.
Babban abin da ya ƙara sanya Amina farinciki, shi ne sauya mata wayar da yayi zuwa wata haɗaɗɗiyar Samsung.
Amina tayi wani uban tsalle ta rungume shi tana shafa bayansa tana murmushi.

Kusan sati biyu, Daddy ya ƙi komawa wurin aikinsa, ya mayar da Amina tamkar matarsa, idan ka zo sai kayi zaton ita ce matar gidan.
Wasu lokutan ida suka bushi iska, idan aka tashi daga makaranta, sai su tafi ɗaya gidan nasa, su wuni a tare sannan su koma gida. Hakan ya ƙara musu tsananin kusanci da soyayyar juna.

Yau suna ɗaya gidan nasa, Kasancewar Asabar ce, ta sanya ta yiwa Baba ƙarya ta tafi wurin Daddy a ɗaya gidan nasa.
Sai dai yau ɗin sai cika take tana batsewa, tun bayan jin cewar su Hajiya Zainab zasu dawo.

"Meenalina, dan Allah ki daina fushin nan"

"Ba dole nayi fushi ba, nasan idan ta dawo tsakanina da kai sai dai kallo, ba kulani zaka dinga yi ba"

Alhaji Ahmad ya ce "Haba Babyna, ya za ayi na ƙi kulaki, kin san matsayinki a zuciyar nan tawa kuwa?"

"Idan matarka tana nan, matsayina mai aikinta, ita da take matarka uwar 'ya'yanka"

"Dan Allah kar ki fara Amina, na san yadda zan tsara mana rayuwar da zamu yi ko bayan ta dawo, ni kaina ba zan iya haƙura da ke ba!!!



(Sai da ku fans ɗina, ina yinku kamar yadda kuke yina kuke ƙaunar rubutuna💞💕)



AYSHERCOOL
08081012143GABA DA GABANTA
               NA
AISHA ADAM AYSHERCOOL

Arewabooks ayshercool7724
Watpad ayshercool7724

55

Hararsa tayi, taji tamkar ta yi masa tsaki, saboda haushin da ya mamaye ilahirin zuciyarta.
Ya kwantar da kai ya cigaba da rarrashinta, yana bata baki a kan zai san yadda komai zai tafi daidai ba tare da wata matsala ba.
  Amina dai kawai jinsa take, ba tare da ta gamsu da maganganunsa ba, dan yadda yake nunawa a kan Hajiya Zainab, tamkar tsoronta yake ji ma.

Bayan sun koma gida, Amina taje ta samu Baba, ya na zaune yana jin radiyo.
Amina ta kalleshi cike da ƙauna ta ce "Baba sarkin radio"

Yayi murmushi ya ce "Bari uwata, ai dole mutum ya saurari radio, domin ka san halin da duniya take ciki, kuma kinga mu da ba muyi karatun boko ba, radion nan makaranta ce a garemu"
Amina ta jinjina kai ta ce "Haka ne, Baba magana nake son muyi da kai"

"To uwata bari in kashe radion" Ya kashe radion ya bata hankalinsa yana saurarenta.

"Baba kaga sakamakon nasarar nan da nayi, na samu kuɗi masu yawa, bayan kayan karatu da na samu" Baba ya jinjina kai ya cigaba da sauraron ta.

"To dama kuɗin suna wurin Daddy, sai muka yi magana kaga Hajara da Zakiru duk tare muke aiki da su, nace a basu wani abu a ciki. Shi ma Daddyn duk da yana da kuɗi ai kaga yana ɗawainiya da mu, ko babu yawa shi ma a bashi wani abu" sai kuma ta yi shiri dan taga reaction ɗin Baba.

Baba ya ce "Cigaba ina jinki"

"Yauwa, to da nace sauran kuɗin, a sai mana gida a ƙauye mu baro cikin gidan yawan nan, sannan a baka jari, amma Daddy ya ce mini ba zasu isa ba, sai na ce ko a je ƙauye a mayarwa da Jarmai kuɗinsa, ya dawo mana da gonarmu, sauran kuɗin a biya ayi mana noma ko?"

Baba yayi murmushi irin na su na manya ya ce "To uwata, na ji amma batun aje ƙauye a mayarwa da Jarmai kuɗi ya bada gona bai taso ba, abu wurin shekara guda. Ni ba zan hanaki yin alkhairi ba, kuma kuɗi naki ne, abin da kika yi na kyauta da sadaka daidai ne, sauran ki bayar a saya miki gona, in an tashi a sayar in haɗa da abin da nake da shi ayi miki kayan ɗaki"

"Kayan ɗaki kuma Baba?"

Ya ce "Eh mana"

"Baba Allah zai kawo wasu, yanzu wannan ma ai babu wanda ya san za a samu, dan Allah Baba ni gonarka nake son ta dawo"

"A'a sai dai a saya miki gona, ai ni yanzu babu abin da wata gona zata yi mini"

Amina ta marairaice ta ce "Baba, baka san yadda nake ji a zuciyata zaman aikin gadin nan da kake, ana wulaƙanta mini kai ba, idan aka sai gona, aka noma abin da aka samu so nake ko kiwo sai a zuba maka, ka koma gida ka huta, Baba bana son aikin gadin nan, ni fa ba dan mutanen da na lissafo suma sun cancanci su samu wani abu a kuɗin ba, da duka zan bayar a sai mana gida. Ko kayi jari ka sauya sana'a Baba"

"Allah sarki uwata, Allah yayi miki albarka, komai lokaci ne kinji, ki daina damuwa, watarana sai labari. Ni dai fatana ki kula da kanki, idan lokaci yayi watarana dole na bar gadi, lokacin kin kawo ƙarfi sosai, sai na koma gefe na huta"

"To ai yanzu ma ina da ƙarfi"

Yai murmushi ya ce "A'a da saura"

Ƙarshe dai suka daddale a kan, za a sai kayan Abinci a kai gida, a sai kiwo a zuba.

Amina ta samu Daddy da maganar yadda suka yi da Baba, ya ce mata shikenan babu damuwa.

Daddy ya samu Baba suka kuma tattaunawa da Baba, ba tare da Amina ta sani ba.

Mamaki ne ya cika Inno, ganin uban tarin kayan Abincin da aka kuma aiko musu da maƙudan kuɗi daga birni, a wai Amina ce ta aiko da su, a sanadin karatun boko ta same su.
Baƙi ciki da hassada suka cika zuciyar su Baffa Lawan, duk da idan an aiko da kayan har da su ake ɗibarwa, su karɓe su koma gefe suna ƙananun maganganu.

Yau ya kama su Fadila zasu dawo, bayan shafe kusan wata guda a ƙasa mai tsarki, kuma ya kama Asabar ce ranar dawowar ta su.
Tun safe Amina da Hajara suke ta faman aiki, yayin da Hajara a ranta take son ganin ya zata kaya, alƙar Amina da Alhaji Ahmad zata ɗore ko kuwa Asirinsu zai tonu a wurin matar gidan.
Daren jiya kuwa Amina kusan kwana suka yi, suna rigima da Daddy duk a kan dawowar Hajiya Zainab, saboda ta san da ta dawo zata ɗora daga in da ta tsaya wurin wulaƙanci, da cin mutunci kamar yadda ta saba ita da Fadila.

Da magariba, Daddy da kansa ya tafi airport ɗaukosu, Fadila na ganinsa ta rungume shi tana murna, kamar ta shekara bata ganshi ba.

Ya kalli Hajiya Zainab ya ce "Sweetheart ya hanya?"

"Alhamdilillah, ashe kana gari na zata direba ne zai zo ya ɗaukemu"

Ya ce "Eh na shigo gari jiya" yayi maganar a taƙaice.

Ai tun a mota, ta fara buge-bugen waya, tana sanarwa su Hajiya Turai sun sauka yanzun nan, gasu a hanyar gida.
Bayan ta gama wayar Daddy ya ce "Haba Madam, daga dawowarki ko gida baki je ba kin fara kiran waya, ai kya bari muje gidan ku huta, in ganku sosai da sosai, tunda mun kwana biyu bama tare"

"Lallai ma kai ɗin nan, kai da wataran sai ka shafe wata uku baka ganmu ba, bamu ganka ba, shi ne yanzu kake wani ga zance ga magana. Kuma idan ban gaya musu ba suwa zan gayawa, ai gara sun san mun sauka lafiya hankalinsu ya kwanta" girgiza kai yayi, ya cigaba da tuƙi, ita kuma ta cigaba da mita.

Ko da suka isa gida, tare suka shiga falo, Zakiru tare da Baba ya biyo su da Akwatunansu.
Hajara na ganin Hajiya Zainab, ta washe baki ta risuna tana gaisheta, sai dai kamar yadda ta saba a wulaƙance haka ta amsa mata gaisuwar, irin wanzuwarta a wurin da rashinsa duk ɗaya a wurinta, take Hajara ta haɗiye murmushinta a ranta ta ce "Shegiyar mata, ai Allah ya ƙara ma abin da mijinki yake yi, mai baƙin hali kawai".

Ai kan sallar isha'i, tuni su Hajiya Turai, da wasu daga ƙwayenta suka cika gidan, suka dinga hayaniya, kamar ba a lokacin ta dawo ba.
Ita dai tunda Amina ta fito ta gaishesu,taga Hajiya Zainab tayi mata kallon banza, ba ta sake komawa ta kansu ba, ta koma ɗakinta tayi zamanta, Sai Hajara ce ta kai musu Abinci.
Gaba ɗaya hayaniyar ta ishi Fadila, ta wuce ɗakinta ta rufe ƙofa, domin ta samu nutsuwa, Alhaji Ahmad kansa sai bar musu gidan yayi, kamar ana taron biki.
Tun a daren ta fara kwance abin da ta zo da shi, ta hau yi musu rabo.

Alhaji Ahmad kuwa, bayan ya fita yayi sallar isha'i, Amina ya kira a waya, suka daɗe suna waya sai da ta tabattar masa da sun tafi, sannan ya dawo gidan.
Ko da ya dawo gidan, yana son sun ɗan yi hira, Hajiya Zainab ta ce ita a gajiye take bacci take ji.

Washegari sai bayan sallar Azahar sannan Fadila ta sanarwa da Yusra cewar sun dawo, Yusra tayi ta murna, ta ce anjima zata zo ta ganta.

Ganin da Hajara tayi kamar Amina na cikin damuwa, ya sanya ta dinga murna a ranta tana cewa Allah ya ƙara. Bayan Amina ta bata kuɗi masu yawa kan dawowar Hajiya Zainab.

Abdul yana ta son ya gaya wa Yusra yana sonta, amma ya kasa bai san ya zata ɗauki abun ba, kasancewar Khalil take so a farko, kuma shima a baya Ƙawarta Fadila yake so, bai san ya zata karɓi abin ba, ga kuma Khalil da yake ƙoƙarin bijiro masa da wani abu daban.

Washegari kamar yadda Yusra ta alƙawarta, taje gidansu Fadila domin ta ganta.
Da Amina ta fara karo a falo, Amina na ganinta tayi murmushi ta ce "Chef Yusy"

Yusra ta ɗan kalleta ta ce "Fadila tana nan ne?"

"Eh tana nan, ina son zan shiga classes ɗin ki na girki ya za ayi?"

Yusra tayi murmushi ta ce "Sai kin zo"

"To amma nawa zaki rage mini, kinga ni bani da kuɗi sosai"

Yusra ta ce "Duk kuɗin da kika samu? Naji ance kin yi nasara a cimpetiton da ake duk shekara a Abuja, amma baki yi mana ko walima ba"

Amina ta ce "Ai ma idan nace kuzo, na san ba zuwa za kuyi ba, ni irin cake ɗin da ki ke yi nake son na iya, mun taɓa oreder sa da 'yan ajinmu yana mini daɗi sosai"

"In dai Cake ne, idan na fara classes ɗin, ki zo na koya miki kyauta, idan na koma gida zan bayar a kawo miki".

"Dan Allah dagaske?"
Yusra ta jinjina mata kai.

"Kaii amma naji daɗi wallahi, Allah ya saka da alheri, aikuwa zan zo, idan kina so nima sai in koya miki abincin gargajiya, irin su dambu, Alkubus, tuwo kala kala, normal tuwo da na masu kamar ciwon sugar, har da su gurasa fa na iya su sinasir da sauransu" ɗan shiru Yusra tayi tana nazartar Amina ta ce "Dagaske duk kin iya wannan girke-girken?"

"Wallahi duk na iya, Inno ta koya mini girke-girke, har su yadda ake haɗa kwaɗon salak, kwaɗon rama da abubuwa kin san sun fi lafiya"

"Gaskiya ne, ko zamu shirya wani business tare ne? Muyi join classes, ki dinga koyar da Abincin gargajiya"

Cikin sauri Amina ta ce "Eh zan iya wallahi" Hajiya Zainab ta fito tana faɗin muryar wa nake ji ne haka?"

"Nice Mummy, na zo Amina ta tsareni da surutu, ina ga ma zamu fara join class tare, tun da na ga ta iya girkin gargajiya"

Haɗe rai Mummy tayi ta ce "Ke da wa? Sai ki ɗau wannan ƙazamar a cikin harkar sana'arki, wa zai mini aikin gidan nawa, shareta dan Allah ya gidan naku ya Mummynki?"

"Tana nan lafiya Mummy, ya hanya?"

"Lafiya lau, Fadilan tana ɗakinta. Ke kum wuce kije kiyi mini abin d ana saka ki, sai shegen surutun tsiya duk wanda ya zo ki tsareshi da surutan banza"
Amina ta juya rai a ɓace, ta bar falon.

Saura kwanaki uku kacal su Amina su fara WAEC, gaba ɗaya a gajiye take, Hajiya Zainab ta tsiro da sabbin salo na muzguna mata saboda taga jarrabawa take fuskanta, tayi ta sakata aiki ta hanata sakat balle tayi karatu, sai dai ta bi dare tayi karatun.

Yau da aka tashi daga makaranta, gidan Daddy ta wuce, domin ta zauna ta huta da yamm sai ta koma gida.
Sai dai tana zuwa ta tarar da Daddy a gidan.
Yayi mamakin ganinta, mussman yadda ya ganta a gajiye.
"Babyna lafiya kuwa?"

A gajiye ta ce "A gajiye nake ne, zuwa nayi na huta na san da naje gida, matarka ba zata bari in huta ba, za tai ta sakani aiki, ni kuma a gajiye nake hutu nake so, jarrabawa zamu fara"

Cikin matuƙar tausayinta ya miƙe ya janyota jikinsa yana mata sannu.
Ta lumshe idanunta ya zare mata hijjabin jikinta, yana ɗan matsa mata jikinta a hankali.
"Da na sani na zo na ɗauko ki daga makarantar, ni gani nayi ma kina ramewa"

"Ba dole in rame ba, wannan matar ta sakani a gaba, kullum cikin zagi da hantara"

"Am sorry on behalf of her, bari in kawo miki ruwa" ya tashi ya ɗauko mata ruwa, ya kawo ya bata ta sha, yayi mata order Abinci.
Kusan tun da Hajiya Zainab ta dawo, basu sake samun damar haɗuwa ba sai yau.
Ta nemi wuri ta kwanta cike da gajiya da rashin bacci da ya sanya mata ciwon kai.

Daddy ya duƙufa Sosai, yana ta aiki a system, Amina ta ce "Daddy aikin me kake yi ne?"

"Lissafi nake, a cikin Azumi zan fitar da Zakka in Sha Allah"

"Mhmm dama kana bada zakka?"

"A'a wannan karon zan fara" yayi maganar yana hararata

Tayi murmushi ta ce "Wa zaka bawa?"

Ya ɗan nisa ya ce "Mai rabo"

Amina ta ɗan nisa ta ce "Ina son dan Allah a taimakawa 'yan garinmu da wani abu daga cikin zakkar, muna da mabuƙata sosai"

"Shikenan, za a duba in sha Allah Meenalina"

"Godiya muke, Allah ya ƙara arziki"

"Amin Sweetheart, jibi in Allah ya kaimu zan koma"

Ta ɗan zabura ta ce "Haba dai?"

Ya jinjina kai ya ce "Eh"

Kamar tayi kuka ta ce "Daddy why?"

Ya riƙo hannunta ha ce "Meenalina, am so much addicted to your care. Idan ina cigaba da ganinki, asirnmu zai iya tonuwa, sannan bana jin daɗin yadda wasu abubuwan suke gudana, alhalin ba zan iya baki kariya ba. Idan na koma na yi nesa da ke, maybe zan fi samun nutsuwa iyakaci dai zan yi matsananciyar kewarki".

Shiru Amina tayi, amma kusa maganar Daddy haka take, idan suna cigaba da ganin juna, kusancinsu sake ƙaruwa yake yi, kuma a kowane irin lokaci, Asirnsu yana iya tonuwa, dan a dawowar Hajiya Zainab, da taƙi yadda su haɗu, har Kitchen ya bita.

"Maganarka haka take Daddy, Allah ya zaɓa mana abin da yafi alkhairi, nima ba zan so asirnmu ya tonu ba, amma kar ka manta alƙawarrukan da ka yi mini"

"In sha Allah ba zan manta ba, zan yi Kamar yadda nayi alƙawarin, zan san hanyar da zan sama mana, kiyi karatu da kyau my love" yayi maganar yana rungumeta yana jin yadda yayi kewarta sosai.

Suna tare har Yamma liƙis, sannan ya kai ta gida ya ajiyeta a bakin layi, ya wuce.

Da daddare Hajiya Zainab tana ta hira da ƙawayenta a waya, Daddy yana gefe yana cigaba da lissafinsa, gefe guda kuma kewar Amina tana damunsa, duk baya walwala. Hakan bai damu Hajiya Zainab ba, ganin yana lissafin kuɗi ya sanya ta matsa kusa da shi ta ce "My dear ya batun zuwa nema wa Khalil aure ne?"

"Ki ɗan bani lokaci tukuna" yayi maganar ba tare da ya kalleta ba.

"Amma  kai fa kace idan mun dawo zaka nema masa"

Daddy ya ce "Yanzu abubuwa sun yi mini yawa, ki ɗaga mini ƙafa sai na koma na dawo tukuna"

A ɗan hasale ta ce "Amma dai ka san na riga nayi maganar da uwar yarinyar ko?"

"Kinga idan ba zaki jira kamar yadda nace ba, ki je ki nema masa auren da kan ki"

"Ta yaya ma e zata nemi aure, wannan ai sai su zata ko ƙarya nake yi?" Shiru yayi bai ce mata komai ba.

Ta sake kallonsa ta ce "Wai lissafin me kake ta yi haka ne?"

"Kuɗin na Zakka ne" ya bata amsa.

Murmushi tayi ta ce "Wow, ashe fa lokaci ya kusa, zan yi magana da Turai, a san abin yi a bayar a gidauniyarta"

"A'a wannan karon, da kaina za bawa waɗanda suka dace" ya bata amsa kai tsaye.

"Kamar yaya, ni ba wanda suka dace ɗin nake bawa ba?"

"Wannan karon haka na ga dama"

Gaba ɗaya tunda ta dawo, ta kasa gane kan Alhaji Ahmad, gaba ɗaya ya canza, sai wasu muzurai yake yi mata, duk maganar da tayi masa, sai yayi fushi ya hayayyaƙo mata abin da ba yayi mata.

"Wai ni Ahmad me kake nufi da ni ne? Babu damar nayi Magana sai ka hauni da masifa, kana wani cika kana batsewa me nayi maka ne? To bari na gaya maka, kuɗin zakkar nan ba wanda za a bawa wallahi, ga in da aka saba bayarwa duk shekara, kawai wannan karon kace ba haka ba".

Bai ce mata uffan ba, ya tashi ya bar mata wajen.

Hajiya Zainab ta sako shi a gaba da tijara kala kala, ta yau daban ta gobe daban, ta tsiri salo salo na rashin mutunci. Hakan ya ƙara rura wutar sanya shi ya koma ya bar mata gidan.

Amina ta makaranta, ya biya yayi mata sallama ya tafi, aikuwa sai da tayi kuka.

Abin da ya faru tsakanin Hajiya Zainab da Alhaji Ahmad, ba ƙaramin ɗaga mata hankali yayi ba, tsawon shekarun da suka shafe a tare, bai taɓa mata abu makamancin haka ba, ya kan yi fushi wasu lokutan, amma ko tayi laifin shi me yake bata haƙuri. Duk abin da ta ce ayi shi yake yi, amma a wannan karon, gaba ɗaya ya sauya mata, sai wani ji da kai yake yana hura hanci.
Da fari tayi tunanin ta gaya wa su Hajiya Turai, amma sai taga yin hakan kamar ta faɗo ne da nuna gazawa, ace kamar ita miji ya yiwa wulaƙanci, dan haka ta ƙudurce zata ɗau mataki da kanta.


A yau ne su Fadila suka koma makaranta suma, domin cigaba da karatun sabon zango.
A wannan karon ma, da result ya fito babu mai grade ɗin Yazid, shi da wani ɗan level 4 duk department ɗin babu mai grade ɗin su.
A wannan karon ranar da aka dawo makaranta, ranar Yazid ya dawo shi ma, sai dai yayi ƙalau da shi ya ƙara haske ya ƙara kyau.
Tun kallon farko da yayi mata, lokacin da ya shigo ajin, ya hanzarin kawar da kansa, a ransa yake faɗin "Tubarkallah, masha Allah". Tayi masa kyau sosai da sosai.

Babu wanda ya kula wani, ƙarewa Yazid yi kamar babu wata alaƙa da ta taɓa shiga tsakaninsa da ita.

Kusan wata guda kenan an shiga na biyu, da komawar Daddy Lagos, Amma duk da yadda Amina ta mayar da hankali a kan karatunta, amma tana jin kewar Alhaji Ahmad sosai da sosai. Sai dai kusan kullum cikin waya suke.
Yana cigaba da kwantar mata da hankali yana rarrashinta. Ya zo gari sau ɗaya cikin Azumi suka haɗu da Amina, ba tare da kowa ya sani ba, sai guards ɗinsa na ɗayan gidan.
Kwanansa biyu idan Amina ta tashi daga makaranta sai ta tafi wurinsa,tayi masa girkin abin shan ruwa, sai bayan an sha ruwa ta tafi gida, sai ta yiwa Baba ƙaryar cewa tana gidansu Azima. Kafin Daddy ya koma, ya tura mata kuɗi masu yawa a account ya ce ta sai kayan salla.

Hajiya Zainab ta sha mamakin rashin nemanta da Alhaji Ahmad bai yi ba, tun da ya tafi ko flashing bai yi mata ba, sai dai ya kira Fadila.
Ita ma kuma Hajiya Zainab girman kai ya hanata kiran sa a waya.

Shiru² bai dawo ba ba suyi waya ba, balle su sake tattaunawa a kan Auren Khalil.

Tuni Amina kuma sun riga sun gama Waec, Neco suke facing, ana ta yi musu lesson a makaranta.

Yau Asabar ce amma zata shiga makaranta, suyi karatu.

Har ta fito falo, Hajiya Zainab ta dubeta ta ce "Ina zaki?"

Amina ta ce "Makaranta ne ake nemanmu, muna ta shirin fara jarrabawa"

"Babu in da zaki, baƙi zan yi girki zaki yi mini"

Haushi ne ya kama Amina ta kalli Hajiya Zainab ta ce "Wallahi bana jin daɗi, kuma zuwana makaranta yana da muhimmanci".

"Ke ta shafa, na gaya miki aiki zaki yi mini, idan kika fita kuma zaki ga abin da zan miki" ta wuce ɗakinta ta bar Amina a falon. Tana shigewa sashenta, Amina ma ta sa kai tayi ficewarta. Dan yanzu kawai tana ɗagawa Hajiya Zainab ƙafa me, amma ta fara ƙulewa. Kuma bata tsoronta.

Baba baya nan yaje ƙauye, tun da aka yi Azumi bai je ba, har salla aike kawai ya yi musu, dan haka a Wannan karon ya samu damar zuwa. Amina tayi tafiyarta makaranta. Ba tare da sake bi ta kan umarnin Hajiya Zainab ba.

Fadila tana ganin Yazid, amma yadda baya kulata, haka ita ma ba kulashin take ba, duk da hakan yana damunta kuma tana da burin taimaka masa kamar yadda tayi niyya da farko.

Hankali kwance Amina ta dawo gidan, kamar ta dawo gidan ubanta.

Kasancewar ba kowa a falon, ta wuce sashinsu, ta yi wanka ta nemi wuri ta kwanta, dan kwanan nan ta kasa gane kanta.
Ta so tabi Baba ƙauye, ko ta ɗan sarara da masifar Hajiya Zainab, amma ba zai yiwu ba, saboda wannan jarrabawar da take gabanta.

"Amina" Hajara ta kira sunanta lokacin da ta shiga ɗakin.

Amina ta ɗaga kai ta kalleta ba tare da ta ce mata komai ba.

"Ki zo Hajiya na kiranki"

Amina tayi tsaki sannan ta ce "Ina zuwa"

Ta miƙe a hankali, tana jin yadda mararta ke ƙullewa tana saki, wanda alama ce ta a kowane lokaci tana iya ganin period.

Ko gezau ba tayi ba, da tayi arba da idon Hajiya Zainab da ke jifanta da wani irin mugun kallo, ga Fadila ita ma a tsaye a falo.

Ta ƙarasa in da suke tana ɗan yamutsa fuska ta ce "Gani"

"Ke! Me nace miki ɗazu da zaki fita?" Hajiya Zainab tayi tambayar kamar ta mari Amina.

"Ai da kika sakani aikin na baki uzurina, baki taɓa sakani aiki na ƙi yi miki ba, komai wahalarsa komai gajiyar da nayi ba, a karo ɗaya dai ai ya kyautu kiyi mini uzuri".

"Ke! Ni kike gayawa haka? 'yar ƙauye

Please Login or Register in order to submit comment