Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gaba da hirarsu akan dangin malam da har yanzu babu wanda ya tako k'afarshi, malam da kan shi ya basu goro ya kuma fad'a musu, sannan jiya ma da kan shi ya sake komawa k'auye ya tunashesu lokacin, amma babu wata gamsassen amsa daga garesu kowa yayi gum da baki saboda su aurenshi da Iya ne basu so ba, abu kuma an ja shekaru gasu da 'ya'ya da jikoki amma a ce sun kasa fahimtar hakane Allah ya nufa. Dan haka jiya d'in yace ma Iya suyi hidimarsu kawai, tsirarun danginshi ba zasu hana yiwuwar wani abu ba, auren 'ya'yanshi ma aka yi shi ba dasu ba bare kuma jikanyarshi, dan haka za'ayi bikin Mimi kuma dama ba wata tsiya suke buk'ata daga garesu ba.


*Yammacin litinin*


Daga farfajiyar gidan take jin shewarsu suna shigowa, kallon Asma'u tayi tace "Su Salma ne fa da Ruky, nasan sun samo muku d'inkin."

Da zumud'i Asma'u tace "Allah yasa." Suna shigo d'akin ya gauraye da hayaniyar yan matan suna murnar samun d'inkinsu na anko wanda zasu saka ranar kamu dana kan amarya, zaune Salma tayi kusan Mimi tana nuna mata hotunan wasu amare da fad'a mata sunan wanda suka musu kwalliya, a haka ta kawo wata amaryar da kwalliyarta tayi kyau sosai kamar inji (ingine) ya mata, da zumud'i Mimi tace "Wannan tayi kyau, wa ya mata?"

Salma ce tace "Sara ce."

Da sauri Zeinaba tace "Baa ita ce jiya Sadeeq ya kaimu salon d'inta ba?"

Asma'u ce tace "Ita ce."

Mimi ce tace "Gaskiya aikinta na kyau, dubi kiga hannayena data wanke min jiya sun k'ara wani d'an banzan laushi wallahi, kinji k'afafuna."

Asma'u ma dariya tayi tace "Ai ni k'afata a hannuna ta kwana wallahi, dan sai nake jin kamar b'era zai iya gwaguye min k'afa."

Dariya suka kwashe da ita inda Salma tace "To kinga tunda ma kun tab'a zuwa dan Allah ki ma Sadeeq magana ya sama mana rendez-vous a wurinta ranar alhamis ta mana kwalliya, akwai tsada fa amma nasan zata mana sauk'i ai."

Asma'u ce tace "Yace fa sun san ta sosai tare sukayi karatu da ita a universitΓ©, kuma jiya daya kaimu yace Asas yace gobe ma a koma saboda gyaran amaryarshi."

Dariya sukayi inda Salma ta bawa Ruky hannu suka kashe tana fad'in "Shegiya Mimi, ta fa d'auko mai zafi wallahi, gayenta ya had'u k'arshe, komai na kece raini ya ke mata."

Yatsina fuska Mimi tayi tace "Ba kamar ke ba da zaki auri sa'an babanmu ba."

Dariya akayi saΓ― Salma data had'e fuska tace "Mimi bana son wulak'anci wallahi, wai me yasa kike min hakane? Kinga fa sati uku ya rage aurena amma saboda kece na zo ina ta zirga zirgan aurenki."

Murmushi tayi tace "To yi hak'uri na daina." Da haka yan matan suka ci gaba da shirye shiryen bikinsu inda kowace ta gwada doguwar rigarta da aka musu iri d'aya mai kyau da dogayen hannaye, saidai babu wacce rigarta ke da d'an kwali hakan na nufin dole su nemi wanda zasu d'aura.

Sun jima a gidan suna hirarsu kala kala ta nishad'i da k'aruwarsu dan Mama ta fita tare da Sahura da Shapi'a, har bayan azahar kafin suka ci abinci da Rauda ta musu mai sauk'i kafin suka bar gidansu suka barta tare da yan uwanta suka ci gaba da farin cikinsu.



*Indai da comment to da aiki tuk'uru insha'Allah.*



*Alhamdulillah*
7/22/21, 8:53 PM - Ummi TandamaπŸ˜‡: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?

*NA*


_SAMIRA HAROUNA_


*SADAUKARWA*


_GA DUKA_

*'YAN AMANA TA*


πŸ’«βœ? *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜? *[ T.M.N.A]* β˜? πŸ“–πŸ–ŠοΈ?

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


*24*



*Asubar talata* tana cikin bacci bata riga ta farka ba Mamar Asma'u data shigo gidan yanzu ta shafa mata lalle a kan ta da hannaye da tafin k'afa, zunbur ta tashi zaune tana kallonta tana mata dariya, ganin ta fita a d'akin sai kawai ta cire lallen na hannayenta ta shafawa fuskar Zeinaba dake baccinta, a firgice ta tashi tana fad'in "Waye? Mimi."

Dariya ta kwashe da ita tare da mik'ewa ta fita a d'akin ta shiga ban d'aki da d'an kwalinta a kai.

Safiya na yi Mama ta dinga aikinsu Yaseen suna raba alawa ta wankan amarya da yamma, Mimi kam banda fad'uwa da gabanta keyi duk jikinta ma yayi sanyi sosai, sai taji tana rasa karsashinta da zumud'inta da ma farin cikinta, misalin 08:00 Mimi dasu Rauda suka shirya suka shiga gidan Maimuna, anan k'awayenta suka dinga zuwa suna shan hirarsu da haka har aka samu wuni, dan kuwa saida la'asar tayi kad'ai aka kirasu suka shigo gidan, lokacin gidansu kuma ya cika da mutane yan uwa da yan unguwa an zo wankan amarya. Daga gurin angaye aka turo da motoci guda takwas dan kai su inda za'ayi wanka, kusan mutanen babu wanda bai je ba saboda wadatar motoci da aka samu, gidan yar uwar su mama dan waankan farko ana yin shi ne a dangin uwa.

Gaba d'aya basu d'auki minti arba'in ba tafiyarsu da dawowarsu, Mimi kam ta jik'a tayi laushi sosai dan tasha wankan ruwan lalle masu d'auke da itatuwan da kakaninmu suka yarda cewa yin wanka dasu yana zubar da duk wata shiririta da shirme, yana k'ara maka hankali da nutsuwa, tun a mota take hawaye har suka zo gida bata daina ba, tunda ta shiga d'aki kuma k'awayenta duk suka watse zuwa nasu gidajen aka barta da su Zeinaba kad'ai.

Alhamdulillah kam aure rahama ne kuma alkairi ne, a dalilin auren Mimi Abba da Mama sun samu gudumuwa sosai daga dangi da kuma abokan arziki, hatta da Alhaji Saminu ya aiko da gudummuwar buhun shinkafa da kuma kud'i har jaka hamsin, duk da dai baya bayar bane cikin dad'in rai, kawai yayi ne dan kar ace bai yi ba amma sosai ya ji zafin yanda Mimi ta banzatar da shi ko wayarshi bata tab'a d'agawa ba. Wasa wasa sai gashi lokaci na ta tahowa kamar almara.


*Ranar kamu*


Ko da k'arfe 08:00 ta buga suna salon ana ma su Asma'u kitso da k'unshi Mimi kuma saida aka fara mata gyaran jiki, ana idawa aka shiga zana mata k'unshi da jan lalle, mai salon d'in ce ta tsaya kan ta zata fara mata kitso k'anana, da sauri ta janye kanta tace "A'a, a'a bana so."

Da mamaki tace "Ban gane ba kya so ba? Kina amarya?"

Kamar zatayi kuka tace "Bana so ni dai, zafi ke akwai wallahi, bana son kitso."

Kamar da wasa Mimi ta ko dage ba za'a mata kitso ba ita kuka zatayi, dole k'arshe ta k'yaleta amma suna ta mata nasiha ta gyara a matsayinta na mace, ita dai saurarensu take bata kula kowa ba. Da azahar su Salma suka zo suma sunyi lalle da kitson su tsaf, dan haka ko da 03:00 tayi na rana suka fara shiri dan dukansu da kayansu suka zo, mimi ma ana ida lallen aka mata siraci ta shiga wanka, tana fito a sauk'ak'e kuma a nutse aka fara mata gyaran kakkauran gashin girarta, kad'an aka rage mata shi hakan yasa yayi kyau sosai tuni fuskarta ta fito shar da ita dake gashin nata bak'i ne wulik, kayan da Hafsat ta kawo mata ranar ta fara sakawa.

Doguwar riga ce abaya kalar ja mai duwatsu da kwalliya, tun ranar da aka kawo kayan Mimi bata duba su ba har Asma'u ta so bud'ewa ta hana, yanzu kam data saka sai suka saki baki suna kallonta, yanda rigarta ta zauna mata d'as a jiki ta mata kyau, ga tsarin rigar na ban mamaki wanda ya birgesu, wato idan sun fahimta komai a mutumce ne ya mata shi dan kar a sab'a k'aida, rigar zubin babbar riga aka mata na maza saidai a rufe take kirip har k'asa tana jan k'asa, gashi hula ce a bayanta irin na rigar sarauta alkyabba, sannan tana da kallabi ware daban wanda ake fara d'aurawa.

Kwalliya aka mata mai kyau da sauk'i wacce zaka rantse abonda aka shafa mata a fuska dama a fuskar ta ta yake, ana gama salllah la'asar dukansu yan matan sun fito sun haska a cikin rigunansu kalar pink na kakkauran yadi mai taushi, inda dukansu aka d'aura musu d'an kwali kala d'aya wanda suka siya.

Dogayen takalma k'afa ciki aka saka mata da jakarsu k'arama mai kyau da walk'iya, ga agogo data kama tsintsiyar hannunta dam ta zauna, kallabin abayar yanda aka d'aurashi daga ciki da kuma hular da aka d'ora mata sai ta fito sak gimbiyarta yar sarki jikar sarki.

Yamma sosai motoci guda uku dukansu k'irar benz suka paka a k'ofar salon d'in, a hankalce kuma a tsare yan matan duka suka kewayeta suka shiga takawa har waje, suna fita Asas ya hangesu daga cikin motar, wani murmushi ya sub'uce masa tare da jin yana sha'awar ya tsokaneta kamar ita d'in *matar yayanshi ce*, a sanyaye ya bud'e motar ya fito tare da bud'e mazaunin da zata shiga ta zauna, duk tsaye sukayi a bayanta saida ta shiga ta zauna ya rufe ya kallesu yace "Nagode k'awaye da gyara min amaryata."

Murmushi sukayi Salma tace "Mu ba k'awayenka bane, ga k'awarmu nan kana shirin rabamu da ita."

Murmushi yayi yana tsaye yana kalli duk suka shiga motar, sai Asma'u data zagaya d'aya b'angaren da Mimi take ta shiga, a hankali suka bar wurin suka d'auki hanyar gidan saukar bak'i na sheikh Abdul Waheed Salman Aliyu Sharif.

Kecup! Suka ji k'arar waya tare da hasken daya d'auke idonsu, da sauri suka kalleshi sai kuma kunya ta kamata ta sunkuyar da kai, murmushi yayi yace "Maah kin ga yanda kika had'u? Har saida na ji gabana ya fad'i tsabar razana."

A hankali ta d'ago matsakaitan idonta da suka sha eyeshadow a tausashe kamar mai rad'a tace "Me yasa gabanka ya fad'i?"

Ajiyar zuciya ya sauke ya kalli Sadeeq yace "Saboda ganin kamar *matar manya* na d'auka, bana so na zama tururuwa uwar jaye-jaye."

A sauk'ak'e ta kalleshi tace "Wannan maganar kamar dani kake, kar kasa na ji ba dad'i mana."

Sunkuyar da kanta ta sake yi shi kuma ya kalli Sadeeq dake fad'in "Ba wannan ba ma abokina, na ga amaryar ta mu kamar jinin sarauta, dan Allah daga wace masauratar take?"

Yar dariya tayi cikin sanyayyar murya tace "Ni ba yar masarauta bace, hasalima ko gidan sarauta ban tab'a shiga ba daidai da gaisuwa, idonku ne kawai suke yaudararku."

Dariya sukayi sai Asma'u data rik'o hannunta tace "Mimi gaskiya ya fad'a, jininki da zubi na tsarin yanayinki kamar na wacce aka haifa a cikin masarauta ne."

Murmushi Asas yayi yace "Kin gani, k'awarki ma haka take gani, amma ba komai karki damu, gaba kad'an zan mayar dake kamar sarauniya."

Murmushi tayi ta sunkuyar da kanta sosai, Asma'u ma dariya tayi tace "Allah yasa."

"Ameen." Ya fad'a yana gyara zamanshi, Sadeeq ne ya saci kallonta ta madubi yace "Ke ma da zaki bada dama ai gaban kad'an sai a mayar dake sarauniyar."

Dariya Mimi tayi tana sinne kanta wani dad'i na ratsata Asma'unta zata samu babban yaro, Asma'u kuma cike da zolaya tace "Wa zai mayar dani sarauniya bayan bana da suffar ko gimbiya?"

Dariya yayi yace "Gani, Allah da gaske nake Asma'u."

Kallon Asas yayi yace "Abokina fad'a mata mana."

Hararanshi yayi yace "Rainin hankali, ban tabbatar dana rik'e tawa a hannu ba zan zauna tayaka jefa k'uri'a? Kowa ya ji da kansa."

Da mamaki ya kalleshi yace "Au! Hakane kenan?"

"Eh d'in." Ya fad'a yana d'auke kai, jinjina kai yayi yace "Ba komai zan rama."

Sake kallon Asma'u yayi ta madubi yace "Asma'u kinji ko? Dan Allah ki bashi kunya mana ta hanyar amince min."

Kunya ce tasa ta sadda kanta k'asa tana wasa da yar wayarta a hannu, jin shiru yasa shi sake marairaicewa yace "Dan Allah *Asma'ul Husna* ki amince min kar na zauce."

D'aga kai tayi ta kalleshi da mamaki, ita ina zata kai babban yaro haka kamar Sadeeq? Bata tab'a saurayin daya taka ko da matakala ta farko na a b'angaren aji bare hawa na uku, ita kam ya zata ce mishu ne yanzu? Tabbas tunda suka san juna yake nuna mata kulawarshi da abubuwa masu wuyar fassara, ta d'auka mutumci ne kawai ashe abinda ke ransa kenan?

Mimi ce ta d'an tsamiketa a cinya hakan yasa ta fad'in "Washhhh!" Da sauri ta kama bakinta tana kallonta, da ido Mimi ta mata alamar ki amince mana, ita kuma ta mata alamar ni a wa? D'an tsaki tayi tare da yin kamar zata daketa, hakan yasa Asma'u jinjina kai tace "To zanyi tunani ko?"

Cikin murmushi Sadeeq yace "Ba matsala, zan jiraki har kiyi tunanin."

Bud'e baki sukayi da mamakin ashe ya ji me ta ce, da hirar raha da nishad'i har suka isa katafaren gidan daya had'u sosai aka k'watashi saboda hidimar da za'ayi.

Tabbas gidan ya cika mak'il da mata manya da yara ga kuma yan mata, saidai maganar gaskiya sun zo ne ganin zahiri da idonsu, tabbas su d'in ahali ne masu ilimi da sani sosai, amma fa suna da wani abu da saika rantse gidan jahilai ne, maganar talaucin gidansu Mimi a yanzu ba shine gabansu ba kamar da aka fad'a musu su waye iyayenta, sai suka zo tabbatarwa da tambayar kansu dame yarinyar tafi na su yaran da dayawa daga ciki aka so had'a Asas dasu amma ya k'i. Yan matan kansu suna so suga yarinyar ne dan su mata kallon hadarin kaji idan da hali ma har su yaga mata rigar mutumcinta.

Ai kuwa yamma na k'ara yin sanyi sai ga motocin angaye sun aje dangin Mimi, yanda suka fara shigowa harabar d'aya bayan d'aya yasa duk akaa kafesu da ido, su Shapi'a ne a gaba suka fara shigowa, hakan yasa wani gungu na 'yan mata kecewa da dariya ganinsu dunk'ul dunk'ul kamar yara amma kuma da fuskar dattijai, ajiyar zuciya Sahura ta sauke tace "Allah gamu gareka, nagode Allah da Mimi bata wurin nan da anyi b'atacciya."

Shapi'a ce tace "Ni kam fatana yanzu ta zo dan naga yanda zata ci uwar yarinya idan aka nemi wulak'anta mu."

Ido Sahura ta zaro tace "Rufa mana aisri Shapi'a, kai tsaye fa zata ce ta fasa auren d'an uwan nasu."

Cike da rashin dana sani Shapi'a tace "Idan tayi haka ma ai sai ta birgemu, wannan ai rashin sanin darajar d'an adam ne kamar ba gadon ilimi Sharif ya bar musu ba."

Murmushi Sahura tayi tace "Ya bar musu gadon ilimi, amma yayanshi kuma sun bar musu gadon dukiya, hakan ya jawo dayawa daga ciki dukiyar ce tafi aiki a tunaninsu."

Tab'e baki tayi tace "Allah ya kyauta musu."

Dogaye da gajeru ne suma haka duk suka samu wuri suka zauna ana d'an gaggaisawa sama sama, hakan ya jawo kowa ware nashi ya koma gefe ana k'us-k'us-k'us, tubarkallah farfajiyar ta cika har kujeru na neman yin k'aranci duk yawansu, dan kuwa kafatanin ahalin Sharif duk sun hallara, kama daga iyalin Aliyu Sharif, Usman Sharif, Salmanu Sharif da sauran abokan arzik'i, sosai Hafsat ke k'ok'arin ganin an samu sanayya da kuma fahimtar juna tsakanin danginsu da dangin Mimi, hakan yasa take ta nunawa iyayensu su Shapi'a a matsayin iyayen Mimi, wasu suna sakin jiki su karb'esu a gaisa, wasu kuma gaba da gaba suke yatsina fuska suna musu yak'e, hakan bai ma Hafsat dad'i ba amma ya ta iya, sharesu tayi ita ma tana fama da cikinta da wunin yau ta ji bai motsa mata ba ga wata muguwar kasala, jefi-jefi kuma sai taji gabanta ya fad'i kawai ba dalili, saidai bata bar ambaton ubangiji ba a bakinta da haka take jin sanyi sanyi a ranta.


Sanda motocinsu suka tsaya angayen ne suka fara fitowa suna shigowa filin, sai k'awayen Mimi da suka jera gwanin sha'awa suka sakata tsakiya tare da Asas dake ta doka murmushi, Mimi kan kanta na k'asa tana fama da rik'e jakar hannunta rigarta kuma na jan k'asa.

Kowa sake waro idanu yayi dan tabbatarwa kanshi abinda yake gani, dangin Mimi da dama sun san kayansu ba daga nan ba indai wajen d'aukar wanka ne da iya gayu, saidai yanda ta zama tamkar wata balarabiya ya k'ara birgesu da kashesu a game da ita.

Inda yan matan nan kuma suka shiga tamtama wai dama haka yarinyar take, sam babu wata makusa a tare da ita da zasu kushe, duk da kwalliya tana canza hallitar mace ta gyarata amma dai sun tabbatar zata yi kyau, na farko tana da dogon hanci ga ta jar fata, su kam idan aka barsu sai su ce wata baralabiya ce, duk sai suka kasa motsawa a wurin dan kwarjini ma suka ji tayi musu yarinyar, sai yan matan amaryar ne da angaye da suka dage suna ta d'aukarsu hotuna, da haka aka isar da Mimi kan kujerarta sai su Asas da suka bar wurin dan dama fa anyi ba dasu za'a yi hidimar ba.

A cikin taron yan matan nan akwai guda d'aya wacce ita ba fa abinda ya kawo kowa ya kawota ba, na ta k'udirin babba ne daya girmi na kowa dan kuwa sak'on Muttak'a ta zo isarwa, tasan kasada zatayi amma kud'in daya bata tare da yi mata alk'awarin aure yasa ta ji zata iya yin koma menene, tun shigowarsu Mimi ta mik'e ta shige zak'ewa akan komai tana kamkamba kamar wata yar uwa. Dangin Mimi kallonta suke yanda rawar kanta yayi yawa suna tunanin wata yar uwace makusanciya ta Asas. Inda suma dangin Asas suke kallonta wata marar hankali daga b'angaren Mimi take, da wannan kallon da duka kusurwoyin ke mata aka kasa samun wanda zaiyi mata maganar shishigewa da take musamman ta b'aangaren abinci.

Magriba na gabatowa Hafsat ta gabatar da masu ruwa da tsaki ayi kamun amaryar, ana idawa Hafsat tasa Aisha da su Fanna suka kawo cake dan ta yanka tunda ba wani abun ci aka ware mata ba ita, da taimakon Asma'u ta yanka Asma'u ta d'an saka mata a baki aka musu tapi ana dariya, *Feena* ita tayi babakere ta d'auki lemu ta tsiyaya a cup na glas, a hannunta dama akwai k'aramar k'waya babu wanda ya kula da tsiyarta bare ya lura har ta saka, mik'awa Asma'u tayi ita kuma ta mik'awa Mimi, amsa tayi ta d'an kurb'a zata aje Feena ta sake fad'in "Ki k'ara mana, ko ruwa baki sha ba fa."

Dayawa kallonta sukayi sai Mimi da take kallonta a matsayin dangin wanda zata aura, wannan kunyar tasa ta d'an k'ara kurb'awa kafin ta aje, Feena kam murmushi tayi duk da bata ji dad'i ba da bata sha sosai ba, amma dai tunda Muttak'a ya bata tabbacin guba ce mai had'ari sauta share kawai, a hankali ba tare da lurar kowa ba tayi kamar tana amsa waya ta fita a wurin.

Ana kwad'a kiran sallah magriba su Asas na dawowa d'aukar amarya, Hafsat ce ta rik'e hannunta saΓ― Asma'u a gefenta sauran yan mata a gaba wasu a baya suka nufi hanyar fita, Mimi dake jin matsanancin murd'awar ciki da jin kamar an rik'e mata numfashi ba tare da ankarewar kowa ba ta tafi baya luuuu! Ta fad'i a wurin, da sauri Hafsat ta kalleta tare da sakin hannunta tana furta "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un! Mimi."

Asma'u ma da sauri ta durk'ushe tana kiran "Mimi, Mimi lafiya."

Take aka rufe wurin ana tambayar lafiya, cikin tashin hankali Hafsat ta d'ago kanta ta kalli Aisha tace "Eesha kira Asas a waje."

Mayar da kallonta tayi kan Mimi, a hankali ta lura da jinin daya fara b'ullowa ta hancinta, cikin tsananin tashin hankalin da take jin bata tab'a riska ba ta daure ta d'ora hannu a kai tace "Na shiga uku, me ya sameta?"

Da gudu Asas ya shigo tare da rakiyar zaratan mazan a bayanshi, suna zuwa suka bud'a musu hanya, da sauri ya durk'usa yana fad'in "Me ya sameta? Me aka mata?"

Shapi'a ce tace "Ba abinda aka mata, ni fa ina ganin ko mayya ce ta kamata a wurin nan?"

Dayawa daga cikin mutanen suka kalleta sai wata mace mai aji sosai da tace "Nan ciki akwai wanda ya miki kama da maye ne?"

Hafsat ce tace "Bana tunanin haka, mu kaita asibiti jini ne yake fita a hancinta fa."

Wata dattijuwa ce tace "To ko tana da iska ne?"

A sukwane Asas ya mik'e tsaye tare da tattara k'arfinshi ya d'auki Mimi cak ya fita da ita da gudu, duk rufa masa baya akayi hankali tashe da tunanin miye zai faru, yana sakata mota yaja da gudun tsiya zuwa asibitin sheikh data fi kusa dasu har da ma gidanshi duk yana kusa da masaukin bak'in na shi, duk tarin tilin motocin dake wurin kad'an ne suka bi su zuwa asibiti dan su san halin da take ciki.




*Gobe d'aurin aure fa*😁



*Alhamdulillah*
7/22/21, 8:54 PM - Ummi TandamaπŸ˜‡: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?

*NA*


_SAMIRA HAROUNA_


*SADAUKARWA*


_GA DUKA_

*'YAN AMANA TA*


πŸ’«βœ? *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜? *[ T.M.N.A]* β˜? πŸ“–πŸ–ŠοΈ?

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


*26*


Ana gama d'aurin auren ya lumshe idonshi yana jimk'e hannunshi kamar zai naushi wani, kabbara aka d'auka a masallacin dan shi ne aure na k'arshe da aka d'aura tsakanin *Maryam Adam Shehu* da kuma *Abdul Waheed Salman Aliyu Sharif*, duk mik'ewa mutane sukayi ana fita da magana a baki, wasu hakan ya musu daidai da son zuciyarsu, wasu kuma hakan bai musu ba ko kad'an, sheikh kam bai motsa a wurin ba haka aka dinga bashi hannu ana mishi addu'ar fatan alkairi, su Abba ma fita sukayi yana kiran gida ba'a samu, dan haka mijin Sahura da suke tare ya jaraba kiranta kuma aka samu, shi ne fa suka sanar musu dan karsu ji abun daga sama kafin su isa gida. Saida yaji masallacin yayi shiru alamar ba mutane kafin ya d'aga kan shi, ai kamar wanda aka kora da gudun tsiya sai kuwa yayi wuf ya mik'e yana sab'a babbar rigarshi ya fita shi ma su Alhaji Ibrahim da Saleh suka rufa mishi baya tare da jami'anshi.

Duk motocinsu suka shiga inda sheikh ya kalli dreba yace "Dan Allah kayi sauri, gidan Hajia zamu je."

"To sheikh." Ya fad'a yana sake murza sitiyarin da kyau, ji yake an k'i kawowa gidan, gaba d'aya gani yake ba'a sauri kamar ya fita yaje da gudu a k'afarshi, tambayar "Anya kuwa Hajia tasan wa ta bani?" Yake yi, numfashi kawai yake saukewa lokaci zuwa lokaci, da wannan tashin hankali suka isa gidan daya k'ara kaurewa da mutane maza da mata, a k'ofar gidan motar ta tsaya sheikh ya fita, duk da hankalinshi a tashe yake kuma sauri yake sosai, amma tafiyar a nutse yake yin ta cikin hankali, gaisheshi ake da girmamawa kamar wani sarki shi kuma yana amsawa da murmushin yak'e a fuskarshi, har suka shiga cikin gidan ya fara hango Hajia a b'angaren Asas zaune a k'ofar shiga falon, mutane duk anyi cirko cirko wasu zaune wasu kuma tsaye babu mai magana.

Da sauri ya isa garesu saida ya kai daf dasu ya fahimci matar Alhaji Ibrahim ma tana tare dasu Kubra da matar Saleh sai Hafsat zaune kan ta a k'asa, kallonta yake yana karantar yanayinta, sosai ta bashi tausayi dan alamu sun nuna tasan abinda Hajia ta aikata musu.

Kallon juna sukayi da Hajia cikin rikitacciyar murya yace "Hajia ya haka? Ina Asas?"

Sake rumgume hannayenta tayi tace "Yana ciki likita na dubashi."

Sake kallon Hafsat yayi, matsawa yayi kusanta ya durk'usawa ya kamo hannayenta cikin na shi, da k'yar ta d'aga idonta

Please Login or Register in order to submit comment