Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dan murnan jin haka, dan shi yafi ma damuwa da Asas d'in saboda yanda ya ga ya zurma da yawa akan ta.

Shigowarshi shi kuma ya mik'e yana fad'in "Sheikh, ka bani wani wurdi nan na neman sa'a."

Yar dariya yayi ya girgiza kai yace "Bana da shi, ni ma nemanshi nake saboda abinda na saka a gabana."

Hannunshi Asas ya kama yana murmushi yace "Ya ustaz muje na ji to miye haka? Kar fa a zo kai ma yarinya ka samu zaka k'arawa yayata abokiyar zama kamar yanda kake fad'a."

Wata suka da Hafsat taji daga zuciyarta zuwa d'an cikin dake jikinta yasa ta saurin kallonsu tana mai tsaresu da ido, aje cokalinta tayi ba tare data d'auke idonta daga garesu ba, su kam juyawa sukayi suka fita sheikh na fad'in "Asas lafiyarka ita tafi damuna akan komai."

Suna fita farfajiyar ya kalleshi yana gyara tsayuwa yace "Sheikh nagode sosai da k'ok'arin da kake akan gaanin na samu lafiya, na tabbata Alhaji bai bar amanarmu a hannun da bai dace ba, Allah ya bamu ikon faranta maka kai ma."

Murmushi yayi yace "To miye a ciki? Mahaifinka namahaifina nono d'aya suka sha, mahaifina ne ya saki mahaifinku ya kama, duk abinda zan muku yan uwana na jini na yi ma."

Jinjina kai yayi yace "Hakane, Allah ya saka da alkairi."

Murmushi kawai ya masa yace "Saika dawo."

Jinjina kai yayi yace "Addu'arka fa sheikh."

Lumshe ido kawai yayi alamar to yana kallo har ya fita daga gidan a tsaleliyar hondarshi.


Duk da ba had'uwa zasu yi ba amma haka ta shirya cikin ratsatsen leshen da Mas'ud ya siya mata a lokacin sallah, wani irin kyau tayi duk da bΓ’ kwalliya bΓ’ ce tayi mai yawa, turare ma yau na musamman ta bud'e a kwalinshi, d'an k'arami ne mai masifar sanyayyen dad'i mai sunan *mukhalat* ta shafa, mayafinta ta d'auka ta ce wa mama zata shiga gidansu Asma'u, bata hanata ba dan tasan mahaifinta ma yana k'ofar gida a lokacin dan ko sallah isha'i ba a yi ba.

Tana shiga a soron gidansu Asma'u suka ci karo da yayanta da suke uba d'aya zai fita, tare gabanta yayi yana kallonta yana murmushi da fad'in "Mimi gari zaki tafi ne?"

Fuska a d'aure tamau tace "A'a, kauce min a hanya."

Wani murmushi ya kuma yi tare da gyara mata ta wuce ta barshi nan, tana shiga da sallama a bakinta, dayawa daga cikin mutanen gidan ne suka amsa har da Asma'u, idon kowa a gidan a kan ta yake yayin da suke shak'ar k'amshin tufafinta dana jikinta daya gauraye illahirin gidan, kowa zuciyarshi na girgiza tana jijjiga akan lamarin yarinyar. Mimi kam ko a jikinta sai ma hannun Asma'u data kama suka shiga d'aki tana fad'in "Wai ke miye haka? Dubi fa yanda kika yi wani gamin gambiza riga daban siket daban, a hakane zaki samu saurayi?"

Tsaki tayi sai Asma'u data fahimci yau kanta take neman juyewa kawai tace "Ina zaki je Mimi kikayi wannaan shirin haka?"

Murmushi ta saki tare da cire mayafinta ta aje akan gadonsu dake shirge da kaya tace "Ko ina, bana fad'a miki Asas zai zo wajen Abba ba, shiyasa na baro gidan."

Wani murmushi tayi ita ma tace "Allah dai ya nuna min Abba ya amince da Asas d'in nan ko hankalina ya kwanta."

Kallonta tayi tace "Idan Abba ya amince saina baki kyautar jaka goma."

Zaro ido tayi tace "Jaka goma fa? Ina ma laifin jaka guda."

Yatsina fuska tayi tana gyara zamanta da wayarta a hannu, bud'e tsaron wayar tayi ta shiga d'an daddanawa, hira suka dinga yi da Asma'u har aka kira sallah isha'i ta saka hijabin Asma'u ta kabbara sallarta dan da alwalarta dama, tana gama akan sallayar wayarta ta shiga vibration, d'auka tayi tare da sakin murmushi, Asma'u kanta murmushin tayi tace "Tunda na ke dake ban tab'a ganin an kiraki a waya kinyi murmushi ba sai yau, Asas kai d'an baiwa ne."

K'ala bata ce ba ta d'auki wayar ta d'ora a kunne, daga b'angarenshi yace "Maah, barka da dare."

A sanyaye cikin b'oye farin cikinta ta k'irk'iro muryar gajiya da kasala ta saka tace "Barka, ya kake?"

Da fara'a yace "Komai ba daidai ba daga yanzu har sanda zan k'araso gidanku mu tattauna da Abba."

A hankali tace "Uhumm!" A shagwab'e cikin sangarta ta autanci yace "Maamah, dan Allah ki tayani addu'a Abba ya bani ke."

Da mamaki tace "To wai me ye idan ka rasani, ka daina jin tsoron zai hana maka ni mana, ka sameshi kan ka tsaye kawai."

Saida yayi kamar zaiyi kuka yace "Shikenan to, amma Mimi ni kad'ai nasan tashin hankalin da zan shiga idan na rasaki."

D'an murmishi tayi tace "Ba zaka rasani ba insha'Allah."

A tausashe yace "Allah ya amince." Shiru ne ya d'an biyo baya kafin sukayi sallama a lokacin ya kawo daidai da kwatancen data mishi tunda rana.

Fitowa yayi daga motar yana gyara rigar shaddarshi gezna kalar ruwan k'asa mai duhu sosai wacce aka ma gajeren d'inki ya mishi kyau, saidai babu hula a kan shi sai gyaren kai irin na matasan zamani. Abba ne dasu Yaseen wanda yaji sauk'i suka jero sun dawo daga masallaci, ganin zasu shiga gidan yayi saurin matsawa yana musu sallama, Abba ne ya amsa tare da mik'a mishi hannu, lura d'Γ  yayi irin hallitar Allahn nan ce ta gajerun mutane yasa Asas cikin ladabi yace "Dan Allah Baba gidan malam Adam nake tambaya?"

D'an juyawa Abba yayi ya kalli Yaseen da Amir kafin ya k'arewa Asas kallo, duk da shigarshi ta yi kama data wayayyun yara ce kawai amma kuma ta fito mishi da haibarshi had'e da kamala ta cikakken bafulatani, dan haka ya d'an saki fuskarshi yace "Yaro ni ne malam Adam a dai layin nan, Allah yasa lafiya?"

Tarrr ya sake zaro ido a kan shi, daga k'asa ya sake d'aukowa ya kalleshi, daga shi har su Yaseen d'in duk tsayinsu bai wuce zuwa cinyarshi dan babu wanda ya kawo k'ugunshi, har gwara ma Amir ya d'an fisu tsayi da kad'an.

Wani irin nauyi ne yaji tare da kunya sun kamashi, sai kawai ya tuna kalaman Mimi na safiyar shekaran jiya da take fad'in akwai baiwar da Allah ya ma iyayenta, shi ma idan ya gansu zai tabbatar da suna da baiwarsu. A take yayi saurin durk'usawa yana shafa sumarshi da fad'in "Ina wuni Baba."

Da murmushi Abba yace "Lafiya lau d'an saurayi, muna lafiya."

Gaisawa sukayi har saida Abba yace "Gashi kuma ban shaidaka ba? Daga ina haka?"

D'an d'ago kan shi yayi ya kalli su Yaseen, hakan yasa Abba cewa "Ku shiga ciki kunji."

Saida suka ga shigarsu kafin suka sake maido hankalinsu ga juna, a sanyaye cike da kunya yace "Abba dama mun had'u da Mimi..."

Tunda ya ji haka sai yace "Dakata samari, bari na kawo mana abun zama ko."

Cikin fara'a yace "A'a Abba da kun barshi, haka ma yayi nagode."

Gyara tsayuwa Abba yayi yana kallon sumar dake kan Asas yana fad'in "Dama mun had'u da ita ne, to na nemi na fara gabatar da kaina ne kafin na fara zuwa wajenta saboda a gaskiya aure ne ya kawoni ba wasa ba, shine na zo da kaina dan gabatar muku da kaina."

Numfashi Abba ya sauke yace "Yaro ya sunanka? D'an wane gida ne kai? Waye mahaifinka? Sannan me ce ce sana'arka?"

Ba tare da jin d'ar ba Asas yace "Sunana Ashraf Sabi'u, ni d'ana ga margayi Alhaji Sabi'u Aliyu Sharif Maina, ina zaune tare da mahaifiyata a unguwar Tchanga, sannan nayi karatu jarida ne amma ina kasuwa ne tare da d'an uwana sheikh wanda ya zama kamar uba gareni, dan gaba d'aya shi yake kula da harkar kasuwancinmu ni da 'yar uwata."

Jinjina kai Abba yayi yace "Masha'Allah, masha'Allah, yayi kyau haka, amma na ji ka ambaci Aliyu Sharif maina, kana nufin kai d'an uwan sheikh Abdul Waheed ne kenan?"

Da fara'a yace "Hakane Baba, mahaifinsa da mahaifina ciki d'aya suke fito."

Da farin ciki ba yace "Masha Allah, abu yayi kyau gaskiya."

D'an kallon Abba yayi yace "Saidai Baba akwai abu guda da ba zan b'oye muku ba."

Gaban Abba ne ya fad'i ya tsira masa ido, d'orawa yayi da "Baba shekara bakwai kenan da Allah ya jarabceni da wani azababben ciwon ciki mai tsanani, a duk shekarun nan mahaifiyata magani take nema min, amma insha'Allah komai ya kusa zuwa k'arshe dan yanzu haka muna ta shirin tafiya k'asar waje ne dan sama min magani."

Wata nauyayyen ajiyar zuciya Abba ya sauke tare da jinjinawa yaron sosai yace "Malam Ashraf wannan ai ba komai bane, ita larura tasan d'akin kowa kuma babu wanda Allah ya wuce ya jarabeshi da ita, Allah ya baka lafiya yasa a yi a sa'a."

Da murmushi yace "Nagode Baba."

Cikin murmushi da jin dad'i Abba yace "Masha'Allah, abu yayi kyau, Allah ya shi albarka."

Gyara tsayuwa yayi yace "Insha'Allah idan na shiga ciki yanzu zan tuntub'i yarinyar a kan maganarka, idan ta amince to fak'at, insha'Allah zan nemeka sai na maka bayani, bana da tamtama akan zuri'ar su sheikh, ina ji kai ma mutumin kirki ne kamar shi, ba zanyi bak'in cikin damk'a amanar 'yata ga wannan ahali ba."

Wuuuuu! Asas yaji kamar zaiyi kwasan karan mahaukaciya da Abba ya d'aukeshi ya goya, ko a haka aka tsaya yasan kam zai samu shiga da izinin Allah, dan haka bakinshi har kunne ya shiga godiya yana mishi addu'ar Allah k'ara girma da lafiya da d'aukaka da sauransu, Abba ma cikin farin cikin yau *uwar ta shi* bata yi masa jaye-jayen nan ba ya shiga shi mishi albarka, da haka suka rabu Asas ya d'auki hanyar gidan sheikh dan tsaigunta masa wannan labari mai armashi.

Mimi ma da tun tsayawar motar ta lek'o tare da Asma'u tsaf ta k'are masa kallo ta kalli Asma'u tace "Gaskiya guyen nan ya had'u, kinga wani mahaukacin shiri kamar yau ne d'aurin aurenmu."

Kallon Asma'u tayi ta kama hannunta suka koma ciki tana fad'in "Ai dole ma Abba ya amince, inba haka ba kuka zanyi."

Dariya kawai Asma'u tayi har suka shige d'akin suna yar hirarsu.



*Masha'Allah*


Alhamdulillah, munsan Allah ya azurtamu da masoya masu d'umbin yawa a k'asarmu Niger da d'ayar K'asarmu Nigeria harda ma sauran kasashe na nahiyar Africa.

Ina masoyan *Sajida* da *Samira* littatafansu??? Marubutan nan masu rubuta littafin *Bak'a ce, Mage* da *Badak'ala, Allura ta tono Galma* wanda kuke kauna har cikin ranku. Ku matso kusa don nuna musu d'umbin soyayya da kaunar da kuke musu inda suka zo maku da sabon littafinsu mai taken *AURE YAK'IN MATA* daga jin sunan kunsan cewa littafin kunshe yake da darussan rayuwa wadanda suka shafi rayuwarmu ta aure,kalubalen da mata ke fuskanta a gidan aure da kuma yanayin zamantakewar aure na zamanin yanzu, duk da ba sabon abu bane, amma namu ba irin nasu bane, sai an gwada akan san na kwarai.

Ga mai bukatar wannan littafi *Farashin mai sauki ne* naira dari uku (300) kacal ga yan Nigeria, yan Niger kuma dala dari ne (500)πŸ‘Œ zaka samu wannan littafi mai dubbin darussa a cikinsa.

_Domin tura kudin siyan littafin ga yan Nigeria sai a tura ta wannan account number din *2377403479* Khadija Umar Abubakar. Zenith Bank. Kuma akwai damar tura kati ta wannan lambar *081-686-594-14* IDAN KA YI TRANSFERT SAI KA TURA SHAIDA TA WANNAN NUMBER +227 93 81 16 18._

_'Yan Niger kuma sai ku tura katin MOOV ko Airtel ta dala dari watau 500 francs ta wannan lambar *+277- 94-98-56-52*_

Mun yadda daku, mun aminta da irin kaunar da kuke muna don hakan muna da yakinin cewa zaku siya don nuna mana kalar soyayya da kaunar da kuke mana da littafanmu.πŸ₯°


*Alhamdulillah*
7/22/21, 8:40 PM - Ummi TandamaπŸ˜‡: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?

*NA*


_SAMIRA HAROUNA_


*SADAUKARWA*


_GA DUKA_

*'YAN AMANA TA*


πŸ’«βœ? *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜? *[ T.M.N.A]* β˜? πŸ“–πŸ–ŠοΈ?

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


*11*


Ko da Abba ya shiga gida kam ya kalli mama yace "Ina Mimi ne?"

Kallon Amir tayi sannan ta kalleshi tace "Tana gidansu Asma'u har yanzu."

Shi ma kallon Amir yayi yace "Je kira min ita."

Gyad'a kai yayi ya mik'e ya fita, 'yar kujerar robar da Amir ya tashi ya zauna yana fad'in "Bak'o na yi yanzun nan, kai uwata da kwashe-kwashe ake, ni ko a ina ta kwaso farin jinin nan? Yarinya kamar wata 'yar sarauta."

Wani murmushi Mama tayi ta saci kallonshi tace "Farin jini ko shirme, hauka ke damunta yarinyar nan."

Girgiza kai yayi yace "Harda farin jini ga uwata, ki duba ki ga ba dan bud'e mata ido da nayi ba da yanzu gidan nan bai zama dandalin tara kowane jahili da sakarai ba?"

Yar dariya tayi tace "Allah dai ya shirya mana ita."

Da fara'a ya amsa da "Ameen." D'orawa yayi da "Yanzu fa kam indai har ba zata saka shirmen nan da ta saka game da lamarin yaron nan Mas'ud ba, to Mimi kam ta dace da miji na gari mai hankali."

Cike da tsantsar damuwa Mama tace "Ni wallahi a tsayar da ranar aurenta shi zai sama min kwanciyar hankali, dan lamarinzamanin nan da rayuwar da Mimi ta saka kanta tana kayar min da gaba."

Jinjina kai yayi yace "Ai dai kin shirya aurar da ita ko?"

Sunkuyar da kai tayi ba tace komai ba, murmushi yayi yace "Indai har komai zai zo mana da sauk'i, to insha'Allahu auren uwata ba zai wuce wata d'aya da rabi ba, dan ni kaina bana son ganinta a k'yal-k'yal d'in nan, tun muna sanin inda take samu wata rana zata rufemu ta bai-bai, duk da muna shaidar halayenta amma ai yaro ka haifesa ne baka haifi halinsa ba."

Cike da tabbaci tace "Tabbas hakane, Allah ya mana jagora."

"Ameen." Ya fad'a a dai-dai sallamar Mimi da Amir a tare, amsa musu sukayi har suka zuba mata ido tana sunkuyawa tun bata k'araso garesu ba ta durk'ushe, kusan a tare suka saki murmushin jin dad'in yanda Mimi take matuk'ar girmama su, tunda tayi wayo ta mallaki hankali ta daina tsayawa a sanda suke tsaye, dukansu hakan na musu dad'i fiye da kima kawai dai basu tab'a nunawa bane, saidai kullum suna mata addu'ar Allah ya bata yaran da zasu mata biyayya ita ma fiye da yanda ta musu.

Cikin nutsuwa Abba dake kallonta yanda kanta ke k'asa yace "Mimi, kinsan wani yaro mai sunan *Ashfar*?"

Da sauri ta d'ago kai sai kuma ta sunkuyar da kanta tana murmushi, Mama dasu Yaseen duk tintsirewa sukayi da dariya hakan yasa shi rarraba ido yana kallonsu, cikin had'e fuska yace "Wai lafiya dariyar ku kuma?"

Cike da kunya mama tace "Malam ai sunan ka fad'a ba daidai ba, ina kyautata zaton Ashraf ne ba Ashfar ba."

Sai lokacin shi ma ya ma kan shi dariya yace "To ni na sani ne, suna ne gashi nan dai idan uwaye suka saka ma yaransu."

Kallon Mimi yayi yace "Kin san shi ne?"

D'an sunkuyar da kai ta sake yi tace "E Abba."

Tsareta da ido yayi yace "Ya zo yanzu gidan nan, kuma izinin neman zuwa wajenki yake, shin kin amince da haka?"

Shiru tayi saida ya sake cewa "Kin amince?"

A hankali ta jinjina kai alamar eh, shi ma jinjina kai yayi yace "Shikenan tashi kije, zan d'anyi bincike a kan yaro na k'ara sanin halayenshi duk da dai d'an babban gida ne, gashi d'an manyan mutane kuma jinin malamai, amma ki sani uwata wannan karan ba zaki min iskancin nan ba, wallahi kika sa na shiga maganar nan kika sake kunyata ni Mimi sadakarki zan bayar."

A zabure ta d'ago tace "Sadaka Abba?"

Yatsina fuska yayi yace "K'warai kuwa, kina shakkar hakane? Ki jaraba ki gani."

Shiru tayi sai mama dake murmushi, tana so ta ce a bayar da sadakar ta ta ai zai fi, amma kunya da kuma girmama sunan sarakuwarta musamman da ya zamana a gabanshi take, Abba ne yace "Tashi ki shiga ciki."

Mik'ewa tayi zata shiga ya bita da kallo yana fad'in "Uwata ba dai zaki daina saka wannan sangen ba ko?"

Juyowa tayi ta durk'usa tace "Abba na daina fa, kawai idan zan shiga gidansu Asma'u ne ko aunty Maimuna nake sakawa fa."

Jinjina kai yayi yana kallonta ta mik'e ta shige d'akin kamar ta shiga taka rawa tsabar farin ciki.

*Yau* alhamis bbu karatu, hakan yasa tunda safe tayi shara da wanke wankenta ta kammala, tana idawa gaban mama ta durk'usa tace "Mama bani dala arba'in zan siyi k'osai da bredi nayi kari."

Wani murmushi Mama tayi tace "Ina ce jiya kinga tuwo aka dafa? Sannan kinga miyar da aka yi a matsayin mahad'in tuwon? Shi ne kike neman dala arba'in a hannu na?"

Girgiza kai tayi tace "Mimi idan ina da dala arba'in d'in da zan baki ai zan iya taimakawa mahaifinku ta hanyar yi mana cefanai me kyau muyi miya."

Wani huci ta sauke da tunanin mafita, ita fa tana da kud'in matsalar tambayar da zata sha yasa take b'oyewa, d'an kallon maman tayi tana karkare akaihunta dake jikin gajerun yatsunta tace "Mama to bari na ga ba zan rasa ba kam a jakata."

Mik'ewa tayi ta shiga ciro jakunkunanta masu kyau dake jikin hannun gado, zaune tayi ta shiga lalubarsu tana zazzagewa kamar gaske, Abba ne ya shigo da sallama d'akin suka amsa, shigowa yayi yana kallonta yana fad'in "Ke kuma lafiya? Me kike nema?"

Cikin ladabi tace "Abba dala arba'in nake fatan samu a nan."

"Me za kiyi da ita?" Ya tambaya kai tsaye, amsa ta bashi tana ci gaba da lalabawa da fad'in "Abba abun kari zan siyo."

K'uri ya mata da ido, duk da yasan halin Mimi tana da saka kanta a uku a wasu lamura, amma maganar tuwo kam tunda yarintarta ne bata son cin shi, shiyasa basa matsa mata da sai ta ci d'in, saidai yana tsoron yanayin rayuwa, baisan ina rayuwa zata kai ta ba nan gaba, ya zatayi kenan? Idan fa su iyayenta sun d'auka wani ba zai d'auki haka ba, laluba aljihunshi yayi ya ciro talatin yana fad'in "Karb'i nan, je ki siyo abinda zaki ci."

Kallonshi mama tayi tace "Bata kayi wai?"

Shiru yayi yana kallon mimi data mik'e da sauri ya ta d'auki hijab ta saka ta fita, k'arasa shiga yayi ya zauna bakin gadon da kyau yana fad'in "To ya zamuyi in ba'a bata ba? Ta fita waje ta nemo muke so? Ai kinfi kowa sanin bata cin tuwo, hakan ba dan d'aukarwa kai bane ko kuma k'arya, hakane take tun fil'azal."

Numfashi Mama t sauke tace "To yanzu daka bata su kana da kud'in ne?"

Girgiza kai yayi yace "Allah zai dubemu ya bamu wasu insha'Allah."

Jinjina kai tayi tace "Allah ya bud'a mana."

"Ameen." Ya amsa dashi kafin ya mik'e yace "Zan fita yanzu, insha'Allah zuwa anjima zan dawo na kawo muku abinda ya samu."

Nan ma jinjina kai tayi tace "Allah ya bada sa'a, Allah yasa a dace."

Amsawa yayi da ameen ya fita a gidan, kwanar daya shiga anan ya samu Mimi tsaye bakin kaskon mai suyar k'osan, murmushi ya saki ganin ta wani d'aure fuska ta dafe k'ugu, yasan saboda su Maryam da su Na'ima na wurin ne dan basa shiri ko kad'an. Har saida ya kawo daf da ita zai wuce ya kalleta yace "Mamana da an baki ki wuce gida kinji."

Sai lokacin ta farga dashi hakan yasa ta saurin sunkuyawa tace "To Abba."

Wucewa yayi ita kuma ta mayar da kallonta ga mai k'osan, su Na'ima kam bushewa sukayi da dariya har da tab'awa inda Maryam ke fad'in "Wa ya ga d'an k'wak'ur, dunk'ul-dunk'ul kamar zai shige a k'asa, a haka kuma aka haifffffffff..."

Saukar marin daya zauna a kumatunta ne yasa ta jan harafin na k'arshe, bata gama fahimtar me ya sauka a kan ta ba Mimi ta kuma kifa mata wani marin, tuni ta canza yanayinta daga nutsatsiyar nan zuwa mahaukaciyar k'arfi da yaji, dan kuwa bakin wuta ta jawo a cikin murhu ta shiga tik'awa Maryam tare da cakumar hijabinta. Cikin tashin hankalin samarin dake gefe zaune da kuma mai k'osan duk sukayi kansu, dan Na'ima na ganin haka ta daka da gudu ta shige wani gida tana fad'in ta kashe Maryam, da k'arfi Bello ya karb'i iccen hannunta daya rage babu wuta a jikinshi yana fad'in "Haba Mimi da hankalinki, me ye haka? Me ya had'aku?"

Kafin ta bashi amsa muryar wani saurayin ta daki ku'nuwansu yana fad'in "Inna lillahi! Ta kashe yar mutane fa."

Duk kallon Maryam sukayi da zafin duka da iccen wutar nan yasa ta fad'uwa a sheme, dan hijabinta ma duk yayi shaidar ya ci wuta, kafin ka ce kwabo wurin har an taru daddazon jama'a, yanda ake ta cacar maganar ana tuhumar Mimi yasa mai k'osan ne cewa "A'a fa! Domin Allah yaran nan basu da gaskiya, ba dan basu da tarbiya ba ai iyaye sun wuce gaban wasa, kuma hallitar iyayen Mimi ai Allah ne ya hallicesu haka, shi ne suka tsaya suna mishi dariya harda shak'iyanci saboda ya wuce ta nan, ni fa ban ga laifinta ba wallahi 'yar halak kenan."

Ruwa aka shafawa Maryam ta farfad'o tana fashewa da kuka da zagin Mimi tana fad'in sai ta rama, Mimi kam uwar k'asaita da isa da fad'in rai, a lokacin da kakar Maryam ta iso lokacin ta matso kusan Maryam d'in tace "Wallahi ba dan anyi gaggawar k'watarki ba, da sai na miki wanka da ruwan man nan, na kasheki na kashe banza wallahi."

Juyawa tayi ta shiga takawa da k'arfi har k'irjinta na wata nutsatsiyar kad'awa a cikin hijabinta, tsuguno tayi gaban farantin k'osan da aka kwashe ta jawo farar leda, a nutse ta shiga k'idayawa kanta k'osan har ta zuba daidai kud'inta, mik'ewa tayi ta kalli mai k'osan ta aje kud'in akan kujerar katakon ta tace "Ga kud'in nan, na talatin na zuba, ko d'aya ban k'ara a kai ba."

Cikin takon izza kamar wacce ta ci kwalliya ta shiga takawa har ta k'arasa gida ta barsu nan ana cecekuce, tana shiga hannayenta ta wanke sosai ta d'auki ledar k'osanta ta shige d'aki, yanayinta sam bai nunawa mama wacce wani abu ya faru ba, dan haka bata tambayeta komai ba sai kallonta da take jefi jefi tana cin k'osan da d'a-d'aya, hayaniyar Zara ta ji da alama dai biyota sukayi a kawo shedarta gida, dan har kukan Maryam take ji wiwi, a sauk'ak'e tayi murmushi tace "Hummm!"

Mama da taji abun a tsakiyar gidansu fitowa tayi dan ta d'auki murya, abun kamar wasa sai kuwa tsohuwar nan Zara ta d'aga musu hankali, dan ta dage sai an bi mata hakk'int dan an ga ita marainiya ce, in ba haka ba kuma zata yi k'arar Mimi wajen yan sanda. Mama baiwar Allah wacce da k'yar ma take kallon ciwon Maryam d'in dan doguwa ce ita ma ta shiga bata hak'uri da jajantawa ganin duk inda jikinta ya samu bakin wutar nan ya fara d'urar ruwa ya mata bororo, saida makwabta suka shigo suka tayata bata hak'uri amma fa ta ce zata jiran uban Mimi ya dawo saita nuna mishi abinda ta ma Maryam.

Duk hargagin da ake tana d'aki zaune tana jin su, Mama kuma kawaici ne ya hanata shigowa ta mataa magana, saida aka ci aka sid'e mama ta shigo tana k'are mata kallo, bata yarda ta d'aga kai ta kalleta ba, sai ma mik'ewa da tayi ta fito ta jefar da ledar k'osan ta d'ibi ruwa ta shiga wanka.

Saida ta gama ta shigo d'akin ta gama shafa mai ta jawo akwatin k'arfenta tana duba kayan da zata saka ta ji mama tace "Mimi kin kyauta yanzu?"

Ba tare data juyo ba tace "Mama, karki shiga zancen nan dan Allah, ba Maryam ba wallahi ko waye a garin nan ya nemi raina min iyayena sai na illatashi, saidai a kasheni ni ma."

Tsuru ta mata da ido tana kallonta ta mik'e tana k'ok'arin saka pant tana kare jikinta da zanin data d'aure k'irji, tsaf ta gama shirinta cikin doguwar rigar atamfa mai kyau, hoda kawai ta shafa da d'an man leb'e kafin ta kashe d'aurin d'an kwalinta, hijabinta ta d'auka bleue wanda ya

Please Login or Register in order to submit comment