Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

hijab wadda zata dinga rufe miki dunduniya!" na zaro ido, “to ai ni hijabai na gabadayansu ma basu kai biyar ba kuma da guda biyu kadai nazo makaranta" ya daga baki cikin mamaki kamar zai yi magana sai kuma ya rufe bakin, ya sake budewa yace “akwai hijabai a cikin kayan lefenki, idan kin tare ma zan dinka miki wasu for now sai kiyi amfani da wadanda kike dasu kafin ki koma" nace “Abbu....?" ya juyo ya kalleni fuskarshi na nuna rashin jin dadi, “r u arguing with me Nafeesah?" nayi saurin girgiza kaina, “to meye?" sai kawai na sake girgiza mishi kai, muka cigaba da tafiya ba tare da munyi magana ba, wani tunani ya darsu a raina. Na hade fuska tare da turo baki nace “to in dai haka ne sai dai kaima ka daina sa irin kayan daka sa yau, Allah kadai yasan iya adadin matan da suka dinga kallonka yau, kai duka ‘yanmatan ajinmu were looking at you with interest in their eyes" daidai lokacin yayi pulling motar zuwa cikin lot din dake gaban hostel dinmu yayi parking, ya kwashe da dariya cikin farinciki da wani abu mai kama da humor, na kura mishi ido ina kallonshi relieved and amazed, at last! Yayi more than murmushi.
Sai da yayi dariyar ta ishe shi sannan ya kalleni, “ni kuma meye aibun tawa shigar?" Armani pants ne a jikinshi da open neck top, ire-iren kayan da suke boye shekaru da girman da yayi su fito da xallan yarinta da kyawun shi. Na turo baki ban amsa ba, hannuna ya kamo ya rike a cikin nashi yana caressing, “girl, Ashe kema kin iya kishi? Ni indai nine baki da matsala dani, ki fadi duk irin kayan da kike so in dinga sawa zan sanya babu musu, m all urs Amour" na sadda kaina kasa ina blushing, na duba naga duk cikin irin kayan da yake sawa babu wanda basu mishi kyau, sai na kauda hirar na fara kokarin janye hannuna daga nashi wanda ya fara sa min tashin tsigar jiki. Ya kalleni fuskar shi a dan hade, “na kula baki son ina rabar ki kwana biyun nan Nafeesah, mai yasa?" duk da maganar da yayi sai dana janye hannuna daga nashi na saka su cikin gyalena, shiru nayi kawai, to in ce masa me? Ina jin kaina kamar wata traitor ko mai laifi idan ya taba ni, I'm feeling awkward idan ya taba ni, feelings ne da ban saba jinsu a cikin rayuwata ba hakan yasa na fara having second thoughts, ko dai don yana abokin Dad ne na kasa sakewa da Al'amuran shi? Ya kuta kawai, “zaki gama kewaye-kewayen ki ne ma ki dawo hanya Nafeesah, ina so zan wuce gida yanzu, me kike so in kawo miki anjima?" nayi saurin girgiza kaina, “babu komi" frankly speaking zan fi so ace ba ma sai ya dawo ba, ya tabe baki “sai wani guduna kike yi fa, kin manta cewa komi wayon amarya sai an sha man ta?" na kalle shi, wani murmushin mugunta ne akan fuskar shi da yasa naji wani tsoron shi yana shiga ta, ya kamo hannuna duk nokewar da nake yi sai da ya kai bayan hannuna saitin bakin shi ya sumbata, nayi saurin bude motar na janye hannuna na fita, sai dana fitan sannan na leka ta tagar motar nace “Abbu a gaida su Hafsy, sai anjima" yayi murmushi kawai yana gyada kai, na juya da sauri na wuce.

A haka har muka gama exams dinmu, ina ta kauce-kauce yayin da Abbu bai fasa abin shi ba sai ma abubuwa da suke karuwa kullum. Kwana biyun nan ya dameni akan wai shi fa lallai sai ya kaini naga gidan mu, ni kuwa nasan muddin na taka kafa naje gidan to sunana sorry, kila warning din dasu Ni'imah da Firdausi suke yi mun na in daure kar in tare da ciki ya tabbata. Tun a ranar da nayi exams dina na karshe na fara hada kayana, na kira Daddy a waya yace washegari zai turo a zo a dauke ni saboda ranar sai da yamma muka gama exams din, nace mishi don Allah ya turo direban tun da safe mu tafi, a matukar kagauce nake da in tafi gida, I have to clear my thoughts and brain kuma nasan gidanmu ne kawai zai bani wannan natsuwar, ga kewar su Daddy da nake yi kamar me, hakika nayi kokari, watanni biyar rigis ba tare dana saka su a cikin idanuna ba. Na kira Ramlah da tace tare zamu wuce Kadunar da ita na sanar da ita, tace zata shirya sai mu biya ta gida mu dauketa nace to muka yi sallama.
Karfe tara na safe kayana sun kammala waje daya, nayi wanka na shirya cikin riga da siket na atamfa, hijabin data zame min mayafi na ajiye a gefen gado a linke, na dauki wayata na fara buga game don ya dan kashe min time kafin direba ya zo. Kiran Abbu ya shigo wayata, gabana ya fadi sosai gabadaya na manta bamu yi sallama dashi ba saboda doki, na dauki wayar na kara a kunnena, “meet me at my office" kadai yace ya kashe wayar, na bi wayar da kallo kamar ba zan tashi ba, can kuma na mike na saka hijabina, Firdausi bata dakin taje rubuta jarabawa don haka na rufe dakin na fita. Zaune na same shi akan kujera fara dake a tsakiyar ofishin da alamun jirana yake yi, na maida kofar na rufe na zauna akan kujera dake fuskantar shi na zauna, fuskar shi sam babu yabo babu fallasa hakan yasa naji sanyin jiki ya mamaye ni, Allah dai ya taimakeni muyi rabuwar aminci yau don na kula da cewa rigima yake ji yau. Murmushi nayi a sanyaye nace “Abbu ina kwana? Ka tashi lafiya?" yace “ke zan tambaya ai, amma ni kin tambayeni tashina lafiya bayan kina neman hana min abinda yake nawa ne?" na dan zamo daga kan kujerar da nake zaune nace “don Allah Abbu kayi hakuri, idan kayi hakuri ma duka kwanaki nawa suka rage kafin a kawo maka ni gabadaya kayi yadda kake so dani?" ya lumshe idanun shi tare da maida kanshi ya jinginar da kujerar da yake zaune, “I tried Nafeesah, I really do. But I can't anymore, all I ask for u is just half an hour, please ki zo muje gidana, I so badly want you Nafeesah!!" na kura mishi idanu, idanun shi a lumshe suke har lokacin, Abbuna ne a gabana yake rokona, da ace zan iya da na mishi abinda yake so domin samun farin cikin rayuwar shi, sai dai ba zan iya din bane, I'm still not ready for it. Mikewa tsaye nayi a hankali, hanya mafi sauki in bar mishi ofishin kafin in kara bata mishi rai, nasan ba zai fasa tambayana ba, ni kuma in yaci gaba da tambaya it's either inyi abu daya cikin biyu; ko dai in sallama mishi ko kuma inyi denying wanda duka cikin biyun babu wanda zai mun dadi, nace “Abbu don girman Allah kayi hakuri, kayi hakuri na wata da watanni ma balle na en kwanaki? I am very sorry, zamu wuce Kaduna yanzu don Allah kar kayi fushi dani Abbu..." na juya cike da sassarfa zan fita. Ban ji lokacin daya tashi tsaye ba sai maganar shi dana jiyo daga bayana, “Please Mana Nafeesahh!!" Ya fada cikin wata irin murya wadda ta narke cikin tsantsar qauna da soyayyah. Kaina na fara girgizawa a tsorace, "Bazan iya ba. Kai fa Abokin Babana ne please kayi hakuri, bazan iya ba wallahi!!" idanunshi ya zuba min wadanda suke a lumshe kamar na mashaya, dama a yawancin lokuta a haka suke, sai dai na yau sun banbanta dana sauran lokutan. Na yau cike suke da wata irin soyayyah, zallar qauna, pure lust, I can sense them radiating from his body. Muryarshi ta kara yin kasa sosai “ina tunanin mun riga da mun gama wannan maganar Nafeesah? saboda Allah mutane nawa kika san sun yi aure irin namu kuma suna zaune lafiya har ma da zuria a tsakaninsu, ko a cikin tarihi ki duba fa, Sayyadah Aisha RTA diyar Sayyidina Abubakar ce wanda ya kasance babban Amini makusanci a wajen manxon mu (S. A. W) nasan kin san da haka ba sai na sake gaya miki ba" maganganun shi haka suke sai dai na kasa convincing kaina da zuciyata" nace “yeah, I know.., I just need time please kayi hakuri" ya girgiza kai, “na gaya miki ba zan iya bane Nafeesah, it's not as if wani sabo ne nake shirin aikatawa" Kai na ci gaba da girgizawa hawaye na sauka akan kumatuna, ya zanyi da raina da rayuwa ta ne ni kam? Ban san ya aka yi ba sai ganin shi nayi a gabana, kafin inyi wani yunkuri yayi pinning dina da bangon ofishin, "I love you Nafeesah....I want you n I know you do, u just don't want to admit it!" "no.... No... I... I" na fara fada cikin in'ina kafin inji wasu tausasan lebba sun hana ni karasa maganar. Lebena na kasa ya kamo ya fara tsotsa cikin wani irin passionate kiss, a hankali na lumshe idanuna tare da kamo nashi leben na sama nima na fara tsotsa, ya saka hannu daya ya zagaya dashi ta kuguna ya kara matso dani zuwa gare shi tare da zura harshen shi cikin bakina muka fara hadamammen kiss, ihu ake a cikin kaina da kwalwata, “Ya Allah! What am I doing? He's my father's Friend for Heaven's sake!! Cewar wani sashe na zuciyata, but hell! I couldn't let him go, sai ma kara rike shi da nayi tsam....

Karan da wayata ta dauka baby kakkautawa ne ya dawo da hankulanmu cikin ofishin, a matukar kunyace na janye jikina daga nashi yayi saurin janyo ni ya rungume a cikin kirjinshi, duk yadda naso in kwace abin yaci tura ina ji ina gani haka na Hakura har wayar ta gama burari ta katse, numfashi yake saukewa a hankali har ya dawo cikin natsuwar shi, ya hade goshina da nashi yana kallona ni kuwa naki hada idanu dashi, murmushi ya saki a hankali, “kin gani koh? We need each other Nafeesah, amma kina hana kan ki abinda zuciyar ki da gangar jikinki ke so, why?" a hankali na daga baki nace “kayi hakuri" ga mamakina sai naji yace “na hakura Nafeesah" na daga kai cikin mamaki na kalleshi, ya daga kafada, “to me zan yi idan ba hakurin ba? Kin san cewa ba zan taba tursasa ki ga yin abinda baki so ba, zan jira har a kawo ki din sai dai kada ma ki roke ni wani abu a wannan lokacin don ba zan ji ki ba...., muje in kaiki hostel din" ya zari makullin mota ya fita, na bishi da kallo ina murmushi, saukin kan Abbu yana burge ni sosai da sosai, Allah ya yaye min fargabar nan da wasi-wasi da nake ji ko na samu na faranta mishi rai kamar yadda yake kokarin faranta min. Na bi bayanshi na fita daga ofis din ya rufe muka tafi. Koda na duba miss call din da aka min direban da daddy ya turo min ne, na kira shi ya sanar dani ya iso nace mishi gani nan. Koda muka isa mun dauki lokaci muna hira da Abbu kafin muka yi sallama dashi akan cewa zamu yi waya, ya kama hannuna yayi kissing bayan hannun kamar yadda ya mayar dashi al'adar shi tun ina jin abun banbarakwai har nazo na saba da hakan yace “m gonna miss you baby" nace “me too" a kunyace, yayi murmushi, da haka yaja motar shi ya tafi. Firdausi ta taya ni dauko kayana muka lode su a bayan booth, daga nan muka yi sallama da ita ita sai nan da kwana biyu zata gama nata exams din, na shiga mota direba yaja muka wuce Kaduna bayan mun dauko Ramlah. Karfe biyu a Kaduna ta mana, da gudu na shiga gidan ina ihun kiran Mommy, ta fito daga kicin tana goge hannunta da kicin towel, na tafi da guduna na rungumeta ina murna, ta janye ni daga jikinta tace “ke tafi can ni, wannan yarinya ban san yaushe zaki girma ba ni kam" na kara shigewa jikinta ina tsalle abina, sai da Ramlah ta shigo sannan na sake ta. Suka gaisa da Mommy kafin muka shiga dakina muka yi wanka muka yi sallah, sai a lokacin na kira Abbu na sanar dashi mun sauka, nan muka danyi hira muka yi sallama sannan muka fita falo muka ci abinci. Da yamma Daddy ya dawo muka sha hira da murnar ganin juna, ko da dare ma dai hirar muka yi har sai da dare yayi sannan na musu sallama na wuce dakina. Washegari Anty Uwani tazo ta daukemu ni da Ramlatu muka tafi gidanta bayan ta sa mun dauki kayan sawar mu kala biyar, ban san me zamu yi ba na dai ji suna maganar Gyaran jiki ita da Mommy ni kam ban maida hankali wajen sanin lallai sai na san me zamu yi ba.
#TeamAbnaf
#OneLove





*♡Jeedderh♡*
[12:22PM, 2/18/2018] ‪+234 703 300 1537‬: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*


*©°•Jeedderh Lawals•°*

*®°•Fikrah Writers Association°•*🖋

This page goes to you, Jedderhs World Group Members, Lobi you dearies sosai da sosai.....
Shafin yau Tukuici ne a gare ki Mayrowh, thank you and lobi you too.....



*50*


Munyi nisa sosai kafin kukan da nake yi ya dauke, Anty Shafa ta miko min handkerchief na share fuska ta dashi, ta bude Jakarta ta ciro kayan kwalliya ta juyo da fuskata ta gyara min kwalliyar dana bata, na juya kaina ga window din motar na fuskanci waje zuciyata cike fal da tunanika iri-iri. Karfe shida muna cikin Kano, kai tsaye unguwar Galadanchi aka wuce damu gidan su Abbu. Can muka tarda mutane na jiran isowar mu, dakin Hajiya Siyama Mahaifiyar su Abbu surika a wajena muka sauka, aka damka musu Amana ita da Dattijan da muka samu a dakin nata, daga nan kuma aka kaini dakin Hajiya Fati nan ma dai gaisuwa da bada amanar ne, bayan an gama aka dauke ni zuwa wajen mahaifin su, ya mun nasiha sosai mai shiga jiki tare da addu'o'i, ya bada abin Sallah, Carbi da Turare aka bani a matsayin tsarabar gidan aure daga nan muka koma cikin mota sai gidan Aurena a Sharada phase 2.
Gida ne flat mai kyau, dakuna uku manya duk an yi jere, akwai toilets a cikin kowane daki, kicin, sai toilet daya a cikin falo kila na baki ne.
Su Ni'imah sune en jagora har zuwa dakina, sai da muka shiga daki Anty Ameenah ta yaye min gyalen kaina duk da haka kin daga kaina in kallesu nayi, Su Anty Shafa daya dakin aka kaisu ni kuma su Ramlah suka zauna a tare dani, nan dai muka dauro alwala muka yi sallah, kasancewar lokacin Sallar Isha'i yayi yasa muka yi har Isha'i din. Muna gamawa aka dire mana plates din abinci, Macaroni jollop da lemuka, tsakanina da Allah cikina a cike yake shi yasa na dinga tsakurar abincin, Sadiya data fara nauyi haihuwa ko yau ko gobe duk da ita aka yi jigilar gaisuwa da ita ko nauyin cikinta bata ji, tace “Amaryar Babban Yaya ya dai baki cin abinci ko dai kazar amarcin kike jira?" na harareta kasa-kasa ganin gasu Anty Ameenah a gefenmu suna zaune, Ni'imah tace “ta fa riga da taci kazar amarcinta tun ranar da aka daura aure, muma ba har muka ci saura ba?" na kuwa kai mata mintsini a cinya tayi tsalle gefe guda tana sosa wajen, Ramlah tace “ku kyale yarinyar nan, tun dazu take nuku-nuku kamar ba ita bace tace tana son auren, lokacin da yunwa zata taso mutum ya nemi abinci kuna ihu?" duk suka sa ihun, “Gida!!" tace “kun gani?!" ni kam sai na tashi na bar musu wajen kawai, na koma kan bencin dake gefen gado na zauna ina satar kallon kayan dakin, komi na ciki silver ne da black, gadon irin kananun Italian beds dinnan ne medium king size sai wardrobe data kusa cinye bangon dakin na gefen dama, dressing mirror, end of bed table, rug carpet, labulaye silver, sai sauran kananun tarkace da ba za a rasa ba amma kayan sunyi kyawu sosai, babu wata hayaniya irin ta kayan dakin zamanin nan.
Su Anty Ameenah suka mana sai da safe suka tafi suka barmu da su Anty Shafa da Ramlah, er hirarraki muka yi kafin Anty Shafa tace yakamata mu kwanta haka, ni na fara shiga toilet nan ma kayan ciki har ba a magana, katoton Jacuzzi tub, sinks, akan canters kuma mayuka ne tun daga na gyaran fata har na gashi ne da turaruka abin ba a cewa komi, na tari ruwan dumi na dan yi relaxing saboda warware gajiya kafin na dauro babban towel na fito na danyi en shafe-shafe na fita, Ramlah ta shiga.
Wardrobe na bude da niyar duba kayan barci, baki na bude a tsorace ina kallon cikin wardrobe din. Layi daya atamfofi ne wasu ma ko dinga su ba ayi ba, sai daya na laces, daya nasu jallabiya ne da dai dogayen riguna, daya nasu materials, saitin kayan barci kuwa sai da suka kwashe biyu, na zaro riga daya na daga ta sama, it looks more like a lingerie yawancin kayan barcin duk ire-iren su ne.
Na juya da rigar a hannuna ina nunawa Anty Shafa, “meye haka Anty?" tace “kayan barci mana" na kara kallon kayan, “you didn't mean... Ni zan saka su koh?" ta harareni, cikin gatse tace “a'ah ni zan sa..., ko kuma shi mijin naki!" na gumtse dariyata nace “amma Allah Anty kayan suna nuna jiki da yawa fa" tace “yi mun shiru malama, don suna nuna jiki sai me? Ina ce dai hakan ba Zunubi bane? Idan kin san ta yadda aka yi kayan nan suka zo nan ba zaki zauna kina ce mun wai suna nuna jiki ba, I specially went to Kamfanin da suke sarrafasu na bada oda, don haka tun kafin raina ya baci ki saka kayan nan, besides kayan nan na arziki ne idan kika yi comparing dinsu da wasu kayan, koda yake ke da kanki zaki san amfanin su kizo kina nema na" sai na gumtse baki na juya na maida rigar na fara laluben kayan sa wa, da kyar na lalubo riga da wando suma dai sai a hankali, wandon 3q, rigar mai hannun vest gasu silk, lokacin Ramlah ta fito nan muka bi lafiyar gado. Anty Shafa kuma ta ajiye katifa a tsakar dakin muka yi light off muka kwanta, kamar jira yake, sakon Abbu ya shigo.

*“Sleep??"* nayi gaggawar tura mishi da, *“about to.... How was your day?"* ya turo *“dama nasan ba zaki iya barci ba baby na, tun yau fa baki ji murya ta ba balle kiga text dina, nima ina kewar ki baby na nasan da kyar barci ya dauke ni yau, amma kar ki damu, na yau ne kawai..., daga gobe babu wanda zai sake shiga tsakaninmu da yardar Allah"* lokacin dana karanta sai da er dariya ta kufce min, kai Abbu is full of self confidence. Na tura mishi *“says wanda yake da mata., plus ni fa barcin ne kawai bai zo ba amma babu wanda nake kewa sai Mommy da Daddy na!"* na tura ina dariyar tsokana, nasan kila har gari ya waye yau muna musayar sakonni ne, sai kuma har barci ya dauke ni bai dawo da reply ba.
Sai da muka tashi sallar Asabar naga amsar daya maido mintuna kadan da fara barci na, *“zaki ce haka ai tunda har yanzu baki zo hannu ba, gobe war haka ki maimaita abinda kika fada yanzu please...." nayi murmushi kawai na maida wayar kasan filo na fada toilet. Muna gama Sallah muka koma wani barcin, sai karfe tara na safe muka tashi. Muka yi wanka muka kimtsa, an kawo mana abinci daga gidan su Abbu muka fita parlour muka karya. Falon madaidaici ne wanda ya dauki wasu rantsattsun beige couches guda biyu an jera su daya ta kalli gabas daya kuma ta kalli arewa, sai wasu Everette chairs navy blue guda biyu suna fuskantar couch daya, a tsakiya kuma an saka babban teburin gilashi kasan shi wasu woods ne suka tokare shi, a sama kuma an dora flower base mai kyau, sai lamp mai kama da bishiya, kasan parlor hardwood flooring aka yi, kai komi dai na falon ya fita very unique, muka hau kan dinning mai cin kujeru takwas muka karya.
Dakina muka koma Anty Shafa sai cafta take sauke min tana karawa duk da wasu abubuwan duk tuni ne take yi mun. Karfe daya munyi sallar Azzuhur sai ga Abbu shi da abokan shi biyu, nayi sauri na dauko hijabi na dora akan kayana, falo muka fita muka gaisa dasu, ban yi gigin daga ido na kalli kowa ba. Ramlah ce tayi jigilar entertaining dinsu, ni kam suna fara cin abubuwan data kai musu nayi wuf na fada daki. Gefen gado na samu na zauna, ban jima ba sai ga Abbu shima ya shigo. Kai tsaye inda nake zaune shima yazo ya zauna a gefena, hannuwana duka biyun ya kamo da daya hannunshi, dayan kuma yayi amfani dashi wajen dago kafadata, ya wani rausayar da kai, “me nayi ne yau kuma Babyn? Babu gaisuwa, babu murmushi, babu kallo?" na sadda idanuna kasa tunda ya rike fuskar, duk yadda naso in daga baki in gaida shi kasawa nayi, wani irin nauyi da kunyar shi da ban taba ji ba naji sun dabaibaye ni, ya nisa, “bari in maida su AbdulHameed gida in kuma dauko direban da zai maida Anty gida sai in dawo gare ki gabadaya koh?" ya kai hannuna bakin shi yayi kissing as usual kafin ya fita.
Yana fita su Anty suka fara shirye-shiryen tafiya, nayi rau-rau da idanuna nan Anty ta samu abin fada, abin mamaki kuma bayan kamar awa daya da taji direba yazo sai kuma ta hau sharar kwallah, nan na rungumeta ina kuka, Ramlah ma tana gefe tana matsar kwallah, Abbu da kanshi ya leko ya sanar da ita zuwan direban. Ta mike tana share hawayenta tare da rataya jakarta, ta kamo hannuna ta rike cikin nata, “to Nafeesah, sai watarana, Allah ya baku zaman lafiya da maigidanki da abokiyar zaman ki, hakurin nan dai da kowa yake gaya miki kiyi da biyayya shi zan kara jaddada miki, sai kinyi exercising hakuri sannan ne zaki ci ribar rayuwar aure duk da nasan ki da hakuri amma dole sai kin kara kinji? Allah ya miki Albarka" na gyada mata kai ina hawaye.
Ta sa kafa ta fara tafiya Ramlatu ta bita

Please Login or Register in order to submit comment