Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tayi tana rik'o hannunshi zata tashi a matuk'ar gigice, da sauri ya rik'e ya mayar da ita ta zauna mutsu mutsu ta shiga yi tana girgiza kai alamar rad'ad'i amma ta kasa magana.

Durk'usawa yayi yace "Kinga yi hak'uri, idan ba haka ba fa jikinki zaiyi ta ciwo ne."

Rintse ido tayi wasu k'walla suka d'aso mata tana cije baki sosai, sake rik'e hannunshi tayi gam ta k'i saki, kallonta yake yana jin k'aunarta na sake shiga zuciyarshi, wani basaraken murmushi ya saki a ranshi yace " *Hak'ik'a tawakallin da nayi ne Allah ya musanya min da alkairi akan abinda nake zargi, tabbas wannan shi ne sakamakon da ubangiji yai min*."

Sakin murmushi ya sake yi yana kallonta ido rufe cikin sanyayyar murya yace " *Ina sonki Maryam*."

Bud'a ido tayi a hankali ta sauke a kan shi, saida ta ja majina ta d'auke idonta a tsaurare tana kawar da kai, cike da rashin jin dad'in yanayin da yake kallonta ya raunana murya yace "Dan Allah mana ki min magana Ryam."

Kallonshi tayi a zuciyarta tace "Kai ne mutum na farko da nake shakkar cizgawa, amma yanzu kai ma lokaci yayi da zaka d'and'ani *sarautar Mimi* ka ji idan da dad'i."

Kamar zaiyi kuka ya sake fad'in " *Mahmi*, kada ki yanke min wannan hukuncin yanzu, ki gafarceni kinji."

Sunkuyar da kai tayi tana cije baki dan sosai take jin zafi a k'asanta, kallonta yayi ya kalli ruwan da take zaune ciki, zunbur ya mik'e yana fad'in "Oh subhanallah!"

Bud'a idonta tayi ta kalli kanta a cikin bahon sai taga yanda zuwan suka canza, a rud'e ta kalleshi ta fashe da kuka amma ta k'i magana, sunkuyawa yayi ya rufe mata baki da yatsarshi yace "Shiru."

Tsaf ta had'iye kukanta sai kallonshi da take tana shashek'a, tana kallo ya bud'e wurin magudanar ruwan suka tafi kafin ya zuba mata wasu masu zafi amma ba sosai ba, kyab'e fuska tayi tana kallonshi da ta je tayi kuka saiyaharareta, ganin su ma ruwan sun canza kala ya sakΓ© gasgata lallai fa tayi k'ari, amma sai bai fad'a mata ba kawai ya taimaka mata ta fito ya aje mata buta yace tayi wanka, har zai fita a ban d'akin sai kuma ya tsaya ya kalli kan ta.

Cike da tuhuma yace "Ban tab'a ganinki da kitso ba, yanzu da kan haka zakiyi wankan tsarki? Taya ruwa zai samu kowane silin gashinki?"

Wani irin turo baki tayi gaba ta rufe ido irin fa ba ruwankan nan, cike da gargad'i yace "Dani kike?"

Bud'e idon tayi ta girgiza kai alamar a'a, k'wafa yayi ya juya ya fita ita kuma ta fara wankan tana mitar "Ba dai ni ka ma haka ba? Gobe kaf a gidajen jarida sai na buga labarinka, malam ba tausayi bare imani."

Tana gama wankan ta fito tana tafiya kamar wacce ta haihu, kayanta ta d'auka ta mayar ta nufi k'ofar fita dan bata ganshi a d'akin ba, had'ewa sukayi a bakin kofar ya kamo hannunta ya dawo da ita, zai zaunar da ita bakin gado tayi tsaye k'erere ta nuna mishi k'ofa da idonta alamar fa fita take so tayi.

Ba tare daya kalli fuskarta ba yace "Kin dawo gidanki kenan."

Da sauri ta juya ta kalleshi yana tattare zanin gadon, kawar da kai tayi ganin yanda zanin ya b'aci tana cije leb'e.

Har ya gama abinda ya ke ya shiga ban d'aki, kuka ta shiga rerawa kmaar wata marainiya tana jin abun duniya duk ya dameta, yana fitowa tsaye ya sameta kamar ta had'iyi tab'arya, yanda take ta share hawaye yasa shi kallonta da kyau yace "Wai ke ba kya gajiya da kuka ne?"

Ko kallonshi ba tayi ba bare ta kulashi, ban d'aki ya sake shiga da kayan baccin daya cire mata ita kuma ta zauna bakin gadon dan k'arfin halin ne take, dafe k'ugu tayi tana girgiza kai ta rintse ido, da sauri ta mik'e sakamakon tunawa da yanda abun ya ratsata da farkon nan, gaba d'aya tsigar jikinta ta ji tana tashi saboda tuna wannan abun al'ajabi, Anya kuwa sheikh ne mai shekarun nan? Ita ai ta d'auka zuwa yanzu irin sojan tayi la'asar d'in nan kad'an take iya zungura.

Zafin daya k'ara tsikararta yasa ta kuma cije fuska tana matsa k'ugunta, yana fitowa tayi saurin sakin fuskarta kamar babu abinda ke damunta.

Daga nan zaune take jin jikinta na wani gab-gab-gab yana rawa, d'an tab'a wuyanta tayi taji masifaffen zafi zazzab'i ya sauko mata, d'ora kanta tayi a cinyarta tayi lak'was abinta, gaba d'aya yanayin jikinta bata jin dad'inshi, abubuwa take ji kawai sabi da bata saba da su ba, fitowarshi daga ban d'akin yasa ta d'ago kanta a hankali amma bata kalleshi ba, gabanta ya durk'usa yana rik'o hannayenta yana kallon fuskarta, cikin rarrashi da tausayi yace "Ryam, ki yi magana kinji, ki ce wani abu dan Allah."

Wani huk-huk-huk ta fara yi tana tuk'ak'o amai, da sauri ta mik'e zata nufi hanyar ban d'aki kawai rawar da jikinta keyi da rashin kuzari suka zubar da ita a k'asa warwas tare da dannowar amai, da sauri ya mik'e ya matsa kanta yana furta "Subhanallah! Ryam sannu kinji."

A galabaice ta kalleshi duk da bata son yi mishi magana da k'yar ta iya bud'a baki tace "Ka cire min abinda ka saka min a ciki."

Da mamaki ya kalleta sai kuma ya saki murmushi yana durk'usawa yace "Ba abinda na saka miki Ryam, watak'ila dan ina tsoho ne shiyasa na k'arar da k'arfi na a yau d'in nan."

Kamata yayi zasu shiga ban d'aki amma ya kula k'afafunta sai hard'ewa suke, d'aukarta yayi suka shiga ta kurkure bakinta suka fito, tana kallo ya tsaftace wurin data b'ata kafin ya d'auki wayarshi, saida ya fita a d'akin kafin ya amsa.

Kafin Rakiya ta zo gidan mintunan da aka d'auka sai Mimi ta k'arasa gigicewa ta fita hayyacinta, abu ga farar fata lokaci d'aya ta zube tayi fiyat da ita, zazzab'i sosai take ji yana taunar k'asusuwan jikinta ga kuma rad'ad'in da k'asanta keyi har yanzu, ko da Rakiya ta zo Mimi bata san tana kan ta ba tsabar raki da kuma wahala, banda muryar sheikh dake kayar mata da gaba ba abinda kunnuwanta ke ji.

Mimi dai da ba allura take so ba, tunda aka kira Rakiya daga asibiti shi da Rakiya dake gaggawa ko ta tafi gidanta ita ma haka sukayi ta rarrashi amma ina, kuma ta k'i magana saidai ta girgiza kai kawai tana share hawaye dan tayi niyya daga yau har gobe sheikh ba zaiji muryarta ba, k'arshe dai Rakiya ce ta kalli sheikh cikin rad'a tace "Sheikh kawai ka rik'e mana ita a mata allurar bacci, dan ba zata tsaya a mata d'inkin nan ba."

Saida ya je inda take zaune akan gadon ya zauna shi ma, jawota yayi a jikinshi ya rumgume, tana ganin Rakiya tana gyara tsinin allura ta nemi zillewa a jikinshi, tsam ya matseta a jikinshi hakan ya hanata damar motsawa sai yan k'afafunta kawai saΓ― kuma gunjin kuka, bata d'ago daga jikinshi ba bacci yayi awan gaba da ita, gyara mata kwanciya yayi kafin ya fita ya d'akin ya zauna falo kan kujera, kan shi sadde k'asa yana tunanin yanda yar mitsitsiyar yarinyar nan ta shayar da shi ruwan mamaki, murmushi kawai yake saki tare da cin burika na kyautata mata da kuma fanshe mata ranar ta.

Fitowar Rakiya daga d'akin ta sashi mik'ewa ya tarbeta, da kulawa ya tambayeta "Ya take?"

Fara'a ta masa tace "Da sauk'i, na mata d'inki sannan na k'ara mata ruwa."

Ajiyar zuciya ya sauke yace "Nagode Rakiya, kiyi hak'uri na saki latin zuwa ga iyalinki kema."

Murmushi tayi tace "Ba komai sheikh aikinmu Kenan."

Kallon d'akin yayi yace "Ba komai dai yanzu ko?"

A ladabce tace "E sheikh, zuwa safe zan sake zuwa da kaina na dubata."

Tana tafiya shi ma fita yayi ya siyo kaji ya dawo, alwala ya d'auro ya shinfid'a sallaya ya kabbara sallah, raka'a hud'u yayi masu tsayin gaske a jowace sujada yana godiya ga Allah daya masa wannan kyauta tare da neman gafara akan zargin yarinya da yayi, abun ne shi ma yafi k'arfinshi, so ne ya rufe mishi ido sai kishi yayi tasiri a zuciyarshi, abinda ya faru a ranar dole ya firgita nutsuwarshi ya jefa zuciyarshi a hali na wasi-wasi, bai san gaibu ba bare yasan gaskiya, dan haka kishi ya dinga d'awainiya da shi ya dinga jin kamar wani ya rigashi.

*04:00* k'arar agogo tasa ta motsawa dan baccin ya saki idonta, da k'yar ta bud'a idonta da suka mata nauyi ta kalli rufin d'akin, dake harda allurar kashe jiki ta mata sai lokacin ta ji wani azababben ciwo ya taso mata na zafin d'inki da kuma musababbin d'inkin, yunk'urawa tayi ta tashi zaune tana sakin hawayen da ita kanta bata so suka taho mata ba, sauke idonta tayi akan sheikh dake gefenta zaune akan sallaya.

Da sauri ya taso ya durk'usa yana fad'in "Ryam kin farka? Sannu kinji."

K'asa tayi da idonta ta kasa kallonshi kuma ba tace komai ba, rik'o hannunta yayi tare da kai d'aya hannun a wiyanta, jikinta da zafi har yanzu sosai tab'a goshinta yayi shi ma dai da zafi alamar ciwon kai, wani huci yayi na rashin jin dad'in halin daya sa yar mutane a ciki, sai ya tuna sanda ta shigo d'in nan tana bashi labarin daya tabbatar k'irk'irarshi tayi.

Mik'ewa yayi yana fad'in "Bari na taimaka miki ki shiga ban d'aki kiyi alwala, lokacin sallah subah tayi."

Hannayenshi ya kai zai kamo na ta ta mak'ale kafad'a alamar um um, turo baki tayi gaba kan ta sadde, cikin rarrashi yace "Haba mana Ryam, muje ko?"

Sake mak'ale kafad'a tayi alamar dai um um, tsaye yayi yana kallonta yana sauke numfashi, nufa hanyar fita yayi yace "Bari to na kawo miki abu ki ci saΓ― ki sha magani."

Tana kallo har ya fita a d'akin, jim kad'an ya dawo d'auke da faranti k'arami, ajewa yayi kusanta ya zauna yana d'an yago naman kazar yace "Yawwa to bud'a bakin."

Sake mak'ale kafad'a tayi har da fad'in "Um um."

Waro ido yayi yace "Shi ma ba zaki ci ba?"

Zuba mishi ido tayi tana kallo, cikin rarrashi yace "Kinga Ryam kiyi sauri ki ci, idan kika gama akwai abinda zan baki kinji."

Kallon da take masa sai ya fara jin ya tsargu dan kamar macijiyar daka kashewa miji ce a gaban idonta, sunkuyar da kan shi yayi yace "Fad'a min me kike so? Ya kike so nayi Ryam? Har yanzu ban ji muryarki ba, kina tunanin hakan abu mai sauk'i ne a gareni?"

Shiru ta masa hakan yasa shi d'ago kai ya kalleta, da sauri ta sauke na ta idon k'asa tana kallon farantin kazar (uwata ba'a wulakanta kazi fa😟) kofin madar daya zubo ya d'auka zai kai bakinta shi ma ta kawar da kai, kamar zai fashe da kuka ya kalleta yace "A'a, wai ya kike so dani ne? Ryam kin k'i ci kin k'i sha kuma kin k'i magana."

Bud'e baki tayi da iya k'arfinta ta fashe da kuka, hankali tashe ya aje kofin hannunshi ya tallabo fuskarta yana fad'in "...



*Alhamdulillah*
7/22/21, 9:00 PM - Ummi TandamaπŸ˜‡: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?

*NA*


_SAMIRA HAROUNA_


*SADAUKARWA*


_GA DUKA_

*'YAN AMANA TA*


πŸ’«βœ? *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜? *[ T.M.N.A]* β˜? πŸ“–πŸ–ŠοΈ?

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


*42*



Bud'e bakinta tayi da iya k'arfinta ta fashe da kuka, hankali tashe ya aje kofin hannunshi ya tallabo fuskarta yana fad'in "" A'a Mimi, me na miki kuma daga magana? Kinga idan ba zaki sha ba to shikenan, amma daina kukan kinji."

Hannaye duka biyu ta rattab'a a fuska tana murzar ido tana ci gaba da kukanta, zaune yayi da kyau kusanta ya jawota ya d'ora kanta a k'irjinshi yana shafa kanta yana fad'in "Shikenan to, haba yan matan tsohonta, so kike ace raguwa ce ke a miki dariya?"

Wata irin shashek'a ta shiga yi da gangan kamar zata had'e zuciya, sake tallabo fuskarta yayi ya marairaice yace "Haba Ryam, so kike sai kin nunawa duniya yau sheikh Abdul Waheed ya zo gareki? Ki daina mana kinji, ya isa haka kar kanki yayi ciwo fa."

A tak'aice dai yanda sheikh yaga wannan dare haka ya wayi gari, rarrashin duniya ba wanda bai mata ba amma ina ta k'i ji, kuma gashu ba lokacin jawo aya ko hadisi bane bare ya tab'osu ko ta saurara, a daddafe yayi sallah ya dawo kan ta ya zauna yana kallonta, idonta sun kumbura sunyi ja har fuskarta ta canza.

Wani dogon numfashi ya sauke yana jin tausayinta na k'ara tsumashi, kukan da take sam bai d'aukeshi na tab'ara ba saina hak'ik'anin gaskiya, kukan shagwab'ar ya mishi yanda yake buk'ata, ya so a ce iya su kad'ai ne a gidan nan da sai ya nuna mata k'arshen zalamarta, zai biye mata ya riritata ya goyata a bayanshi ya mata dokin wuya yanda dole tayi shiru, da zai aje komai na shi ne ya shiga faranta mata rai har sai yaga hak'orinta sun bayyana da sunan dariya.

Tsaf take k'are masa kallo daga rufe fuskarta daa tayi da hannaye tana murzawa wai ita me kuka, sai yanzu ne ta kula ashe fa ustazun nan d'an gaye ne, askin fa kad'an ne ya banbantashi da irin na yan zamani, kawai dai shi ya aske duguzar ne sosai yanda ba'a barta a doron kan ba, amma har wani gyaran fuska yanda gemun ya masa sai ta ga ya birgeta yau kam, ga jallabiyar data fito da surarshi sosai.

Hannayen na ta daya kamo yasa ta rintse ido tana shashek'a, cikin sanyin murya yace "Ryam, zaki sha chocolat?"

Girgiza kai tayi alamar a'a, d'an jim yayi yana kallon gefe alamar tunani sai kuma yace "Zaki sha madara?"

Sake girgiza kai tayi alamar a'a, da sauri yace "Zaki sha ice cream?"

Girgiza kai ta sake yi alamar a'a, d'orawa yayi da "To fad'a min me kike so?"

K'ura masa ido tayi da k'yar ta bud'i bakinta murya can k'asa tace "Gidanmu nake so."

Tsura mata ido shi ma yayi, a take a shiga tunanin ta ya zai kaita gidansu a halin da take cikin nan? Kowa yasan ya zo wa wannan yar yarinyar? A gaskiya yana jin kunya kula ba zai iya ba, shi fa Hafsat ma baya so ta samesu a halin nan, gashi kuma ba zai iya kaita wajen Hajia ba dan kamar akwai cin fuska ma, duk da uwa take gareshi amma ai 'yarta yake aure, haihuwa kuma ba wasa bace, tun suna kawaici suna kawar da kai wata rana shaid'an da zai fara zugasu da saka musu tunani marar kyau.

Rik'o hannayenta yayi da kyau yana kallon fuskarta yace "Ryam, ba zamu je gidanku ba gaskiya, amma idan kina so zamu je wani wuri, na tabbata zai k'ayatar dake, kina so?"

Zuba mishi ido tayi kamar bata gane yarenshi, lumshe ido yayi alamar rok'o yace "Dan Allah Ryam."

Rufe idonta tayi alamar ba ma zata kula shi ba kenan, mik'ewa yayi tsaye ya daddage ya daka mata tsawar data saka ta zabura ta bud'a ido sanda yake fad'in "Dake nake magana malama kina min shiru."

Kyab'e baki tayi zata fashe da kuka ya nunota da yatsa ya sunkuyo daf da ita yace "Kika min kukan nan saina kuma zazzabga miki bulalar da zata fahimtar dake me nake nufi."

Tsaf ta had'e kuka tayi k'asa da kanta, nuna mata k'ofar ban d'aki yayi yace "Maza je kiyi wanka kiyi alwala kiyi sallah."

Jiki na kakkarwa ta shiga saukowa daga kan gadon, saidai allurar da har yanzu bata gama sakin jikinta yasa k'afafunta kasa d'aukarta, shirin fad'uwar da tayi yasa shi azamar tallabota jikinshi, cak ya d'auketa ya nufi ban d'akin da ita yana kallon fuskarta fuskarshi a had'e yace "Yarinya sai taurin kai, bakya gane magana cikin sauk'i."

Tsayar da ita yayi ya shiga cire mata kayan jikinta, nok'ewa ta shiga yi ita ma hakan yasa shi d'aga kai ya kalleta yace "Miye na kunyar kuma? Ba mun zama d'aya ba?"

D'auke kanta tayi tana kumburo baki, murmushi yayi yace "Shikenan bari ki gani, aidai zakiyi k'orafin na kalleki babu kayana ne ko? To bari muyi wankan a tare."

Kar-kar-kar! Jikinta ya fara ta shiga taka k'afafunta zata fita a ban d'akin, rik'ota yayi ya had'ata da k'irjinshi yana kallon fuskarta yace "To miye a ciki? Ni ba naki bane?"

Ko kallonshi ba tayi ba ta shiga sinne kan ta k'asa, b'alle botir d'in rigar yayi tare da tattarota daga k'asa yayi sama da ita, yanda ta ganta kwance a k'irjinshi da babu riga sai kwantaccen bak'in gashin daya kusa mamaye knirjin mai sulb'in gaske kamar na kan shi yasa ta saurin juya baya, hakan ya bashi damar k'arasa cire...😎 ya jawota ya had'a da jikinshi, yanda yaji jikinta ya fara d'aukar zafi da gaske ga rawar da yake mata yasa shi sakin murmushi ya d'ora hab'arshi a kafad'arta cikin kunne ya rad'a mata "Ryam ga ki da tsoro amma kuma ke ma kina bada tsoro."

Kakkaucewa ta shiga yi saboda kayan jikinta daya fara shirin cire mata, bai bata damar matsawa nesa da shi ba saida ya rabata da kayanta, yanda jikinsu ke gugar na juna tana jin duk wata hallita ta bawan Allahn nan a fatar jikinta sai ta nemi numfashi ta rasa, gaba d'aya ta sarewa lamarin mutumin ko ta ce lamarin maza.

Duk girmanshi, duk shekarunshi, duk matsayinshi yanzu nan ya aje su gefe har ya tsaya gabanta babu kaya zasuyi wanka? Tunda taja numfashinta sama bata maido shi ba ita dai ta k'ame wuri d'aya ta rintse idonta dan bΓ’ zata iya kallonshi ba. Sheikh ko a jikinshi, wanka yake musu sosai cikin nutsuwa tare da wasa da ita, Mimi dai abun jin shi take wani iri, ita dake burin d'an k'aramin mijinta suyi wanka tare sai gashi yau old man ne ke mata wanka kamar baby.

Tana jin sanda ya kashe panpon ruwan suka tsaya, jim kad'an taji yana saka mata rigar wanka, kamo hannunta yayi suka fara takawa tana jin k'asanta na d'an mata zuzar zaren d'inkin nan hakan kuma na k'ara mata rad'ad'i.

Kan kujera ya zzunar da ita gaban madubi, mai ya d'auka ya durk'usa ya fara shafa mata man, kallonshi take yanda har yanzu towel ne a k'ugunshi, sam sai yake mata kamar ba tsoho ba, yanda yake d'aukarta da yanda yake sarrafa jikinshi ba alamar manyanta irin ta tsofaffin da zaka ga suna fama da ciwon baya k'afafu da sauransu. Yanda take kallonshi idonta bud'e yasa shi sakin murmushi yace "Inna Issa har yanzu ba zaki min magana ba."

K'in d'auke idonta tayi a kan shi, d'an murmushi kawai ya sake saki ya ci gaba da murza mata mai, yana gamawa doguwar riga abaya ya d'auko a cikin kayan daya k'ara zuba mata na ban mamaki, pant ya d'auko da bras ya sake durk'usawa ya zura mata k'afafun, kamata yayi ta mik'e zai k'arasa saka mata sai kuma ya kalleta, d'an sosa kai yayi da irin alamar jin kunya yace "Yan matan tsohonta, anya kuwa wannan zai isheki? Ni fa kallon baby nake miki."

D'auke idonta tayi daga kan shi ta k'arasa saka wandon, tam ya mata alamun dai ya matseta sosai, d'aukar bras d'in tayi ta saka ita ma haka ta mata kip, d'aukar rigar tayi ta saka da sauri ya zaunar da ita kan kujerar, macaji ya d'auka ya fara caje mata gashinta, tsaf ya d'aure mata shi da mad'auri sannan ya d'auki kallabin rigar ya fara yane mata kan cike da k'warewa, yana gama mata ya tallabo fuskarta ya sumbaci goshinta sannan ya nuna mata sallaya yace "Kiyi sallah, zan je na saka kaya nima."

Takawa tayi ta k'arasa gaban sallayar, tana ganin fitarshi a d'akin tayi saurin cire pant d'in nan dan yana tab'ata a jikinta sosai tana jin zafi saboda d'inkin da aka mata, sallah ta kabbara shi kuma ya shiga d'akinshi dake nan b'angarenta dan shiryawa.



*Asa-Ma'u*


Tunda Asma'u ta zauna jiran Mimi ta ga ba alamarta sai kawai ta ma Hafsat sallama suka taf tare da Kabiru, ita ma suna zuwa gidan suka had'e da Asas, ita kanta sai ta ji kunya da suka had'u da shi ba'a gida ba, a d'arare ta bishi suka nufi na su gidan suma.

A daren kam tasha abubuwa da dama, kunya, fad'uwar gaba, farin ciki da kuma bak'ar wahala, dan kuwa Asas ya nuna mata ya samu lafiya, sun sha amarci sosai da kuma soyayya har garin Allah ya waye, daga wajen Hajia kawai yasa aka kawo musu abinci suna ci ya dunk'ule matarshi a bargo suka shiga ramuwar bacci.

Sake matseta yayi a jikinshi yace "Husna."

A hankali ta amsa da "Na'am."

Cikin taushin murya yace "Kina so na?"

Sinne kanta tayi a k'irjinshi tana d'an shafa cikinshi da hannunta ke kai tana murmushi, cikin shafa bayanta yace "Ina jinki mana, ko ba kya so na?"

Girgiza kai tayi a hankali tace "Ni ban ce ba."

"To me kika ce kenan?" Ya fad'a kai tsaye, cike da jin kunya tana b'oye fuskarta a jikinshi tace "Taya zan ce bana son mijina wanda a yanzu ya zama sirrina, a yanzu fa babu wani abu daya mana shamaki ni da kai, ko na so ka ko na k'i ka ka riga daka zama wani b'angare na jikina."

Matseta yayi sosai ya sumbaci kanta cikin dadad'an murya yace "Ina sonki *Asmy* na, ina sonki sosai, Allah barmu tare."

Cike da jin ya k'arawa kanta girma da farin ciki ta matseshi ita ma cike da jin kunya murya k'asa k'asa tace "Ni ma haka."


D'an tsakulkuli ya mata yana dariya yace "Ke ma me? Sai kin fad'a fa malama ko nima na dawo da kayata na rik'e."

Cikin bille bille ta shiga k'yalk'yala dariya tana fad'in "Nima haka, na fad'a to na fad'a."

Dakatawa yayi yace "Me kika fad'a to? Fad'i ko kuma na sake juyewa a kan ki yanzun nan, dama ba isata kikayi ba dan naji kin k'ara wani irin dad'i."

Dukanshi tayi a k'irji cike da kunya tace "Kai wallahi, haba dai."

Cikin dariya yace "Gaskiya na fad'a ai, na tabbata shirya min kanki kikayi kafin dawowata."

Girgiza kai tayi tace "Ni ba abinda nayi."

"Kin tabbata?" Ya tambaya yana lek'an fuskarta, jinjina kai tayi alamar eh, murmushi yayi yace "To yanzu fad'a min na ji, ke ma kina so na?"

Turo baki tayi tace "To wai me yasa ka damu da sai na fad'a maka nima? Ka yarda da abinda na fad'a maka mana."

Mak'ale kafad'a yayi yace "Um um! Kawai ki fad'a min Husna ko nayi kuka."

Waro ido tayi ta kalleshi da mamaki yanda kam duk ya kyab'e fuska shi shagwab'abb'e, kunya tasa ta rufe fuska tace "To ni ma ina sonka."

Sake k'amk'ameta yayi yana murmushi yace "Ko ke fa, har na ji dad'i."

Cikin farin ciki suka samu baccinsu a nutse suna k'amk'ame da juna kamar dama can asali masoya ne.




*Mim-Sheikh*


Cikin wata dakakkiyar shadda ya shigo d'akin wacce ta sa shi bayyana sak a angonshi, fara ce shaddar ga rigar daya d'ora irin ta malamai ga hula da takalmi k'afa ciki, shagala tayi da kallonshi dan gaskiya da zata iya bud'a baki a wannan lokacin tayi magana to zata ce "Kayi kyau." Ne, amma data ga yana mata murmushi saita d'aure fuska har saida ya tsaya gabanta yace "Zamu iya tafiya?"

Mik'ewa kawai tayi ta nufi hanyar fita, rik'e hannunta yayi suka kalli juna, ba alamar sakin fuska yace "Bana son jin shirun nan idan muka fita, zan d'auki wannan shirun ne kawai saboda ni na ja, amma iyalina ki girmama min su ta hanyar bud'a baki kiyi magana idan sun miki, Hafsat a gaba take da ke, karki jira sai ta gaisheki kafin ki gaisheta."

Shafa kumatunta yayi yace "Kin gane?"

Sunkuyar da idonta tayi saboda k'wallar da taji sun cika mata ido, tallabo fuskarta ya sake yi cikin sanyin murya yace "Kiyi hak'uri kinji,

Please Login or Register in order to submit comment