Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da kaina take fada min tana nanatawa kamar karatu.

Cikin wata hudu ne lokacin da muka je aka duba, babu wata damuwa ko matsala a tare dani sai hawan jini wanda ba wani damuwa bani tunda dama it's a normal thing a wajen mata masu ciki, an dai bani abubuwa da zan dings ci da kuma abubuwan daya kamata inyi da wanda ba zan yi ba domin rainon cikina cikin sauki da kwanciyar hankali. A cikin mota a hanyar mu ta dawowa daga asibitin Abbu ya riko hannuna yana shafawa a hankali yace “ya zancen aiki ya tafi koh?" na gyada mishi kai ina murmushi. Yayi er dariya tare da cewa “ai Doctor Salmah ta fada min cikin jikin ki ne yasa kika zama short tempered woman, haba! I was wondering dalilin da yasa mutum mai sanyin hali irin ki ya zama mai fada da zuciya cikin dan kankanin lokaci, amma tun da na gano kan abin, zamu dinga kiyayewa bacin ranki don tace hakan zai iya sawa jinin ki ya hau..... Allah ya sauke min ke lafiya baby" nayi murmushi nace “Ameeen Abbu nah..!".


Cikina sai daya shiga watanninshi na bakwai sannan ya fara girma saboda da babu wani girma kuma babu laulayi ba komi sai fresh da nayi da kuma cin abinci da shan tatacciyar madara. Kafin in shiga watan haihuwa ta kuwa na zama shirgegiya, zama da kyar tashi da dabara. Kullum na kan zagaye gidan sau hudu ko biyar don ance hakan yana da kyau sosai. Yanzu dai haihuwa kadai muke jira, komi is ready, hatta da cokalin da za a ba baby ruwa dashi ranar da aka haife shi an siyo an ajiye, komi unisex Abbu yake siyowa kuma guda biyu, duk da dai naki yin scanning amma Abbu da Anty Mubeenah har ma da sauran mutane suna cewa wai girman cikina irin na en biyu ne, don Abbu ma cewa yayi wai yana mafarkin ya ganni ina wasa da yara biyu ina miko mishi su, ni dai fatana kawai Allah ya sauke ni lafiya.

Ranar wata Talata na tashi da matsananciyar nakuda, nan muka kwasa Zuwa asibiti. Nakuda nayi mai tsawo da wahala kusan yini daya ina abu daya, abin ya gigita ni. Ban taba sanin cewa zafin nakuda nake yi ba. Abbu da yayi jan ido ya shigo labour room din sai waje aka yi dashi saboda dana shiga mood din “ duke kai ne ka janyo min wannan wahalar..." abin bai yi kyawu ba. Sai zuwa bayan Maghrib Baby ya fito, nan na fara ajiye numfashi, sai dai me? Wani ciwon ne ya sake turnike ni kafin kace me?! Wani yunkurin sai ga wani babyn. Na maida kaina kan gadon asibitin na kwantar ina ajiyar numfashi da karfi, nurse din data karbi haihuwar ta duba yaran tace “Masha Allah!! Maza ne Allah ya raya miki su!!". Tuni yaran suka hade dakin da kukan da aka san lafiyayyun jarirai nayi. Nan dai aka shirya mu muka fito tsaf damu. Throughout lokacin babu abinda nake furtawa fili da ciki sai ‘Rabbir-ham huma kamar Rabbiyaani Swigaara...!!' wa Mommy na da duk wasu matan duniya, haihuwa is really not a simple thing.

Ana fito damu Abbu da yara suka shigo, nan fa suka lullube yaran suna murnar samun kanne, Abbu dai ya samu ya lallabo yazo inda nake ya tallabo ni a cikin jikin shi ya rungume yana shafa bayana. Ya dago goshina ya bani peck a kumatuna, “well-done Baby, kinyi kokari really! Allah ya albarkace ku ke da ‘ya‘yanki" nace “ameen... Wani irin baby kuma? Ga babies dinka can" ya juya ya kallesu ya juyo ya kalleni yana murmushi, “me na fada miki? You were going to give me twins, next year ma haka, n the other year, n the other too...!" na zaro ido ina cewa “mutuwa kawai kake rokar min!" yayi dariya tare da saki na yaje ya dauki yaran, Anty Mubeenah kuma ta matso tana jera min sannu.
Sai washegari aka bamu sallama muka wuce gidanmu muka cigaba da karbar barka har zuwa ranar suna inda yara suka ci sunan Abdul-Qadir da Mukhtar (Sunan Daddy na) muna kiran Abdul-Qadeer Ameer shi kuma Mukhtar Daddy. Aka yi taron suna aka watse aka bar mu da yara da Dattijuwa Hanne daga Malumfashi muna wankan jego.

Cikin dan tsakanin Abbu ya bude min babbar plaza wadda Daddy na ya cike min rabin shagunan plazar da kaya ana kula min dasu, rayuwa ta ko wani fanni tana gara mana cikin dadi da kwanciyar hankali babu abinda zamu ce da Ubangijin mu sai dai Godiya....


*****

“Ameer!! Daddy!!!" na fito falo ina kwalawa yaran kira, Anty Mubeenah dake kicin tana dambun nama duk da ba girkinta ba ne, tana taya ni hada abubuwan motsa baki da muka saba yi saboda baki da kuma emergency food. Ta leko tace “ya aka yi ne ake neman dears haka?" naja tsaki, “yaran nan daure su zan fara yi a jikin gado gaskiya, kullum jan magana da barna kamar wasu beraye? Kwalbar turare na mai kyau fa kawai suka dauka daga kan mirror suka hada ta da bango, shine da suka ga ta fashe suka tsere" Anty tayi Dariya tace “aikuwa yanzu suka bi su Qaseem garden wai suna tennis" nayi kwafa, “I'll just go and register them a makarantar su Qaseem ma kawai ko na samu sawaba da sanyin zuciya" Anty tayi dariya tana girgiza kai tace “ke da yaran nan naki koh?" ni kuma na juya zuwa dakina.

Abbu yana kwance akan sofa yana karatun jarida da yake ranar hutu ce, ya miko min hannu na karasa gefen shi na zauna ina turo baki, yayi dariya “yau naji ikon Allah! Ni da bani na bata miki rai ba sai kuma fushi ya dawo kaina, dama ana haka ne?" na turo baki “Allah ni wannan yaran naka ka saka su a makaranta kafin su saka min hawan jini, kullum sai sun shigo sun min barna ni da Antyn su. Hafsy yanzu da makullin dakinta take yawo saboda Ameer. Kayan dakin yaran nan babu abin dauka duk sun bata, jiya suka balle wardrobe din da muka sayo musu last week a Prada saboda Allah meye haka??"

Abbu ya kwashe da dariya har da kwanciya akan kujera, nayi kuta, “na kula dama kai kake daure musu suna rainin wayau. Yara ba a isa a musu magana ba kawai sai ka hau cewa wai yara ne, har sai yaushe zasu girma??" ya juyo dani yana kallon idanuna, “sai wani kumburewa kike yi kina fada baby, Anya?? Kin san da cikin su Ameer ma fa haka kika dinga yi?" da sauri na dukunkune fuskata a kirjin shi. Ya shafa kaina yace “da gaske ne hasashe na kenan? Masha Allah La Quwwata Illaa Billah! You are going to bless me with another child again... Ohh Nafeesah the thing I have for you.... You Are Indeed a Blessing!!" na kara rungume shi a jikina sosai. Kamar yadda a shekaru masu dama da suka wuce, nake jin zill da duk farincikin duniya idan naji ni a kirjin mijina, yanzun ma hakan take. Har yau muna son junanmu, har yau muna girmama junanmu, har yau muna rungumar junanmu a halin farin ciki ko akasin sa. Babu abinda ya ragu daga son da muke wa junanmu.

Ya dago fuskata yace “that call on a celebration... Tunda yara suna nan zamu fita gobe, party and welcome our little princess... Mata zaki haifo mana yanzu baby.... Hafsy tace tana so ta koyi kitso, kinga idan muka samu mace shikenan sai ta koya a kanta koh?" na zaro ido ina dariya tare da kara shigewa cikin jikinshi, “Noo... Guda daya ta isa Abbu... En biyun nan ba sauki daga haihuwar har rainon, kana dai ganin yadda muke fama dasu a gidan nan" ya hade fuska ta da tashi har hancina yana gogar nashi... “haka kike tunani dai....". Kokarin zurfafa abin yake yi, har na saddakar na lumshe idanuna, yana gab... Saura kiris... Kawai sai barammmm!!! Karan turo kofa da sauri..... “Mammiiieeee!!!!" nayi sighing tare da bude idanuna, fararen kayan dana saka musu yanzun nan kafin su fasa min turare, sun yi dikin-dikin da datti da yake ba a jima da gama ruwa ba. Na zaro ido, “what??!" na fara kokarin tashi, Ameer ne ya fara xubawa a guje nan Daddy ya bi bayan shi, na juya na kalli Abbu, shrugging yayi tare da daukar jaridar shi yana murmushi, na girgiza kai tare da mikewa nabi bayan yaran ina kwala musu kira kamar dai yadda na bude shafin......

*_Alhamdulillah! Masha Allah Laa Quwwata Illa Billah!!_* It has been really a very big hell of a ride, right?! But Mashaa Allah!! Mun kawo karshen shi.

Littafin NI DA ABOKIN BABA NA kirkirarren labari ne, baya da nasaba da rayuwar wani/wata, idan wani abu yazo daya da naki/naka, to wannan 100% arashi ne kawai.

Ina mika dimbin gaisuwa ta zuwa ga Dimbin masoya, mabiya Littafin Ni Da Abokin Baba Na! The Facebookians, Wattpadians, Whatsappians, and all, thanks ya very much da duk kaunar ku a gare ni yayin Posting din littafin, gyarerekin ku da karfin gwiwar ku, I Appreciate!!

Gaisuwa ta Musamman zuwa ga mutanen Fikrah! Kungiya ta hadin kai da ban mamaki, Ina gaishe ku da kuma godiya a gareku baki daya.

Abokiya, Yaya kuma Kanwa ta gari; Anty Zee, Alkhairin Allah ya kai miki a duk inda kike.

Masoya, mu tara a littafina na gaba mai zuwa cikin hukuncin Allah! Har kullum, it's Jedderh Lawals!!

N it happens to be my Birthday today you know....
Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels


Please Login or Register in order to submit comment