Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sauk'i ko?"

D'an kallon sheikh tayi kafin ta jinjina kai alamar to, a hankali ya taka ya k'arasa daf da Asharf ya zauna bakin gadon, rik'o hannunshi yayi yana kallon kyakyawar fuskar Ashraf, duk da ba ciki d'aya suka fito ba amma yana bala'in son d'an uwanshi, sun shak'u sosai tun yana yaro, ladabinshi gareshi da kuma k'iriniyarshi suna birgeshi, kusan baya da aboki bayan yaron duk da kuwa ba tsaranshi bane, amma yanzu haka da zai samu sab'ani tsakaninshi da yayarshi na zaman tare, to shi yake ajiyewa tsakaninsu ya ja musu kunne.

Lumshe ido yayi kafin ya sake bud'ewa, addu'a ya shiga karantawa yana tofa masa kusan minti talatin, su kuma kallonshi suke dan bai d'aga murya ba bare su ji su amsa da ameen, dan haka suna ganin ya sakin hannun Ashraf suka amsa da "Ameen."

Mik'ewa yayi ya kalleta yace "Mu tafi." Kallonsu Hajia yayi yace "Saida safenku."

A nutse suke takawa masu tsaron na gaba shi kuma suna baya tare da ita, suna fita mai tsaron ya kama murfin mota zai bud'e mishi, d'aga mishi hannu yayi alamar a'a, dakatawa yayi ya koma mazauninshi, da kanshi ya bud'e mata ta shiga ta zauna kafin ya rufe ya zagaya d'aya b'aren suka bar asibitin.



*Alhamdulillah*
7/20/21, 9:04 AM - Ummi TandamaπŸ˜‡: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?

*NA*


_SAMIRA HAROUNA_


*SADAUKARWA*


_GA DUKA_

*'YAN AMANA TA*


πŸ’«βœ? *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜? *[ T.M.N.A]* β˜? πŸ“–πŸ–ŠοΈ?

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


*3*


Kasancewarshi malami zai sa kayi mamaki idan kaga tabkeken gidan da mai gadi ya bud'e musu suka shiga, amma idan kasan margayi Alhaji Aliyu Sharif zaka tabbatar wannan ba komai bane, dan tsohon shahararren d'an kasuwa ne daya tara mahaukatan kud'i kuma ya mutu ya barwa magadansu, haka na su iyayen suma suka musu suka bar musu suka gaji nasu kason, haka kuma sheikh Abdul Waheed ba malamin ci da ceto bane, d'an kasuwa ne haka kuma a cikin gwamnati ma shi d'in mai bawa gwamna shawara ne akan harkar data shafi ilimi. Shigarsu k'ayataccen falon yasa yara tasowa da gudu suna musu oyoyo, da murna shi ma ya d'auki k'ananan yana rumgumesu a jikinshi, babbar cikinsu kam a hankalce ta k'arasa kusa da mahaifiyarta tana fad'in "Momy sannu da dawowa, ya jikin tonton?"

Da murmushi ta amsa mata da "Jikinshi da sauk'i, dan mun baroshi ma yana bacci."

Da nutsuwa yarinyar tace "Allah ya bashi lafiya." Da fara'a tace "Ameen."

Sauke yaran yayi yana kallon yarinyar yace "Uhm! *mamana* shi ne ko a kulani? Sai mamanki ko? To na yi hushi ma."

Dariya tayi ta matsa kusa da shi ta kama hannunshi tace "Abu, kayi hak'uri, ina tambayar jikin tonton d'ina ne."

Dafa kanta yayi yace "Ku masa addu'a kun ji, zai samu lafiya insha'Allah."

Da kai ta amsa masa tare da fad'in "Insha'Allah Abu." Murmushi ya mata shi ma yace "Masha Allah."

Kallon *Hafsat* yayi yace "Zan shiga ciki."

Da ido ta masa alamar "Ina zuwa." Wucewa yayi yana murmushi tare da cire babbar rigarshi irin ta malamai da bata da wuya sai hannaye kawai, kallon *Aisha* tayi tace "Eesha, ku je d'akinku ki taimakawa k'annanki su watsa ruwa su saka kayan baccinsu, dare yayi kin ji."

Da ladabi tace "To Momy." Kallon k'annanta tayi su uku tace "Muje."

Mai bi mata ne ya kalli uwar yace "Momy, amma ai ban da ni ko?"

Dariya tayi tace "Kai ai yanzu saurayi ne."

Murmushi jin dad'i yayi tare da wuce suka haye sama inda d'akunansu suke, mik'ewa tayi da k'yar saboda k'afafunta da suka kumbura sakamakon cikin dake jikinta na wata biyar ta nufi d'akin sheikh, falo ne mai zaman kan shi dake zagaye da litattafai na ilimi daban daban da littafi mai tsarki kala kala anyi jere dasu, kai tsaye d'akin baccin ta wuce ta samu har ya shiga wanka, zaune tayi bakin gadon ta d'aga muryarta tana fad'in "Shi ne ka shiga ka barni ko? Ai zaka koma ne dan da kan ka zaka min wankan yau."

Yana jin ta sai murmushi da yayi bai amsa mata ba, bai wani jima ba ya fito da rigar wanka a jikinshi, yana dariya, kama hannunta yayi yana fad'in "Muje na miki to, shikenan?"

Turo baki tayi tace "To me yasa zaka tafi ka barni?"

Murmushi ya sakΓ© yi yace "A gafarceni to."

Murmushi tayi ita ma tace "To na gafarceka sheikh nawa."

Zip d'in rigarta ya ja zai cire tayi saurin cewa "A'a nagode, zan yi da kaina ai."

Lumshe ido yayi ya girgiza mata kai alamar a'a yace "Ki barni, ina so na samu ladar, zanyi koyi da annabina ne manzon rahama, yayi wanka tare da matanshi yayi raha da dariya dasu."

Jinjina kai tayi tace "To ai ni yanzu kunya nake ji, wannan abun fitowa yake sai nayi muni."

Dariya yayi sanda ya kalli cikin data nuna mishi, shafa kumatunta yayi yace "A rayuwar aure babu kunya tsakanin ma'aurata, karki manta addininmu shine addunin da yafi kowane kunya hasalima ya koyar da mu jin kunya, amma a bisa haka ya fayyace mana komai game da rayuwar aure da yanda zamu tafiyar da addininmu, manzon Allah (S.A.W) yafi budurwar data fara k'irgen dangin kunya, yanda take jin kunya ta kasa sakewa da mahaifiyarta ma, a cikin gidansu ta kan zama kamar marar gata ko bak'uwa, amma a haka ya warware mana addininmu, kama daga yanda zaka samu najasa a jikinka har zuwa yanda zaka tsaftaceta, saida ya fad'a mana, dan haka wannan cikin kar ya sa ki cuceni ko ki cuci kan ki, kin ji Hafsat."

Da kai ta msa alamar to, tana kallo ya cire mata kayan duk ya d'aure mata jiyoyin jikinta da k'aramin tambihinshi, hannunta ya ja zuwa ban d'akin ya shiga wankaceta soso da sabulu, saida ya gama mata suka fito, duk da d'akinshi ne amma a nan ya samu rigar baccinta ya saka mata, kwantar da ita yayi ya kalli fuskarta yace "Kiyi bacci kin ji, kin wuni ba kya jin dad'i yau hakan yasa na kai ki wajen Hajia, gashi alamu sun nuna a can ma baki samu hutu ba."

Murmushi tayi tace "To, kai fa?" Murmushi yayi shi ma yace "Zan kwanta, amma zan fara dubo yaran nan na gani."

Jinjina masa kai tayi ta bishi da kallo cikin doguwar farar rigarshi har ya fice a d'akin.



*Maryam*


Dake jiya saida Bello yasa yaran gidan suka cika musu kaf mazubin ruwa dake gidan yasa yau bata tsaya jiran ruwa ba, wanka kawai tayi ta shirya dan tafiya makaranta, fitowa tayi cikin hijabinta fari k'ar har k'asa rumgume da Alqur'aninta a k'irji, zaune tayi a kan tarmi tana kallon k'annanta dake cin d'umamen tuwo, yatsina fuska tayi tana ayyana ba zata iya cin shi ba, ta d'auko kud'in da mijin Maimuna ya bata Alhaji *Saminu*, idan ta je makaranta ta samu ko alala ta ci, fitowar mahaifinsu daga d'akin yasa ta saurin sauka daga turmin ta durk'usa kan ta a k'asa, saida ya tsaya gabanta cikin ladabi tace "Abba ina kwana."

Da fuska a washe ya amsa da "Lafiya lau Maryam, har an shirya?"

Jinjina kai tayi tace "Eh Abba." Kallon su Amir yayi dake cin abinci yace "Ku hanzarta to karku tsayar da ita."

D'an satar kallonshi Maryam ta yi a ran ta tana fad'in "Su ba yara ba ace sai na jera tare da su mun tafi?"

"Maryam." Mahaifinta ya kira sunanta, da sauri ta d'ago tana zuba mishi idonta, masha Allah, daga mahaifiyarya zuwa mahaifinta har k'annanta duk hallitarsu iri d'aya ce, dan kuwa mahaifiyarta ma har tafi mahaifin tsayi, dan shi ba zai wuce gwiwar Maryam d'in ba, k'annanta ma haka suke can cikin k'asa a haka kuma mai bi mata shekararshi goma sha hud'u, hakan yasa take matuk'ar kunyar tsayawa a tsaye idan iyayenta na tsaye, tana jin nauyinsu sosai da girmama halittarsu, shi ya sa bata iya tsayawa idan ba a hali na tafiya take ba. Cikin dattako *malam Adam* yace "Ku kula kinji, Allah ya tsare."

Jinjina kai tayi tace "To Abba, ameen." Kallon mahaifiyarsu yayi yace " *Rabi'a* zan fita, da wani abu ne?"

Shiru tayi kan ta a k'asa tana mai jin kunyar fad'a masa ba su da abinda zasu sarrafa da rana su ci, kunyar yaran yasa ta kasa yin maganar, lura da yayi yasa shi komawa d'akinsu, mik'ewa tayi ta bi bayanshi hakan yasa Maryam bin su da ido, saida suka b'acewa ganinta ta kalli k'annan nata, harara ta zabga musu tace "Wai sai yaushe zaku gama cin tuwon ne ku kuma? Sam ba kwa gajiya da had'iyar tuwo."

Tsaki tayi ta mik'e tsaye tana ci gaba da kallonsu, cikin sauri suka shiga turawa dan kar ta fara d'imarsu da k'ulli, suna kammalawa suka mik'e suka wanke hannayensu suka sha ruwa, daidai nan suka fito daga d'akin y'a nufi k'ofa uwar da duka yaran suka bishi da addu'a, yana fita suma suka bi bayanshi suka fita, suna gaba tana baya tana takonta a hankali a haka har suka k'arasa makarantar dake bayan gidansu.


*Asibiti*


Saida suka gama gaisawa ya samu kujera ya zauna yana kallon Ashraf dake zaune yana kurb'an shayi, murmushi suka sakarwa juna inda sheikh yace "Ya jikin na ka?"

Lumshe ido yayi yace "Jiki da sauk'i, ina so ma su sallami idan zai yiwu."

D'an hararenshi yayi yace "Gaggawar me kake? Wani abu kake shiryawa ne?"

Dariya Hajia tayi tace "Tambayeshi dai, ya manta jiya a some muka kawoshi nan."

Yanda ya tsareshi da k'ananan idonshi yasa Ashraf cewa "Shekh ka fahimta mana, zaman a nan babu abin da zai k'ara min ko ya rage min, na ji sauk'i kawai su sallame ni."

Rantsatsen rigarshi mai kama da alkyabba irin ta sarakuna ya d'an jawo daga gaba yana ci gaba da kallonshi, sanin ba zaiyi magana yasa Ashraf cewa "Wato kafi son nayi ta zama a nan ko? Saboda baka so na dinga zuwa gidanka ina damunka."

Murmushi yayi cikin taushin murya yace "Da zasu rik'e min kai d'in ai da naji dad'i, dan na gaji da zaryar da kake min a gida kullum."

Dariya Hajia da Ashraf suka yi inda ya kalleshi yace "To ba ga irinta ba, ni kam da zaka saka baki a sallameni, na rantse maka sai nayi budurwa gobe goben nan."

D'aga girarshi d'aya yayi kamar wani gogaggen d'an duniya tare da murmushin gefen labb'a yace "Da gaske?"

Saida ya had'e fuska yace "Ka sa a sallameni ka gani."

Cikin dariya Hajia tace "Sheikh kasa baki to, idan haka ta faru ai zan fi kowa farin ciki, watak'ila Allah ya dubeshi ya bashi lafiya sanadiyar auren."

Wata tattausar ajiyar zuciya ya sauke yana ci gaba da kallon Ashraf, d'an murmusawa yayi yace "Shikenan, amma idan sun ce da wata matsala ba zan takurasu ba."

Babu wanda yace wani abu har ya mik'e yana gyara babbar rigarshi ya fita, ya d'an jima kafin ya dawo musu da takardar sallama, Ashraf na murnar zai tafi gida sheikh na mishi dariya da fad'in "Kamar wanda ya aje mata hud'u."

Shi ma dariya yayi yace "Mata hud'u fa? Ai ni ra'ayina na yin mace d'aya ne, kuma ma me ya aikeni karambanin yinace hud'u? Bayan kai ma da ke ustazu d'aya gareka."

Wani k'ayataccen murmushi yayi yace "Ni ma ina nan ina nema, zan k'ara ne ai dan samun wannan tagomashin na masu mata sama da d'aya."

Da zolaya Ashraf yace "Kenan tare za muyi auren?"

Sake d'aga masa gira yayi wanda hakan ya zama jikinshi yace "Watak'ila."

Turo baki yayi yana hararenshi yace "Lallai ma sheikh d'in nan, wato zaka wa 'yar uwata kishiya kuma shi ne kake fad'a ma a gabana."

Wani murmushi yayi ya juya ya kalli Hajia dake ta had'a kayansu dan tafiya bata kula da su ba yace "Na fad'a a gaban Hajia ma bare kuma kai."

Hajia ce tace "Ni ai murna zanyi da faruwar haka, tunda arzik'i ne zai ci uban na da."

Dariya sukayi sai sheikh daya sake sunkuyar da kai dan bai d'auka tana jin su ba, suna had'a kayan suka fito da sauri masu tsaronshi su biyu suka karb'i kayan hannunshi wanda ya karb'a a hannun Hajia, dake a mota biyu suka fito yau dan wajen aikinshi zai tafi yasa d'aya motar masu tsaronshi ne d'ayar kuma shi da su Ashraf da Hajia har suka isa gida, sai dai bai shiga ciki ba saboda lokaci ya tafi sosai.


*Maryam*


Hutun minti talatin aka fito dan mai buk'ata yayi buk'atarsa, a cikin ajin suke zaune tare da k'awayenta suna ta hira inda wasu ke cin abinci, ita ma robar alala ce gabanta inda Asma'u ke kallonta da mamaki dan bata d'auka zata iya cinye wanda ta siyo ba, saida ta ga ta ida ta d'auki ledar pure water ta tsotse ta jefar Asma'u tace "Masha'Allah, lallai yau na tabbatar Mimi ba matar k'aramin mutum bace ke."

Harara ta wurga mata tace "Ban gane ba, me ya faru?"

Saida ta kalli robar ta kalleta tace "Alalar dala arba'in fa kika cinye ke kad'ai."

Tsaki tayi ta sake hararenta tace "Miye a ciki? Kud'inki ne ko nawa?"

Girgiza kai tayi tace "A'a naki ne, Allah baki hak'uri."

Tab'e baki tayi ta kalli wacce ke kusanta tare da zura mata hannu tace "In ga wayarki Jamila na tura vidΓ©os."

Wayar ta mik'o mata tana fad'in "Ban da sababin vidΓ©os fa har yanzu, na wa'azi ne kawai aka turo min jiya."

Saida ta fara dubawa kafin ta kalleta tace "Wai duk wa'azin shi ne kika turo?"

Da murmushi tace "Eh, yana birgeni wallahi saboda ya iya wa'azi."

Tab'e baki tayi tace "Shi ne ke birgeki? Ko kuma wa'azinshi? Ko kuma ilimin da Allah ya bashi?"

Cikin rashin damuwa tace "Duka ma wallahi." Dariya 'yan matan suka saka inda Asma'u tace "Da alama dai Jamila da sheikh Abdul Waheed zai ce yana sonki da gudu zaki auresa."

Da sauri ta kalleta tana dariya tace "Wallahi tsaf kuwa, ai ko bai fad'a ba da zan ganshi ido da ido ma ni saina rok'eshi ya aureni."

Da mamaki Maryam ta kalleta tana nuna wayar tace " *Tsohon*? A hakan ma ke zaki rok'esa?"

D'auke kanta tayi tace "Tabb'! Lallai da kin wulak'antamu."

Jamila ce ta turo baki tace "Wallahi bΓ’ tsoho bane, dubeshi da kyau fa."

Tab'e baki tayi tace "Na gani, amma akwai wa'azin da yayi yake bayanin wani abu daya faru, a lokacin ya ce yana da shekara ashirin da shida, ni kuma Abba na ya fad'a min yana neman auren mamana aka yi wannan al'amarin, a lokacin shi yana ashirin da shida shi ma, hakan na nufin shekarunsa *arba'in da bakwai* fa, kinga kenan tsoho ne tunda sa'an babana ne."

Dariya sukayi sai wata dake kusa da Asma'u tace "Gaskiya indai hakane tsoho, fuskarshi ce dai bata cika nunawa ba."

Asma'u kam cewa tayi "To ko ni dai da zai aureni wallahi zan amince, tunda yana da ilimi."

Maryam kam tab'e baki ta sake yi tace "Allah ya rabani na rasa wa zan aura sai sa'an babana."

Jefawa Jamila wayarta tayi ta mik'e zata fita dan wanke hannu tana fad'in "Wannan ai lalata k'uruciyarku kuke son yi."

K'arar da wayarta tayi yasa Asma'u d'auka tana dubawa tace "Mimi Mas'ud ne ke kiranki."

Shiru ta mata saida ta wanke hannayen ta dawo ta zauna ta karb'i wayar, datse kiran tayi tare da kashe wayar gaba d'aya, Asma'u dake kallonta tace "Me yasa kika kashe?"

Kallonta tayi tace "Shi mahaukacin ina ne da zai kirani yanzu bayan yasan ina makaranta."

Jamila ce tace "Watak'ila dan yaga lokacin hutu ne, wallahi ya damu dake mutumin nan Mimi."

Banza tayi da su hakan yasa Asma'u cewa "An tab'o mata hirar data tsana a duniya, kuyi harkar gabanku kawai."

Tab'e baki Maryam tayi tace "Da dai yafi kam."

Wata hirar aka shiga saidai Asma'u kam ta damu sosai da abinda Maryam d'in ta fad'a mata cewa Alhaji Saminu ya bata kud'i, dan haka hankalin kowa na tafiya wani wurin ta sake gyara zamanta tace "Mimi, me yasa da Alhaji Saminu ya baki kud'in nan kika karb'a? Ba kya jin tsoro ke?"

Kallonta tayi tace "Tsoro kuma? Na me?"

D'an numfashi ta sauke sai kuma tace "Idan fa yace yana son ki?"

Wata dariya ta kece da ita har da d'an bubbuga table d'in kafin ta tsagaita ta kalleta tace "Ya ce yana so na? To sai me? A gaban idonsa zan fad'a masa ba zan iya aurensa."

Ba tare data d'auke idonta daga kanta ba tace "Me yasa? Amma naga mutumin kirki ne."

Wawan tsaki taja tace "Ke yanzu dan ina mahaukaciya sai na yi soyayya da Saminu? Bayan kasancewarshi tsoho fa kin ganshi k'ato da shi, me zanyi da shi ni kam."

Murya k'asa k'asa tace "To indai hakane ki daina karb'ar komai daga hannunshi dan Allah, ni wallahi tun rannan da muka je gidan naga ya cika kallonki da yawan kiranki na ji ina zargin akwai abinda yake nufi a kan ki."

Yatsina fuska tayi tace "Wannan shi ya shafa wallahi, ni ko a jikina."

Jin an busa usur d'in dake nuna lokaci ya k'are kowa ya shiga aji yasa Mimi sassauta murya tace "Malam yace da yamma wajen walimar sabka zamu tafi, da uniforme zamu je ko kayan gida?"

Ita saida ta sassauta murya tace "Bari a tashi sai mu tambaya mu ji."

Shigowar malamin yasa akayi shiru babu mai magana sai mayar da hankali a kan shi da kowa yayi, inda duk wani mai waya tuni ya kasheta dan an hana zuwa da ita, masu taurin kai ne ke tahowar da ita.



*Alhamdulillah*
7/22/21, 12:06 AM - Ummi TandamaπŸ˜‡: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?

*NA*


_SAMIRA HAROUNA_


*SADAUKARWA*


_GA DUKA_

*'YAN AMANA TA*


πŸ’«βœ? *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜? *[ T.M.N.A]* β˜? πŸ“–πŸ–ŠοΈ?

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


*4*


A marairaice ya kalli Hajia yace "Dan Allah Hajia ki barni na fita, wallahi na fi jin dad'i idan ina waje."

Ita ma a marairaice tace "Ashraf ba wai na hanaka fita bane, ka jira jikinka ya k'ara sauk'i mana."

Kamar zaiyi kuka yace "Hajia na ji sauk'i fa, ba abinda nake ji a jikina yanzu."

Da alamar tuhuma tace "Ka tabbatar?"

Cike da tabbaci yace "Na tabbata Hajia, insha'Allah babu abinda zai faru ki kwantar da hankalinki."

Jinjina kai tayi tace "Ashraf burina d'aya ne a duniyar nan naga ka samu lafiya, ciwon cikin nan naka yana d'aga min hankali fiye da tunaninka."

Murmushi ya mata yace "Kenan Hajia baki da burin ganin nayi aure?"

Turo baki tayi tana dukanshi a kafad'a tace "Dan na ga kayi auren har 'yan mata na dinga lissafa maka dake cikin ahalin nan, amma ka rufe ido ka nuna baka so basu ma ka ba."

Jujjuyar da kan shi yayi yace "Hajia ai duk cikinsu ne babu wacce ta dace da kalar tsarina."

Baki sake da mamaki tace "Iyeh! Wato har wata kalar tsarinka kake fad'a? To fad'i na ji ko zan iya samo maka."

Dariya yayi ya gyara zamanshi yace "Hajia ni wayayya nake so mai ilimi, 'yar zamani da kuma tsafta wacce ta iya kwalliya, sannan wacce zata dinga kwantar min da hankali."

Rik'e hab'a tayi tace "Ashraf matar sakawa a gaban mota kake nema?"

Tintsirewa yayi da dariya ya mik'e ya fita har da d'an gudunshi har ya bar gidan a galleliyar motarshi.


*Sheikh*

A hankali yake juya kujerar kanshi na kallon sama amma idonshi rufe, hannunshi rik'e da katin gayyatar da aka kawo masa daga wata islamiyya da zasuyi sabkar Alqur'ani mai girma, jefi jefi ya kan sauke ajiyar zuciya saboda tunanin da zuciyarshi ke bijiro masa, dan gaskiya yana matuk'ar son ganin ya k'ara aure, ba dan Hafsat ta gaza ba ko baya jin dad'in zama da ita, kwad'ayin ladar da zai samu yake, yana son ganin shi ma kimarshi ta k'aru fiye da ta mai mace d'aya. Saidai abinda ke hanashi bai wuce tunanin 'yan matan yanzu ba, yaran da ko iyayen da suka haifesu basa iya tank'warasu, yaran da idonsu a tsaye a kai saman kai suke nuna maka baka waye ba, yaran da basa da hak'uri da juriya, yaran da waya da k'awaye suka fi komai mahimmanci a garesu, hakan yasa yake d'an dakatawa wasu lokutan, saidai kamar yanda yanzun zuciyarshi ke raya masa kawai zai rufe ido ne ya je ya nemi alfarmar malamin kan ya duba masa yarinyar daya yarda da tarbiyarta da nagartar iyayenta, idan ya masa haka shi da kan shi zaiyi yak'in neman k'uri'ar aurenta. A hankali ya bud'e idonshi tare da d'ora yatsanshi a kan kybord d'in na'urar ya turawa sakataranshi sak'on ya amince da gayyatar kuma zai je da kan shi da misalin 04:30 na yamma.


*Maryam*

12:00 cif na rana suka taso, a hanya ma dai hirarsu bata fahimtar juna bace tsakaninta da Asma'u, dan akwai banbanci ra'ayi sosai a tattare dasu, tana cikin b'acin ran da Asma'un ta k'unsa mata a kan maganar wani saurayi da ita har ta manta da lamarinshi ma wai ta ci kud'inshi dayawa, bata tsoron ya k'i yafe mata? Shi ne fa ta hau take ta masifa take fad'in "Ai bani na ce ya so ni ba, kuma ni ban tab'a bud'a baki nace a bani ba saidai kai ne ka d'auka ka min."

Mas'ud suka tsinkaya a kan dallelen mashin d'inshi yana danna wayarshi, wani uban tsaki ta kuma ja tace "Shi kuma me yake mana a k'ofar gida?"

K'wafa tayi hakan yasa Asma'u cewa "Sai ma kin tambaya? Wurinki ya zo mana."

Tab'e baki tayi tace "Duk da dama ina son ganinshi, amma ba zan ganshi yanzun ba, dan ni ba'a min haka wallahi."

Rab'a Asma'u tayi zata giftata ta wuce tayi saurin rik'e hannunta tace "Ina zaki tafi Mimi? Karki masa haka mana."

Tsaki ta kuma yi tace "Ke sake ni, shigewa zanyi na barsa mana."

Da mamaki tace "Amma kinsan wurinki ya zo ko?"

Fizge hannunta tayi tare da wucewa da sauri ta barta tsaye tana mamakinta, ai kam ko kallon kusurwar da yake ba tayi ba ta shige cikin gidan tana mitar ita zai wa dirar mikiya kamar wani ubanta? Shigewarta kawai ya gani hakan yasa shi tsayawa sagale da baki yana kallonta, saida ya tabbatar ita ce dai kafin ya d'an d'auke kan shi yana basarwa, kad'an daga aikin Mimi kenan, ya rasa gane wane irin so yake mata da har yake iya shanye komai daga gareta haka, ta masa wulak'anci ta ja masa aji ta yarfa shi fiye da kima, amma ya jure ya nace saboda tunanin ta kusa zama tashi, lokaci kad'an ya rage shi ma ya fara nashi salon mulkin, duk da dai ya tabbatar ba zai iya muzguna mata ba, amma saiya rama ko da na kwana d'aya ne dan taji idan da dad'i.

Shi yasa baya nuna bai ji dad'i ba idan ta b'ata masa, ko ba komai Mimi ta yi, ta had'u iya haduwa da kowane namiji zai so samunta a matsayin ta shi, ga ta da wani siddabarun saurin dukan k'irjin namiji, indai kana da rai da lafiya sannan tsufanka bai kai k'adamin da baka sha'awar mace ba, to idan kaga Mimi zuciyarka zata amsa ma ka saidai kayi shiru

Please Login or Register in order to submit comment